Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
fahimci me, ya juye tass a filet ya kuma dauki wani mug ya cika da ruwan zafin da aka dafawa Abban su. Sannan ya mike tare da nufar kitchen ษ—in gidan ya dauki gwagwanin milo ya zuba son ran shi, sannan ya kuma juyawa ya zuba madara. Bai damu da sugar ba, dan yasan suna dafa ruwan zafin da sugar. katon bread ya gani ya yanki wanda zai iya ci. Ya fito tare da nufar dakin Hajiya uwani, yana Shiga Aseed yaja mishi Center table, ya daura abin karyawan. Cikin nutsuwa ya kalli Hajiya Uwani da suke karyawa ita da yaranta, yace mata. "Ummi! Yau ba zaki jira Uwar Aliyu bane?" Murmushi tayi sannan ta ce. "Bari kai dai, ina sauri ne. Kuma bana son su makara ne, dan seven saura kadan." Bai kuma magana ba, ya cigaba da karyawan shi, yana cikin cin abincin Ya jiyo muryan Hajiyar mu tana cewa. "Wallahi idan baka shiga tsakani na da Aamil ba, wallahi zan saya Ghali da Ali su mishi mugun duka, dan iskan yaro. Ka ja mishi kunne ko kuma nayi Abin da zai damu da kanshi." A zuciye ya mike zai fita. Hajiya uwani ta ce mishi. "Dawo ka zauna!" Dan dole ya dawo ya zauna, ta cigaba da karyawa, tana gamawa ta shige d'akinta tare da dauko sabuwar Shadda, ta ajiye mishi sannan ta juya tare da cewa. "Jalil,Aseed, Ashiq, Abdul Jalal maza ku fito. Ina jiran ku zan muyi latti!" Da sauri suka fito tare da ษ—aukar school bag dinsu, suna zuwa kusa da Aamil suka karasa gurin shi, tare da rungume shi suna fadin. "Brother! Idan naje hadeja ka cewa Aunty Sidrah muna sonta" Abin ya bashi mamaki, zai yi magana tasaka hannu a baki. "Duk da na gari, burin shi ya farantawa iyayen shi da sauran mutanen gari. Dan haka ga shaddar nan, ka dauka kaje ka ganta, sannan ga jakar can na kayan kwalliya ce, Please And please, karka kunyata mu, a gaban Baban Atiku don Allah kaje lafiya ka dawo lafiya. Muna jiran sakamakon mai Kyau." Gyada kan shi yayi cikin nutsuwa, yana cizon lips d'inshi. Tabbas sai yaci kutmar kaniyar yarinyar da ake bashi sallahun ya gaida ta. Tana gama gaya mishi haka ta ficcewarta, dan akwai wani key a hannun ta, idan ya tashi zai ja mata kofar ta ne. Yayi tafiyar shi. Tana tafiya ya mike tare da fitowa tsakar gidan, yaji ana kus-kus a shashin Hajiya, kamar ba zai magana ba, kawai ya leka domin sun saba cin mutuncin juna yana shiga ya kalli Hasnah da Musa, suna musu akan shi. Bai damu ba, ya shiga dakin da yaji ana gulmar dake window ta baya take. "Ai Hajiya ina gaya miki ba yace baya son Hasnah ba, toh wallahi yar gidan Iro marigayi za a kwaso miki a jikan da kike cin alwashin sai yar gidan gwamna zai auro miki, domin Sidrah ba budurwa bace yarinya ce karama." "Ke hinde! Ba dai Sidrah wacce take hannun Lantana ba, wallahi zan kuwa ci mutuncin Ma'aruf. Ni zaiwa bakin cikin." "Hmm! Ai gwara yayi miki bakin cikin, mata baki san kome ba sai tsantsar mugunta, wallahi ba dan wancan mutumin yaron ki ne ba, sai na karya miki kafarki. Ke kuma Hinde maza ki tattara wadancan gardawan na dawo hadeja muka yi ido hudu dasu sai na baki mamaki, munafukai kawai." "Bana son rashin kunya ni Kanwar Ubanka ce!" Ta faษ—a mishi cikin tsawa. "Dalla yi min shiru, wallahi nazo na sami yaran sai na karya kafafun su, tunda gidan Uban na ne." Ya faษ—a. "Toh kwashashe, Zuri'ar masu fitsari a tsaye, dan banza jinin masu jan kunne. Zan ci uban mangofak ma. Dan haka ficce min a daki." _Assalamun Alaikum sisters! Wannan labarin ruwa biyu! Rayuwa ce irinta malam bahaushe! Wanda yake tafe da manuniya biyu! Tsarin hausawa da tsarin turawa! Don Allah idan bai miki ba, karki b'ata lokacin ki gurin karantawa! Domin zaki iya haduwa da abin da bai miki ba kiji Haushi na! And salon shi daban ne da sauran labarai daga sunan kawai zaki fara fahimtar haka thank You ๐Ÿ’– _ #Mai_Dambu [11/13, 8:05 PM] My Zahrah: ๐‘๐”๐–๐€ ๐๐ˆ๐˜๐” <๐‘ฒ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’š๐’Š ๐‘ซ๐’‚๐’š๐’‚ ๐’Œ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’Ž๐’Š ๐’…๐’‚๐’š๐’‚ ๐‘ฒ๐’š๐’‚๐’–๐’•๐’‚> https://my.w.tt/pvpSrJ4R5ab โ„๐”ธโ„ค๐”ธ๐•‚๐”ธ ๐•Žโ„๐•€๐•‹๐”ผโ„'๐•Š ๐”ธ๐•Š๐•Š๐•†... แด๐š๐ข_แด…๐š๐ฆ๐›๐ฎ Bismillah Rahmani Raheem _Dedicated to all Black beauty ๓ฐขช Daga manyan har kananun idan ke baka ce Wannan shafin naku ne! ๐Ÿคฉ๐Ÿ˜๐Ÿ˜˜ _ 0โƒฃ3โƒฃ Ball yayi da wani jug wanda yake dauke da kunu. Yana huci tare da kallon Hajiya yace mata. "Wallahi sai na karya kafarki, munafukar mata, kamar yadda kuka rabani da uwata, Allah sai na rabaki da naki d'an." Ya juya tare da barin gurin su. Yana jan tsaki, tun da ya shiga shashin sa, me dauke da dakuna biyu da kuma kitchen sai dan tsakar gida, da baranda, tare da kitchen ษ—in waje, da kuma wani a cikin falon gidan, sai dan gurin wanki da wanke wanke a waje, sai kuma dan backyard da yake dan bayan gidan inda zaka ayi shanya idan aka yi wanki. Gidan zaman mace daya ce, babu wani abu da za a kara bayan haka. Gidan yayi kyau sosai, domin na yaran da ake ji dasu ne aka mishi. Tsaki yayi tare da kaiwa bangon, yana kuma jan Allah ya isa tsakanin shi da mutanen da suka raba shi da mahaifiyar shi. Dan haka yayi wanka ya shirya tsaf, sai ษ—aukar kamshi Oud 24hrs yake, cikin Izzah y kalli madubi yaga yadda Allah ya zuba halittar shi bai san lokacin da ya sake wani irin murmushi ba, dan yayi imani kaf Jigawa babu hadadden gaye irin shi, most ontop population guy, in Jigawa. Penny loafer shoe kiran kamfanin vinci ya saka,. takalmin da shaddar sunyi match yayinda hular shi zanna bukar ya tafi da zaren aikin rigar shi. Wani sarka ya saka a hannun shi kamar kaca, bayan ya ya saka agogon shi. Cikin kuzari irin ta jajjurtacce namiji yake tafiya tare da cilla key din motar shi sama, yana cafkewa. Turuss ya tsaya dai dai lokacin da ta bude mishi zig din rigarta. "Aamil! Sai yaushe zaka dai na guduna? Yanzun duba fa, ina haukar ka, baka ciwo na. Ina matuฦ™ar kaunarka" takowa yayi ba laifi yace a ranshi. Kallonta yayi sama da kasa, yarinyar tana wuta. Kallon boons ษ—inta yayi wanda suka ฦ™asance kamar an hura balloon, sun leko daga kayan jikinta suna mishi wani blush! Fincikota yayi cikin nutsuwa yana kallon fuskarta! Kashe mata ido yayi sannan yace mata. "Gaskiya bazan auri yar Hindatu ba. Da dai kin nemi muyi Shagali ne zan iya gayyatar ki d'akina, amma aure." Hade bakin su tayi tare da saka hannu a keyar shi,yana kaunar shagali. Rike bayanta yayi. Tare da gyara mata tsayuwa, sannan ya rungume ta suka fara takawa bata san inda yake kai taba, har sai da ya dangana da cikin gidan, Ana gulmar Hajiya Uwani suka hango Aamil rungume da mace. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun! Amma wannan yaron anyi kwasa she. Yar waye ka samu zaka lalata musu ita, shine dan ka cika dan isk..." Ture Hasnah yayi tare da takowa gaban Hindatu yace mata. "Idan zan yi Shagali da Yan mata, Yaran manyan nake nima. Wacce Ubanta zai boye abin kunyar da tayi dan kare martabar ba yar da babu wanda yasan inda dangin Ubanta yake! Ke kuma na kuma kama ki!" Shafa wuyar shi yayi alamun babu abinda ba zai faru ba. Daga haka ya bar musu gidan, karshe gulmar da aka rufe kenan, daga hmm sai hmm yar me gulma tayi ciki. *** Hadeja Unguwar Gandun Sarki. Babban gida ne mai dauke da tarihi, kuma me dauke da mutane kusan dari da wani abu, maza da mata yara da manyan, a takaice family house ne nasu Alhaji Ma'aruf, gidan Sassa ne daban-daban, gida ne da yake dauke da matan aure sama da arba'in da uku. Domin kowani shashin ba zaka raba shi da mata uku zuwa huษ—u ba. Shashin Haliru nan ne shashin babban Yayan su Alhaji Ma'aruf, sai shashin Baba Mamman! Da shashin Baba Idi, sai shashin Marigayi kamilu wanda rikicin Jos ya ritsa dashi tare da Matar Shi da kuma yaran shi biyu. Sidrah ce kadai Allah ya tsiratar da ita, inda aka samu yan hadeja suka ce sun san familyn ta . ... Kasancewar ana sanyi sosai, duke take jikinta yana rawan sanyi, hawaye na diga a cikin ruwan wankin da aka sanyata yi, gashi ana busa wata irin iska me shiga jiki. Lantana ta leko cikin sababi tace. "Yau naga abinda ya ishe ni bai ishe Allah ba, zaki gama kizo ko karya ko sai nazo naci kan uwarki, shegiya mara kunya, wankin da bai wuce awa daya ba kin dakile sama da awa biyu a gurin." A tsora ce ta kalle inda maganar ke fitowa tace. "Innah yanzun zan gama!" "Kar ma ki gama shegiya me ruwan mutanen daji." A sanyayye take gurje kayan tare da kai hannunta daya tana sosa kanta, zuwa wuyar ta. Yarinya ce da bata wuce shekara goma sha daya ba. Baka ce irin bakin nan da zan iya kiran shi Golder Black! Domin fatarta ya nuna haka, baka wuluk ce, mai wani irin sheki fatarta, sai dai kashh. Ba zaka ga wannan shekin ba, sabida zunzurutun Datti da dauษ—a da suka lullube kyakyawan fatarta, Yanayin jikinta Dan Karami ne, bata da auki dan siririya ce, mara auki. Daga fuskarta hancinsa dogo har baka, amma sanadin makeron da ya cinye rabin fuskarta ya sanya baka hango kome sai wasu irin kuraje kananu. Wuyarta kuwa zuwa kanta, Ya ilahi. Wasu jerin gwanon kuraje ne wanda kwarkwata take haifar da shi idan yayi yawa akan mutum, hannu bibbiyu ta saka tana sosa kanta, wanda yake dan kare da kitso zanen yawo wanda yau kusan watan shi biyar tun auren Yayanta Atiku wanda yake dab sanda ne a garin Kwara. Bakinta kuwa wanda ya kasance dan Karami, ya farfashe sabida sanyin hunturun da ake fama dashi,. Hannunta da ta saka duka biyu akanta, wasu irin Kano suka yi, dan fatar hannun har wani tashi yake, da za ayi dace a saka sosan karfe ( ๐Ÿคฃ๐Ÿคฃ๓ฐฃธ๐Ÿคฃ๐Ÿ˜‚ Wallahi Aamil ina baya ka buhun ubata ๐Ÿ˜๐Ÿ˜’๐Ÿ˜Ž๐Ÿ™† ) Toh tabbas zasu tashi, kafarta wanda suka kasance kananu, wasu manyan faso ne, wanda tsabar girman su, da za a saka Naira ba makawa zasu shiga ciki, kuma su sami mafakar siyasa. Haka samar kafarta ya tsatsage, sabida rashin kulawa. Rigar jikinta kawai zaka kalla ka fahimci, wata tsohuwar roba ce, da tasha gwagwarmayar duniya. Wato da zaka kalli yadda rigar yake, tasha dinkin zare da allura, amma a haka bai hanata yagewa ba. Domin kuwa, hannun rigar zuwa wuyar rigar reto yake. Tayi futufutu, ta fita hayacinta ga wani abun yunwar da take ji kamar ba zata rayu ba. Dan jin take uwar hanjinta yana wani irin murษ—awa. Tana tsakiya da sosa kanta, aka sake mata rankwashi,. Tsakiyar kanta tana cewa. "Shegiya algunguma, wato kece kawai malam ya damu dake shine zai hadaki da Bature mu kuma gamu banza ya, zaki ci uwarki mara mutunci kwasheshiya kawai.". Rike kanta tayi hawaye na zuba mata. Tana kallon Innah Azumi da gefen idanunta tausayi. Can sai ga Iya Larai ta shigo ta samu tsakiyar bayanta, dai dai tana wankin ta dirmata dundu. Cikin jin haushi tace. "Munafuka me kama da mayu, a rasa wacce ta dace da Amil sai ke, yar banza me muni kamar kashin dare." Kafin ta gama wankin matan gidan sun mata likis. Dakyar ta samu ta gama wanke kayan ta kuma ษ—aukar bokiti ta nufi cikin gidan domin dibo ruwan wanke wanken da zata yi. A hankali take tafiya cikin tsarin yanayi. Me dauke da nutsuwa da hankali, take takawa. Tana zuwa bakin rijiyar ta dauki guga ta fara jan ruwan sai ji tayi an make kiyarta kamar zata fadi ta juya. Cikin tsoro tace. "Yaya Ummu!" Buge mata bushashen bakinta tayi sai ga jini, rike bakin tayi, sauran yan matan gidan suka fito, sai da suka mata duka, sannan suka watse aka barta a kwace a bakin rijiya. Zuwan Lantana da Kande tace mata. "Toh fa Lantana yar sarki mulki take ji gata can gindin rijiya kwance.". Kwafa tayi sannan tace mata. "Bani faskare naje na sheme yar banza yarinya, Ni zata janyowa tereren Bankad'a, biyar bashin dan kishiya. Wai me yasa da aka zo kashe danginta suka bar mana yar banza me manyan idanu kamar na gurjiya." "Hmm! Wai ai dan ma baki ganta ba, sai kace itace ke sayan omon wanki." Abinda ya kuma fusata Ran Lantana kenan, ta kuma janyo faskare tayo waje tana rantsuwa sai ta sheme yar banza ayi auren da toshe. Koda ta fito hango Baba Mamman yasata juyawa da itacen gida, ya dawo da Sidrah. Ya kalli Lantana yace mata. "Kiji tsoron Allah! Duk Yaranki suna daki, sai Sidrah kika tura diban ruwa, Inda Kamilu da Safiya suka tafi muma wata rana muna gurin, bai dace ku hana yarinya hutawa ba. Ke jeki dauki abincin kici." Yana gama fadar haka ya juya abin shi. Ya fita haka ta rab'e a jikin bango. Tana jiran a bata bakin rabonta. Wani kofi Lantana ta nuna mata, wanda kuษ—a suna gama gaษ—ษ—a akai wanda kunun ciki ya kasance kadan ko kasar kofin, sai tukunyar dumame wanda yake gurin wanke wanke. "Ki dauka Jikar jikar azakafi." Jikinta yana rawa ta nufi gurin wanke wanke, ko hannu bata wanke ba, ta soka wasu mugayen faratan ta, masu ษ—auke da mugun datti. Ta fara cin abincin kamar wacce ta samu nama. Sai da Lantana ta bari hankalin Sidrah yayi nisa da cin abincin kawai ta rufeta da duka, sai da ta mata likis, tana huci sannan ta barta. Bayan ta gama jin dukarta ta mike taje ta dibo ruwan wanke wanken, ta zauna tai tana yi ana b'ata kwanukan, har aka gama abincin rana bata tashi ba, kasancewar dambun tafasa ce, tana samu ta mike aka nuna mata cikin tukunyar dambun, tace mata. "Sai ki kankara na san zai isheki!" Gyada kai tayi tare da zama ta kankare, sannan ta fara ci a hankali. Tana gama ci tasha ruwa, a gurin ta baza hakarkari sai barci. (Kyakyawar gabatarwa Jarumar mu! Kuyi hakuri jaruma ta bata kai dan bata cikin most ontop population Celeb! Bahaushiya ce yar yankin Kasar hausa) Tunda ya nufi Unguwar, yake yatsina fuska, domin ya tsani shigowa garin Hadeja, musamman unguwar kakanin shi,. A hankali yake tusa kan motar shi, kasar wata bishiyar durumi, wasu irin yara ya hango yan gajajjeru masu rusa rusan ciki, da shafefen duwawu, fuskarsu da kuwa, tagwayen majina ce, wacce ta bushe. Hade da bushashen kunu, sannan kansu gwandal gwandal, gashi sunyi fari sol da kasa, sakamakon hunturun da ake bugawa na kata'i, idanun Aamil ne ya sauka akan wani yaro wanda majina kore shar ya sauko daga kofar hancin shi, aikuwa ya janye ta tare da jan hancin, ya kuma laso inda ( ๐Ÿคฃ๐Ÿ˜‚๐Ÿคญ Wallahi ban tab'a labari me ban dariya irin wannan ba, ina dalili an sani karewa yaran cikin gari tanadi) da harshen shi kofar hancin shi. . Wani irin amai yaji, tare da kauda kan shi akan yaran, hango wata yarinya yayi tana cusa hannunta a cikin kofar hancinta tana sakace tasono, zata kai baki ai bai san lokacin da ya nemi sauke amai ba, da sauri ya fita tare da barin gurin bayan ya rufe motar. Cikin gidan Ya nufa, inda ya hadu da Sahiya tare da Harira, suna ganin shi suke fara sake mishi murmushi da yalayalan hakoran su. Daure fuska yayi, tare da kauda kan shi. Ya nufi cikin gidan. Bakin shi dauke da sallama, a hankali yabi sassan gidan ya gaishe su, sannan ya nufi shashin Baba Haliru. Da sallama ya shiga cikin gidan. Ya tsaya a bakin kofar. "Lale maraba da zuwa! Sannu mutanen dutse Barka da zuwa." Murmushi yayi sai da Khaleesah ta had'iye yawu, dan tana karanta littafin hausa, bata tab'a cin karo da wanda aka tab'a fasalin namiji Irin Aamil ba, kai ko zata mutu ta dawo, tayi imani zata fi wancan sakaryan da aka bashi yarinyar da ko girma bata yi ba, nan aka shiga jera mishi ruwa, da abinda zai ci. Shi dai idanun shi na nima mishi gimbiyar da ake ihun yaje ya ganta. Sati Uku da suka gabata. Alhaji Ma'aruf shi da Wan shi da suke Uba daya suke tattaunawa akan yanayin cigaban da ake samu na kasuwancin shi anan yayi shiru cikin damuwa kafin yace wa Malam Haliru. "Wato Yaya wannan dukiyar da ake kasuwancin dashi ba nawa bane! Na Hauwa ne! Ina son Aamil ya nutsu ya kuma rike dukiyar Mahaifiyarshi, amma abu yaci tura dashi ake wawar dukiyar ma. Gashi baya jin magana shine kwaso yan mata kwaso samari azo a cika min guda da shaye shaye." "Toh kayi mishi aure mana!" Kallon wan yayi sannan yace. "A ina zan sami wacce zata iya zama dashi?" "Akwai mana! Ba za a rasa ba. Ni zan duba mishi ko nace na duba Mishi. Akwai Yar Kamilu. Yarinyar, tana shan azaba a cikin gidana, idan nayi magana kamar na kuma kunna mata azabar ce. Bata da wani girma sabida bata wuce goma zuwa sha daya ba. ....idan aka bashi ita, zata zame mishi karfen kafa, domin zata zame mishi reno zai yi. Kafin ya gama haukar shi ta shiga jikin shi. Wanda haka zai sanya. Ya gane cewa ana hakuri dashi, idan tayi mishi kuskuren kuma ya had'iye. Amma kayi nazarin abun yarinyar tana wahale na gaji da ganinta cikin kangin rayuwa.... #Mai_Dambu.. [11/13, 8:05 PM] My Zahrah: ๐‘๐”๐–๐€ ๐๐ˆ๐˜๐” <๐‘ฒ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’š๐’Š ๐‘ซ๐’‚๐’š๐’‚ ๐’Œ๐’‚ ๐’”๐’‚๐’Ž๐’Š ๐’…๐’‚๐’š๐’‚ ๐‘ฒ๐’š๐’‚๐’–๐’•๐’‚> https://my.w.tt/sGJtOL2t7ab โ„๐”ธโ„ค๐”ธ๐•‚๐”ธ ๐•Žโ„๐•€๐•‹๐”ผโ„'๐•Š ๐”ธ๐•Š๐•Š๐•†... แด๐š๐ข_แด…๐š๐ฆ๐›๐ฎ Bismillah Rahmani Raheem #Abun ki 0โƒฃ4โƒฃ Raba idanun shi yake, a hankali yana niman inda halittar zata fito mishi. gefe guda kuma yana sauraron kus-kus din da mutanen gidan suke. A ranshi yace. _Ashe ko ina ba a rasa wahalallu_ "Ke Altine! Ina Sidrah take?" Tura baki yarinyar tayi sakamakon tambayarta da Babatar tayi mata, ta juyawa tayi ta tab'e baki tare da nuna mata Kofar madafin tace mata. "Innarmu gata can ya she kamar asara a gidan biki" Juya idanun shi yayi ya sauke a can arewa maso yamma na gidan ya hango wata buntuntuna, tana kwance sai barci take. Tun bai ga fuskarta ba yaji amai ya taso mishi, dakyar ya mike tare da cewa. "Toh zan tafi." "Toh Alhaji karami, dan bature. Mungode yanzun zata zo." Yana fita Inna Lantana tana bin shi da mugun kallo. Sabuda mugun kyashi da hassada da ta sakawa ranta, Sahiya ta nufi inda Sidrah take kwance ta kifa mata mari, tare da shureta da kafa tana fadin "algungunman kawai. Bak'ar kaddarar kin hana kowa farin ciki, gwara ma ki mutu da yanzun nice da wannan zukekken ganyen!" Tashi tayi jikinta na rawa, tace mata. "Ya..." Kifa mata mari tayi sai da ta daina gani. "Kiyi hakuri ba zan kuma ba!" Ta faษ—a tana shasheka kuka, "Maza dauki wancan kazamin hijabin An dubu kije gurin shi jaka kawai." Daga haka ta fita jikinta na rawa, har ta kusan fita waje sai da Ado da ฦ™arara, kamar wacce ta mishi magana. Ya samu gaban Hijab din, ya watsa mata tare da guduwa. Kaษ—e jikinta tayi tare da fita. Tun daga nesa ya hango ta. Bakin cikin da yake ji, kamar ya kashe kan shi dan haushi. Yana ganinta ya shiga motar tare da nuna mata inda zata zagayo. Daga cikin zauren gidan Sahiya Ummu, Mabaruka, Kibษ—iya, suna kallon su. Ganin ta shiga motar shi basu san lokacin da suka ja wani mugun tsaki ba, sabida sun gama mutuwa akan shi. Wani irin wulakantaccen kallo yayi mata sannan yace. "Ba zan kuma zuwa ba, idan kuma na kuma zuwa ki sani zan baki kyauta mutuwa ce! D'aga min rigar ki na gani!" Jikinta na rawa ta shiga cire hijab din jikina wanda yasha mugun dattin Bala'i. Sannan gaban Hijab ta yage har kasa, wuyar hijab din ne a rike da hijab din, sannan wani irin zarni da warin Datti yake fitarwa, sabida rashin wanki da kulawa. Wani banzan kallo yayi mata me kunshe da bakin cikin kana da kyakyaminta wani karin malolon takaici ne ya tsaya mishi me cike da tashin hankali, sannan yace mata. "Dama a haka suke tunanin zan zauna dake? Babu kome a kirjin ki? Toh idan kika ce zaki aure ni yankan rago zan miki keee!" Ya but mata tsawa, wanda ya sanya ta zabura, take fitsari ya fita a jikinta, zunzurutun tsoron shi da ya kama ta, wani irin ษ“aci rai yaji kamar ya rufe ta da mugun duka, aikuwa ta d'ago dagwala dagwalar idanunta akan shi. Dukar motar yayi cikin tashin hankali ya juya tare da watsa mata wani mugun kallo tare da bude aljuhun motar shi ya fidda kudi yan dari biyar, ya watsa mata, sannan ya kuma ce mata. "Bude min rigar ki na gani?" Ya faษ—a yana bude mata idanu, cikin cool Voice tace mishi. "Malam ya ha..! Toshe hancin shi yayi tare da kakarin amai, ya bude motar ya shiga sheka amai, kamar wanda yaci mugun abu. Sororo ta tsaya tana duban shi. Kallon me cike da tsoro yana juyawa yace. "Na shiga uku na lalace, meye nayi da zafi aka hada ni da wacce zata kashe ni, ke sidira kike ko Sidrah, billahil azim zan b'atar dake matukar aka kuma ce miki zan zo ki gudu kawai, domin zan kai ki inda ake yanka mutane na sayar da wannan karamin kanki, su yanka ki.". Shiru yayi cikin takaici da jimamin wannan hadin gwarmai da aka mishi, kamar wanda aka ce Mishi ya kalle ta yaga tayi hamma, "innalillahi wa'inna ilaihi rajioun Ya Allah, ke fitar min a mota!" Ya daka mata tsawa. Wani irin abu taji ya tokare mata wuya, cikin zubda kwalla tace mishi. "Kayi hakuri bazan kuma ba!" Sake tozali da yayi da red teeth ษ—inta wanda suka yi wani tsatsa daga jikin dasorinta, ya dashi cewa da ฦ™arfi. "Am deeply death, ke zombia ce, idan mutum yayi kuskure kika cije shi da wannan hakoran ki, zama dodo zai yi dan haka fita idan na kuma zuwa garin nan a sanya ni a Lazza a daure. Munmuna me kama da, dark ghost get out." Ya daka mata tsawa, ai kuwa ta juye mishi sauran fitsarin dake cikin maranta. Ji yayi kamar yayi ta kurma ihu, tare da jibgarta ko zai samu sassaucin abinda tayi mishi. Allah Sarki, tana fita ta koma bayan durumi ta zauna tare da cusa kai a tsakanin cinyoyinta, ta fashe da kuka tana faษ—in. "Me yasa baku tafi dani ba? Me yasa da zaku mutu baku janyo ni mun mutu tare ba? Mama na gaji da kome bana so kudawo ku tafi dani, wallahi bani son zama a nan." Ta fada cikin kuka me ban tausayi, yadda take kukan sai jikin mai sauraro ya mutu. "Ke

Chapter 2 of 13