Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
abin yin gulma , tabbas zai koyawa Aysha hankali tunda duk itace sanadin hakan , Yana fita daga motar yayi b'angaren sa duk ransa a dagule....... Hameed tunda ya koma k'asar America yakasa komai sai tunanin Aysha , daga ya rufe idanun sa itace keyi masa gizo , tunda yadawo kwata kwata abokan aikin sa suka kasa gane kansa , Aleeya budurwar sa wacce suke aiki tare babu irin tambayar da batayi masa ba akan canzawar sa amman yace bakomi , kullum in yadawo daga wajen aiki bashi da burin daya wuce ya keb'e kansa yana tunanin Aysha , abinda ke damunsa rashin sanin yaya take da kuma rashin dabara dabaiyi ba ta anso number wayar ta , yanke shawara yayi na tahowa Nageria kawai kozai samu sauk'i inya ganta....... Tunda garin Allah ya waye Aysha taji batason yau ko soro ta lek'a , d'akin ta ta koma ta kwanta tana danna wayar ta , kiran Alhaji Na Lamma ne ya shigo tana kallo amman tak'i d'agawa , sai dayayi mata kira biyar amman tak'i d'agawa , daya ke datar ta a bud'e take sai ganin test d'in sa tayi ya shigo ta whassp , nan ma ta bud'e tagani amman tak'i masa reply , Daga k'arshe ma ta kashe datar ta ta ajiye wayar tayi kwanciyar ta abinta , tana kwance taji yaro ya shigo yana fad'in " wai ana kiran Babyn dad'i a waje , a zabure Aysha ta mik'e tana fad'in " nashiga uku waye zai min wannan aika aika haka ? bata gama tsora ba sai dataji muryar Gogal na fad'in " wace ce kuma Babyn dad'i agidan nan ? kaje kace banan gidan bane kaji wannan suna haka mara amfani da ma'ana kuma , haka tai ta fad'a har yaron yafita , Aysha jitayi jikin ta na rawa tamkar mazari da sauri ta d'auko hijab tasaka zata fito takuma jin yaron yadawo yana fad'in " wai ance anan gidan take kuma tasan kanta , Aysha tayi saurin fitowa tana fad'in " kai wannan wanne irin abune haka ? muje naga wanne d'an iska ne yake mana wannan abu haka , Gogal itama ta fito tana fad'in " nima dai bari nazo naga waye me wannan aike haka da bashi da mutunci , Aysha da sauri ta dakatar da Gogal tana fad'in " bari naje nagano ki koma kawai basai kin fito ba .... Aysha na fitowa waje taga Jabir tsaye ya hard'e cikin k'ananun kaya abinsa , yana ganin fitowar ta ya fara wani shu'umin murmushi yana kallon ta , tana k'arasowa a fusace tace " wai kai me kake nema a cikin rayuwa ta haka da kake damuna ? Jabir yayi murmushi sannan yace " kan ki nake nema inaso ki anshi soyayya ta ki huta dani kawai , tsaki Aysha taja sannan tace " idan kuma ban ansa ba fa ? Jabir ya matso gaf da jikin ta yace " in baki ansa ba kuma kin san sauran zancen , dan duk duniya sai tasan wace ce ke , ta yadda kike shigar mutunci kina cin zarafin hijab da nik'af , kina janyowa ana b'atawa masu irin wannan shigar taki suna , inaso kisani zan fad'a miki hanyoyin da zaki bi dan bin umarnina ki zauna lafiya , Aysha tace " inaso kasani ko kafita daga cikin rayuwata ko kuma insa afitar mun dakai , kuma soyayyace bazan tab'a yin ta dakai ba saboda kaima ba soyayyar Allah zakayi min ba , murmushi Jabir yayi sannan yace " kin tab'a gani anso karuwa soyayyar Allah ne ? ai tsakanin ka da ita kawai ka murji jikin ta ka shige kabarta a wajen , ni bani da kud'in da zan biyaki in murji jikin ki amman inaso ko taya ya sainayi amfani dake , Aysha tace " hakan ba k'aramin kuskure zakayi ba kuwa a cikin rayuwar ka , tana gama magana ta juya zata tafi taji yace " Babyn dad'i ki saurari tambayoyin da Kakarki zata miki akan wannan sunan , dan sai tasan komai game da rayuwar da kikeyi har wannan motar da aka baki kika yi mata k'arya , Aysha duk da tanajin tsoro amman haka ta dake bata nuna masa ba har ta shige cikin gida abinta.......... *In naga Comment inci gaba sannan in k'ara yawan typing* _In kuma bakuyi ba intafi hutu sai bayan sallah ajini_ *'Yar* *Mutan Kanawa* _Ce_ 😍🌹 [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR* *HANNU* πŸ€’πŸ€’ _NA_ *Zee* *MD* *Hamdala* *Writer's* *Association* πŸ’ͺ https://www.facebook.com/111403834371046 ✨✨ *{{* *H.W.A* *}}*✨✨ *Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim* _Page._ 14 Alhaji Na Lamma jikinsa har rawa yake wajen neman number Farouq , goge zufar dake zubo masa yayi tare da danna kiran number Farouq , yana d'agawa yace " Daddy na anso komai gani nama taho yanzu , Alhaji Na Lamma da sauri yace " maza ka juya ka koma mata da dukkan abinda ka anso , Farouq a tsorace yace " what Daddy in koma mata dasu kace fa ? Alhajin yace " Ae maza ka juya kamaida mata dasu nace , yana gama fad'ar haka ya kashe wayar yayi cilli da ita kan kujera ya mik'e yana zagaye d'akin nasa , tambaya ya shiga yiwa kansa " taya akayi wannan yarinyar ta shammace shi haka batare da yasani ba ? tabbas duk yadda zaiyi sai ya raba ta da wannan video ko zai samu sukuni , mutuk'ar wannan video yana tare da ita to zuciyar sa zata kasan ce cikin zullumi , haka yashiga kaikawo goge zufar dake zubowa jikin sa , duk ac dake aiki a d'akin nasa sai yaji kamar ba su saboda zafin dayake ji......... Farouq juyawa yayi da kan motar yakoma gidan su Aysha , Farouq mamaki ne yakamashi ta yadda akayi Daddyn nasa yace akoma mata da komai , yana tafe yana nazarin wane irin Abu Aysha tayiwa Mahaifin nasa har ya sauko haka ? bai wani dad'e ba ya k'araso k'ofar gidan su Aysha , yana zuwa ya fito daga motar ya zo k'ofar gidan yashiga bugu da k'arfi tamkar zai karya musu k'aure , Aysha dama tana zaune tana jiran zuwan sa , tana jin yana wannan bugun ta mik'e a hankali tayo hanyar soron gidan nasau , tana zuwa ta zare sakata tana duban Farouq d'in , shima ita yake kallo cikin kwayar idon sa ta hango zallar tsanar ta , itama kuma anata idon hakane dan ta tsani Farouq sosai , wurga mata takardun yayi tare da mukullun motar ya juya zai tafi , Aysha tace " haka kake yiwa uwarka kenan inkaje bata abu ? a fusace Farouq ya juyo tamkar d niyar marin Aysha wayar sa ta shiga ruri , dubawa yayi yaga sunan Daddyn sa ya d'aga , yana d'agawa Alhaji Na Lamma yace " inaso kabata hak'uri akan abinda kayi mata sannan in zaka bata hak'urin inaso ka rissina tamakar yadda kakeyimin , Farouq wani abu yaji yatsaya masa a k'irjin sa tamakar ya had'iyi zuciya ya mutu , baice komai ba ya kashe wayar yana duban Aysha yace " menayi miki haka kika zab'i kiyi min hukunci ta wannan hanyar ? nabaki hak'uri akan abinda nayi miki nida abokaina amman kink'i saurarena , kuma ko a lokacin da nayi miki wannan abu ai naji ba a cike kike ba , kinga daman ked'in *'Yar Hannu* ce , murmushi Aysha tayi sannan tace " kayi abinda Mahaifinka yace kayi yanzu katafi , kasan dare ne yanzu hakan ba rana ba bare ka tsayar dani , Farouq ya rissina tamkar yadda mahaifinsa ya umarce sa yabata hak'uri sannan ya shige yabar k'ofar gidan da tarin tsanar Aysha , da kallo Aysha ta bishi tana murmushi sannan ta maida k'ofa ta rufe tayo cikin gida abinta...... Washe gari Aysha tana tashi tagama had'a musu abin kari , Bayan sun karya tayi wanka ta fito sannan tacewa Gogal " tanaso taje gidan da zasu koma d'in taga meye babu a ciki , Gogal tace " ai da samo mana masu kura kikayi suka zo suka dib'i kayan inyaso basai mun nemi komai ba , Aysha tayi murmushi tana duban Gogal tace " ai wahala zasu sha masu kura Gogal sai dai motar , amman bari naje dai nadawo sai muga yadda za'ayi , shigar ta ta tayi wacce tasa ba ta rufe ko 'ina na jikin ta tafice daga cikin gidan.... Tayi nisa a tafiyar ta taji ance " Malama Aysha *'Yar* *Hannu* , ko bata waiwaya ba tasan Jabir ne , dan yanzu kusan shine babbar matsalar ta a cikin rayuwa , duk inda tasa k'afa tasan yana bibiyar ta amman dole tayi maganin sa tun kan dare yayi mata , wata dabara ce ta fad'o mata kawai ta juyo tana murmushi tace " Malam Jabir manyan gari yakake ? Jabir cike da mamaki yace " lafiya lau nake kema ina fatan hakan kike ? Murmushi tayi sannan tace " gashi kuwa kagani , Jabir ganin Aysha ta saki jiki dashi yasa yafara tunanin ko barazanar da yayi mata ce yasa taji tsoro , cike da jin shi wanine yace " ina zuwa haka manyan gari ? murmushi Aysha tayi sannan tace " wata k'awa tace baban ta yarasu shine zanje mata gaisuwa , Jabir yace " Ayya Allah yajik'ansa in kindawo anjima sai muyi magana ko ? Aysha tace " babu damuwa sai nadawo d'in , Allah yadawo dake lafiya ya juya yabarta ta nufi titi tana dariyar mugunta...... Gate hause d'in Alhaji Na Lamma Aysha ta nufa , tana zuwa tasamu me gadin gidan a k'ofar gate a tsaye yana jin redio , tana zuwa tayi masa sallama ya amsa yana kallon ta tamkar wanda yaga wata halittar daban , Aysha tace " inason shiga gidan nan dan zan duba wani abu , Megadin ya dube ta sama da k'asa sannan yace " baiwar Allah taya zanbarki ki shiga cikin gida batare da nasanki ba ? kuma koda nasanki taya zan bud'e miki Alhalin Alhaji bai cemin in bud'e miki ba ? d'age nik'af d'in Aysha tayi tana kallon sa sannan tace " kashiga ka gayawa Alhajin kace me gidan ce tazo tanason suyi magana , mai maita wa Megadi ya shiga yi yana fad'in " Me gidan ce tazo , haka ya bud'e gidan da saurin sa yatafi isarwa da Alhaji sak'o..... Alhaji Na Lamma yana zaune a falor sa yana shan ruwan lipton yaji shigowar me gadi , izini yamasa yashigo suka gaisa , nan ya sheda masa zuwan Aysha da kalmar datace ya fad'i , Alhaji Na Lamma najin ance Me gidace tazo ya mik'e da sauri tamkar zai tuntsira yayo waje , Me gadin nasa ma acikin falor yabarshi tsaye baki bud'e , cikin ransa yace " wannan wacce shu'umar yarinya ce tasa Alhaji wannan rawar jiki haka ? shima biyo bayan sa yayi suka fito wajen ........ Aysha na tsaye abinta sai k'arewa unguwar kallo take , cikin ranta tashiga yaba tsarin unguwar na rashin hayaniyar mutane , ga kuma gidaje masu kyan gaske tamkar a turai layin , muryar Alhaji ce ta katse ta da yace " sannu da zuwa Hajjaju , Aysha ta bisa da kallo daga shi sai gajeran wando kana gani kasan baisan ya fito ba , dariya ce taso kama Aysha amman ta maze cimin ranta tana fad'in " tsohon banza kawai maganin ku ai , dan kuna da kud'i sai kurunga amfani da hakan kuna lalata yaran mutane , kana da Matanka amman saika had'a da bibiyar matan waje , a fili kuma ta amsa masa ciki ciki tamkar batason maganar , bud'e mata k'aramar k'ofar yayi yace " bisimillah mushiga daga ciki ko sai muyi magana , shigewa Aysha tayi batare da tace dashi uffan ba abinta....... Sai data shiga falor tasamu guri ta zauna tana kuma k'arewa falor kallo , tabbas gidan yayi kyau sosai dan yagama burgeta shiyasa takeson gidan , Alhaji Na Lamma shima zama yayi yana duban ta cike da kulawa , Aysha ta gyara murya tace " anjima nakeso mudawo gidan nan shine nazo nagayamaka kayi sauri ka kwashe duk wasu abubuwanka masu muhimman ci daga ciki , sanin kan kane nida Kakata zamu dawo cikin gidan kuma batasan yadda akayi nasamu gidan ba , Alhaji Na Lamma yace " duk yadd kikeso haka za'ayi yanzu kuwa........ [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR* *HANNU* πŸ€’πŸ€’ _NA_ *Zee* *MD* *Hamdala* *Writer's* *Association* πŸ’ͺ https://www.facebook.com/111403834371046 ✨✨ *{{* *H.W.A* *}}*✨✨ *Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim* _Alhamdulillah_ *Am* *Back* ✍ _Page._ 16 Aysha sosai ta maida hankalin ta tana kallon Farouq , duk da bawata maganar arzik'i yake mata ba ba laifi ta fahimci wani abun , kusan awa d'aya suka kwashe yana nuna mata sannan suka d'auko hanyar dawowa gida...... koda suka zo k'ofar gate d'in gidan ya tsaya batare da ya shiga ba , itama batace masa uffan ba ya sauka daga cikin motar yayi tafiyar sa , fitowa Aysha tayi taje ta k'wank'wasa k'ofar gidan , Habu ne ya zo da sauri ya bud'e mata yana fad'in " sannu da zuwa har kundawo kenan ? Aysha tayi murmushi tace " wallahi har mundawo ashe in mutum ya nutsu ma babu wuya koyan motar , murmushi Habu yayi yana fad'in " Allah yasa anfara a sa'a Aysha tace Ameen...... Komowa tayi ta shiga cikin motar ta zauna sannan ta kunna tashigar da ita ciki , a laifi sosai Aysha tana da basira , shiyasa ko a makaranta malaman ta suke alfahari da ita ..... Jabir sosai yake zuwa club club wai ko Allah zai sa yaci karo da Aysha , sai dai kwata kwata bai san zuwa club baya cikin layin Aysha ko kad'an , ganin yajera kwana biyu yana yawon neman ta yasa yagaji ya hak'ura da zuwa , sai dai sosai Aysha tabashi mamakin yadda a wannan karon tafishi wayo , tabbas duk inda take a fad'in garin nan sai ya nemo ta , zai nuna mata shima ba kanwar lasa bane ...... Kwata kwata Aysha ta manta da wani Jabir wanda tayiwa lak'ani da d'an sa'ido , Rayuwar su sukeyi ita da Gogal da Habu cikin kwamciyar hankali , gashi kullum sai Farouq yazo sunfita koyan motar , yanzu haka har ta iya sosai amman tak'i tabarsa ya huta.... Gogal sosai ta murje tayi wani kyau abinta , abinka da farar fata tamkar katab'a ta jini ya fito , kullum tana cikin ac ga kwana cikin ac ba ruwan ta da sauro , sosai Aysha take kulawa dasu wajen cin abinci medadi , duk da yanzu hankalin Gogal yana kan Aysha akan yadda taga tana kashe kud'i , kwata kwata Aysha ta manta da yadda take bida komai a b'oye kar Gogal tagani , yanzu har wayar ta babba ta bayyana ta tana fito da ita , yauma kamar kullum suna zaune a falo suna kallo Gogal hankalin ta nakan Aysha wacce ke danna wayar ta tanayin chat d'auke da murmushi a fuskar ta , ganin kwata kwata ta maida hankalin ta ga waya yasa Gogal yin gyaran murya tace " wai Sayyada yaushe kika samu wannan Aba haka ? Aysha sai da taji hanjin cikinta ya ya mutsa kafin tayi ta maza tace " Batawa bace Gogal , ta Asma'u k'awar nan tawa ce na aro ta , kinsan ina koyan motar to dole sai da irin wayoyin nan zan iya , Gogal dayake ba sanin kai tayi ba tuni Aysha ta zage tashiga shirya mata k'arya , Gogal duk da ta yadda da Aysha d'ari bisa d'ari amman sai tasamu zuciyar ta dayin rawa akan Maganar Ayshar , haka dai tabar abin aranta batare da takuma cewa Uffan ba....... Hameed kusan kullum sai yaje Unguwar su Aysha , amman kullum indai yaje zaisamu gidan yadda yabarshi , yauma yana zuwa hakan ce ta kasance kamar kullum , tsayawa yayi yana nazari sai ganin wani yaro yayi zai wuce , kiran sa yayi yaron yazo Hameed yace " dan Allah k'anina ko kasan inda masu gidan nan suka tafi ? yaron yace " wallahi tashi sukayi kuma bansan inda suka koma ba , Hameed ya maimai ta kalmar tashi sannan yace " kozaka shiga wancan gidan ka tambayo min inda suka koma , yaron ya kalli gidan sannan ya kalli Hameed yace " ai gidan mune kuma bamu san inda suka koma ba , nan Hameed ya zaro d'ari biyar yabawa yaron yana fad'in " ungo to nagode kaji , yaron ya ansa yana godiya shikuma ya juya yanufi motar sa yatafi .... Alhaji Na Lamma yana zaune a falon sa na sama yana nazarin wasu takardu , Farouq ne ya shigo d'auke da sallama abakin sa sannan yasamu waje ya zauna , gaida Mahaifin nasa yayi cike da girma mawa sanna yace " Daddy ina son yin magana dakai , Alhaji Na Lamma yadubi d'an nasa wanda yaga ya rame sosai yace " ina saura ranka , Farouq yanisa sosai sannan yace " Daddy dan Allah meye had'in ka da wannan yarinyar da har take irin wad'an nan abubuwan ? murmushi Alhaji Na Lamma yayi irin nasu na manya yace " cool down my luvly son babu abinda ya had'amu da ita kawai dai kabar wannan maganar banason kadamu , Farouq sosai yaji rashin dad'in yadda mahaifin nasa yake neman mai dashi k'aramin yaro , duban Daddyn nasa yakuma yi sannan yace " a gaskiya Daddy bazan iya hak'ura ina kallon k'aramar yarinya tana juya ka yadda takeso ba , zan je nasa meta ko wacce za'ayi wallahi sai dai ayi , mik'ewa Farouq yayi a fusace zai fita Alhaji Na Lamma yayi saurin dakatar dashi da cewa " Farouq karka kus kura kace zakaje wajen Aysha , ko kamanta laifin da kayi mata kai da abokan ka ne ? shuru Farouq yayi tare dayin k'asa dakai , cikin zuciyar sa yafara fad'in " lallai wannan yarinayar ta wuce tunanin sa wato har ta sanar da Daddyn sa abinda suka mata , baigama tunani ba yaji Daddyn nasa nacewa " inaso kafita daga sabgar Aysha , tsakanin ka da ita koya mata motar sai kuma in ta buk'aci kayi mata wani aiken , dan haka ka kiyaye banson insake jin wani abin ya b'illo , k'asa dakai Farouq yayi sannan ya amsa da to ya fice daga d'akin...... Da kallo Alhaji Na Lamma ya bi bayan Farouq , cikin ransa yace " laifinka yafi yawa sosai agun Aysha fiye da nawa laifin , nasan saboda tasan kai d'ana ne tazab'i ta rama abinda kayi mata ta wannan sigar , tabbas nasan dole wata rana Dole zata gyaru tadaina rayuwar da take , Allah yagani inasonta da aure a yanzu inda zata amince min amman nasan baxai yuwuba ma , Gashi ta sabamin da jikinta kuma haryanzu banji jiki me dadi irin saba duk irin neman matan danayi..... Hameed yau tunda yatashi yake shaawar zama a k'ofar waje dan ya k'arewa unguwar tasu kallo , kujera ya fito da ita ya zauna tare da lapton d'insa yafara danna wa , dai dai lokacin Aysha tayi shigar ta ta hijab har k'asa tare da saka Nik'af ta fito wai zataje makaranta , tana fitowa tafara kalle kalle tamkar me neman wani abin , dai dai lokacin Hameed ya d'ago da kansa yana duban saitin wajen da Aysha take , da sauri ya mik'e yana kallon inda take sosai , cikin zuciyar sa yafara magana " tabbas wannan in ba Aysha bace to 'yar uwar tace , dan irin yadda Aysha take shigar ta itama wannan d'in haka takeyi , gashi yanayin jikinsu d'aya anya bazaije yaga fuskar taba ko Ayshar sace ? ...... [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR HANNU* πŸ€’πŸ€’ _NA_ *Zee* *MD* *Hamdala* *Writer's* *Association* πŸ’ͺ https://www.facebook.com/111403834371046 ✨✨ *{{* *H.W.A* *}}*✨✨ *Bisimillahir* *Rahamanir* *Rahim* _Alhamdulillah Ala Kulli HalinπŸ™πŸ»_ _Page._ 15 Aysha tace " wannan me gadin inaso ka sallamesa dan bana buk'atar sa , sannan kajawa Farouq d'anka kunne lallai karya kus kura ya tako mana cikin gida , Alhaji Na Lamma tana magana yana kallon ta tamkar ya janyota ya shak'eta ta mutu kowa ya huta , tamkar Aysha tasan me yake ayyana wa tace " kanajin tamkar ka shak'eni na mutu kowa ya huta ko ? to kasani ko ka kashe ni dole bazaka tsira ba , dan komai da mukayi k'awata tasani kuma tana da videon komai a gunta itama , murmushi Alhaji Na Lamma yayi sannan yace " meye ya kawo maganar kisa kuma Allah ma ya kiyaye ni ko kiyashi ban tab'a kashewa wa bare kuma mutum , mik'ewa Aysha tayi tana nuna masa ko ajikin ta maganar sa sannan tace " ni zan tafi sai wani lokacin in mun sake had'uwa , dan banaso ko sau d'aya naga k'afar ka agidana mutuk'ar na tare , sannan wannan kujerun karka kwashe su ina son su da kayan kallon nan , Alhaji Na Lamma yace " duk nabar miki su babu damuwa , ni da shawarar da nakeso muyi itace me zai hana ki amince kawai muyi aure da irin wannan rayuwar , nayi Alk'awarin yi miki duk abinda kikeso mutuk'ar kika amince min , Aysha ta dubi Alhaji Na Lamma sosai sai sannan tafara k'are masa kallo ganin wani k'aton tumbin sa , gashi wani bak'ikk'irin dashi sai wani murmushi yake shi ala dole ya burgeta , Itama murmushin tayi sannan tace " kayi hak'uri Alhaji ka riga ka makara , bazan auri wanda nasan d'an sa kafin nasan saba , da sauri Alhaji Na Lamma ya dube ta alamar son jin k'arin bayani " ta d'aga kai alamar da gaske take tace " tabbas Farouq yasan ni shima tunkafin nahad'u dakai , kaga bazan iya aurenka ba kuma koda aure zanyi gaskiya banajin zan iya auren ka Alhaji , dan haka nabarka lafiya sai wani lokacin , tana gama fad'ar hakan bata jira cewar saba ta fice daga cikin Falor gaba d'aya...... A ranar su Aysha da Gogal suka tare a gidan Alhaji Na Lamma , da suka tashi tarewa basu gayawa kowa ba dan Aysha tace basai kowa yasani ba dan kar ayi musu shune tunda anga sun sami ci gaba , Habu me shagon gidan su harshi suka tare agidan saboda yana da kirki kuma suna shiri sosai dasu , motar Aysha tasa Alhaji ya tura Farouq ya d'auko ta ya kawo mata gidan da zummar fara koya mata motar cikin satin ....... Hameed tunda ya sauka a airpot yake jin wani sanyi yana ratsa zuciyar sa , tabbas zaiyi k'ok'arin shawo kan Aysha wannan lokacin , dan yana sonta sosai bayajin zai barta takuma kufce masa , a haka direban gidan su yazo ya d'auke sa suka nufi gida .... Jabir Sai dare ya nufo gidan su Aysha dan jin maganar data ce masa zasuyi , yana zuwa yasamu gida a rufe da k'aton kwad'o , shima shagon Habu haka yake a rufe da k'aton kwad'on , har wajen k'arfe goma yana k'ofar gidan yana jiran yaga ta inda zasu b'illo , ganin sha d'aya har ta gota yasa yabar k'ofar gidan yatafi...... Washe gari haka yakuma zuwa k'ofar gidan kamar yadda yabarsa haka yagansa , tunani ya shiga yi akan ina suka tafi haka har suka kwana ? yana tsaye yaga wani yaro zai shiga jikin gidan yace " zonan kaji , yaro yazo Jabir yace " dan Allah k'anina kasan inda masu gidan nan suka tafi ? yaron yace " Gogal tashiga gidan mu jiya tace tashi zasuyi zasu koma wani gidan , Jabir yace " tashi kuma ? yaron yace Ae , Jabir yace " kasan inda suka koma dan Allah ? Yaron yace " wlh bamu san ina suka koma ba , dan bawanda yarakasu bare aga gidan , Jabir yace " to nagode sosai k'anina kaji , Yaron yatafi abinsa yabar Jabir tsaye yana kai komo , cikin ransa yace "dama tasan tashi zasuyi shiyasa ta tsaya ta saurareni jiya harda cemin wai zamuyi magana , tabbas duk inda kuka koma saina nemoki Aysha bazan tab'a k'yaleki ba...... Aysha tunda suka koma Gogal keta mamakin girman gidan , Habu kansa yayi mamakin ace wai a makaran ta Aysha aka bata kyautar gidan , dan shifa dama tuntuni yana zarginta dan dai bashi da hanyar tuhumar ta , Gogal sosai ta jinjinawa wanda yabawa Aysha kyautar wannan gida haka , ta dubi Aysha tace " gaskiya kowaye yabaki kyautar gidan nan yana da mugun kud'i sosai , wannan gida kamar gidan masu kud'i , yakamata ace kin kaini wajen sa nayi masa godiya dashi da malaman naki , Aysha sosai taji fad'uwar gaba amman sai ta dake tace " dama sonake sai mun nutsu muje kiyi musu godiya dan kwanan na ma zamu kuma yin wata musabik'ar , itace wacce in Allah yabani naci to kujerar makka za'abani , wata zabura Gogal tayi tace " Makka fa Sayyada ? Aysha tace " E mana Gogal , to kowannan gidan da motar ai sunfi kujerar Makka tsada , Gogal tace " Alhamdullilah Allah yasa kici kinga sainaje a madadin ki in sauke farali , nan Aysha ta shiga tsara Gogal zancen k'arya da gaskiya ita kuma tana yadda....... Yamma nayi Hameed ya shirya cikin shigar sa ta Alfarma , sai zabga k'amshi yake tamkar wani sabon ango ya nufo gidan su Aysha , yana zuwa yaga gidan rufe da k'aton kwad'o , take yaji k'irjin sa ya buga yafara addu'ar Allah yasa ba tashi sukayi daga gidan ba , haka yagama zama amman ba wanda yazo wucewa ma bare ya tambayesa , haka ya juya ya tafi jiki a sanyaye yana jin tamkar ya fashe da kuka.......... Aysha ta kira Alhaji Na Lamma akan aturo mata Farouq zai fara koya mata motar , basu fi minty Ashirin da waya ba saiga

Chapter 5 of 13