Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sosai da wanda muke Sch d'aya da kuma wanda suke cikin Family d'in mu , amman bantab'a jin soyayyar su araina ba kamar yadda lokaci d'aya naji soyayyarki , tun had'uwar mu naji kin shiga raina sosai tamkar wacce muka fito ciki d'aya , dan Allah Aysha inaso kibani shawara akan Soyayyata da Khalid , tunsan da mukazo gidan nan naku nida shi har yau ban kuma samun kan sa ba , kullum da irin uzirin da yake bani kwata kwata ko kirana bayayi a waya , gashi in nakirashi nan ma sai ya katse yace aikine yayi masa yawa , kuma yau d'in nan da safe Daddy ya tabba tar min da rashin zaman sa sosai a kasuwa , narasa me ke damun Khalid kwata kwata da ya canza lokaci d'aya , hawaye ne suka taru a idanun Ruma ta rik'e hannun Aysha tam taci gaba da magana " wallahi Aysha ina mutuk'ar k'aunar Khalid shiyasa na damu , Aysha tausayin Ruma ne ya rufe ta cikin ranta tace " tabbas na tausayawa Zuciyarki data kamu da Soyayyar wanda yake Gaibu , a fili kuma ta zame hannun Ruma daga nata tana mik'ewa tsaye , juyawa tayi tana kallon mirrow wanda take hango Rumar ta ciki tana share hawayen ta , a hankali Aysha tace " shawara 'Daya zan iya baki a yanzu itace ki hak'ura da Khalid , kallo ta Ruma tayi sannan tace " meyasa zakice narabu dashi ? Aysha cikin ranta tace " saboda baku dace dashi ba , shi mugune azzalumi ke kuma salaha ce me mutunci wacce tafito daga gidan mutunci , a fili kuma tace " Abinda yasa nace kirabu dashi bawai ina nufin kirabu dashi kidaina kulashi ba a'a inaso kibashi nan da kwana biyu muga yadda za'ayi , indai har cikin kwana biyun nan bai zo wajen ki ba to tabbas Khalid ya canza budurwa sai mu shirya d'amarar k'wato shi , Ruma tayi shuru tana nazarin maganganun Aysha , tabbas Aysha gaskiya tafad'a mata dan Mumyn ta ma sai da tace mata hakan , dan haka cike da gamsuwa ta yarda da shawarar Ayshar ta shirya yin hakan , Aysha ganin ta amince yasa tace " gaskiya Ruma inaso ki rage damuwa dan kin rame sosai , dubi yadda kika fige tamkar wacce tayi jinya , Ruma tayi murmushi sannan tace " wallahi wanda inyi jinya akan yadda zuciyata ke gasuwa , Aysha tayi tsaki sannan tace " wallahi soyayya batayi ba , shiyasa bana d'orawa kaina wannan tension d'in dan bazan iya ba , iya kacina da maza kawai in anshi 'yan canji na inbar su , dan nasan wallahi soyayya b'ata lokaci ne kawai , Ruma ta kalli Aysha tana mamakin kalmar da ta fad'a , a hankali tace " Aysha wai kina nufin kice baki tab'a Soyayya ba ? kuma wanne canji kike karb'a a wajen maza har kika fi fifitashi akan Soyayya ? Aysha tayi murmushi tace " amsar tambayar ki nanan tafe nan bada jimawa ba , dai dai lokacin aka kira sallar Magriba , toilet Aysha ta fad'a tayo arwala tare da shimfid'a sallah ya dan gabatar da sallah , Ruma da yake fashin sallah take shisa bata mik'e ba har Aysha ta idar , duban ta Aysha tayi sannan tace " kizo muje muci abinci dan yunwa nakeji ni , Ruma tace " sai da naci abinci nataho kawai muje kici kirakani hanya zan tafi , Aysha tace " malama muje kawai muci abinci tare , nasan bawani abinci kika ci ba kina wannan damuwar , haka suka fito palor suka samu Gogal ta tashi , kan Dinning Aysha ta kallah aikuwa Gogal gar tagama girki , Ruma tace " gaskiya Aysha bakida murunci nasan girkin nan Mama ce tayi , zama sukayi kan Dinning Aysha na bud'e kular abincin , dambun shinkafa tagani wanda yaji kayan lambu wada tattu sai k'amshi yake , tuni Aysha taja filet ta zuba musu suka fara ci............ [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR HANNU* 🤒🤒 _NA_ *Zee* *MD* *WOMEN WRITERS ASSOCIATION* 📚 (Domin Marubuta Mata ) ✨ (W.W.A) ✨ https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/ *Bisimillahir Rahamanir Rahim* _Page._ 26 Shurun da Aysha tayi ba k'aramin tayar da hankalin Hameed yayi ba , duban ta yayi cike da sallama wa aran sa baza ta soshi ba ko kuma wani ya riga sa , a hankali ya furta " kinyi shuru Aysha plss dan Allah kidaure kice min wani abu wallahi zuciya ta gab take da bugawa , k'wayar idanun sa ta kallah nan ta hango zallar soyayyar ta da k'auna , tabbas dagaske yake yana son ta amman baza tayi saurin yadda dashi ba , dan lokaci da Farouq yazo mata kusan shima da irin wannan salon yazo mata , dan haka haryan zu tarasa yadda ake gano soyayyar gaskiya , duk da idanun Hameed sosai ya fallasa abinda ke cikin zuciyar sa , jikin ta a sanyaye tace masa " inaso kabani lokaci plss komai na yanke zakaji ni , Hameed ya dubi Aysha kamar zaisa kuka yace " inajin kafin lokacin d zaki d'ibar min kibani amsa ta to zaki iyajin zuciya ta ta buga na mutu , dan Allah Aysha ki tausaya min zuciya ta bak'uwa ce a soyayya , akan ki tafara so kuma akan ki zata k'are shi ki tausaya min , Aysha tace " kabani ko zuwa gobe ne sai muyi magana , komai na yanke zakaji kuma kadaina damuwa sosai kar ka rauna ta zuciyar ka , sosai Hameed yaji dad'in kalmar k'arshe da Aysha ta furta masa , bayan sun tab'a hira yayi mata sallama tare da ansar phone number ta...... Hameed na tafiya Khalid yazo ko gida bata shiga ba , yana k'araso wa ya janyo ta jikin sa yana shin shinar ta kamar wani bunsuru , ture sa tayi da k'arfin ta sannan ta shiga magana " haba Khalid a cikin gidan mu fa kake meyasa kake min irin hakan ? yanzu in wani yagan mufa shikenan ka janyo min magana , Murmushi yayi sannan yace " Sorry Babyna kinsan in kina tare dani ji nake kamar ko da yaushe in kasan ce cikin lallausan jikin naki , tab'e baki Aysha tayi sannan tace " ina kayana suke ? Khalid yace " Muje daga motar sai muyi hira daga nan ki d'auko abinki , Aysha samun kanta tayi da jin tsoro batason meyasa bataso Hameed ya ganta tana irin wannan rayuwar ba , a gaskiya baza ta fita tashiga motar Khalid ba gudun kar Hameed yaganta , tunda bai b'oye mata komai ba ya sheda mata a cikin unguwar gidan su yake shima , kallon Khalid tayi sannan tace " bazan iya zance ba yau saboda kaina yana min ciwo , kasan dai yau tunda rana muke tare don haka kayi hak'uri zuwa gobe , Khalid bai so haka ba kwata kwata dan so yayi su shiga motar ko k'irjin ta yasamu yasha zai rage ruwan marar sa da yataru , amman sanin halin Aysha in batason abu to bazatayi ba yasa ya k'yaleta , juyawa yayi ya nufi cikin motar ya d'auko mata ledojin kayan ta , yana kawo mata ta ansa tana fad'in " yakama ta fa kaje wajen Ruma dan tadamu dayawa , Khalid yaja tsaki sannan yace " k'yaleta dan Allah wallahi saboda takurar ta nakashe wayata , Daddyn tama ya kirani nayi masa k'aryar banajin dad'i kwana biyu , Murmushi Aysha tayi sannan tace " yakamata dai ka duba ta ko sau d'ayane , tsaki yaja sannan yace " mezan samu a tare da ita in ba kayan haushi ba , kwata kwata bata wani waye ba kullum kanta a duhu yake , kawai ki share ta zan d'aga wayar ta in ta kira ince mata banjin dadi , Da haka sukayi sallama Aysha ta shige cikin gida abinta , shikuwa Khalid yana tsaye ya k'urawa Mazaunan ta idanu har tashige abinta Sannan yatafi...... Tunda Aysha ta shiga gida tayi sallah sannan ta kwanta , sai dai ko alamar bacci bataji saboda daman ba baccin takeji ba , tunanin Hameed ne ya dami zuciyar ta dan dagaske ta gano zallar k'aunar ta a k'wayar idanun sa , itama tun sanda ya taimake ta taji acikin zuciyar ta ya kwanta mata , Abinda yasa take share sa sabida tana jin tsoron maza , duba da yadda ko wanne namiji in suka had'u dashi bashi da buri sai ya kusan ce ta da iskan ci , amman zata fallasa masa kanta ta sanar dashi ko wacece ita , in har yaga zai amince mata to in kuma jin hakan zai nisan tasu dama ita bata saka akai ba , da haka tagama tunanin ta tare da d'auko wayar ta ta kunna data , tana hawa Whaspp taga tarin sak'onni daga maza kala kala , haka tashiga duba na dubawa tana share wad'an da basu da amfani ...... Ruma tana komawa gida bayan tayi wanka ko abinci bata kallah ba , dan dambun dataci a gidan su Aysha ya k'osar da ita , Mumyn tace t dube ta tace " wai Ruma ko kun samu sab'ani da Khalid ne naga kwana biyu baya zuwa ? Murmushin takaici Ruma tayi sannan tace " ko d'aya Mumy kawai dai bansan me yake damun sa ba kwana biyun nan , Daddy ma yace ko kasuwa yanzu baya zuwa sosai kuma inna kira sa a waya baya d'agawa , Mumy tayi shuru tana nazari kafin tace " tabbas to akwai wani abun amman kiyi masa test ko zaki samu kiji meke damun sa , Ruma tace to Mumy zanyi masa insha Allah , daga haka ta mik'e tayiwa Mumyn sai da safe ta nufi d'akin ta ..... Tana zuwa ta bud'e data ta hau Whaspp , sak'onni ne suka shiga shigowa saboda dad'ewar datayi bata hau ba , duk wad'an da suka mata magana k'awayen tane sai wata Number guda d'aya wacce bta san taba taga kamar anturo mata pic , kamar zata wuce sai kuma ta fasa ta dawo tashi ga , tana shiga cikin pic d'in k'irjin ta sai da ya buga ganin wanda yake jikin pic d'in , Khalid tagani yana shan Nonon wata budurwa wacce bataga fuskar ta ba , zoom d'in hoton tayi ta k'ara tabbatar da ba gizo ida nun ta keyi mata ba , a hankali ta furta " Khalid dama haka kake ? shiyasa ya guje ta saboda tak'i yarda su kauce hanya , kullum burin Khalid yatab'a jikin ta , takan ce masa yayi hak'uri suzama Mallakin juna har gajiya sai yayi da ita , wato bazai iya hak'ura har lokacin da zasuyi aure ba sai da yaje yana neman mata , hawayen dake gangaro wa a fuskar ta tayi saurin gogewa , tabbas Khalid ba mijin aure bane tunda ya kasance fasik'i , tamkar zata kira Aysha sai kuma ta fasa gudun kar ko tayi barci ta dameta , number da aka turo mata sak'on tashiga kira , sai dai akashe ake ce mata haka tai ta gwadawa amman ana sheda mata tana kashe , number Khalid tashiga kira tana ring amman fir yak'i d'agawa , tabbas ta hak'ura da Khalid koda shine autan maza , kuka sosai Ruma take tanajin tsanar Khalid na ratsa jikin ta , ta yanke wa ranta ba wanda zata sanar wa da abinda tagani , kawai dai baza ta k'ara kula Khalid ba itama ta hak'ura da sonshi koda zai kashe ta , da wannan tunanin Bacci b'arawo yayi gaba da Ruma...... Washe gari Aysha na tashi ta d'auki layin da ta turawa Ruma hoto tasa akan waya , tana shiga whaspp taga alamar Ruma taga sak'on da ta tura mata , murmushi Aysha tayi sannan ta d'auki layin datake amfani dashi tashiga kiran Ruma , dai dai kokacin Ruma na zaune a cikin d'akin ta na tunani , koda kiran AYSHA yashigo da sauri ta d'aga tana jin wasu zafafan hawaye na zubo mata , murya a sanyaye tace " Yar uwa dafatan kin tashi lafiya ? Aysha tanajin muryar Ruma tasan kuka tasha kuma tasan wannan pic d'in data gani ne zai sa ta kukan , Aysha tace " lafiya lau natashi 'Yar uwa sai dai kuma tunda naji muryar ki nasan 'Yar uwa ta tana cikin damuwa , ina fatan ba akan wannan Guy d'in kike damuwa , plss 'Yar uwa banason kidunga saka damuwa aranki , haka kawai ya saka miku ciwon zuciya yazo ya gudu ya barki , aikuwa Ruma me jiran k'iris tuni tashiga rera kuka tamkar 'yar goye , kukan da Ruma keyi har cikin zuciyar Aysha , dan har ga Allah itama tana k'aunar Ruma , dan haka takeso tayi ta rabata da Khalid ko hankalin ta ya kwanta itama , nan Aysha ta shiga kwantar wa da Ruma hankali har tasamu tayi shuru , duk da Ruma bata shedawa Aysha abinda yasa ta kuka ba , itama kuma bata tambaye ta ba tunda tagane sak'on ta datakeso ta isar ya isa , nan sukayi sallama tare da yi mata alk'awarin itama zatazo gidan nasu gobe , ...... Bayan sungama waya da Aysha Ruma tasake gwada number da aka turo nata pic , ga mamakin ta sai taji number ta shiga ba bata lokaci , sai da ta kusa katsewa sannan aka d'aga tamkar ba'ason magana , Ruma tace "naga sak'on da aka turomin da wannan Number , sai dai inaso in sanar miki ko kad'an ban damu ba , shida ma namiji ai inyayi abu ado ne agaresa kuma hakan bazai tab'a mana soyayyar mu ba , inaso kisani in so kike ki rabamu to ina me tabbatar miki da kinyi kad'an , yanzu nafara son Khalid har sai yazamo mijina , Murmushi taji anyi mata cike da gadara da isa sannan aka furta " haba 'yan mata ki kama bakin ki , ai Khalid ya ruga da yayi miki nisa sai dai ki hangesa , kuma wannan pic din ba komai bane akan abinda muke yi da Khalid , inhar kina so ki tabbatar da waye Khalid to gobe da misalin k'arfe biyar na yamma kizo Taheer gate place hotel zaki abinda zai baki mamaki , kitt aka kashe wayar batare da ta yi magana ba , Ruma sake bin wayar tayi amman sai jitayi har ankashe , badan tanason Khalid tace haka ba kawai tanaso tagane ko shiri ne ko kuma gaske ne , amman lallai gobe sai taje Taheer Hotel taga abinda akeson tagani , dan itama tanaso takama Khalid da hujja wacce zata tabbatar masa da tasan waye shi , ......... *Comment* plss *'Yar Mutan Kanawa* _Ce_ 🌹💞💔 [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR HANNU* 🤒🤒 _NA_ *Zee MD* *WOMEN WRITERS ASSOCIATION* 📚 ( Domin Marubuta Mata ) ✨ (W.W.A) ✨ https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/ *Bisimillahir Rahamanir Rahim* _Page._ 29 Tabbas Jabir ya wuce duk tunaninta , Mamakin yadda yasan sirrikan ta tashiga yi , koda yake bazatayi mamaki ba duba da tun farko dama tasan shu'umine sosai , shiyasa tun farko taji jinin ta bai had'u dashi ba amman duk da haka sai bibiyar ta yake , yanzu gashi yana neman janyo mata Gogal tayi fushi da ita , kuma hakan ba k'aramin tashin hankalin ta bane dan ko kad'an batason Gogal tayi fushi da ita , duk duniya bata da kowa sai Gogal itace gatan ta itace duk wani farin cikin ta , da ita tabud'i ido tun tasowar ta dan haka dole ta guji duk wani abunda zai b'ata ranta , gashi Dr. Yace mata tana gab da kamuwa da matsala a kwakwalwar ta , duk da Aysha ta k'udur ta aran ta bazata k'ara aikata zina ba tunda har shirinta na k'arshe yau takeson kammala shi , Amman tuni taci Alwashin tabbas saita koyawa Jabir Hankali dan haka itama zata bibiyesa batare da yasani ba , ...... Wayar tace tashiga ruri ta duba dan ganin me kiran nata , Khalid ne haka ta katse batare da ta d'aga ba , wata tsanar sa ce ke nunkuwa a zuciyar ta duk sakon na duniya , zama tayi a bakin gadon ta tashiga tunanin yadda zata samu wacce zata tura Hotel anjima , tabbas tasan Ruma zataje Hotel d'in dan ko iya wayar da sukayi ya tabbatar mata da hakan , whaspp d'in ta ta bud'e tashiga wani group datake ciki , duk wad'an da suke group d'in *'Yan Hannu ne* dan daga masu yin lez sai masu neman maza , duk da bata magana a group d'in amman sukan biyota Prvt tallata Hajar su , duba Contact d'in su tashiga yi d'aya bayan d'aya , tsayawa tayi a Contact d'in wata tsaleliyar budurwa me suna Leeemah , take Aysha ta kunna data tare da shiga direct Message tace mata Hy , aikuwa taci sa'a Leeemah na kan online tuni ta dawo mata da Reply na Hy My dear you'r welcome , Aysha tace " kozan iya magana dake in babu damuwa ? Leeemah tace " bawata damuwa Uwar ruwa ina jinki , sunan da Aysha ke amfani dashi shine Uwar ruwa , Aysha tace wani aiki nakeso zakimin yaud'in nan inba damuwa ? Leeemah tace " fad'i komai kikeso kan ki tsaye zanyi miki shi , Aysha tace yanzu dai kina wane gari dan inji , Leemah tace "Ina garin Kano unguwar Gadon k'aya , Aysha tace " gud inaso kimin wani aiki anjima a Hotel d'in Taheer gate palace , Leemah tace angama Uwar Ruwa fad'i yadda aikin zai kasance , Nan Aysha ta sheda mata tana so su had'u a Hotel d'in k'arfe hud'u da rabi dai dai , daga nan zatayi mata bayanin yadda zata yi aikin , take Leemah tayi Na'am nan suka gama magana , Aysha kafin ta kashe datar ta ta kuma nemo Number Ruma ta tura mata voice d'in muryar Khalid , wanda yake fad'in bason ta yake ba kawai saboda kud'in Mahaifin ta yake kulata , amman da zarar ya aure ta yasamu kud'i to zai auri kalar matar da yakeso , harda yadda yake cutar Mahaifin Rumar a kasuwa batare da yasani ba , duk voice d'in da sukayi sai da Aysha ta turawa Ruma sannan a k'asa ta rubuta " ko zaki iya sheda wannan muryar waye ? daga haka ta kashe datar ta ta sauka gaba d'aya daga kan Whaspp d'in ...... Wajen k'arfe Uku Aysha ta shirya cikin shigar ta ta kamala tafito , d'akin Gogal tashiga tasa meta a zaune tana jan cazbi , durk'usawa Aysha tayi sannan tace " barka da wannan lokacin Gogal ya jikin naki ? ba yabo ba fallasa Gogal tace jiki da sauk'i , Aysha tace "Allah yak'ara miki lafiya da nisan kwana me amfani , Gogal bata amsa da Ameen d'in data saba ba tayi shuru , Aysha takuma risinawa tace " ga Abinci can a kan Dinning nadafa miki ni zan wuce makaranta , Gogal batare da ta dube ta ba tace " Allah ya kiyaye Aysha ta mik'e ta fita...... Koda ta fito sai da tagama dube duben ta bataga kowa ba sannan ta kama hanyar fita bakin titi , wayar ta ta ciro tashiga kiran number Leeemah , tana d'agawa tace mata gatanan tana shirin fitowa itama , nan Aysha ta kashe wayar sanan ta kira number Khalid , yana d'agawa yace " Sweet yau kwata kwata kin ki bari naji muryarki dayawa , muna fara waya kike katsewa kodai nayi laifine ? murmushi Aysha tayi sannan tace " babu laifin dakayi yau nayi busy ne sosai , to Babyna ina fatan baki gaji da yawa ba dan kinsan yau zan danneki dayawa , Aysha wani takaici taji ya kamata amman sai ta dake tace " bangaji ba My Baby kasan akan ka zan jure komai , Khalid cike da murna yace " dama zakiyiwa Uncle d'inki dabara da munkwana tare mufaran ta ran juna sosai , Aysha tace " karka damu zan gwada nagani ko zai barni , Khalid har wani shauk'i yake yana ce mata shifa tun yanzu zai shirya dan ya matsu da yawa , itama tace masa yanzu zata shirya taje takama musu d'akin tunda ya turo mata kud'in , nan sukayi sallama Aysha tana duban wayar tana murmushin mugunta..... Ruma wajen k'arfe uku ta d'auki wayar ta tana shiga Whaspp , sak'onni ne suka shiga shigowa cikin wayar a ciki ta kuma ganin number da aka turo mata pic d'in Khalid , hannun ta har rawa yake wajen bud'e sak'on taga me suka sake turo mata , tana bud'ewa taga Voice guda uku ajere , tuni ta bud'e bayan ta karanta rubutun k'asa , Muryar Khalid tashiga ji yana bai yana yadda yake shirya komai , jikin ta har tsuma yake tanajin wata iriyar tsanar Khalid , bayan duk tagama ji ta mik'e da saurin ta ta nufi d'akin Mumyn ta , tana zuwa ta kunna mata Voice d'in Muryar Khalid itama tashiga ji , bayan tagama ji ta kamo mata hotunan da aka turk mata tare da sheda mata ance k'arfe Biyar taje Hotel d'in Taheer taganewa idon ta komai , nan Mumyn ta tashiga salati tare da cewa bari takira Daddy ta sanar masa dan suma suje Hotel d'in dan tabbatar wa , aikuwa koda suka sanar masa cewa yayi sutaho Hotel d'in su had'u acan dan shima dama yagaji da abinda Khalid d'in keyi masa na rashin zuwa kasuwa , ashe ashe akwai abinda ya taka shiyasa yake haka , ..... Tuni Ruma da Leeemah sun Bayyana a Hotel d'in Taheer , tana gama kama d'aki ta nemi Number Ruma ta tura mata Room number d'akin , ciki suka shiga nan ta tsarawa Leeemah komai yadda zata tafiyar dashi , basu dad'e da zuwa ba saiga Khalid ya iso sai faman zabga k'amshi yake , akan idanun Ruma da iyayen ta ya fito daga motar batare da yagan suba ya nufi Reception......... *kumin Comment kuga ruwan Typing*✍🏻😜😝😝 [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR HANNU* 🤒🤒 *NA* *Zee* *MD* *WOMEN WRITERS ASSOCIATION* 📚 ( Domin Marubuta Mata ) ✨ (W.W.A) ✨ https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/ *Bisimillahir Rahamanir Rahim* _Page._ 27 Washe gari tunda safe Aysha take shirya yadda Khalid zai shiga hannu , tunowa tayi da jiya yace mata 2m .A account d'in sa kuma sunje shopping ta cinye masa 1m da dubu d'ari uku , ya siya mata gold sark'a da kuma zobuna , yanzu in ta auna cikin Account d'in Khalid saura dubu d'ari Bakwai , dole yanzu zata shirya cinye sauran canjin daya rage masa , dan bataso ko canji ta bar masa bare yaji dad'in cutar wasu agaba , tanaso ta maida shi talakan k'arfi da yaji tunda dama motar dayake hawa ta gidan su Ruman ce Yake d'auka , wata dabara ce ta fad'o mata da sauri ta d'auki waya zata kira Khalid , wata Number tagani ana kiranta da ita , da kamar bazata d'aga ba sai kuma wata zuciyar tace d'aga kiji ko waye , d'agawa tayi tare da yin shiru batayi magana ba , daga cikin wayar taji muryar Hameed yana fad'in Assalamu Alaikum , muryar tasa tuni ta ratsa duk wani sassa na jikin ta , idanuwan ta ta lumshe sannan tace " wa'alaikas salam , Hameed wata ajiyar zuciya yaja dan duk a tunaninsa baza ta d'aga wayarsa ba amman sai gashi ta d'aga , My Angel dafatan kin tashi lafiya kuma ina fatan dai ba bacci kike na tashe ki ba ? Murmushi Aysha tayi karo na farko a rayuwar ta dataji 'Da namiji ya burgeta , kuma wannan shine karo na farko da aka tab'a kiran ta tare da tambayar ta tashi lafiya , duk Namijin da zai kira ta sai dai yace mata A inah zasu had'u ko kuma yana Hotel kaza tazo tasa mesa , baruwan su da tambayar lafiyar ta su dai kawai burunsu tazo su aikata Fasik'an ci , karo na biyu dataji ta tsani zina dan bata da wata riba sai dai k'arshe ma ka had'u da tarin dana sani , a hankali ta furta masa " natashi lafiya kaima ina fatan hakan daga gareka , Murmushi Hameed yayi har Aysha najiyo sautin yace " lafiya lau nima natashi sai dai zuciya ta datake d'auke da farga da tarin k'alubale , Aysha ta d'an fito da ido a tsorace tamkar yana gaban ta tace " wanne irin Fargaba da k'alu bale kuma ? murmushi yayi sannan yace " Zuciya ta tana jiran amsar da zata samu daga gareki kinga kuwa dole na kasance cikin fargaba , Murmushi tayi sannan tace " kar kadamu komai zai zo da sauki kawai dai kajira lokacin yayi , Hameed yace " lokaci ya kusa tunda zuwa anjima zanji komai dan haka yau kisa aranki kina da mara lafiya mai buk'atar tallafin ki , murmushi ta kuma yi tace " sai najika ta kashe wayar batare da tajira yace mata wani abun ba , kallon wayar tayi tamkar me gano Hameed d'in aciki tace " in na biye masa sai yaja zancen da hira har nazo na furta abinda zuciya ta bata yanke ba , ....... Number Khalid ta nemo sannan ta shiga kiran sa , sai dai har ta katse bai d'auka ba ko baya kusa da wayar ko kuma yana bacci , ajiye wayar tayi sannan tafito palor dan ganin ko Gogal ta fito , bata gan ta ba hakan yasa ta shiga kitchen ta hau girka musu abinda zasuyi kari dashi , Kunun gyad'a ta dama tare da soya musu dankalin turawa , tana gamawa ta d'auko ta ajiye akan dinning sanna ta d'auki na Habu ta mik'a masa , koda ta shigo cikin d'akin ta ta koma sannan ta fad'a wanka toilet

Chapter 9 of 13