Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
, tana fito tasaka wasu riga da wando pakistan , rigar takawo mata har gwiwa wandon kuma daga k'asa n sa ya d'an tsuke amman kayan sosai sunyi mata kyau , wani hijab d'an k'arami iya kafad'a ta d'auka ta zura tare da fito wajen Dinning , Ganin Gogal tayi a zaune itama tana shan Kunun gyadar , tana zuwa ta gaida ta sannan tace " ai tund'azu na fito naga baki fito ba , Gogal tace " natashi ne jikin nawa babu dad'i shiyasa , amman yanzu naji sauk'i tunda gashi nafito ina karyawa , Aysha tace " kwana biyu ma ai bakizo munje ganin likita ba , bari mugama karyawa yanzu sai muje kiga likita dan ciwo tun yana k'arami ake tarar sa , Gogal batayi musu ba dan tanason ganin likitan itama , Bayan sun kammala Gogal ta mik'e zatayi wanka ta shirya su tafi , Aysha kuma ta shigs d'akin ta ta kuma gyara jikin ta tare da feso turare sannan ta fito , zama tayi a palor jiran fitowar Gogal...... wayar ta ce ta shiga Ring ta d'auka dan ganin waye me kiran nata , Khalid tagani tayi murmushin mugunta tare da d'agawa cike da kissa , Hy Babyna kankana uwar ruwa kinsan har mafarkin ki nayi wallahi jiyan nan kin bani dad'i , kusan sumar dani kikai fa gaskiya ina kwad'ayin ki yauma ki daure muhad'u , Aysha tayi wani murmushin mugunta sannan tace " kar ka damu ai ni takace kuma kaima nawa ne komai kakeso zanyi maka , in ban faranta ranka ba ran wazan faran ta My Dear ,, wani dad'ine ya kama Khalid tare da wani shauk'i , tabbas bazai yi gangancin rabuwa da Aysha ba saboda ta ko'ina tagama had'uwa , katse masa tunani tayi dacewa Babyna inason kamin wata alfarma dan nasan nafi k'arfin komai agurinka , Khalid yace " inajinki Babyna fad'i kome kikeso indai ina dashi to zanbaki , Aysha tace " Wata Auntyna ce tayi order kaya shine aka rik'e mata , yanzu haka sunce mata indai zasu sakar mata kaya to dole sai ta turo musu da kud'i dubu d'ari shida da Hamsin , kuma kwata kwata kud'add'en hannun ta basu kai hakan ba , shine tamin magana akan in nemo mata dan Allah zuwa lokacin da zasu sakar mata kayan nata , Kayan 10M. tayi order da zarar ansakar mata kayan zata baka kud'in , Khalid yayi d'an dum sannan yace " Babyna kinsan kwata kwata kud'in Account d'ina yanzu saura dubu d'ari Bakwai , dama jiya na fad'a miki ko nawa ne aciki kuma kinga kinyi siyayya a ciki , amman bakomai ai nima Auntyna kuma banaso ace Babyna tana damuwa , dan nasan indai ban baki ba wani zaki ce saki tambaya nikuma ina kishin hakan , nan Aysha tashiga yiwa Khalid godiya tare da masa dad'in baki , tuni ya shagalce yaji ko 20M. Ta tambaya zai bata tunda ta wuce haka a gunsa , dan shi yagama tsaida magana ita zai aura tunda ga yadda ta sarrafashi jiya ta gama dashi , yayi sex da mata da yawa amman ba wacce ta iya sarrafashi tamkar Aysha , gata Allah yayi mata baiwar ni'imah tamkar k'orama , a kasalan ce yace " Babyna ki turomim account d'in da zan sa kud'in , Aysha ta amsa masa da zata turo sannan tace " kawai ka turomin dubu d'ari Bakwai d'in sai in ciri dubu Hamsin d'in naje nakama mana Hotel anjima , aikuwa ba musu Khalid na rawar jiki ya turawa Aysha duka dubu d'ari bakwai d'in , koda Aysha taji kud'in sun shigo tayi wani murmushi sannan tace " taka ta k'are Khalid sai wani kokacin , Aysha bazaka sake ganin koda tafukan hannun ta ba bare yakai ka da ganin jikin ta , tasan yanzu bashi da ko ficika a account kuma yau zai zama tarihi a gidan su Ruma , .... Gogal ce ta fito suka fice harabar gidan , motar Aysha tashiga tare da bud'ewa Gogal , Gogal da k'yar ta yadda ta shiga saboda cewa tayi Aysha bata iya motar ba zataje ta yar da ita , Habu yana dariya yace " aikuwa ta iya sosai Gogal kishiga kawai Allah ya tsare sai kun dawo , Da Ameen Gogal ta amsa tana shiga sannan tace " kijanina hankali nidai , ......... Sorry kuyi hakuri😰😰 [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR HANNU* πŸ€’πŸ€’ _NA_ *Zee MD* *WOMEN WRITERS ASSOCIATION*πŸ“š ( Domin Marubuta Mata ) ✨ (W.W.A) ✨ https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/ *Bisimillahir Rahamanir Rahim* _Page._ 30 Yana shiga ya kira number Aysha , tana d'agawa ya tambaye ta Room number d'akin datake , nan ta fad'a masa ya kashe wayar ya nufi d'akin.... Tuni Aysha tashiga toilet yayin da Leeemah ita kuma ta haye gado tana lulleb'e jikin ta da bargo , Khalid yana zuwa ya tura k'ofah dan ta sheda masa k'ofah a bud'e take kawai yashigo , koda ya shiga ganin Aysha akan gado kawai yafara cewa " wato Babyna har kingama shiryawa ni kike jira ko ? da k'yar Leemah ta 'iya kwai kwayon muryar Aysha tace " haba Dear kawai kataho nima a duk na zak'u kai kawai nake jira , dayake kanta na cikin bargo shiyasa baidamu da canjin dayaji muryar ta tayi ba , tuni yahau cire kayan jikin tare da fad'in "Babyna ko tayin cire kaya babu kin wani shige bargo , hayewa gadon shima yayi tare da shigewa cikin bargon , dai dai lokacin su Ruma da iyayen ta suka banko k'ofar cikin d'akin , dayake ya manta bai rufo shiyasa suka sameta a bud'e , shima kuma adai dai lokacin yaga fuskar Leeemah yabud'e bargon cikin furgici , aikuwa idanun suka had'a da Alhaji Ashir da Mumyn Ruma da ita kanta Ruman , da sauri Khalid ya rintsa idanu yana jiran yaga wai ko mafarki yake , sai dai jin Muryar Alhaji Ashir ya tabbatar masa da ba mafarki yake ba idanun sa biyu , Alhaji Ashir yace " Nagode wa Allah daya nunamin halinka tunkafin na had'a zuria dakai , duk cin amanar da kake shirin yimin kuma naji komai , azzalumi macuci duk kud'adena dakasan ka d'iba kadawo min dasu , nabaka nan da awa 24 in bahaka ba zansa a kullemin kai , samnan Mota ta dakake yawo kana dibar matan bariki kuna yawon banza kabani mukullin abata na wuce da ita , Ruma ta kallesa da mugun kallo tace " Mayaudari Munafiki Allah ya tsareni daga tarkon ka ta sanadin Karuwar ka , ta kalli Leeemah tace " nagode miki da yadda kika farkar dani daga baccin danake , kika cireni daga duhu zuwa haske kika rabani da auran Fasiki Macuci , ina miki fatan shiriya daga wannan rayuwar da kika saka kanki kema , tana kaiwa nan ta fice daga cikin d'akin tana jin wani abu me zafi a k'irjin ta , tabbas Khalid ya cuceta da ya dasa mata son shi aranta , tasan kafin fitarsa dole sai tasha wuya ,.... Alhaji Ashir ya nufi kan dirowar gado ya d'auki mukullin motar sa ya fice daga d'akin , dama Mumy tunda Ruma ta fita itama tabi bayan ta suka fice dukan su daga d'akin....... Khalid kallon sa ya maido kan Leeemah yace " dan Ubanki wace ce ke ? tuni ya fito daga cikin bargo yana neman abinda zai doki Leeemah dashi , da sauri Aysha ta fito daga toilet tana fad'in " dakata Khalid karka kuskura kadake ta , jiyowa yayi yana duban Aysha sai sannan yafara tunanin duk makircin tane itace ta had'a masa wannan shirin , kallon ta yashiga yi tare dajin wata tsanar ta aransa , Cikin kakkausar murya ya furta " menayi miki kika sakamin da irin wannan abun ? kin tozartani a idanun sirikaina sannan kin zubarmin da mutunci , inaso ki fad'amin dalilin ki nayi min wannan tozarcin haka , wani shu'umin Murmushi Aysha tayi sannan ta zauna a gefen hannun kujera tace " Khalid kenan Manyan gari , Inaso kasani Nice Ayshar Gogal wacce ka lalatani , kaine namijin da yafara ketamin mutuncina , ka Yaudareni ka wulak'antani sannan daga k'arshe ka gujeni , ta sanadin abinda kamin yasa nazama *'Yar Hannu*, tundaga lokacin jikina yazama abin hutawa ga Maza masu hali irin naka , sai dai duk iskancina inayin sane akan taku , na dad'e ina jiran wannan ranar da zatazo ace gashi kazo hannuna amman ban samu ba sai yau , kad'auka kaci bulus ko ? ka d'auka Ayshar da ka lalata bata duniya ma ko ? to kasani na rok'i Allah yakawoni wannan ranar da zan d'au fansa akan ka , kuma daga rana irin ta yau natashi daga sunan *'Yar Hannu* nakoma Asalin sunana Sayyada Aysha , wata zufa ce ta karyowa Khalid jin Ayshar Gogal ce wacce yayiwa Fyad'e har tasamu ciki tazo masa da maganar cikin ya koreta , To ya akayi yakasa gane itace ? taya tazama wata hamshak'iyar mace haka ? wannan gidan datake to gidan waye sanin da yayi musu basu da kowa kuma basu da komai , to gidan waye wannan d'in datake a cikin sa ? kuma ina Gogal tabbas yasan ya aikata wa Aysha ba dai dai ba dole hakkin ta ya bibiyesa...... [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR HANNU* πŸ€’πŸ€’ _NA_ *Zee* *MD* *WOMEN WRITERS ASSOCIATION* πŸ“š ( Domin Marubuta Mata ) ✨ (W.W.A) ✨ https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/ *Bisimillahir Rahamanir Rahim* _Page._ 28 Tunda suka fara tafiya Aysha ta kunna karatun Alk'ur'ani me girma , sabanin indai ita kad'ai zata fita sai dai tasa Music tana ji , a haka har suka k'araso Cikin Asibitin , samun waje Aysha tayi ta faka motar sannan suka suka fito ita da Gogal suna takawa har cikin harabar zaman masu ganin likita , wajen bud'e files Aysha taje tagama biyan kud'i sannan tadawo su ka zauna suna jiran kiran Dr. .... Ba'afi Minty 5 ba aka kirasu suka shiga ciki , Bayan tambayoyin da Dr yayi wa Gogal akan yadda takejin jikin nata tashiga bashi bayani yana rubutawa , nan ya shiga baya shawarwari game da yadda zata kula da jikin ta , ya sheda mata hawan jini gare ta kuma yana neman tab'a mata kwakwal wa mutukar bata daina saka damuuwa aran ta ba , Aysha ta dubi likita sannan ta dubi Gogal tace " tunanin me kikeyi haka da har yake neman rikita kwakwal warki ? dan Allah Gogal kirage saka damuwa aranki duk duniya kinsan bani da kowa in bake ba , kema kina so narasaki ne ? Gogal tayi murmushi sannan tace " Aysha mutuk'ar bakiyi aure ba to tabbas bazan daina damuwa ba , Aysha tace " Aure lokaci ne Gogal indai lokacin yi yazo ko nashirya ko ban shirya ba to tabbas zanyi , nidai kici gaba da yimin addu'a Allah yazab'amin miji nagari , Dr yayi murmushi yana duban su dan sun burgeshi sosai , nan yace da gaskiyar Hajiya gaskiya yakamata ace k'anwata kin yi auren nan dan Hajiya tasamu farin ciki , Aysha tayi murmushi tana cewa " zanyi lokaci Dr . Nan suka mik'e yabasu kati tare da ce ma Aysha lallai su siyi magun gunan ta dunga sha , .... Bayan fitowar su Aysha ta shiga wajen sai da magunguna ta siyo samnan ta fito , tana fitowa suka nufi wajen da motar su take zasu shiga , kamar daga sama Aysha taji ana k'wala mata kira " Aysha Uwar ruwa kankana uwar dad'i daga ina zuwa ina ? cak Aysha ta tsaya wata zufa tana karyo mata , Gogal itama juyowa tayi tana kallon wanda yake kiran Ayshar da wannan sunan , Jabir ne a tsaye ya hard'e hannun sa a kan k'irjin sa yana zuba mata wani murmushi tare da shu'umin kallo , Aysha tayi ta maza ta dake tana d'auke kai tamkar bata gansa ba , murfin motar ta ta bud'e tare da cewa Gogal " shigo mutafi Gogal kinga ana rana kar ta dameki da yawa , Gogal tace " waye wannan d'in ? kuma wanne suna naji yana kiranki dashi haka ? Aysha tace " anya dani yake kuwa dan ni bantab'a ganin saba ma sai yau , sai dai ko nayi masa kama da wata wacce yasani ne , Jabir yayi wani shu'umin murmushi yace " Hajiya barka da wannan lokacin ya gida , Gogal tadubesa sannan tace " lafiya lau amman yaro inaso insan kai waye kuma meye had'in ka da jikata naji ka kirata da wani banzan suna ? Murmushi Jabir yayi sannan yace " ki tambayeta zakiji komai daga bakin ta nabarku lfy , yana gama kaiwa nan ya dubi Aysha ya kashe mata ido tare da barin wajen , Aysha jitayi tamkar tabi bayan Jabir ta rufesa da duka saboda abinda yayi mata , Gogal zubawa Aysha idanu tayi tana mata kallon tuhuma tabbas akwai abinda Aysha keyi wanda bataso tasani , in ba haka ba taya zai kirata da irin wannan sunan haka , Aysha duk jikin ta yayi sanyi ganin irin kallon da Gogal keyi mata , Gogal xagayawa tayi ta shiga motar yayin da Aysha ta d'an tsaya tana nazarin yadda zata kare kanta a wajen Gogal , a haka ta shiga motar taja su suka bar harabar asibitin....... Tunda suka taho har yanzu Gogal batayi magana ba kuma bata kalli inda Aysha ke tuk'i ba , Aysha cikin ranta sai tsinewa Jabir take da irin abinda yayi mata , a haka suka k'araso cikin gidan Gogal ta fice daga motar tashige cikin gidan abinta , Habu sai sannu da zuwa yake masu amman ko kallon sa Gogal batayi ba ta shige , zama Aysha tayi a cikin motar ta tana jin tamkar kar tashiga cikin gidan , me zata cewa Gogal ta kare kanta ta nuna mata batasan Jabir d'in ba , ta dad'e a zaune a cikin motar kafin ta fito tashiga cikin gidan gwuwa a sab'ule , ... Tunda Gogal ta shiga cikin gidan take zagaye palor gidan , tabbas dole akwai abinda Aysha ke b'oye mata , ita kanta akwai wani abun in Aysha tayi sai tashiga mamakin Ayshar , tana tsaye a hakan Ayshar tayi sallama ta shigo cikin palor , k'arasawa Aysha tayi kusa da ita tana cewa " dan Allah Gogal karki saka abun nan aranki kinajin abinda likita yace miki , wani kallo Gogal tayi mata sannnan tace " inhar kinaso in yarda dake to lallai inason sanin gaskiyar komai , Aysha cikin zuciyar ta ta furta " bazan iya gaya miki gaskiyar komai yanzu ba , amman nasan wata rana sai kinsani duk b'oye b'oye na , a fili kuma ta furta " iya gaskiya ta nafad'a miki wallahi bansan shi ba ban kuma tab'a ganin sa ba , ranar nan ma dana dawo daga makaranta akwai wasu mata da nahad'u dasu a hanya suma sunkirani da irin sunan da wannan d'in ya kirani dashi , dana tsaya a wajen su nace bani bace suna kallona suka yarda , sai dai sunce min akwai wata 'Yar uwar su wai muna kama da ita sosai in dai aka gan mu to tabbas za'ace 'yan biyu ne , kuma suka tambayeni suna na na sheda musu nan ma sukace sunan mu d'aya da ita , Aysha data kalli Gogal ta gefen ido ta ga yadda maganar ta shigeta tuni tayi k'asa da gwuwowin ta taci gaba da magana muryar ta na rawa tace " bana b'oye miki komai Gogal kinsani , dan Allah kar zuciyar ki tafara rawa akaina ki yarda da Ayshar ki bazata tab'a aikata wani abu wanda zai saka zuciyar ki tayi rawa akanta , tuni jikin Gogal yayi sanyi tasamu waje ta zauna tana kallon Ayshar , sai dai har yanzu zuciyar ta takasa yardar mata abinda Ayshar tace , nisawa tayi sannan tace " shikenan na yarda Allah ya kyauta , cikin zuciyar ta ta k'udurce lallai yanzu dole tasa ido sosai akan Aysha shine kawai zai tabbatar mata da gaskiyar abinda Ayshar tace , Aysha ta d'auko jakar ta ta zuge tare da d'auko magungunan Gogal tana fad'in " bari na d'auko miki ruwa kisha magungunan yanzu saboda yanayin jikin naki , Gogal tace " barshi kawai zan shiga d'aki na kwanta zansha kafin na kwanta d'in , tana fad'in haka ta mik'e tashige d'akinta....... Aysha tabi bayan ta da kallo har ta shige , mik'ewa tayi tashiga cikin d'akin ta da sauri tana rufo k'ofah sannan ta d'auko wayar ta tashiga laluben number Jabir , dama ita tana da number sa shine dai bashi da ta ta , aikuwa tana kira number tashiga sai da ta kusa katsewa sannan ya d'aga , Aysha cike da jin zafin sa tace " me kake nema dani ne mai nayi maka da kake bibiya ta kakeso kasa Kaka ta cikin tashin hankali ? Jabir tunda tafara magana yagane wace yafara wani shu'umin murmushi , sai data gama sannan yace " Hajiya Aysha kenan ashe kina gari daman , aini na d'auka ko kina wata k'asar saboda yadda kika samu duniya , wata tsawa ta daka masa sannan tace " ina so kafad'amin meye damuwar ka dani da kake bibiyar rayuwata ? Jabir yace " Aysha ina bibiyar ki ne dan inasonki kuma inaso ki shiryu kidaina abinda kike , sai dai kashh kinkasa bani dama ko sau d'aya inyi magana dake , kuma koda yaushe cikin shigar dani kike saboda kin maidani wani wawa , Abinda yasa nayi miki haka kuma saboda ta hakan ne kawai nasan zaki nemeni muyi magana , kuma gashi hasashena ya gayamin gaskiya , Aysha meyasa kika zab'i ki ringa shiga rigar mutunci kina aikata fasik'an ci ? kuma abin haushin duk abinda kike har yanzu kakar ki takasa ganewa , nikuma abinda nakeso shine ki tagane wace ke ko zaisa ki gyara halinki , Aysha a fusace tace " meye damuwar ka da shiryuwata da rashin ta ? kai uba nane ko wani nawa da zaka shiga rayuwa ta ? inaso kasani wallahi mutuk'ar baka rabh dani ba indai na juyo kanka bazaka ji da dad'i ba , Jabir yace zakimin yadda kikayiwa Farouq ne da Mahaifinsa ko ? take k'irjin Aysha ya buga cikin zuciyar ta tace " wannan kodai ba mutum bane taya yake sanin komai nawa ? katse mata tunani yayi da cewa " kina mamaki da yadda nasan komai naki ko ? to kamar yadda kika iya taku nima haka nake nawa , nabarki lfy ki k'ara shiri My Aysha naki Jabir d'an sa idon ki , tuni yakashe wayar yabar Aysha da waya rik'e a hannu tayi tsaye cak....... *Comment* plssπŸ₯°πŸŒΉ [11/08, 3:43 pm] Maman Islam: *'YAR HANNU* πŸ€’πŸ€’ _NA_ *Zee MD* *WOMEN WRITERS ASSOCIATION*πŸ“š ( Domin Marubuta Mata ) ✨ (W.W.A) ✨ https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/ *Bisimillahir Rahamanir Rahim* _Page._ 32 A b'angaren Hameed kuwa duk wata damuwar sa yanzu ta ragu , farga bar sa guda d'ayace Akan Aysha Ko zata amince masa ? ranar duk wani iri yake jin sa Allah Allah yake dare yayi yaje yaji me zata ce masa , Hajiyar sa sai tambayar sa take meke damun sa amman sai yace mata bakomai , ko abinci kasa ci yayi ranar haka ya yini cikin d'akin sa , sai wajen magriba yayi wanka ya shirya sannan ya fito....... Ana idar da sallar Magriba Hameed yanufi gidan su Aysha , sai dai me yana zuwa yasamu gidan a rufe da kwad'o, wata fad'uwar gaba yaji ta ziyarce sa cikin zuciyar sa yashiga cewa " haba Aysha meyasa zaki yimin haka ? nasan saboda ni kika kuma tashi daga wannan gidan , da kin san baki da amsar da zaki bani da kin cemin inyi hak'uri bakya sona , tuni idanun Hameed sukayi jawur saboda takaicin ganin gidan a rufe , ya dad'e a tsaye a k'ofar gidan yana kai kawo har yagaji ya juya ya nufi gida , sai dai yana zuwa k'ofar gida ya tsaya ya kasa shiga yana nazari , wata zuciyar tace masa " kodai kaje tsohuwar unguwar su ko nan sukaje ? tunda yasan dai ba tashi sukayi ba , haka ya shiga gida ya fito da motar ya nufi unguwar su Aysha ta da...... Aysha tana zaune cikin motar har aka idar da sallar Magriba , tuni tagama yankewa kanta zata shiga cikin gidan tayiwa Gogal bayanai koda zata kashe ta , tasan duk duniya bata da kamar ta kuma bazata iya guduwa tabar ta ba , haka ta fito daga cikin motar tanufi cikin gidan..... Gogal tun sanda taje Makarantar su Aysha ta buk'aci son ganin Shugaban Makaranta , koda suka shiga office suka gaisa dan yasan Gogal sosai , nan take tambayar sa Ya k'ok'ari da hidima sannan ta fara masa godiyar irin Kyautar da Aysha tasamu , shuru yayi yana nazari kafin yace " ban fahimci abinda kike nufi ba , nan tashiga ce masa kyautar gida da Aysha tasamu da kuma motar har ana shirin bata kujerar saudiya , nan Shugaban Makaran ta yashiga jimami da jinjina maganar ta , andad'e ana kawo masa zancen Aysha tana yawon banza kwata kwata bai mai da hankalin sa akan hakan ba , yasan Aysha ta dad'e bata zuwa makaran ta amman inda yayi kuskure shine bai je yasamu Gogal da maganar ba , nan ya shedawa Gogal komai nagame da halayen Aysha , kuma yace baisan zancen gida da motar ba , dan yafi shekara d'aya da rabi rabon da yaga Aysha tazo makaranta , koda Gogal taji maganar shugaban Makaranta tuni jikin ta ya d'auki rawa , take ta yi masa sallama suka nufo gida ita da Habu........ Bayan ta kwaso kayan ta ta sheda wa Habu shima ya kwaso nasa kayan , nan suka nufo tsohon gida suka bud'e tare da taimakon Habu suka gyara gidan , tunda Gogal ta shiga cikin gida tashiga d'akin ta na da ta kwanta saboda zazzab'in da ke barazanar rufe ta , hawaye ne yashiga zubowa ta idanun Gogal cikin zuciyar ta tashiga cewa " tabbas Aysha kin cuceni kin cuci rayuwar mu , menene wanda kika nema kika rasa da kika zab'i irin wannan Rayuwar ? tamkar wacce Aysha ke gaban ta tadunga fad'in " wanne irin fad'i tashine banyi ba dan ganin rayuwar ki tasamu nagarta , wata zuciyar tace " kina da laifi kema taya zaki dunga ganin ta tana kashe kud'i amman kiyi shuru , haka dai Gogal ta shiga zancen zuci tare da ambaton istigifari dan neman tuba akan sakaci datayi har Aysha tazama haka , jira take taga Ayshar zata biyota nan gidan ko kuma bazata biyota ba ? kuma in tazo me zata ce mata wacce k'aryar zata kuma yi mata a karo na biyu..... Aysha tana shiga cikin soron gidan tafara sallama a hankali , muryar ta har rawa take tana k'ara yin sallamar , jin ba'a amsa mata ba yasa tashiga tsakar gidan da duhu yafara mamayewa , haka ta nufi cikin d'akin Gogal d'in wanda ta taga shi kad'aine a bud'e , nan ma sallama tayi tana me raba idanuwa dan ta hango inda Gogal d'in take , da k'yar ta hangota a kan sallaya tayi jigum tamkar wacce ma bata motsi , cikin sanyi murya Aysha ta furta Subhanallah , daga bakin k'ofah ta tsaya tare da zubewa kan gwuiwowin ta tana sharar Hawaye , Sunfi Minty 5 a haka kafin Gogal tafara magana " Aysha meyasa kika zab'i wannan bak'ar rayuwar ? Meyasa kika canza halayyarki da nasanki tun asali da ita ? Aysha kin cuceni da kika maida rayuwar ki a banza , kin zab'i siyar da mutuncin ki akan son kud'i da kuma kyale k'yalen duniya , kin ci Amanata a matsayina na wacce nazamar miki uwa da uba , duk da ina da laifi nayin sakaci har kika zama cikakkiyar *'Yar Hannu* , nakasa saka idanuwa akanki nakasa bibiyar yadda kike mu'amala da kud'i , nabi son zuciya na dunga d'ora miki wasu nauyikan namu , bandamu da irin kud'in da kike samu ba bandamu da irin yadda kike siyo mana kayan Abinci ba , duk da kin yi min k'aryar cewa koyarwa kike a Makaran ta ake biyanki , amman ban bibiya na tabbatar da gaskiya ne ko kuma ba gaskiya ba , hawayen dake zuba a fuskar ta ta goge kuma dai dai lokacin 'yan nefa suka kawo wuta , Aysha idanun ta akan Gogal itama sai zubda hawaye take tanajin wata iriyar nadama na shigar ta , tabbas tayi nadama da irin rayuwar da ta jefa kanta a ciki , kawai shashshekar kukan su ce ke tashi a cikin d'akin , Gogal ta dube ta tace inaso a karo na biyu kifad'amin gaskiyar abinda yasa kika zab'i irin wannan rayuwar , kuma wallahi in har kika kuma yimin k'arya wlh bazan yafe miki ba , nan Aysha tasa kuka tare da duban Gogal tace " zanfad'a miki wallahi amman dan Allah karki tsaneni kuma karki koreni wlh bazan iya rayuwa ba mutuk'ar bana tare dake , runtse ido Gogal tayi cike da tsawa tace " kifad'amin inajinki ,....... Aysha tuni tashiga bawa Gogal labarin yadda akayi tafara bin maza , tunda ga kan Fyad'en da Khalid yayi mata da kuma cikin da yashiga har ta zubar dashi da yadda Farouq yayi mata shima , duk irin mazan da ta kula da kuma irin yadda take yi inzataje gun su bata b'oyewa Gogal ba sai data gaya mata , ..... Gogal tuni tayi mutuwar zaune dan take tafara nuna Aysha da d'an yatsa tana k'ok'arin yin magana , wani tarine ya turnik'e ta ta dafe k'irjin ta sannan ta daina motsi , da gudu Aysha ta nufeta tana k'wallah k'ara " dan Allah Gogal ki yafemin wallahi natuba

Chapter 10 of 13