Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels 11/13, 8:05 PM] My Zahrah: 𝐑𝐔𝐖𝐀 ππˆπ˜π” <𝑲𝒂 π’”π’‚π’šπ’Š π‘«π’‚π’šπ’‚ π’Œπ’‚ π’”π’‚π’Žπ’Š π’…π’‚π’šπ’‚ π‘²π’šπ’‚π’–π’•π’‚> ℍ𝔸℀𝔸𝕂𝔸 π•Žβ„π•€π•‹π”Όβ„'π•Š π”Έπ•Šπ•Šπ•†... Bismillah Rahmani Raheem. https://my.w.tt/EcTsIaOy2ab _Allah subhanahu wata'ala ya halicci d'an adam domin ya bauta mishi, kuma bawai zaka kare shi da kome bane! Sabida babu abinda zaka yi dan ka biya shi wannan kyautar da yayi mana! Koda miskala zarratin bazamu tab'a karen shi da kome ba! Haka zalika ba zamu rage shi da kome ba! An karbo hadisi daga d'an Abbas, yace Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya fada mana cewa! Da zamu hadu mutanen farkon mu da mutane karshen mu, mu roki Allah. Dukkan mu zai amsa bukatar mu! Ba tare da ya manta daya min mu ba! Ashe kuwa dole bawa ya kasance mai godewa Allah da ni'imar da yayi mishi! A duk cikin halittun da Allah yayi. Babu wanda Allah ya karrama shi kamar D'an Adam, a cikin Alqur'ani mai tsarki Ubangiji yayi batu da yawa akan Dan Adam! Ya kuma bashi labarin kanshi a cikin Alqur'ani! Ubangiji yana sane yayi mu masu banbancin Halitta. Wasu farare! Wasu bakakke! Wasu kuma zabiyoyyi! Kuma yana sane da banbanta mana ra'ayin mu akan addini! Sannan ya kaddara wasu fararrun alamari zasu iya shigowa tsakanin mu! Dan haka da wannan nake kuma godewa Allah da ya bamu ni'imar da bamu isa mu saya ba sai dai mu gode mishi!_ Alhamdulillah! 1989/ July/ 21 Jigawa state Hadeja General hospital. 0⃣1⃣ "Dan Ubanki idan kika kuma shigowa rayuwar Ma'aruf sai na saka an yanka min ke. Anyi min Gunduwa Gunduwa da namarki, bake mayya ba sai na cofin Babanki yar shegiya, tsinaniya. Kai idan na kuma see you a najeriya, a go cofin kan uwarki bake magret ba toh ko markade kike babu sassauci a tsakanina da ke, yan banza me manyan idanu, maza take yor culot maki sakawa ki bar garin nan dan uwarki kar na kuma ganin yor lege, a garin nan yar banza me manyan idanu." Cikin shashekar kuka matar da bazata wuce shekaru ashirin da hudu ba, ta durkusa a gaban wata mata wacce idanunta Babu alamun rahama tace cikin bagwaren hausan da bai gama rike bakin ta ba, "RiΖ™o yaro sai Maman shi don Allah ku bani baby na, i swear ba zan kuma came back to Ma'aruf ba, please baba" Tauuu suka dauke ta da mari sai da ta dungura, dai dai shigowar Nurse dakin da aka kai Magret, cikin jin haushi Nurse din tace. "Amma baku da imani, taya mace daga haihuwar ta ko hutawa bata yi ba, zaku zo ku sakata a gaba! Kuna cin mutuncin ta, haba ku kuwa!" Kallon jelar gashin Magret a hannun Surayyah tayi. Cikin mamaki take kallon tsantsar rashin mutunci a idanun su. Takowa ta yi tare da d'ago matar cikin tausayawa ta ce. "Mutanen na basu da imani, kuma zasu iya cutar dake, idan kika tsaya sai sun baki yaronki. Kiyi hakuri kinji." Kallon kayan jikin jikin Hauwa. Riko hannunta tayi suka saka kai zata fita, ta kwace hannunta, tana kuka tare da fadin. "Karku rabani da Yarona, ku bani Yarona." Haka Nurse Salamatu taja ta suka fita. Kuka take kowa ya ganta sai ya tausaya mata, har suka bar ward din, sannan ta kaita wani daki ta bata kaya ta saka, riga daban zani daban. Sai dan kwali, da ta daura. Hawaye na zuba mata. Ta ce mata. "Please ga Yarona a hannun Allah yana kuma hannunki, ki saka ido akan shi, ki kuma bani layin asibitin nan zan tafi idan na isa, US zan kira ki. Don Allah karki cire idanunki akan shi yaro karami sun hanani shi." Haka ta riko hannun ta suka fita sai da ta samu wani a koru kura, ta sakata wanda zai kaita Kano. *** Bayan tafiyarta Suka dauki yaron suna kara jin haushin Hauwa wacce yar asalin Ζ™asar Amurika ce, tafiyar Ma'aruf can karatu ya hadu da ita, inda suka yi aure sannan ya dawo da ita, Magret William yar wani shahararren attajiri ne a garin newyork, ita kadai ya haifa, uwarta ta mutu ta barta, shi ne ya dauki son duniya ya daura mata, ya nuna mata wata irin SOYAYYA kamar me, sai dai zuwan Ma'aruf Adamu Hadeja, ya sata juyawa Soyayyar Mahaifinta baya tace tana son Ma'aruf, duk yadda Uban yaso karta fada mugun rayuwa, haka taki fir. Sannan aka yi aure tsakaninta da Ma'aruf, sai da suka shekara biyu. Sannan Ma'aruf ya gama karatu, yace zasu zo ganin gidan zai dawo da ita. Tunda suka biyo jirgi suka dire a kano, taga yadda kasar Najeriya yake, take tsoron barinta Ζ™asar Iyayenta ya kamata, tunda suka shigo hadeja. Ta haΙ—u da Muguwar uwar miji, da yan uwan miji, tare da Yayar mijinta, da farko sun dawo da arziki me mugun yawa, wanda Baban Magret ya basu, kafin su koma, amma suna zuwa Yaya Hindatu ta kwashe kome hatta kayan sakawar Hauwa sai da suka kwace. Suka wurga mata wasu matattun kaya, haka ta yi ta rayuwa, watan su biyar aka daura mishi Aure da Surayyah. Yar mijin Yaya Hindatu, tunda ta shigo gidan suke. Mata cin mutuncin, tare da wulakantata. Sun dake ta, sun zage ta. Gashi Ma'aruf yana dawowa zasu fadi karya da gaskiya babu bincike zai hauta da duka, wahala tayi wahala. Tun bata jin Hausa har ta koya dan dole. Abin takaici da ban tausayi, tana samun ciki zasu zubda mata shi, shi yasa wannan cikin tana samun shi ta boye musu baya gayawa kowa ba, har ta fara zuwa asibiti a sace. Zuwa lokacin da ta haihu. Sun kwace yaron ne, wai dan karta tafi dashi dan burin su. Tayi nesa da Ma'aruf karta zauna dashi domin ko sun hada su, sukan shirya. Kuma sun san idan ta tafi da yaron Ma'aruf zai bita, idan kuma suka sake ya bita, sunce zata rike musu shi. Da wannan nazarin Yaya Hindatu ta zuga Baba Mero ta kora keyar Hauwa. Dan haka lokacin da Ma'aruf ya dawo, Baba ta fashe da kuka tana kallon shi tace mishi. "Dama sai da muka gaya maka, Ba zata tab'a sonka ba, gashi nan ta gudu ta bar yaron da yake cike da bukatar soyayyarta, tur da wannan rayuwar, abin tausayi yaron da aka haifa ko dumin Mahaifiyarshi bai ji ba ta tsallake shi" a zuciye ya amshi yaron, sannan ya zuba mishi ido, kwalla na zuba mishi, ya sumbaci goshin yaron sannan ya kalli Mahaifiyarshi yace. "Gashi nan sunan shi Aamil! Zan tafi na nima mishi abinda za a na bashi, yana sha. Ita kuma Hauwa Ubangiji ya min Sakayya, Ni da Yarona." Ya mike a hankali ya bar dakin. Murmushin mugunta tayi sannan tace. "Babu shegiyar da zata mallake min Yarona." Ta cigaba da kula da jinjirin. Har Baban shi ya kawo madarar da za a cigaba da bashi. A wahale Aamil ya taso, ga rashin uwa. Yaron haka yayi ta fama da cututtukan, irinta Yara. Lokacin da ya fara rarrafe, haka zai bata jikin shi da kashi, Baba cikin jin haushin kulawar da Uban yaΖ™e mishi zata zage karfin ta ta zabga mishi duka, wani lokaci ya shiΙ—e. Wani lokaci haka zai yi shiru, yana sauke ajiyar zuciya. Zai yi wuya ta dake shi bai kwanta ciwo ba. Duk da gidan da suke family house ne, me cike da sassa masu yawa, shi yasa babu wanda yake sanin uΖ™ubar da Baba Mero da Hindatu suke bawa Aamil. A hankali yaron yake girma, sai ya taso baya shiga cikin mutanen gidan nan. Sai ya zama na ya taso da mugun tsoron mutanen gidan. Kullum yana cikin dakin, yana da shekaru biyar, Baban shi ya samu aiki a Jigawa. Dan haka da ya tashi komawa da matar shi Surayyah, sai ya dauki yaron, dakyar Baba ta barshi, ya dauki Yaron, suna komawa can kuwa ya saka yaron a makarantar boko da islamiyya. Sai dai idan ya tafi aiki, Surayyah bata taΙ“a bawa Aamil abincin matukar Ma'aruf yana gida zata cika mishi kwano har yana zuba, idan kuwa baya nan toh, wallahi azabar duniya sai ta bashi, ta dake shi ta kona mishi hannu. Ta zuba mishi gishiri, haka zai ta kuka tana dariya. A hankali ya fara shanye irin azabar da take mishi, idanun shi ba bushewa. Yana wani irin kangarewa, tare da zama mafadaci. A bayan gidan su yan shaye shaye suna zama, idan ta daidaici dawowar Baban Shi zata kora shi gurin, yana Shigowa gida zata ce. "Yaya nifa na fara gajiya da halin Aamil idan zaka zaga gurin yan shaye shayen nan yake zama. Ka duba ma!" Yana zuwa zai same shi a gurin su, riko Yaron yake zuwa gida yayi ta dukar shi, kamar wani baba. Ita kuma haka na mata dad'i, haka zata yi ta murna. Gashi Allah bai bata haihuwa ba, duk wanan azzabar ta take bawa Yaron. A hankali yake girma, rashin jin shi yana kara bunkasa, fitinar shi na kara hauhawa. Har zuwa lokacin da ya cika shekaru talatin cif a duniya..   Wani irin bakin ciki ne ya tokare mishi kirji, kallon Aamil yayi wanda ya fito daga ban daki, ga budurwa da ta kwana a d'akin shi tana shafa mai, Ganin Alhaji Ma'aruf yasata mik'ewa tana kare jikinta, dauke kai Aamil yayi tare da kallon yarinyar yace. "Dan Ubanki ba nace kar na same ki a waje ba, ki fita kafin naci Ubanki!" Ya daka mata tsawa. Da sauri ta, dauki kayanta, tare da fita zata saka. Abban shi ya matsa mata. Ta fita, tana mita ganin sai lokacin Aamil zai gabatar da sallar asuba. Karfe bakwai saura Kwata. Wani abin yaji ya tsaya mishi a rai, kwalla na cika mishi ido. Yana tsaye har ya idar da sallah,kallon shi yayi sannan yace mishi. "Ubangiji kana ganin Bawanka, na fita hakkin shi na bashi tarbiyya, na kuma bashi ilimi. Ya Allah ban san me nayi ka bani shi Zakka ba." Cikin jin haushin Abban shi yace mishi.. "Idan baka bukata ka kore ni mana kamar yadda kuka raba Ni da Uw..." Tass ya wanke shi da mari, sai da yaji marin sosai, dan haka ya juya tare da cewa. "Yau zan bar maka gidanka, na shiga duniya, nasan akwai mutanen da zasu rike ni, kasan aka kaunata ka samar dani, baku da wani aiki sai aibata Mahaifiyata, toh wallahi zan bar maka gidanka, tun tasowata ban san soyayyar kowa ba. Ban san dadin Kowa ba, haka na taso cikin kunci da rayuwa mara amfani, idan nayi abu kace ba tarbiyyar da kayi min ba kenan, ka tsane ni, bayan baka san meye yake faru da ni ba, taya nima bazan dasa maka bakin ciki ba, zan tafi na barku ku zauna da mutanen da suka fi maka ni?". .daga haka ya fice ya bar dakin har ya isa bakin kofar, Baban Yace mishi. "Kaje kaga Sidrah?" Cikin zafin rai ya juyo yana huci yace mishi.. "Abba kace baka kaunata mana! Wancan yarinyar da babu wanda ya kaita muni itace zan aura! Yarinyar da bata wuce Jaririyar ba kake cewa naje na ganta! Yar shekaru tara, wallahi ko a yar wanke wanke gidana bata kai ba balle yar da zan aura, Ni babu ita a cikin rayuwa, duk da ana gaya min cewa mahaifiya baturiya ce, karshe sai ka Hadani da bakace, meye nayi da zafi da zaku rasa kyawawan mata, ku bani sai wancan mummunar me kama da kwarangwal, yarinyar da kafin namiji ya moreta sai bayan nan da shekaru ashirin. Wallahi idan zaka nimawa Ali ita ba laifi, amma." "Tabbas da kai za ayi auren! Ko kana so ko baka so! Aamil sai ka auri Sidrah, domin ba zan lamunci zubda min mutuncina da kake yi ba, kaka dauko yaran mutane kana lalata tarbiyyar su. Sanan naka hankoron mace kyakyawa, su matan da kake lalata su ba kyawawa bane? Ko iyayen su basu kaunar su ne? Toh wallahi ka wuce hadeja gurin kaga Sidrah Wallahi ka kuskura na samu labarin baka je ba, tabbas sai na hukuntaka, dan ba zaka zubda min mutuncina ba, wanda nayi kai shekaru aru-aru ina tanadin su, sabida kai na da kimata." Daga haka ya mai da hannun shi baya. Tare da barin d'akin.. wani uban ihu ya Aamil ya buga tare da dukar Kofar dakin shi. *Alhamdulillahi gani nan na dawo a wani Lovestory labarin yasha banban da saurar. Ku biyo Alkalamina...... 🀩 . Kuyi hakuri Daula biyu! Insha Allah sai sabon shekara zaku ji ni, Ruwa biyu kuma Insha Allah! Ko na cigaba a watan da zamu kama ko kuma, A karshen shekara Insha Allah! Ya danganta da lokacin da na samu ne!* *Nagode sosai* #Mai_Dambu [11/13, 8:05 PM] My Zahrah: 𝐑𝐔𝐖𝐀 ππˆπ˜π” <𝑲𝒂 π’”π’‚π’šπ’Š π‘«π’‚π’šπ’‚ π’Œπ’‚ π’”π’‚π’Žπ’Š π’…π’‚π’šπ’‚ π‘²π’šπ’‚π’–π’•π’‚> https://my.w.tt/U2ZCTqQj4ab ℍ𝔸℀𝔸𝕂𝔸 π•Žβ„π•€π•‹π”Όβ„'π•Š π”Έπ•Šπ•Šπ•†... Bismillah Rahmani Raheem 0⃣2⃣ "Taya za a ace min na auri ugly girl. Me zanyi da mace munmuna irin Sidrah yarinyar da bata wuce Jaririyar ba. Idan na yarda na shiga Lazza a daure." Ya kuma kaiwa kofar duka, tare da make kanshi. Yana wani haki dan masifa, a fusace ya saka kayan shi ya fito daga dakin. Tsakar gida ya fito, yana kallon yadda yaran gidan kowa ke shige da fice. Gyara zaman hular kan shi yayi tare da nufar cikin gidan, duk abinda ya gani a gaba shi ball yake dashi. Ba tare da ya damu da koma meye ba, yana isa kofar da zata shiga da shi tsakar gidan su, ya ja tunga ya tsaya. Tare da zabgawa Hasnah wani irin kallon banza, sannan ya kauda kan shi, ya taka a hankali isowa inda Hajiya Surayyah take soyar kosai. Ya gyara zaman facing cap din shi yadda zai kafta rashin mutunci a silale ba tare da ya kalli fuskar kowa ba. Gyaran muryan yayi duk yan kanen shi suka dare, tare da komawa can gefe suna zare ido. Domin sun san shi hukuma ne, bai da mutunci ko na miskala zarratin, bayi da hakuri kamar rina haka yake, fushinsa yafi na mayunwacin zaki, idan yana yinka duk duniya babu wanda ya isa yace baka kai ba, haka idan ba ya yinka babu wanda ya isa yace kayi balle yayi ka, wato Aamil ruwa biyu ne..yana da sassayar hali, kuma yana da baudaddiyar hali, yana iya zama na tsawon watanni bai yiwa kowa magana ba, idan kuma aka kuskura yana gida yara suka cika shi da Hayaniya zai kama yaro yayi ta bashi azaba kamar yadda suka mishi. Mutum ne mai mugun don abu me kyau. Sai gashi ya kasance gidan su bakake ne! Musamman Familyn su. Shi kuma ya kasance ruwa biyu, Mahaifiyar shi baturiyar Amurka, mahaifin shi bahaushen hadeja. Aamil zai iya juya harshen sa ya dai na magana da kowa cikin harshen Hausa, sai English ba tare da yaji ko dar ba. Sannan yana iya zuwa kofar Church ya zauna, duk bala'in da Christian zasu mishi ba zai tashi ba sai lokacin da yaji a ranshi ya tashi zai tashi. A duniya ya tsani mutane uku! Baba Mero wacce suke kiranta da Hajiya. Sai Yaya Hindatu, wacce suke kiranta da Goggo hinde, sai Hajiya Surayyah wacce suke kiranta da Hajiyar mu. Dukkan su da sunan su yake kiran su. Sai dai Hajiya Uwani wacce ta kasance matar Alhaji Ma'aruf ta biyu, sai Amarya shi wacce suke kiranta da Hajiya Amarya. Alhaji Ma'aruf yana da mata uku cif, Hajiya Surayyah uwargida sai Hajiya Uwani wacce take Binta, sai Hajiya amarya wacce take karama, A gidan Sun ware Hajiya Uwani basu yi da ita, gashi itace kusan Alhaji Ma'aruf yake ji da ita, domin itace take jibance da al'amarin Aamil kasancewar ita tayi karatun boko da na addini, sai ya zama na tana kokarin ganin ta karkato da hankalinsa kan karatu. Hajiya Surayyah da Hajiya Amarya wacce sunanta Karimah. Basu da mutunci. Kuma suna tare da Yaya Hindatu da Hajiya. Yanzun haka gidan cike yake da yara Domin wani irin haihuwa ake kirin na gasa. Idan wannan tana da ciki toh Insha Allah ko Shayarwa kike sai taje ta kwaso ciki. Sabida jahilci, idan ka cire Hajiya Uwani wacce take tsarin iyali. Saboda tana koyarwa a jami'ar jihar Jigawa,kuma tana yawan tafiya course. Dan haka ta cewa Alhaji Ma'aruf. "Yallabai! Zaka yi hakuri gaskiya, bazan takura kai na da haihuwa akai akai ba, sabida ni ma'aikaciya ce, kuma ina yawan tafiya karo ilimi, kaga ba zan iya tara yara ina barin su a gida babu kulawa ba, dan haka zan iya daukar lokaci zuwa lokaci kafin na haihu." Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya riko hannunta, ya ce mata. "Babu laifi! Nima da ace wadancan zasu bani hadin da mun samu tazarar Haihuwa, domin Kinga Karimah sai da aka min magana a haihuwar Yusuf, aka ce mahaifar tana bukatar kulawa da hutu. Da kaina na kaita aka bata maganin da zata na sha na wasu watanin, amma kawai wata biyar sai naji wai tana da ciki, wallahi abin ya dame ni, kuma ba kome ya kawo haka ba. Sai kishi tunda taji Surayyah na da ciki shi kenan, magana ya kare." Murmushi tayi sannan ta ce. "Manta da batun kowa, ni bana son damuwa, kai ne a gabana!" Yaran Hajiya Surayyah, goma ga cikin na sha daya, Ali shine babba. Ghali ya yake binshi. Jamila take bin Ghali. Sadiya, Harira, Mariya, Dejangala, Haruna, Muttaka, sai Halima. Hajiya Uwani kuma duk yaranta biyar ne. Muhammad Aashiq, Aseed, Abdus Samad, Jalil da Jalal, Twins ne. Amma basu kama da juna ko daya. Hajiya Amarya itace kuma take da yara mata huΙ—u. Zakiyah, Ihsan, Mufidah, sai Muwaddah. Sai Yusuf. Da kuma ma cikin jikinta. Yaya Hindatu, tana da yara biyar. Musa, Sai Dayyabu da Abdullahi, sai Hasnah da Baria. Gidan Alhaji Ma'aruf, yana da matukar kokari. Domin bayan Kanwar shi akwai matasa kusan guda bakwai a cikin gidan. Da suke karatu a karkashin kulawar shi. Faruq, Mujaheed, Sulaiman. Ismail, Mahmoud, Saleh. Bala. Isah. Duk suna zama mishi a shagunan shi da suke cikin kasuwar Dutse. Duk yadda zan muku bayani akan gidan Alhaji Ma'aruf, ba zaku fahimta ba. Domin gida ne wanda baya rabuwa da baki daga kauye. Shi yasa yake noma, yana noma shinkafa, dawa, gero, masara da kuma wake da wanke suya. Sannan yana noman rani. Inda ake fidda mishi kayan lambu. Har da ya'yan itace. Sannan tsarin gidan Alhaji Ma'aruf, a bayyane yake. Domin shi baya bada kudin kome akwai duk abinda ake bukata. Kayan miya idan lokacin shi yayi. Sawa yake a kawo mishi. A yanka wasu a shanya, wasu kuma a markade su a zuba a babban deep freeze, maggi kuwa kullum ake kawo laida daya daga kasuwa. Mangyada da Manja, ana kawo rabin jarka yalo ne. Sai bushashen kifi, da ake kawowa daga numan. Duk ranar girkin mata, zata jika gero da dawa, a markade shi. Sannan a tacce shi. Washi gari kuma da sassafe yan matan gidan da masu aiki zasu tashi da gyaran wake, kafin karfe bakwai matar da take da girki ta fara soya. Masu aiki na tayata, babu batun masu aiki su zasu miki kome dole ki fito. Sannan kafin ya fita zai tara yaran shi da kuma matan ya tambayi kowacce abun da take bukata, ya ajiye musu dubu uku uku, yaran kuma dubu daya daya. Sai ya shiga dakin mahaifiyar shi ya bata dubu biyar, kanwar shi dubu biyu. Yaranta dari biyar biyar.. A kasuwa kuwa, idan ka cire Ghali, wallahi hatta Aamil cutar mahaifin shi yake, domin suna diban dukiyar shi, bana wasa ba. Sai dai bai da ikon ya kore su, domin yana da yakinin idan bai mutu ba, Allah zai bashi wanda zai kare mishi dukiyar Hauwa. Dan ba nashi bane, na Hauwa ne. Gashi Allah ya sanya albarka a cikinta. Duk yadda suka kai da su b'arnan Allah sai ya duba niyyar dake cikin zuciyar shi ya kuma bunkasa dukiya. Ba zai tab'a mantawa ba, duwatsunta masu daraja, ta dauka ta bashi lokacin da yake faffutikar niman aiki, bai san dasu ba. Ta cire tace mishi. "Ma'aruf! Gashi nan ina ga zasu saya da daraja, ka fara yin kasuwanci mu gani kafin ka sami aikin gwamnati, dan ko mahaifina da kasuwanci ya fara aikin gwamnati." Guda goma sha biyu, ta rike sauran sha biyun dan guda ashirin da hudu ne. Wannan kenan.. Kerere yayiwa Hajiya Surayyah a kai, tana zuba kullu a wuta ya kalli wanda ta kwashe sunyi kyau murmushi ya sake mata, kafin ta

Chapter 1 of 13