abin yin gulma , tabbas zai koyawa Aysha hankali tunda duk itace sanadin hakan ,
Yana fita daga motar yayi b'angaren sa duk ransa a dagule.......
Hameed tunda ya koma k'asar America yakasa komai sai tunanin Aysha , daga ya rufe
idanun sa itace keyi masa gizo , tunda yadawo kwata kwata abokan aikin sa suka kasa gane
kansa , Aleeya budurwar sa wacce suke aiki tare babu irin tambayar da batayi masa ba akan
canzawar sa amman yace bakomi , kullum in yadawo daga wajen aiki bashi da burin daya wuce
ya keb'e kansa yana tunanin Aysha , abinda ke damunsa rashin sanin yaya take da kuma
rashin dabara dabaiyi ba ta anso number wayar ta , yanke shawara yayi na tahowa Nageria
kawai kozai samu sauk'i inya ganta.......
Tunda garin Allah ya waye Aysha taji batason yau ko soro ta lek'a , d'akin ta ta koma ta
kwanta tana danna wayar ta , kiran Alhaji Na Lamma ne ya shigo tana kallo amman tak'i
d'agawa , sai dayayi mata kira biyar amman tak'i d'agawa , daya ke datar ta a bud'e take sai
ganin test d'in sa tayi ya shigo ta whassp , nan ma ta bud'e tagani amman tak'i masa reply ,
Daga k'arshe ma ta kashe datar ta ta ajiye wayar tayi kwanciyar ta abinta , tana kwance taji
yaro ya shigo yana fad'in " wai ana kiran Babyn dad'i a waje , a zabure Aysha ta mik'e tana
fad'in " nashiga uku waye zai min wannan aika aika haka ? bata gama tsora ba sai dataji
muryar Gogal na fad'in " wace ce kuma Babyn dad'i agidan nan ? kaje kace banan gidan bane
kaji wannan suna haka mara amfani da ma'ana kuma , haka tai ta fad'a har yaron yafita , Aysha
jitayi jikin ta na rawa tamkar mazari da sauri ta d'auko hijab tasaka zata fito takuma jin yaron
yadawo yana fad'in " wai ance anan gidan take kuma tasan kanta , Aysha tayi saurin fitowa tana
fad'in " kai wannan wanne irin abune haka ? muje naga wanne d'an iska ne yake mana wannan
abu haka , Gogal itama ta fito tana fad'in " nima dai bari nazo naga waye me wannan aike haka
da bashi da mutunci , Aysha da sauri ta dakatar da Gogal tana fad'in " bari naje nagano ki koma
kawai basai kin fito ba ....
Aysha na fitowa waje taga Jabir tsaye ya hard'e cikin k'ananun kaya abinsa , yana ganin
fitowar ta ya fara wani shu'umin murmushi yana kallon ta , tana k'arasowa a fusace tace " wai
kai me kake nema a cikin rayuwa ta haka da kake damuna ? Jabir yayi murmushi sannan yace
" kan ki nake nema inaso ki anshi soyayya ta ki huta dani kawai , tsaki Aysha taja sannan tace "
idan kuma ban ansa ba fa ? Jabir ya matso gaf da jikin ta yace " in baki ansa ba kuma kin san
sauran zancen , dan duk duniya sai tasan wace ce ke , ta yadda kike shigar mutunci kina cin
zarafin hijab da nik'af , kina janyowa ana b'atawa masu irin wannan shigar taki suna , inaso
kisani zan fad'a miki hanyoyin da zaki bi dan bin umarnina ki zauna lafiya , Aysha tace " inaso
kasani ko kafita daga cikin rayuwata ko kuma insa afitar mun dakai , kuma soyayyace bazan
tab'a yin ta dakai ba saboda kaima ba soyayyar Allah zakayi min ba , murmushi Jabir yayi
sannan yace " kin tab'a gani anso karuwa soyayyar Allah ne ? ai tsakanin ka da ita kawai ka
murji jikin ta ka shige kabarta a wajen , ni bani da kud'in da zan biyaki in murji jikin ki amman
inaso ko taya ya sainayi amfani dake , Aysha tace " hakan ba k'aramin kuskure zakayi ba kuwa
a cikin rayuwar ka , tana gama magana ta juya zata tafi taji yace " Babyn dad'i ki saurari
tambayoyin da Kakarki zata miki akan wannan sunan , dan sai tasan komai game da rayuwar
da kikeyi har wannan motar da aka baki kika yi mata k'arya , Aysha duk da tanajin tsoro
amman haka ta dake bata nuna masa ba har ta shige cikin gida abinta..........
*In naga Comment inci gaba sannan in k'ara yawan typing*
_In kuma bakuyi ba intafi hutu sai bayan sallah ajini_
*'Yar* *Mutan Kanawa* _Ce_ ππΉ
[11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR* *HANNU*
π€π€
_NA_
*Zee* *MD*
*Hamdala* *Writer's* *Association* πͺ
https://www.facebook.com/111403834371046
β¨β¨ *{{* *H.W.A* *}}*β¨β¨
*Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim*
_Page._ 14
Alhaji Na Lamma jikinsa har rawa yake wajen neman number Farouq , goge zufar
dake zubo masa yayi tare da danna kiran number Farouq , yana d'agawa yace " Daddy na
anso komai gani nama taho yanzu , Alhaji Na Lamma da sauri yace " maza ka juya ka koma
mata da dukkan abinda ka anso , Farouq a tsorace yace " what Daddy in koma mata dasu kace
fa ? Alhajin yace " Ae maza ka juya kamaida mata dasu nace , yana gama fad'ar haka ya
kashe wayar yayi cilli da ita kan kujera ya mik'e yana zagaye d'akin nasa , tambaya ya shiga
yiwa kansa " taya akayi wannan yarinyar ta shammace shi haka batare da yasani ba ? tabbas
duk yadda zaiyi sai ya raba ta da wannan video ko zai samu sukuni , mutuk'ar wannan video
yana tare da ita to zuciyar sa zata kasan ce cikin zullumi , haka yashiga kaikawo goge zufar
dake zubowa jikin sa , duk ac dake aiki a d'akin nasa sai yaji kamar ba su saboda zafin dayake
ji.........
Farouq juyawa yayi da kan motar yakoma gidan su Aysha , Farouq mamaki ne yakamashi
ta yadda akayi Daddyn nasa yace akoma mata da komai , yana tafe yana nazarin wane irin Abu
Aysha tayiwa Mahaifin nasa har ya sauko haka ? bai wani dad'e ba ya k'araso k'ofar gidan su
Aysha , yana zuwa ya fito daga motar ya zo k'ofar gidan yashiga bugu da k'arfi tamkar zai
karya musu k'aure , Aysha dama tana zaune tana jiran zuwan sa , tana jin yana wannan bugun
ta mik'e a hankali tayo hanyar soron gidan nasau , tana zuwa ta zare sakata tana duban
Farouq d'in , shima ita yake kallo cikin kwayar idon sa ta hango zallar tsanar ta , itama kuma
anata idon hakane dan ta tsani Farouq sosai , wurga mata takardun yayi tare da mukullun motar
ya juya zai tafi , Aysha tace " haka kake yiwa uwarka kenan inkaje bata abu ? a fusace Farouq
ya juyo tamkar d niyar marin Aysha wayar sa ta shiga ruri , dubawa yayi yaga sunan Daddyn sa
ya d'aga , yana d'agawa Alhaji Na Lamma yace " inaso kabata hak'uri akan abinda kayi mata
sannan in zaka bata hak'urin inaso ka rissina tamakar yadda kakeyimin , Farouq wani abu yaji
yatsaya masa a k'irjin sa tamakar ya had'iyi zuciya ya mutu , baice komai ba ya kashe wayar
yana duban Aysha yace " menayi miki haka kika zab'i kiyi min hukunci ta wannan hanyar ?
nabaki hak'uri akan abinda nayi miki nida abokaina amman kink'i saurarena , kuma ko a lokacin
da nayi miki wannan abu ai naji ba a cike kike ba , kinga daman ked'in *'Yar Hannu* ce ,
murmushi Aysha tayi sannan tace " kayi abinda Mahaifinka yace kayi yanzu katafi , kasan dare
ne yanzu hakan ba rana ba bare ka tsayar dani , Farouq ya rissina tamkar yadda mahaifinsa ya
umarce sa yabata hak'uri sannan ya shige yabar k'ofar gidan da tarin tsanar Aysha , da kallo
Aysha ta bishi tana murmushi sannan ta maida k'ofa ta rufe tayo cikin gida abinta......
Washe gari
Aysha tana tashi tagama had'a musu abin kari , Bayan sun karya tayi wanka ta fito sannan
tacewa Gogal " tanaso taje gidan da zasu koma d'in taga meye babu a ciki , Gogal tace " ai da
samo mana masu kura kikayi suka zo suka dib'i kayan inyaso basai mun nemi komai ba ,
Aysha tayi murmushi tana duban Gogal tace " ai wahala zasu sha masu kura Gogal sai dai
motar , amman bari naje dai nadawo sai muga yadda za'ayi , shigar ta ta tayi wacce tasa ba ta
rufe ko 'ina na jikin ta tafice daga cikin gidan....
Tayi nisa a tafiyar ta taji ance " Malama Aysha *'Yar* *Hannu* , ko bata waiwaya ba tasan
Jabir ne , dan yanzu kusan shine babbar matsalar ta a cikin rayuwa , duk inda tasa k'afa tasan
yana bibiyar ta amman dole tayi maganin sa tun kan dare yayi mata , wata dabara ce ta fad'o
mata kawai ta juyo tana murmushi tace " Malam Jabir manyan gari yakake ? Jabir cike da
mamaki yace " lafiya lau nake kema ina fatan hakan kike ? Murmushi tayi sannan tace " gashi
kuwa kagani , Jabir ganin Aysha ta saki jiki dashi yasa yafara tunanin ko barazanar da yayi
mata ce yasa taji tsoro , cike da jin shi wanine yace " ina zuwa haka manyan gari ? murmushi
Aysha tayi sannan tace " wata k'awa tace baban ta yarasu shine zanje mata gaisuwa , Jabir
yace " Ayya Allah yajik'ansa in kindawo anjima sai muyi magana ko ? Aysha tace " babu
damuwa sai nadawo d'in , Allah yadawo dake lafiya ya juya yabarta ta nufi titi tana dariyar
mugunta......
Gate hause d'in Alhaji Na Lamma Aysha ta nufa , tana zuwa tasamu me gadin gidan a
k'ofar gate a tsaye yana jin redio , tana zuwa tayi masa sallama ya amsa yana kallon ta tamkar
wanda yaga wata halittar daban , Aysha tace " inason shiga gidan nan dan zan duba wani abu ,
Megadin ya dube ta sama da k'asa sannan yace " baiwar Allah taya zanbarki ki shiga cikin gida
batare da nasanki ba ? kuma koda nasanki taya zan bud'e miki Alhalin Alhaji bai cemin in bud'e
miki ba ? d'age nik'af d'in Aysha tayi tana kallon sa sannan tace " kashiga ka gayawa Alhajin
kace me gidan ce tazo tanason suyi magana , mai maita wa Megadi ya shiga yi yana fad'in "
Me gidan ce tazo , haka ya bud'e gidan da saurin sa yatafi isarwa da Alhaji sak'o.....
Alhaji Na Lamma yana zaune a falor sa yana shan ruwan lipton yaji shigowar me gadi , izini
yamasa yashigo suka gaisa , nan ya sheda masa zuwan Aysha da kalmar datace ya fad'i ,
Alhaji Na Lamma najin ance Me gidace tazo ya mik'e da sauri tamkar zai tuntsira yayo waje ,
Me gadin nasa ma acikin falor yabarshi tsaye baki bud'e , cikin ransa yace " wannan wacce
shu'umar yarinya ce tasa Alhaji wannan rawar jiki haka ? shima biyo bayan sa yayi suka fito
wajen ........
Aysha na tsaye abinta sai k'arewa unguwar kallo take , cikin ranta tashiga yaba tsarin
unguwar na rashin hayaniyar mutane , ga kuma gidaje masu kyan gaske tamkar a turai layin ,
muryar Alhaji ce ta katse ta da yace " sannu da zuwa Hajjaju , Aysha ta bisa da kallo daga shi
sai gajeran wando kana gani kasan baisan ya fito ba , dariya ce taso kama Aysha amman ta
maze cimin ranta tana fad'in " tsohon banza kawai maganin ku ai , dan kuna da kud'i sai
kurunga amfani da hakan kuna lalata yaran mutane , kana da Matanka amman saika had'a da
bibiyar matan waje , a fili kuma ta amsa masa ciki ciki tamkar batason maganar , bud'e mata
k'aramar k'ofar yayi yace " bisimillah mushiga daga ciki ko sai muyi magana , shigewa Aysha
tayi batare da tace dashi uffan ba abinta.......
Sai data shiga falor tasamu guri ta zauna tana kuma k'arewa falor kallo , tabbas gidan
yayi kyau sosai dan yagama burgeta shiyasa takeson gidan , Alhaji Na Lamma shima zama
yayi yana duban ta cike da kulawa , Aysha ta gyara murya tace " anjima nakeso mudawo gidan
nan shine nazo nagayamaka kayi sauri ka kwashe duk wasu abubuwanka masu muhimman ci
daga ciki , sanin kan kane nida Kakata zamu dawo cikin gidan kuma batasan yadda akayi
nasamu gidan ba , Alhaji Na Lamma yace " duk yadd kikeso haka za'ayi yanzu kuwa........
[11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR* *HANNU*
π€π€
_NA_
*Zee* *MD*
*Hamdala* *Writer's* *Association* πͺ
https://www.facebook.com/111403834371046
β¨β¨ *{{* *H.W.A* *}}*β¨β¨
*Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim*
_Alhamdulillah_
*Am* *Back* β
_Page._ 16
Aysha sosai ta maida hankalin ta tana kallon Farouq , duk da bawata maganar
arzik'i yake mata ba ba laifi ta fahimci wani abun , kusan awa d'aya suka kwashe yana nuna
mata sannan suka d'auko hanyar dawowa gida......
koda suka zo k'ofar gate d'in gidan ya tsaya batare da ya shiga ba , itama batace masa
uffan ba ya sauka daga cikin motar yayi tafiyar sa , fitowa Aysha tayi taje ta k'wank'wasa k'ofar
gidan , Habu ne ya zo da sauri ya bud'e mata yana fad'in " sannu da zuwa har kundawo kenan
? Aysha tayi murmushi tace " wallahi har mundawo ashe in mutum ya nutsu ma babu wuya
koyan motar , murmushi Habu yayi yana fad'in " Allah yasa anfara a sa'a Aysha tace Ameen......
Komowa tayi ta shiga cikin motar ta zauna sannan ta kunna tashigar da ita ciki , a laifi
sosai Aysha tana da basira , shiyasa ko a makaranta malaman ta suke alfahari da ita .....
Jabir sosai yake zuwa club club wai ko Allah zai sa yaci karo da Aysha , sai dai kwata
kwata bai san zuwa club baya cikin layin Aysha ko kad'an , ganin yajera kwana biyu yana
yawon neman ta yasa yagaji ya hak'ura da zuwa , sai dai sosai Aysha tabashi mamakin yadda a
wannan karon tafishi wayo , tabbas duk inda take a fad'in garin nan sai ya nemo ta , zai nuna
mata shima ba kanwar lasa bane ......
Kwata kwata Aysha ta manta da wani Jabir wanda tayiwa lak'ani da d'an sa'ido ,
Rayuwar su sukeyi ita da Gogal da Habu cikin kwamciyar hankali , gashi kullum sai Farouq
yazo sunfita koyan motar , yanzu haka har ta iya sosai amman tak'i tabarsa ya huta....
Gogal sosai ta murje tayi wani kyau abinta , abinka da farar fata tamkar katab'a ta jini ya
fito , kullum tana cikin ac ga kwana cikin ac ba ruwan ta da sauro , sosai Aysha take kulawa
dasu wajen cin abinci medadi , duk da yanzu hankalin Gogal yana kan Aysha akan yadda taga
tana kashe kud'i , kwata kwata Aysha ta manta da yadda take bida komai a b'oye kar Gogal
tagani , yanzu har wayar ta babba ta bayyana ta tana fito da ita , yauma kamar kullum suna
zaune a falo suna kallo Gogal hankalin ta nakan Aysha wacce ke danna wayar ta tanayin chat
d'auke da murmushi a fuskar ta , ganin kwata kwata ta maida hankalin ta ga waya yasa Gogal
yin gyaran murya tace " wai Sayyada yaushe kika samu wannan Aba haka ? Aysha sai da taji
hanjin cikinta ya ya mutsa kafin tayi ta maza tace " Batawa bace Gogal , ta Asma'u k'awar nan
tawa ce na aro ta , kinsan ina koyan motar to dole sai da irin wayoyin nan zan iya , Gogal
dayake ba sanin kai tayi ba tuni Aysha ta zage tashiga shirya mata k'arya , Gogal duk da ta
yadda da Aysha d'ari bisa d'ari amman sai tasamu zuciyar ta dayin rawa akan Maganar Ayshar ,
haka dai tabar abin aranta batare da takuma cewa Uffan ba.......
Hameed kusan kullum sai yaje Unguwar su Aysha , amman kullum indai yaje zaisamu
gidan yadda yabarshi , yauma yana zuwa hakan ce ta kasance kamar kullum , tsayawa yayi
yana nazari sai ganin wani yaro yayi zai wuce , kiran sa yayi yaron yazo Hameed yace " dan
Allah k'anina ko kasan inda masu gidan nan suka tafi ? yaron yace " wallahi tashi sukayi kuma
bansan inda suka koma ba , Hameed ya maimai ta kalmar tashi sannan yace " kozaka shiga
wancan gidan ka tambayo min inda suka koma , yaron ya kalli gidan sannan ya kalli Hameed
yace " ai gidan mune kuma bamu san inda suka koma ba , nan Hameed ya zaro d'ari biyar
yabawa yaron yana fad'in " ungo to nagode kaji , yaron ya ansa yana godiya shikuma ya juya
yanufi motar sa yatafi ....
Alhaji Na Lamma yana zaune a falon sa na sama yana nazarin wasu takardu , Farouq
ne ya shigo d'auke da sallama abakin sa sannan yasamu waje ya zauna , gaida Mahaifin nasa
yayi cike da girma mawa sanna yace " Daddy ina son yin magana dakai , Alhaji Na Lamma
yadubi d'an nasa wanda yaga ya rame sosai yace " ina saura ranka , Farouq yanisa sosai
sannan yace " Daddy dan Allah meye had'in ka da wannan yarinyar da har take irin wad'an nan
abubuwan ? murmushi Alhaji Na Lamma yayi irin nasu na manya yace " cool down my luvly
son babu abinda ya had'amu da ita kawai dai kabar wannan maganar banason kadamu ,
Farouq sosai yaji rashin dad'in yadda mahaifin nasa yake neman mai dashi k'aramin yaro ,
duban Daddyn nasa yakuma yi sannan yace " a gaskiya Daddy bazan iya hak'ura ina kallon
k'aramar yarinya tana juya ka yadda takeso ba , zan je nasa meta ko wacce za'ayi wallahi sai
dai ayi , mik'ewa Farouq yayi a fusace zai fita Alhaji Na Lamma yayi saurin dakatar dashi da
cewa " Farouq karka kus kura kace zakaje wajen Aysha , ko kamanta laifin da kayi mata kai da
abokan ka ne ? shuru Farouq yayi tare dayin k'asa dakai , cikin zuciyar sa yafara fad'in " lallai
wannan yarinayar ta wuce tunanin sa wato har ta sanar da Daddyn sa abinda suka mata ,
baigama tunani ba yaji Daddyn nasa nacewa " inaso kafita daga sabgar Aysha , tsakanin ka da
ita koya mata motar sai kuma in ta buk'aci kayi mata wani aiken , dan haka ka kiyaye banson
insake jin wani abin ya b'illo , k'asa dakai Farouq yayi sannan ya amsa da to ya fice daga
d'akin......
Da kallo Alhaji Na Lamma ya bi bayan Farouq , cikin ransa yace " laifinka yafi yawa sosai
agun Aysha fiye da nawa laifin , nasan saboda tasan kai d'ana ne tazab'i ta rama abinda kayi
mata ta wannan sigar , tabbas nasan dole wata rana Dole zata gyaru tadaina rayuwar da take ,
Allah yagani inasonta da aure a yanzu inda zata amince min amman nasan baxai yuwuba ma ,
Gashi ta sabamin da jikinta kuma haryanzu banji jiki me dadi irin saba duk irin neman matan
danayi.....
Hameed yau tunda yatashi yake shaawar zama a k'ofar waje dan ya k'arewa unguwar
tasu kallo , kujera ya fito da ita ya zauna tare da lapton d'insa yafara danna wa , dai dai lokacin
Aysha tayi shigar ta ta hijab har k'asa tare da saka Nik'af ta fito wai zataje makaranta , tana
fitowa tafara kalle kalle tamkar me neman wani abin , dai dai lokacin Hameed ya d'ago da
kansa yana duban saitin wajen da Aysha take , da sauri ya mik'e yana kallon inda take sosai ,
cikin zuciyar sa yafara magana " tabbas wannan in ba Aysha bace to 'yar uwar tace , dan irin
yadda Aysha take shigar ta itama wannan d'in haka takeyi , gashi yanayin jikinsu d'aya anya
bazaije yaga fuskar taba ko Ayshar sace ? ......
[11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR HANNU*
π€π€
_NA_
*Zee* *MD*
*Hamdala* *Writer's* *Association* πͺ
https://www.facebook.com/111403834371046
β¨β¨ *{{* *H.W.A* *}}*β¨β¨
*Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim*
_Alhamdulillah Ala Kulli Halinππ»_
_Page._ 15
Aysha tace " wannan me gadin inaso ka sallamesa dan bana buk'atar sa , sannan
kajawa Farouq d'anka kunne lallai karya kus kura ya tako mana cikin gida , Alhaji Na Lamma
tana magana yana kallon ta tamkar ya janyota ya shak'eta ta mutu kowa ya huta , tamkar Aysha
tasan me yake ayyana wa tace " kanajin tamkar ka shak'eni na mutu kowa ya huta ko ? to
kasani ko ka kashe ni dole bazaka tsira ba , dan komai da mukayi k'awata tasani kuma tana da
videon komai a gunta itama , murmushi Alhaji Na Lamma yayi sannan yace " meye ya kawo
maganar kisa kuma Allah ma ya kiyaye ni ko kiyashi ban tab'a kashewa wa bare kuma mutum ,
mik'ewa Aysha tayi tana nuna masa ko ajikin ta maganar sa sannan tace " ni zan tafi sai wani
lokacin in mun sake had'uwa , dan banaso ko sau d'aya naga k'afar ka agidana mutuk'ar na tare
, sannan wannan kujerun karka kwashe su ina son su da kayan kallon nan , Alhaji Na Lamma
yace " duk nabar miki su babu damuwa , ni da shawarar da nakeso muyi itace me zai hana ki
amince kawai muyi aure da irin wannan rayuwar , nayi Alk'awarin yi miki duk abinda kikeso
mutuk'ar kika amince min , Aysha ta dubi Alhaji Na Lamma sosai sai sannan tafara k'are masa
kallo ganin wani k'aton tumbin sa , gashi wani bak'ikk'irin dashi sai wani murmushi yake shi ala
dole ya burgeta , Itama murmushin tayi sannan tace " kayi hak'uri Alhaji ka riga ka makara ,
bazan auri wanda nasan d'an sa kafin nasan saba , da sauri Alhaji Na Lamma ya dube ta
alamar son jin k'arin bayani " ta d'aga kai alamar da gaske take tace " tabbas Farouq yasan ni
shima tunkafin nahad'u dakai , kaga bazan iya aurenka ba kuma koda aure zanyi gaskiya
banajin zan iya auren ka Alhaji , dan haka nabarka lafiya sai wani lokacin , tana gama fad'ar
hakan bata jira cewar saba ta fice daga cikin Falor gaba d'aya......
A ranar su Aysha da Gogal suka tare a gidan Alhaji Na Lamma , da suka tashi tarewa
basu gayawa kowa ba dan Aysha tace basai kowa yasani ba dan kar ayi musu shune tunda
anga sun sami ci gaba , Habu me shagon gidan su harshi suka tare agidan saboda yana da
kirki kuma suna shiri sosai dasu , motar Aysha tasa Alhaji ya tura Farouq ya d'auko ta ya kawo
mata gidan da zummar fara koya mata motar cikin satin .......
Hameed tunda ya sauka a airpot yake jin wani sanyi yana ratsa zuciyar sa , tabbas zaiyi
k'ok'arin shawo kan Aysha wannan lokacin , dan yana sonta sosai bayajin zai barta takuma
kufce masa , a haka direban gidan su yazo ya d'auke sa suka nufi gida ....
Jabir Sai dare ya nufo gidan su Aysha dan jin maganar data ce masa zasuyi , yana zuwa
yasamu gida a rufe da k'aton kwad'o , shima shagon Habu haka yake a rufe da k'aton kwad'on ,
har wajen k'arfe goma yana k'ofar gidan yana jiran yaga ta inda zasu b'illo , ganin sha d'aya har
ta gota yasa yabar k'ofar gidan yatafi......
Washe gari haka yakuma zuwa k'ofar gidan kamar yadda yabarsa haka yagansa , tunani ya
shiga yi akan ina suka tafi haka har suka kwana ? yana tsaye yaga wani yaro zai shiga jikin
gidan yace " zonan kaji , yaro yazo Jabir yace " dan Allah k'anina kasan inda masu gidan nan
suka tafi ? yaron yace " Gogal tashiga gidan mu jiya tace tashi zasuyi zasu koma wani gidan ,
Jabir yace " tashi kuma ? yaron yace Ae , Jabir yace " kasan inda suka koma dan Allah ? Yaron
yace " wlh bamu san ina suka koma ba , dan bawanda yarakasu bare aga gidan , Jabir yace " to
nagode sosai k'anina kaji , Yaron yatafi abinsa yabar Jabir tsaye yana kai komo , cikin ransa
yace "dama tasan tashi zasuyi shiyasa ta tsaya ta saurareni jiya harda cemin wai zamuyi
magana , tabbas duk inda kuka koma saina nemoki Aysha bazan tab'a k'yaleki ba......
Aysha tunda suka koma Gogal keta mamakin girman gidan , Habu kansa yayi mamakin
ace wai a makaran ta Aysha aka bata kyautar gidan , dan shifa dama tuntuni yana zarginta dan
dai bashi da hanyar tuhumar ta , Gogal sosai ta jinjinawa wanda yabawa Aysha kyautar wannan
gida haka , ta dubi Aysha tace " gaskiya kowaye yabaki kyautar gidan nan yana da mugun kud'i
sosai , wannan gida kamar gidan masu kud'i , yakamata ace kin kaini wajen sa nayi masa
godiya dashi da malaman naki , Aysha sosai taji fad'uwar gaba amman sai ta dake tace " dama
sonake sai mun nutsu muje kiyi musu godiya dan kwanan na ma zamu kuma yin wata
musabik'ar , itace wacce in Allah yabani naci to kujerar makka za'abani , wata zabura Gogal tayi
tace " Makka fa Sayyada ? Aysha tace " E mana Gogal , to kowannan gidan da motar ai sunfi
kujerar Makka tsada , Gogal tace " Alhamdullilah Allah yasa kici kinga sainaje a madadin ki in
sauke farali , nan Aysha ta shiga tsara Gogal zancen k'arya da gaskiya ita kuma tana
yadda.......
Yamma nayi Hameed ya shirya cikin shigar sa ta Alfarma , sai zabga k'amshi yake
tamkar wani sabon ango ya nufo gidan su Aysha , yana zuwa yaga gidan rufe da k'aton kwad'o ,
take yaji k'irjin sa ya buga yafara addu'ar Allah yasa ba tashi sukayi daga gidan ba , haka
yagama zama amman ba wanda yazo wucewa ma bare ya tambayesa , haka ya juya ya tafi jiki
a sanyaye yana jin tamkar ya fashe da kuka..........
Aysha ta kira Alhaji Na Lamma akan aturo mata Farouq zai fara koya mata motar , basu fi
minty Ashirin da waya ba saiga
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 13