kawai ta yi tana jin wani abu kamar nadamar gaya masa na kamata, dan yanda ya kafa masifa a cikin wayar kai kace Sa'ad ɗin ne a gabansa, duk da faɗa ko cacar baki ba ta taɓa haɗasu ba, magana ma wannan ba ta haɗasu, sai su haɗu a wuri su baje ba tare da wani ya kalli wani ba, duk yadda Takawa da Galadima suka so haɗa kan bayin Allahn nan sun ƙi haɗuwa har yau har gobe.
"Yanzu ni dai ba gaya maka na yi dan ka rufeni da faɗa ba, na gaya maka ne domin a samu mafita"
Muhibba da tsawar da yake mata ke naiman kurmanta mata kunne ta gaya yayin da yake tsaka da balbala bala'in nasa da ya saba. Shiru ya yi yana huci kamar macijin dake gaf da kai sara, ya rintse ƙananun idanuwansa yana murza goshinsa, can kuma ya buɗe idonsa yana sauƙe numfashi da ƙyar, kamar wanda ya kinkimi buhun hatsi.
"Nan da next week nake sa ran zan ɗauki hutun ƙarshen shekara, kuma Nigeria zan zo, idan na zo zan naimi izini a wurin Takawa na taho nan da ita, domin ƙwararrun likitoci su dubata a gano a inahin abin da yake damunta, likitocin Nigeria ub*n me suka sani..."
(In ji Hammad🤥, ba cewar Candy ba ce)
"To Ya Hammad, Allah yasa dai su yarda"
"Suka yarda aka kaita wurin wani mahaukaci ma..."
Ya ƙarashe da tsaki, bai ko bari sun yi sallama ba ya katse ƙiran, gaba ɗaya wannan batun ya dagula masa mood ɗinsa. A ɗaya ɓangaren bayan ya katse ƙiran Muhibba ta sauƙe wayar tata tana binta da harara kamar da aka ce mata ga Hammad ɗin nan, ko da yake in aka ce shi ɗin ne ma ba ta isa haɗa ido da shi da garaje ba, domin bakin rijiya ba wurin wasan yaro ba ne. Sa'ad ne ke sakar musu fuska ita da Aysher, shi yasa suka bi suka raina shi, saboda shi ke musu wasa, amma Hammad ko kallo ba su ishe shi ba ballantana ya musu wasa. A fili ta ja tsaki tana faɗin.
"Masifaffe!"
*Kauyen Yarimaru, Gembu, Mambilla, Taraba state.*
Wasu magidanta ne guda biyu durƙushe a ƙasa, kowanne cikin su biyun ya haɗe hannayensa suna kuka cikin naiman yafiya suke kallon wani mutum dake zaune kan kujera, duk yawan shekarunsu da idan aka haɗa da nasa za su iya haifar ɗa kamarsa, roƙonsu suke cikin naiman sassauci. Tun da ya zauna a kan wannan kujerar tasa ta gado bai ko motsa ba ballantana ya basu damar sa ran yana jinsu ko kuma zai iya yafe musu kamar yanda suke rokon yafiyar tasa. Ɗan ƙaramin littafin “Hisnul Muslim” ne riƙe a hannunsa, a hankali fatar bakinsa ke motsawa yana bin harufan larabcin dake rubece a cikin littafin ɗaya bayan ɗaya yana karantawa hankalinsa kwance, kamar ba shi ne yasa a hukunta magidantan da za su iya haifarsa ba, kuma hukunci mafi ƙasƙanci, domin ƙananun yara ya sa suka zanesu da bulali kamar a makaranta.
“... Mun haɗaka da Allah GURU ka mana rai, ka ƙyalemu haka, Wallahi ba za mu sake kai ƙararka wurin ‘yan-sanda ba!”
Ɗaya daga cikinsu ya faɗi yana kuka wiwi kamar ƙaramin yaro, dan ba ƙarya sun doku kamar jakuna masu taurin kai. Sai a lokacin da ya yi maganar Guru ya samu damar janye idonsa daga kan littafin hannunsa ya ɗorasu a kansu su biyun dake durƙushe gabansa jikinsu yana kyarmar tsoro, littafin ya rufe yana taɓe bakinsa.
“Wa ya gaya muku cewar za ku ci gaba da rayuwa bayan yau? Ai sai kuna raye za ku kai ƙarar tawa ko Tijjani?”
Ya ƙarashe da tambaya yana kallon wanda ya yi wancan furucin, jin batun za a kashesu ya ƙara rikitar da su, dan haka suka ƙara ƙaimi wurin roƙonsa kan ya yafe musu, hayaniyar da suke naiman tada masa da rana tsaka yasa ya toshe kunnensa da hannu ɗaya, sannan ya ɗaga kai ya kalli yaransa wanda kallo ɗaya ka musu za ka musu kuɗin goro ka kirasu da ‘yan daba. Da ido kawai ya yi wa ɗaya daga cikinsu alama, shi kuma ya kalli ƙananan matasan da da wuya za ka samu wanda ya haura shekaru 20 a cikinsu, cike da iko yace.
“Ku ɗaukesu daga nan”
Haka yaran suka kamasu suka ɗaukesu daga wurin, su kuma ba su fasa magiya da naiman a yafe musu ba, duk kuwa da su aka yi wa laifi.
“Me kake so a musu Oga?”
Yaron nasa da alamu suka nuna cewa shi ne na hannun dama ya tambaya yana sunkuyawa a saitin da yake, ajiyar zuciyar kwanciyar hankali ya yi, sannan ya ɗora ƙafarsa ɗaya kan daya, ya buɗe littafin alamun zai ci gaba da karatun da yake.
“Ku kullesu na tsawon kwana uku, bayan ruwa ban yarda a basu komai ba, kwanakin nan ba na jin son a kashe rai, dan haka kawai a sake su bayan kwana ukun, ko ba komai zuwa lokacin na san jikin ta ƙaura yay la’asar”
Maganar ta fito cikin salihin amon muryarsa na masu imani a baka, a zuci kuwa ƙannen shaiɗan. Shi fa har yanzu an rasa a wani state za a aje shi, shin ɗan daba ne ko ko bawan Allah mai imani? Tun da Guru yake a duniya bai taɓa shan ko da sigari ba ballantana aje kan sauran kayan maye, ammam kuma a gaba ɗaya yankin duk wani mai safarar kayan maye to a bayansa yake, babu kalar kayan ta'addacin da ba ya kawowa yankin. Haka kawai idan ta raya masa zai sa a ɗauko matasan cikin gari ya basu kayan maye su sha, da haka da haka har ya janyesu su koma yi masa aiki, irin hakan ce ta haɗosu da ɗan Tijjani.
Lokacin da Tijjani ya samu labarin ɗansa ya fara shaye-shaye tare da tallafawar Guru bai yi ƙasa a gwiwa ba wurin kai ƙararsa ofishin ‘yan-sandan cikin garin Gembu. Aka zo aka kama shi aka tafi da shi can, sai dai kafin su dawo cikin Ƙauyen Yarimaru har Guru ɗin da aka kama domin fuskantar hukunci ya rigasu dawowa, a’a ƙarshe ma a ƙofar gidan Tijjanin suka same shi zaune, har yana tambayarsu sai yanzu suka samu ƙarasowa?
Ba Tijjani da Halliru ne kaɗai suka taɓa shigar da ƙara a kan Guru ba, jama’a da dama sun yi hakan, sai dai ko an kama shi ba ya daɗewa zai fito, saboda yana da ɗaurin gindi a wurin ‘yan siyasar yankin. Ganin cewa doka ba za ta yi aikinta a kan Gurun ba yasa jama’a suka fidda rai a kan lamarin, suka naɗe hannayensu suka koma gefe suka zubawa sarautar Allah ido. Idan ka ga Guru a zahiri za ka iya rantsuwa da sarkin da ya hallici kowa da komai kan bai san yanda ake mugunta ba, kana ganinsa ka ga mutum mai cike da kamala da kuma nutsuwa. Amma a cikin zuciyarsa ban da tarin mugunta da ƙeta babu komai, idan yace zai rantse kan bai taɓa kisa ba za a yarda, domin shi kansa ya san bai taɓa kashe wata rai da hannunsa ba, sai dai yasa yaransa su kashe.
Rayukan da suka salwanta dalilinsa ba su da adadi, goyon bayan ‘yan siyasa da ya samu shi ne ya ba shi ƙwarin gwiwar cin karansa babu babbaka, domin duk aikin da suke so a musu tabbas zai saka ayi, saboda shi ba zai yi da kansa ba, to hakan yasa su ma suka ɗaure masa gindi yake ta’addacinsa yanda ya so, duk da abin na damun jama’ar gari da dama, babu wanda ya isa ya yi magana a kai, saboda in ka ce ƙala to za ka yi ta ranka. A kaf duniya mutum ɗaya ne ke iya takawa Guru birki, kuma shi ne tsohon malaminsa Malam Yakubu.
*Kauyen Kinkin, yankin kabilar Hadzabe, kusa da tafkin Eyasi, arewacin Tanzania, Africa.*
AKIRA POV.
Cikin dajin da ya cika da dogayen ciyayi, akwai wata ƙatuwar bishiyar kuka, wadda aka fafake cikinta ya zamto kamar kogo. Sa’ilin da hasken rana ya ɗaga ya haske ƙofar kogon bishiyar, kai tsaye a kan idonta ya sauƙa ba tare da ɓata lokaci ba ta farka, ta tashi zaune tana hamma, a lokaci guda kuma cikinta ya soma ƙugin yunwa, saurin sauƙe hannayenta da ta ɗaga sama domin yin miƙa ta yi tare da dafewa cikinta dake kiran ciroma-ciroma. Fuska ta yamutsa sannan ta miƙe tsaye, wannan T-shirt ɗin da ta zama kamar tare aka kawosu duniya ce a jikinta, asalin kalar rigar orange ne, amma saboda ba ta samun gatan wanki ballantana ta samu ‘yar uwarta da za a saka yayin da take hutawa yasa ta koɗe ta koma wata kala da ba ta da suna. Bayan T-shirt ɗin babu komai a jikinta sai zanin da suka zaba ɗaurawa bisa kafaɗunsu, sai kuma tarin sarƙoƙin dake wuyanta, da waɗan da ke ƙugunta har da na kai wanda aka haɗa da guntun didigaggen gashin kanta.
A daddafe ta samu ta fice daga cikin kogon, sai ta tsaya a bakin kogon bishiyar dafe da cikinta tana kallon hasken rana da ya ɗaga sosai, duk da tana jin yunwa yanzu ba ta isa ta shiga cikin gari ba. Domin sarkin ƙauyen nasu da kansa ya haramta mata kwana a cikin garin duk ranar asabat, kuma idan garin ranar Lahadi ya waye ba ta da ikon shiga cikin garin sai rana ta tsaya a tsakiya, wato wajejan karfe sha biyu na rana, a cewarsu hakan zai nisantasu daga fushin abar bautarsu.
Bayan da ta zo duniya mahaifiyarta ta mutu, a ranar kuma jaruman ƙabilar tasu suka tafi wani daji dake kusa da su farauta, kaɗan daga cikinsu ne suka dawo, sauran duk sun yi asarar rayukansu a can, ciki kuwa har da mahaifinsu. Kuma a washe garin ranar aka kaita gaban abar bauta domin raɗa mata suna, a yadda al’adar garin take, za a aje jaririyar da ake son sanya mata suna a gaban abar bautar, sannan malamin ɗakin bautar zai zauna da yashi a gabansa ya yi rubuce-rubece na taurarin haihuwar yarinyar, bayan haka za a tsaya a ga ikon abar bauta, domin ita da kanta za ta zana sunan da ya dace da yarinyar a kan yashin nan da aka rubuta taurarin haihuwarta.
Sai dai ita Akira nata sunan ya zo da tangarɗa, a’a maimakon ma su ga suna sai suka ga an rubuta tsinuwa, to daga nan ne fa abin ya samo asali, sai aka zauna aka fara bincika yarinya, tun da ake haihuwa a ƙabilar Hadza ba a taɓa haihuwar yarinyar da ta kai Akira baƙi ba, baƙa ce ƙirin babu ko da ɗison fari a kan fatarta, sannan ba a taɓa haihuwar jaririyar da idonta yake wata kala ba sai ita, su dai sun saba ganin ƙwayoyin idon jama’arsu a matsayin baƙaƙe ko kuma brown, amma ita nata idon kalar na mage ne. gaba ɗaya sai aka tattara hujojjin hallitar da yarinyar ta zo da su, da kuma abubuwan da suka faru ranar da aka haifeta, sai suka fitar da hukunci kan tabbas wannan yarinya da aka haifa musu ba komai bace face tsiniwar abar bautarsu a kansu. A wancan lokacin sun so kasheta, Amma Nikamba yayanta shi ne yace a ba shi ƙanwarsa, kada su kashe masa ita domin a yanzu bayan ita ba shi da kowa, tun da iyayensu sun mutu. Da ƙyar da fama suka yarda suka ba shi jaririyar, shi da kansa ya saka mata sunan AKIRA wanda a yaren Hadzane AKIRA na nufin (haske).
Tun a wancan lokacin wannan dokar ta hana Akira kwana a cikin ƙauyen duk ranar asabat ta soma. Domin ranar Asabat rana ce wadda suke gudanar da sha’anin bautarsu a cikinta. Hakan yasa ba su bari ta zauna musu a gari gudun jawo masifa. Har kwanan gobe jama’ar ƙauyen ba su ɗauketa a matsayin ɗaya daga cikinsu ba, kawai dai tana rayuwa a cikinsu ne, amma ko da yaushe fatansu shi ne ganin barinta duniya, har yanzu ko wani iftila’i da zai faɗo musu za su danganta shi da ita ne, tun ba ta da wayo har ta zo ta san me hakan ke nufi, tun tana jin zafin abin har ya zame mata jiki.
Wani daddaɗan kukan tsuntsu ne ya karaɗe wurin da take, hakan yasa ta miƙe tsaye baki buɗe tana dariya, kanta ta ɗaga sama tana naimansa a kan bishiyar kukar, tana ganinsa ta ƙara tintsirewa da dariya, tsuntsun ya saki kukansa mai daɗin sauraro, ita ma sai ta ci gaba da kallonsa tana tsuke bakinta, kafin a hankali bakinta ya fara fitar da wani sauti da ya yi kama da na tsuntsun, idan ya yi ita ma sai ta yi, sai kuma ta yi dariya, ba tsuntsun kaɗai ba, a wannan wurin da take kwana ta saba da dabbobi da dama, wani lokacin ko ba ranar asabat ba ta kan zo ta kwana, kwanan wurin ma ya fi mata daɗi, tun da cikin ƙauyen ba daɗinsa take ji ba. Tun tana jiran zuwan Nikamba ɗauke da abin da za ta karya har ta fidda rai, ta ma yi fushi da shi, dan ita ba haka suka saba ba, duk sanda za ta kwana a cikin dajin sassafe zai zo ya kawo mata abinci ta ci, amman yau ga shi har ranar na shirin zuwa tsakiya bai zo ba.
Cikin jin haushin biris da ɗan uwan nata ya yi da ita ta nufi cikin dajin, ƙafarta ko takalmi babu, tana tafe tana wata waƙa cikin yaren nasu na Hadzane. Duk in da za ta ga wata dabba babba ko ƙarama to za ta tsaya, sai ta gama shaɗancin kuma sai ta ci gaba da tafiya, da haka har ta iso wurin da wasu ciyayi suke, tsugunnawa ta yi ta kama ƙasan ciyayin ta soma tsigosu daga cikin ƙasa, idan ta ciro kuma sai ta cire jijiyar ciyawar, ta cillar da ganyen, domin ya zama mara amfani a ganinta. Sai da ta ciro wanda ta san zai isheta, kafin ta tare jijiyoyin tsirran da ta cire, ta kama wata bishiya dake wurin ta hau, ta zauna tana kallon dangin jakin daji (Zebra) suna shan ruwa a wani ruwa mai gudana kusa da inda take, zamanta ta kuma gyarawa za ta fara cin jijiyar ciyayin da ta ciro a ƙasa ta ji Nikamba na ƙiran sunanta.
“Akira!”
Banza ta masa ta fara cusawa a bakinta tana taunawa da ƙyar, dan da can ma idan ba ta samu abin ci ba su take zuwa ta ci, ba ita kaɗai ba, hatta jama’ar ƙauyen nasu na cin jijiyar tsirran.
“Akira bu ta shay” (Akira sauƙo)
Cewar Nikamba sanda ya iso jikin bishiyar da take kai, kanta ta sauƙe ƙasa ta kalle shi ta tsakiyar ƙafafunta, ta haɗe rai tana kumbura bakinta, irin abin da ta saba ke nan idan ranta ya ɓaci.
“Bikakke buta shay” (Ba zan sauko ba)
“Bu ta shay ji bu” (Ki sauko na ce)
Sai ta girgiza masa kai, ganin da gaske ba za ta sauƙo ɗin ba yasa ya kama stem ɗin bishiyar da take zaune a kai, kawai ya soma jijjigawa. Ihu ta ƙwala tare da sakin abin da ke hannunta ta rungume bishiyar daga sama tana kuka.
“Nikamba ka bari! Zan sauƙo, zan sauko”
Ta faɗa muryarta na shaida tsoron da take ciki, Nikamba ya tsaya kamar yadda ta buƙata.
“Taho”
Ya ɗaga hannayensa sama ya miƙa mata, ta kalle shi wasu guntayen hawaye kwance a kuncinta, a hankali ta kama ta sauko, ya riƙota ya ƙarasa sauƙo da ita.
“Yunwa kike ji?”
Ita ce tambaya ta farko da ya fara mata bayan ta sauƙo.
“A’a”
Ta ba shi amsa har yanzu da guntun jin haushinsa a muryarta, dariya kawai ya yi, dan yasan ƙarya take.
“Da gaske ba kya jin yunwa?”
“Eh...”
Ba ta gama amsawa ba cikin ta ya yi wani uban ƙugi, ta yi sauri ta dafe shi kumbura bakinta, Nikamba ko dariya kawai ta ba shi.
“Ga abincinki nan, sai da na tsaya na dafa miki shi, shi yasa na makara”
Ya ƙara she yana miƙa mata wani abu mai kamar kwano, wanda aka yi shi da duma, Akira ta karɓa ta buɗe, take ta washe baki ganin kayan cikin dabba a dafe, bayan ruwa da gishiri babu komai a cikin girkin.
“Zauna ki ci... idan kin gama za mu je kogi”
Ta gyaɗa kai tana zaunawa a ƙasa, sannan ta fara ci a da sauri-sauri, duk kuwa da zafin da yake da shi.
____________
_Wannan Guru ɗin, ya zo da nasa sabon salon gadarar, bari mu zuba ido mu sha kallo, domin har yanzu ba mu je ko ina ba…_
_Sannan kar a manta da KAWA ZUCI paid book ne_
#SalmaAhmadIsah
#MiniCandy
#Bahadejiya
#KawaZuci
```````````````````````
*ƘAWA ZUCI*
*©SALMA AHMAD ISAH*
*06*
*State Servidor Public Hospital, Rua Borges Lagoar,1083 Vila Clementino, Sao Paulo, Brasil.*
PEDRO POV.
A bakin titi taxi ɗin da ya hau ta sauƙe shi, ya fito yana goya jakarsa a baya, kai tsaye cikin asibitin ya shiga, ya wuce reception ya nufi elevator. Yana shiga ya danna lambar hawa na biyar, sannan ya ja baya yana rungume hannayensa. Elevator na isa hawa na biyar ta tsaya sannan ƙofarta ta buɗe ya fito ya raɓa mutanen da ya iske tsaye a bakin elevator ɗin suna jiran fitowarsa domin su shiga su ma.
Tun kafin ya karasa ɗaki mai lamba 89 ya fara jiyowa hayaniyarta, kansa kawai ya girgiza sannan ya bude ƙofar ɗakin ya shiga kai tsaye, abin da yake hasashe shi ne ya tabbata, ya san in har ba lokacin shan maganinta ne ya yi ba babu abinda zai sa suna musu da nurses irin haka. Zaune take a kan gadon marasa lafiyar dake ɗakin, ta tsare nurse ɗin dake tsaye a cikin ɗakin da manyan idanuwanta tana mata masifa, a shekaru ba za ta haura sha bakwai ba, fara ce sosai irin farin turawa, sanye take da kayan marasa lafiya na asibitin, baƙin dogon gashin kanta daga gefe ya kwanta a kan kafaɗarta, daga ɗaya ɓangaren kuma an yi gajerun kitso guda biyu da ba su kai ƙarshe ba, (wato side braid), manyan idanuwanta ta janye a kan nurse ɗin ta kalle shi.
“Yauwa Hard Rock, gara da ka zo, ka gayawa wannan matar cewa ba a mini dole, a kan me za ta ce sai na sake shan magani, bayan ɗazu da Ibrahim ya zo ya bani na sha...”
Pedro ya ƙanƙance idonsa yana mata kallon nazari, sai kuma ya kalli nurse ɗin, ba tare da ya tambaya ba ta girgiza masa kai alamun ba ta sha maganin ba. sai ya sauƙe hannayensa dake harɗe a ƙirjinsa ya soma takowa zuwa cikin ɗakin.
“Ni kallonta ma ba na so, ka ce ta fice”
“Juliana?”
Ya ƙira sunanta cike da tuhuma, kanta a ƙasa ta ƙi yarda su haɗa ido, kamar da aka ce idan suka haɗa ido asirinta na ƙaryar da ta yi ta sha maganin sanda Ibrahim yana nan bayan ba ta sha ɗin ba zai tonu.
“Tun muna shaida juna ni da ke ki karɓi magungunanki ki sha!”
Idanuwanta ta fara ƙifƙiftawa, tana ɓata baki alamun za ta yi kuka, hannu ya miƙawa nurse ɗin ta ɗamƙa masa tray ɗin hannunta dake ɗauke da magungunan Juliana ɗin. Ya zauna a gefenta yana aje tray ɗin a tsakaninsu, sannan ya sauƙe jakar bayansa ya fito da ruwan roba daga ciki. Ya ɓallo maganin da ya san shi ne wanda take fara sha ya miƙa mata, tana wasa da sarƙar dake wuyanta me pendant ɗin cross ta dube shi bakinta na rawa, alamun gaf take da fashewa da kukan, ƙarshen girarsa ta ɓarin hagu ya ɗage yana sake miƙa mata alamun karɓi mana.
Sharrr hawaye suka zubo daga idonta, ta miƙa hannunta ba dan tana so ba ta karɓa, ta ɗaga kanta sama ta cilla maganin, sannan ta karɓi robar ruwan da ya bata ta kora da shi. Ta sauƙe kanta tana grigiza shi, da ɗacin maganin ya ziyarci sashen ɗanɗanonta sai ta fashe masa kukan sangarta.
“Da ma ai na san ba ka sona, na san ka tsaneni, Allah sarki Julia marainiya, ba ta da kowa, shi ma Badar ɗin ya daina sonta, tun da ya tursasata kan sai ta sha magani mai daɗi...”
Kamar ɗazu, yanzu ma haka ya tsaya kawai yana kallonta, kuka take har da su face manjina.
“Kin gama?”
Ta kalle shi jin abin da yace.
“Ga maganinki, maza shanye dika”
“Wai yanzu ba za ka ji tausayina ba Hard Rock?”
Ta ƙarashe tana kama damtsen hannunsa da duka hannayenta biyu, ta maida fuskarta yanayin ban tausayi, har da su ƙif-ƙifta masa ido duk dan ya tausaya mata.
“Gata ɗaya zan miki shi ne kula da lafiyarki, maza ki shanye wannan”
Ya ciro hannunta daga jikin hannunsa, sannan ya buɗe tafin hannunta ya zuba mata ƙwayar maganin, sannan ya ɗanka mata ruwa a ɗayan hannun nata. Ta kalli ruwan da maganin, sannan ta kalle shi.
“Na sha?”
Ta tambaya kamar ba ta san abin da yake nufi ba ke nan.
“Maza sha My Fairy”
“Shikenan, Jesus loves me”
Ta tari aradu da ka ta jefa ƙwayoyin a bakinta ta bi su da ruwa, tana haɗiyewa ta ƙanƙame jikinta saboda yanda take jin ɗacin maganin har ƙirjinta.
“Yauwa Julia May god be with you... zan je na ga Dr Lima, ki haɗa kayanki da na dawo za mu tafi gida”
Ya miƙe ya fita ya barta zaune tana ta binsa da kallon haushin abin da ya mata yanzu. Kamar yanda yace sai da ya je ya biya bills sannan ya nufi office ɗin Dr Lima, a hanya wani mutum ya bige shi ba da sani ba, hakan yasa takardun dake hannunsa suka daɗi.
“Ka yi haƙuri ban kula ba”
Cewar mutumin da ya bige shi ɗin.
“Ba komai”
Ya faɗa yana shirin tsugunnawa domin ɗaukan takardun da suke zube a ƙasa kusa da ƙafafun mutumin, ƙiris ya rage hannunsa ya kai kan takardun wani abu kamar wulgawar walƙiya a cikin hadari ya wuce a idonsa, wani abu da ya faru a can baya, lokacin da suke gidan marayu.
_“Na ji an ce me cin abinci a ƙasa kare ne...”_
Maganar da har ya mutu ba zai taɓa mantawa da ita ba ta kutso cikin tunaninsa, abin sai ya zame masa kamar yanzu yake faruwa, domin a wancan lokacin ma ya tsugunna a ƙasa kamar haka, ya ɗaukan wani cake dake yashe a ƙasa, sannan kamar dai a wancan lokacin, ƙafafun Mateus na kusa da cake ɗin bayan ya gama mitsike shi a ƙasa. Mateus! Wani mutum ɗaya da ya azabtar da rayuwarsa kamar yanda mahaifiyarsa ta masa... Yatsunsa da ya miƙa dan ɗaukan takardar ya dunƙule, sanna ya miƙe ya kalli mutumin dake tsaye har yanzu.
“Kai ya kamata ace ka ɗauko mini su”
Ya nuna takardun dake kusa da ƙafafun mutumin, wani irin kallo ya masa na rainin hankali.
“Ban gane ba”
“Bari na ganar da kai…”
Ya faɗa yana tattare hannun rigarsa alamun zai kai duka, da sauri mutumin ya tsugunna ƙasa ya kwaso takardun, sannan ya miƙe ya damƙa masa su ya taɓa shi ya wuce da sauri yana faɗin ko dai ba shi da hankali ne. A hankali Pedro ya juyo bayan ya bi shi da kallo, ya ci gaba da tafiya. Yana isa office ɗin Dr Lima ya ƙwanƙwasa ƙofa, daga ciki aka ba shi izinin shiga, ya bude kofar kai tsaye ya shiga, ya rufeta lokacin da suka haɗa ido da Dr Lima dake cikin office ɗin.
“Pedro? Ƙaraso ka zauna”
Cewar likitan da fara’arsa, wani guntun murmushi Pedro ya masa sannan ya amsa ya ƙarasa ciki ya zauna a wurin da Dr Lima ya nuna masa.
“Yau na kawo Julia an mata gwajin da kace za ayi… yanzu haka ma tafiya za mu yi, shi ne na ce bari na zo mu yi magana a kan aikin da za a mata”
Dr Lima ya jinjina kansa bayan Pedro ya gama masa bayanin.
“Ai na ganta ɗazu… Kuɗaɗen aikin sun samu ne?”
Kansa ya girgiza yana ƙarawa da.
“A’a tukunna dai, amma ina da tabbacin nan da sati mai zuwa zan gama haɗa kuɗaɗen, tun farko na gaya maka cewar ba zan zuba ido ina kallon Julia ta mutu ta barni ba, zan yi komai domin ceton rayuwarta”
Dr Lima ya yi murmushi.
“Na sani Mr Santos, amma akwai buƙatar ka ƙara ƙaimi wurin haɗa kuɗaɗen nan, domin har yanzu babu abin da ya sauya a ciwon nata, dole a gaggauta mata aiki in ba haka ba za ta iya mutuwa yau ko gobe!”
SA'AD POV.
Murmushi ne kwance kan fuskarsa yayin da yake chat da sabuwar budurwar da ya yi, a kai a kai Aysher dake cin abinci a can gefe
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 14