Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tuban Allah , Allah muntuba Allah kayafemana πŸ‘πŸ»πŸ‘πŸ»πŸ‘πŸ»πŸ‘πŸ» *Tammat* *Alhamdulillah Allah yakawomu K'arshen littafin 'Yar Hannu , Abinda nayi ba dai dai ba Allah ka yafemun , wanda nayi dai dai kuma Allah yasa mu amfana dashi ,*πŸ‘πŸ»πŸ‘πŸ» _Nagode sosai Masoyana ta yadda kukai ta bibiyar littafina batare da gajiyawa ba , Allah yabar k'auna Ina muku fatan Alkairi_πŸ™πŸ» *tabbas komai yayi farko akwai k'arshen sa* *Taku a ko yaushe* *'Yar Mutan Kanawa*🌹🀝🏻πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯° [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *Cigaban 'Yar Hannu*πŸ€’ 22 Kiran Aysha zatayi dan taje gidan su ta bata shawara akan Khalid dan gaskiya tunanin sa yadame ta , gashi ta rasa kan sa kwata kwata dan ko kiran sa tayi kwata kwata baya d'agawa , ganin datar ta tayi a bud'e sak'onni na shigowa rufe datar tayi sannan ta shiga neman number Ayshar kiran ta tayi har takusa katsewa sannan Aysha ta d'aga , lokacin suna tare da Khalid a manne suna zabga love , ka rantse wasu shahararrun masoyana na gaskiya , amman ina ko wanne da burin dayake ransa , d'aga wayar tayi tana fad'in " K'awata ya akayi kwana biyu , Ruma tace " lafiya lau dan Allah kina gida ? Aysha tace " bana gida amman indai zuwa zakiyi kibari zuwa anjima sai mu had'u , Ruma tace to shikenan sai kindawo , Aysha ta katse wayar tana jin tausayin Ruma har cikin ranta , dan tasan tabbas tafi son Khalid akan son dayake mata , dan yadda ta karance sa kwata kwata ba dan Allah yakeson Ruma ba kawai saboda dukiyar Mahaifinta yake sonta , kuma da sannu zata rusa masa duk wani shirin sa , zata yi k'ok'arin raba Zuciyar Ruma da soyayyar sa , sai tasa Ruma ta tsanesa tsana mafi muni , ta kallesa suka had'a idanu ya wani kashe mata ido , itama murmushi tayi masa a zuciyar ta tana fad'in " ka kusa yin kuka da idanunka , dan tuni tasamu labarin yadda yasamu aka d'aukesa kasuwa da k'yar , kuma babu laifi mahaifin Ruma yana masa sallama me tsoka shiyasa yafara shigowa gari , yanzu lokacin da zata fara rabashi da kud'in jikin sa yayi , dan sotake sai ta rabashi da kud'in jikin sa sannan ta Rabashi da Ruma da kuma kasuwan cin sa , sai yaji irin ciwon da taji a zuciyar ta na rabata da Mutuncin ta dayayi......... [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR HANNU* πŸ€’πŸ€’ _NA_ *Zee* *MD* *WOMEN WRITERS ASSOCIATION* πŸ“š ( Domin Marubuta Mata ) ✨ (W.W.A) ✨ https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/ *Bisimillahir Rahamanir Rahim* _Page._ 23 Aysha ta dubi Khalid tace " kasan da wa mukayi waya ? Khalid ya girgiza kai yana fad'in " taya zan san da wa kikayi nasan dai mace ce , Murmushi Aysha tayi sannan tace " Mutuniyar ka wai zatazo yau in ina gida , Khalid ya tab'e baki sannan yace " nasan indai tazo to sai tayi zan cena , kinsan Allah Baby ni nafison inyi rayuwa da wa yayyiyar mace irin ki , inason inga budurwa ta tana bani kulawa kamar yadda kike bani , Ruma babu abinda ta iya sai k'auyan ci itafa ko romance bata bari muyi , kullum sai ta runga cewa in k'ara hak'uri in mukayi aure tazama tawa komai sai yadda nayi dashi , ... Aysha tuni taji wani ciwo a zuciyar ta yataso , tabbas ko wacce mace me mutunci babban burin ta shine ta tsare mutuncin kanta , amman ita ta k'arfi da yaji aka b'ata mata mutuncin ta , ta sanadin haka yanzu gashi ta lalace ,hawaye ne suka cika mata idanun ta tayi saurin maidasu , dan bata so ko da wasa Khalid yasan damuwar ta , Khalid yaci gaba da magana " kin san wani Abu Baby ? Aysha ta girgiza kai alamun a'a , yace ko sau d'aya bantab'a son Ruma ba , saboda bata d'aya daga cikin Matan da nake da burin aura , kawai ina kulata ne dan kud'in Baban ta , kuma sannan ina son dukiyar kaf tazama tawa nan gaba bayan babu shi , Aysha ji tayi wata tsanar Khalid ta nunku a cikin ranta , tabbas Khalid azzalumine kuma sai takawo k'arshen zaluncin sa nan ba da jimawa ba , Murmushi tayi nasu na asalin 'Yan duniya ta dubesa tace " to meyasa ka yadda zaka aure ta bayan kuma bata d'aya daga cikin matan da kakeso ka aura ? Murmushi Khalid yayi sannan yace " Baby ai kinsan a k'ark'ashin Mahaifinta nake kinga da kunya 'yar sa ta nuna tana sona nak'i amincewa , da zarar komai yadawo hannu na zan iya rabuwa da Ruma ko kuma na auri wacce rai na keso , Aysha tace " gaskiya kai d'in ka iya buga game amman karkaje fa ayi maka Babban bugun da ya wuce naka , Dariya yasa yana fad'in " waye zai bugani alhalin ba wanda yasan meye a zuciya ta indai bake ba dana fad'a miki , kuma ni nasan ina da tabbacin bazaki fad'awa Ruma komai ba , Aysha tayi murmushi tace " haba Dear taya zan tona maka asiri , ai in nayi haka tamkar na tonawa kaina asiri ne nima , kadaina ma fad'in haka dan kasan ni taka ce kai nawa ba ta yadda za'ayi inga wani abu da zai zo ya kawo maka matsala batare da na kaudashi ba , haka Aysha ta karkace tashiga yiwa Khalid dad'in baki sosai , nan yayi mata alk'wari komai takeso tafad'a zai siya mata , ... Aysha tanajin haka ta kashe masa ido tace " account d'inka da zurgi kenan My Dear ? Khalid cike da shauk'in so yace "2 milloine acikin account d'ina yanzu , sai kinsan dayake ban dad'e dafara zuwa kasuwar ba , kuma ahakan ma ina had'awa da cuwa cuwa batare da me wajen ya lura ba , nan Aysha taji sirrin Kud'in da Khalid yake dashi , Murmushi tayi cikin ranta tace " yanzu zaka fara rabuwa da 1 Million kafin nan da kwana biyu ka rabu da sauran ma , cike da kissa Aysha tace " ni yanzu abinda nakeso kawai shine muje kasiyamin zobunan gold da sark'a dan ina son du sosai , Khalid ganin irin yadda Aysha ta kwanto jikin ta ajikin sa ga Na shanun ta rabin su duk sun fito yasa shi rud'ewa tare da cewa " muje Baby angama ,...... Jabir tunda suka rabu da Aysha yake ta dakon kiran ta amman shuru , gashi ya gwada layin ta amman baya tafiya kwata kwata , damuwa ya shiga sosai tare da fad'in " wato wayo Aysha tayimin batare da nagane ba , meyasa na yadda nabar ta ta tafi batate da nabi bayan ta ba ? tabbas indai yakuma ido biyu da Aysha bazai barta takuma raina masa hankali ba , kuma ai yagane number motar ta dakuma kalar motar tabbas zai ci gaba da neman ta tamkar yadda yayi kwanaki , ....... Yau saura kwana biyu Hameed yabar k'asar Nageria , hankalinsa sosai yatashi ganin har yakusa tafiya bai samu Aysha ba , yaje sau biyu unguwar su Aysha yana ganin ko Allah zai sa yayi sa'a sundawo , sai dai ko kad'an basu dawo ba kullum gidan arufe yake , yauma yana zaune a k'ofar gate d'in gidan su yana chat da wani abokin sa a can k'asar London , kwana biyu zaman cikin gidan baya masa dad'i saboda Hajiyar sa ta damesa da Maganar Abida , shikuma har ga Allah bason maganar yake ba , shifa indai ba Aysha ba haryanzu baiga macen data yi masa ba , dan acan ma London akwai mata wad'an da suke son sa sosai amman duk yak'i basu fuska........ Koda su Aysha sukaje wajen saida sark'ok'i , sai da Khalid ya siya mata na Million d'aya da dubu Hamsin , dan zab'a tayi sai dataji masu kud'i dayawa tace su takeso , Khalid sosai yaji fitar kud'in amman gudun kar ta gane ya dake tamkar wani Alhajin Birni , da suka taho hanya tasa shi ya biya da ita wani Shopping Mall tayi siyayyar dubu d'ari nan ma ya biya , Khalid suna fitowa ya nuna shima yanaso tabashi jikin ta dan haka su biya Hotel yakama musu waje , ko kad'an Aysha bata damuba dan dama jiran wannan ranar take , dan tasan daga wannan ranar bazai k'ara ganin Nonon ta bama bare jikin ta , haka sukaje Hotel Khalid ya kwashi gara sosai ,kusan sumewa yayi saboda sambatu dan iya jin dad'i yajishi a tare da Aysha , sai yake ganin ko nawa ya kashe mata bai fad'i ba ganin yadda ta rud'ashi shima , sosai yayi mamakin yadda Aysha ta k'ware wajen iya wasanni ,ko dayake bazai mamaki ba ganin ta wayayyiyar Yariya wacce tagaji da had'uwa, haka suka gama d'ebewar su sannan sukayi wanka suka nufo gida...... Aysha tun a farkon layin su tasa Khalid ya sauke ta , koda zata fita daga motar sai da Khalid yace " Babyna yaushe zamu kuma had'uwa ne ? dan gaskiya kinjiyar dani wani dad'in da ban tab'a ji ba sai sau d'aya , Murmushi tayi sannan tace " sau d'aya Dear ashe katab'a yin sex ? Khalid yace " natab'a kwanciya da wata yarinya duk ba'ason ranta ba mukayi kuma shine farkon yina nima bana cikin nutsuwa amman haryanzu abin na raina , Aysha wani abune yataho mata ya tokare k'ahon zuciyar ta , kallon sa tayi cike da tsana tace " Saboda me ya tsaya maka arai kuma alhalin kace ba'ason ranta kayi ba ? jin yadda tayi maganar yasa ya dube ta , sai sannan Aysha tayi saurin ankarewa ta sassauta muryar ta tace " sorry Dear tausayin yarinyar naji ,amman meyasa kayi mata haka Alhalin bataso ? Murmushi yayi sannan yace " gaskiya sha'awarta tadameni kullum in muna tare to sai kinga abata a mik'e saboda yadda nake shaawar ta , ban daina jin hakan ba har sai randa na kusan ce ta , tana kuka tana magiya amman haka idona ya rufe na keta mata mutuncin ta , Aysha jitayi kamar a lokacin Khalid yake keta mata mutunci , hawaye ne ya cika idon ta wanda ta kasa iya maidasu , tabbas Khalid ya zalince ta dan shine sanadin komawar ta wannan rayuwar , yanzu waye zai aure ta a irin wannan rayuwar tata ? Meza tacewa Yaranta dazata haifa nan gaba ? taso ace Mijinta wanda zai aure ta shine zaifara sanin ta a duniya , amman Khalid ya rusa mata duk wani shirin ta ya lalata mata rayuwar ta , yasa taci gaba da sab'on mahaliccin ta , duk da tashiryu bayan zubar da cikin da tayi wanda yayi mata , Farouq shine ya maida ta ruwa shima yasa ta koma *'Yar Hannu* , tabbas Khalid azzalumine ya cuceta a rayuwar ta , jin tayi shuru yasa Khalid yin magana yace " meye naji kinyi shuru My Baby ? wani guntun Murmushi tayi sannan tace " wallahi danaji abunda kayiwa Yarinyar nan sai na tuno da wani Malamina a makaranta nima da yayimin fyad'e , Khalid yace " ayya sorry Baby kice mugun malami shine yafara yi mana hanya , nima kinsan Allah nine nafara yiwa yarinyar nan hanya , daga baya tasamu ciki nikuwa nayi mata korar kare , dan a ganina taya za'ace daga kwanciya sau d'aya wai ciki yashiga ai tazo da iskanci , sotake na aure ta ganin bata da wani asali gasu talakawa ba k'aruwa yasa na yi mata fata fata muka rabu , Aysha jitayi in bata yi saurin fita daga motar Khalid ba to tana gab da had'a masa jini da majina , shiyasa tayi saurin d'aukar kayan ta tace "muyi waya My dear , bata jira cewar saba ta fice da sauri abinta , Khalid ko ajikin sa bai kawo komai ba sai ma bin Mazaunan ta dayayi da kallo yana kuma wassafo dad'in daya sha ajikinta....... Hameed yana zaune kamar ance masa ya kalli hanya ya hango Aysha ta nufo ta wajen dayake , da sauri ya mik'e yana murza idanun sa itace dai ba gizo take masa ba , kwata kwata Aysha bata kula da Hameed ba har tazo ta gifta ta gaban sa , haka yashiga binta batare da yayi magana ba , sai datazo k'ofar gidan su lokacin Habu na zaune yanajin radio ta wuce shi yana mata sannu da zuwa , da yauwa ta amsa ta shige ciki abinta shikuma Hameed yaja ya tsaya gana yiwa Habu sallama......... *Ina mutukar Son Comment d'inku Masoyana* _Yin Comment shine ke k'ara mana k'aimin yin Typing_✍🏻✍🏻 *Saina jiku* *'Yar Mutan Kanawa* _Ce_ 🌹😘πŸ₯° [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR HANNU* πŸ€’πŸ€’ _NA_ *Zee MD* *WOMEN WRITERS ASSOCIATION*πŸ“š ( Domin Marubuta Mata ) ✨ (W.W.A) ✨ https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/ *Bisimillahir Rahamanir Rahim* _Page._ 34 Aysha firgigit tayi ta mik'e dan batasan sanda tafara baccin ba , duban Hameed tayi sannan tayi k'asa da kanta dan wani kwarjini yake mata , shuru sukayi kowanne yana sak'e sak'e aransa , can Hameed ya nisa yace " kishiga Office d'ina sai ki kwanta a ciki in bacci kike ji , Aysha a hankali tace " ba bacci nakeji ba yanzu ma bansan sanda nafara gyangyad'i ba , Hameed ya dube ta sannan yace " amman kinsan dai nan akwai sauro kuma cizon sa zai iya haifar miki da zazzab'i , Aysha tace " ai zan iya shiga d'akin da Gogal take inyaso danaga ta farka sai na fito ko , Hameed yace " ai dama ba'a hanaki shiga ba kwata kwata kawai dai a yanzu tunda tana farkon ciwon dole in ta farko taganki abin zai dawo mata sabo , amman nan da zuwa safiya ma insha Allah zaki iya shiga ko yaushe kikeso , Aysha ta share hawayen da ya gangaro mata sannan tace " nagode Dr bari nashiga kafin ta farka sai na fito , bata jira cewar sa ba ta tura k'ofar d'akin tashige abinta........ Hameed komawa yayi office d'in sa ya had'a ruwan tea yana sha , tunowa yayi ba lallai in Aysha taci komai ba , da sauri yatashi ya d'auki flast d'in shayi da biscuit ya nufi wajen nata , .. Yana zuwa ya tura k'ofar d'auke da sallama sai dai ji yayi shuru ba a amsa masa ba , gadon da Gogal take ya kallah yaga idanun ta a bud'e alamun ta farka , tuni ya duba ko inah baiga Aysha ba , hakan ya sheda masa ta fita kenan dataga Gogal d'in ta farka , to ina ta shiga tunda bai ganta a waje ba kafin ya shigo ? gadon ya nufa d'auke da murmushi yana fad'in " sannu da jiki Mama dafatan yanzu babu abinda ke miki ciwo ko ? Gogal ta d'aga kai batare da tayi magana ba , Hameed yace " bari na had'a miki ruwan tea kisha sai inbaki magungunan ki kisha ko , da sauri ya had'awa Gogal ruwan shayi sannan ya tashe ta ya jingina jikin filo, hawowa yayi kan gadon da kofin tea yashiga bata a hankali yana lallab'a ta , aikuwa babu laifi sosai Gogal tasha ruwan shayin wanda yaji kayan k'amshi , .. Duk abinda akeyi Aysha na hangen su ta cikin toilet d'in d'akin , tunda taga Gogal tafara motsi tayi saurin shigewa toilet d'in tare da addu'ar Allah yakawo Dr.Hameed d'in , Allah kuwa ya amshi addu'ar ta saigashi yazo har da Shayin sa a hannu , dama tunani take me za'abawa Gogal d'in taci gashi dare yayi , yadda Hameed ke bawa Gogal tea cike da nuna kulawa ba k'aramin birgeta yayi ba , take taji wata k'aunar sa na ratsa duk ilahirin jikinta tabbas Hameed shine irin mazan da mata ke muradin samu , da ace lokacin da take Sayyadar tace da babu abinda zai hana ta amincewa da auren Hameed , dayake toilet d'in a tsaftace yake shiyasa Aysha bata damu da zaman ta a ciki ba,.... Hameed ya kammala bawa Gogal magungunan ta , duban sa tayi kamar zatayi magana sai kuma ta fasa , Hameed yayi murmushi yace " ki kwantar da hankalin ki karkisa damuwa aranki yanzu ki kwanta ki huta zuwa safiya , Gogal itama murmushin ta maida masa batare da tace komai ba ta kwanta a hankali da taimakon Hameed..... Hameed zama yayi a gefen Gogal yana ta danna wayar sa , ba'afi minty 10 ba Gogal ta koma bacci abinta , rufe mata jiki Hameed yayi tare da rage mata gudun fanka sannan ya mik'e zai fita daga d'akin , gani yayi ana k'ok'arin bud'e toilet dan haka ya tsaya dan ganin waye , Aysha ce ta fito tana sunkuyar da kanta k'asa , Hameed cikin ransa yace " dama tana cikin toilet duk wannan dadewar ? A fili kuma ya kalleta yace " Dama kina cikin toilet ? Aysha ta d'aga masa kai batare da tayi magana ba , d'an tab'e baki yayi sannan yace mata "ga tea can a flast ki tsiyaya kisha sannan ya mik'a mata biskit yace "ki had'a da wannan dan nasan ba lallai inkinci wani abun ba , yana gama bata tasa sannu biyu ta ansa tare da yi masa godiya ya shige ya fice daga cikin d'akin....... Washe gari tun asuba Aysha ta farka dama ba wani bacci tayi me tsayi ba , shiga toilet tayi ta d'auro arwala sannan ta fito ta shimfid'a d'an kwalin ta ta tada sallah , bayan ta idar ta zauna tana lazimi da yatsun hannun ta , abinda Aysha bata lura ba shine tun fitowar ta daga toilet Gogal ta farka ta zuba mata idanuwa , wani kallo Gogal takewa Aysha wanda yake nuni da tanajin harda sakacin ta a lalacewar da yarinyar tayi , kuma a yanzu tadaina ganin laifin Ayshar dan duk acikin abinda yafaru da ita ta had'u da yaudarar 'Yaya maza ne , Abinda yafi d'aga mata hankali shine jin wai har ciki Aysha tayi kuma taje ta zubar batare da ita ta fahimci hakan ba , tabbas tayi sakaci sosai kuma nadama tashige ta na yadda tayi sakaci da rayuwar Marainiyar Allah , hawayene suka shiga zubowa ta idanuwan Gogal tanajin tausayin kansu , yanzu wane namijin arziki ne zaiso Ayshar har ya aure ta ? tabbas wannan abu zaiyi wuya tunda ta riga tazama uwar mata , Aysha d'aga hannu tayi tana addu'a akan Allah ya bawa Gogal lafiya tare da neman gafarar ubangiji akan laifikan ta data aikata , hawaye na zuba tana fad'in " Astagafurullah Allah natuba kayafemin bazan sake aikata zina ba , duk addu'ar da takeyi Gogal najin ta tana kuma amsawa da Ameen , sai da ta shafa addu'ar sai taji Muryar Gogal nacewa Sayyada zo ki kaini band'aki in kama ruwa nima nayi sallah , Aysha da sauri ta waiwayo dan batasan sanda Gogal d'in ta tashi ba , wani sanyi taji a ranta hakan na nufin Gogal ta rage fushi da ita kenan , da sauri ta nufi wajen gadon tana kamo ta tashigar da ita band'aki , bayan ta gama kama ruwa tayi arwala sannan Aysha tazo ta fito da ita daga cikin toilet d'in ,..... Bayan ta idar da Sallah Aysha ta dube cike da jin wata iriyar kunyar ta tace " ina kwana ya sauk'in jiki ? Gogal ta amsa da lafiya lau jiki Alhmd babu inda kemin ciwo , shuru ce ta biyo baya kafin Gogal tayi gyaran murya tace " Aysha inaso kibani aron hankalin ki , tabbas kinyi wauta da tun farkon da Khalid ya kusan ceki baki gayamin ba , da tun a lokacin zan d'auki mataki akan hakan , amman saboda kina tsoron kar nashiga damuwa yasa kika cuci kanki har abin ya girmama , duk da nima nataka rawa a komawar ki haka ta b'angaren sakaci da rashin saka idanu akan ki , duk irin yadda kike kashe mana kud'i bantab'a kawo wa ba a makaran ta kike samu ba , tabbas nima nayi kuskure babba kuma ina neman yafiyarki a akan hakan , Aysha da take kuka tunda Gogal tafara magana da sauri tace " baki da laifin komai Gogal , nice na zalinceki da halayena masu kyau taya zaki yadda zan aikata wani halin makamancin wannan , ban daina shigar mutunci ba ban kuma daina janyo aya ba duk lokacin damu ke tare dake , nice na yaudareki da fuska biyu wacce na zama saboda dalilin d'aukar fansa , tunda ga lokacin da Khalid ya yaudareni kuma yazo ya gujeni tare da gayamin maganganu mara sa dad'i nafara shirin d'aukar fansa araina , kwata kwata banyi basirar cewa cutar da kaina zanyi garin d'aukar fansar ba , idanuwa na sun rufe wutar d'aukar fansa na ruruwa a cikin zuciyata , na d'auki fansa Kamar yadda na k'udurta amman ina meyin tarin nadama da abinda na aikata wa rayuwata , wallahi natuba Gogal bazan k'ara aikata zina ba har nakoma ga mahaliccina , jikin Gogal ta kwanto tana kuka me tsuma zuciya tare da tarin yin nadama game da son zuciyar ta data bi.......... _Ina farin cikin sanar da Mata 'Yan k'walisa da Amare masu shirin shiga daga ciki , ga dama ta samu maza ku garzayo dan gyara jiki tare da mallakar tsumi gangariya ,_ *Akwai maganin gyaran nono ga macen da take shirin yaye yaron ta , ga turarukan gyaran jiki dana turara d'aki da na wanka tare da Humrah me ratsa zuciyar megida , akwai kulacca da man shafawa me kamshi ,* _Uwargida Amarya maza ku garzayo dan mallakar naku , gyara shine mace Mata kutashi ku gyara dan kwato mazajenmu daga wajen matan banza 🀝🏻πŸ₯°_ *Dan samun kayanmu ku tuntubi wannan number 07046107812* Sai najiku🀝🏻πŸ₯° An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 13 of 13