Reading LAUJE CIKIN NAƊI by ZAINAB FALALU Chapter 5 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shirun da yawa yasa ta murɗa handle ɗin duk a
tunanin ta ba ze buɗe ba

Aikuwa tana murɗawa ya buɗe,

Leƙawa tayi ciki, ganin babu kowa yasa ta jayo ƙofar da niyar kullewa, amma sam zuciyar ta
taƙi barin azalzalar da lokaci zuwa lokaci takan ji hakan



Sam mumtaz kasa daurewa tayi seda ta biye wa azalzalar zuciyar ta taƙara shiga office ɗin



Memakon data shiga ta yi abinda aka aiketa,
Ina ta mance tunda ta ɗora idanun ta akan abin hannun data gani ajiye akan teburin likitar ta
nufe shi kanta tsaye, jikin ta babu inda baya rawa tsabar luguden data ke ji a cikin zuciyar ta

Tana kaiwa teburin ta dafe abun hannun nan dake ta walwali da ɗaukar idanu daga ganin shi
kasan dutse ne me mugun daraja

Tana ɗauka ta zira shi a aljihun doguwar rigar ta

Seda ta tabbatar da taji shi a jikin ta tukun ta sauke ajiyar zuciya me nauyin gaske, bata sake
kallon komi a wajen ba ta juya tafice da mugun sauri har tana harɗewa da ƙafafuwan ta.




Mumtaz na fitowa daga office ɗin dattijuwar likitar na shawo kwana,

Juyawar da mumtaz tayi yasa likitar bataga fuskar ta ba

Kafin ta ƙaraso mumtaz ta yi gaba,

Gaba kaɗan ta ƙara se ga Abba ƙ
Fuska a ɗaure yace

"daga kiran dr se kije ki shantake?"



Da sauri ta sadda kanta a ƙasa, duk a tunanin ta ze gane abinda tayi a cikin ƙwayar idon ta,
tace



"Bata cikin office ɗin, shine na tsaya jiran ta, da naga bata dawo ba shine na tawo"



"okay" kawai Abba ƙ yace ya juya suka koma ɗakin.




Su Abba na shiga ɗakin likitar ta turo ƙofa itama



Da fara'a sosai a fuskar ta suka gaisa da su Abba, sannan ta ƙarasa kusa da mama dake zaune



Mumtaz kam ƙasa tayi da kanta tana ƙara jin faɗuwar gaban ta na daɗa tsananta, a hankali ta
saka hannun ta cikin aljihu ta lalubo abin hannu taji yana nan
Ajiyar zuciya ta sauke wanda yasa daga mama har likitar kallon ta.



Murmushi likitar tayi, sannan tace

"wannan ajiyar zuciyar fa ƴammata"
Itama ƙaƙalo murmushin tayi, bata ce komi ba ta tashi ta shige toilet.




Kallon ta Abba ƙ yayi yace

"Yanzu mumtaz ke cemin kina son gani na"



Gyara zaman glass ɗin fuakar ta tayi tukun tace



"Eh, matar ka na son in sallame ta, ni kuma saboda yanayin jikin ta da na gani yasa nace ba
yanzu ba, ta zauna ta ƙara jin sauƙi, da dai naga ta nace yasa nace in kazo ayi min magana"



Kafin Abba ƙ yayi magana ya junaid yace



"Kiji wata magana se kace ƙaramar yarinya fa"




Murya a sanyaye mama tace

"Ni fa saboda tafiya ta umara nace a sallame ni, a can ne zan kai ma ubangiji kuka na yarda ya
kamata, kuma ko ba haka ba ai ina ganin dr Sanaa kuma ta san problems ɗina sosai"



Kallon ta Abba ƙ yayi yace

"Yaushe ne tafiyar to?"

A gajerce mama tace "next tomorrow"



Numfashi ya sauke a hankali tukun yace

"Ki yi discharging ta kawai, na manta sam da zuwan namu can ma"



Cike da fara'a likitan tace "yarda kuka ce ai, fatan mu a samu lafia ai"
Kafin goma na dare Abba ƙ ya gama da bills ɗin tas

Ankai komi mota, da kanshi ya kama matar shi ya riƙeta mumtaz na biye da su a baya
Ya junaid ya musu sallama ya tafi.



Seda Abba ya zaunar da mama a seat ɗin gaba kafin ya zagaya ya shiga

Mumtaz kuma na baya, yaja motar suka fice

Daidai gate mumtaz tayi ido biyu da khalid da suka taɓa haɗuwa a kasuwar seda gold



Tsaf sun gane junan su, da sauri khalid ya sauke glass da niyar yima mumtaz magana, kafin ma
ya gama saukewa ta kawar da kanta gefe, gaban ta naci gaba da bugawa haka kurin



Ganin ta kauda kanta yasa da sauri ya gangara gefe yayi parcking, kafin ya ƙaraso motar su
Abba yaja sunyi gaba



Mumtaz na ganin sun wuce ta waigo da kanta tana kallon shi ido cikin ido, shima yayi tsaye ya
kafe ta da nashi idanun har motar ta ɓace ma ganin shi.



SHARE PLS

ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR



👹
MAKIRCI
KISHI DA ALJANA
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI
WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg19-20

Jiki a mace yace

"Tunda har Allah ya sake nuna min ke to tabbas zamu sake haɗuwa dake!"

Still jiki a mace ya juya zuwa inda yayi parking ya shiga ya ƙarasa shiga ciki



Office ɗin da mumtaz ta fito ɗazu naga ya sanya kai ciki, yana shiga ya iske dattijuwar nan
tsaye tana dube dube ranta a mugun ɓace

Sallama ya sake yi a karo na biyu tukun taji, bata waigo ba ta amsa



Da mamaki khalid ya ƙarasa kusa da ita haɗe da faɗin

"Lafia kuwa mami?"



Ƙaramin tsaki taja, tana aje book ɗin ƙarshe data ɗaga tace



"Hmm, bracelet ɗina na aje anan ɗazu da zanyi alwala, emergency call da na samu ne na
mance ban ɗauka ba na fita, amma abun mamaki na duba sama ko ƙasa ban gani ba"



Sanin muhimmancin abun a wajen Mami ne yasa shima ya zage yana taya ta nema,
Aikuwa abun hannu yace ɗauke ni inda kk aje

Abu kamar wasa seda mami ta koma har inda taje ɗazu amma babu shi ba alamun shi



In ranta yayi dubu to ya ɓaci, sosai ta ɗauki abun hannun nan da muhimmaci ba wai dan
tsananin tsadar shi ba, se dan daga hannun wacce ya fitone yasa tayi mugun ɗaukar shi da
muhimmanci a rayuwar ta



Kankace me idanun mami yayi jajir tsabar ɓacin rai, macece me sauƙin hali amma tana da
mugun fushi in abu ya kaita maƙura
Tsabar gajiyar da ta yi ne yasa ta zauna a ɗaya daga cikin kujerun dake jere a office ɗin nata



Hannun daman ta tasaka ta tallafe kuncin ta na dama,

Shiru tayi tana sake nazari ko zata tuna ƙila ba anan ta ajiye shi ba

Amma tsaf iya tunanin ta me hasasho mata komi ba



Jiki a mace ta tashi bayan khalid ya haɗa mata hand bag ɗin ta da duk wani abu da ya san tana
tafiya gida dashi



Murya a tausashe khalid yace



"Kiyi haƙuri mami, tunda kaf garin nan bracelet ɗin irin shi ne kaɗai baze yi wahalar ba, in ma
ɗaukan shi akayi to ba ze wuce sedawa za'ayi ba,
Se mu bada sanarwar kama duk wanda aka gani ya kaishi kasuwa"



Ajiyar zuciya mami ta sauke, bayan ta gyara zaman ta a cikin motar tace

"har na ɗanji sauƙi a raina, Allah ya dubeni yasa a ganshi da gaggawa, kafi kowa sanin yarda
nasa shi a raina, infact ma a gaban ka goggo ta damƙa min shi gaf da Allah ze karɓi rayuwar
ta"



Sosai khalid ya kwantar mata da hankali, basu kai gida ba yayi ta making calls yana bada
sanarwa akan abun hannun.




Tunda Mumtaz ta shiga ɗaki take kallon abun hannun, sosai idanun ta suka cika da ƙwallar
rashin sanin ta mecece

Jiki a sanyaye tace

"Kodai inje in maida?"
Jitayi zuciyar ta na raɗa mata "banda abunki mumtaz in kika kaishi kasuwa ba ƙaramin kuɗi zaki
samu ba, se kiyi ta hidimar ki ba se kin takura mama ko Abba da tambayar bani bani ba"



Knocking ƙofar ɗakin da akayi ne ya katse mata tunani, da sauri ta mayar da shi cikin aljihun ta
tukun taje ta buɗe ɗakin



Altine ce tsaye a ƙofar, mumtaz na buɗewa tace

"mama na kiran ki"



Bayan ta tabi, ita tayi kitchen, mumtaz tayi can ƙaramin palon maman inda matar uncle
junaid(yayan mama) tazo se wasu daga cikin ƴan'uwan su



Gaishe su tayi kanta a ƙasa ta wuce inda mama ke kishingiɗe, manya manyan ledoji jube a
gaban ta

Seda ta zauna tukun tace

"gani mama"



Idon maman a rufe ta nuna wa mumtaz ledojin gaban ta tace

"hijabai ne, ki ware naki, nima ki haɗa min nawa a cikin babbar akwatin nan da na haɗa kayan
tafiyar mu"



Da "to" ta amsa, da ɗai-ɗai da ɗai-ɗai ta ɗauki ledojin tayi sama da su

Seda ta gama haɗa wa mama nata tukun ta wuce da nata da se a yanzu ta harhaɗa kayan
tafiyar ta, duk uban shelar da mamar tayi mata kusan sati kenan amma bata haɗan ba se
yanzu.



A daren duk suka koma gidajen su da adduar samun lafiya ga mama, wanda har yanzu babu
wanda yasan sabab ɗin ciwon maman.
Mumtaz na kwance wajen ƙarfe ɗaya da rabi na dare ta fara jin ƙarar kunna motacin gidan



A mugun sukwane ta sakko daga kan gadon ta leƙa ta window



Su umma b, mummy, da aunty ne, se Amal, hasfa, Bilkisu yarinyar ƙanwar umma babba ce, se
najwa itama mummy ce ke riƙe da ita, da Amir ɗan gidan mummy se mahmud autan Aunty



Da sauri mumtaz ta janyo wayar ta tayi dialing no ɗin Amal

Bugu biyu Amal ta ɗaga tayi saurin yin ƙasa da murya dan kar hafsat dake kusa da ita taji ta
faɗa wa umma b



Mumtaz tace

"Ina zakuje da tsohon daren nan? nasha tafiyar se daren gobe fa?"



Murya ƙasa-ƙasa Amal tace "ɗazu naji umma b na cewa an raba tafiyar ne saboda jikin mama
wai, so kune zaku tawo gobe"



Daga can mumtaz ta taɓe baki, murya ciki-ciki tace

"Ta daiyi munafurcin data saba yi"

Daga can Amal tace

"banji ba fa," sake taɓe baki mumtaz tayi tukun tace

"se mun haɗu kawai" ta tsinka wayar ta

Murmushi kawai Amal tayi, dan yanzu sam ta dena mamakin sauyin ƴar'uwar tata kuma ƙawarta

Maida wayar tayi jaka ta juya ta shiga kusa da Bilkisu

Mota biyu sukayi zuwa airpot, wajen huɗu saura jirgin su ya ɗaga zuwa ƙasa me tsarki.
WASHE GARI

Mumtaz na ganin zuwan sakina ta bar mata sauran aikin da mama ta saka ta

Ɗaki ta nufa hijabi ta ɗauka se wannan abun hannun da zuciyar ta ke ta azalzalar ta akan ta
saida shi

Ta ƙofar da Abba ƙ ke shigowa tabi cikin sanɗa dan kar Altine ko sakina suji motsinta take tafia

Seda ta ɓulle zuwa gate tukun ta saki jikin ta tafara tafiya normal

Abunda bata sani ba shine, ya faruk ya ba me gadi lasisin kiran shi a duk lokacin da ƴammatan
gidan zasu fita, be ware sunan ta ba gudun zargi ko wani abun daban, se yace dukan su har da
wanda ake riƙon su a gidan kuwa



Yana ganin tunkarowar ta gate ɗin ya zaro wayar shi kuwa

Tana ficewa ya danna ma ya faruk kira, murya a ƙasa yace

"yallaɓai, yanzun nan hajiya mumtaz ta fita"



"nagode" ya faruk yace ya tsinka wayar, yana gab da shigowa layin gidan ne daman, tunda gate
man ya kira shi ya samu waje ya tsaya, be kashe motar ba yana zaune a ciki ya baza idanu
yaga ta ina zata ɓullo



Zaman kusan minti biyar yayi tukun ya hangota,

In wani ne da be san ta ba ya ganta zece a nutse take tafiyar ta

Amma shi da yayi mata farin sani kallo ɗaya yayi mata ya gane ba gaskiya tattare da ita



A ɗan gaba da shi kaɗan ta samu kekenapep ta hau



Beyi ƙasa a gwiwa ba ya bi bayan su a hankali,

sosai gaban shi ke faɗuwa dan sam be yarda da fitar ta ba
Haka zalika a dokar gidan ba'a aiken ƴaƴa mata ko nan da can hasalima basu hawa motocin
haya balle a kai ga kekenapep,

duk rintsi ana musu wannn alfarmar na kaisu duk inda suke so



Sannu a hankali yake binsu har suka dangane da bakin babbar kasuwa



A tsorace mumtaz tace

"sauke ni a nan kawai mlm"



Waigowa me keken yayi yace

"bamu zo ba ai hajiya, kasuwa gold na ɗan gaba wannan babbar kasuwa ce ai"



Dallaro mishi manyan idanun ta tayi tukun tace

"na sani ai ɗan'iya, a nan naga damar sauka"

Ta ciro ɗari biyar ta miƙa mishi sannan ta sauka.



Ya faruk na ganin ta sauka yayi saurin ciro wayar shi ya danna mata kira



Yana kallon sanda ta kalli wayar, memakon ta ɗauka sema murguɗa baki datayi, yana kallo tana
motsa baki alamun magana take, maganar ma yasan be wuce rashin kunya ce



Seda yayi mata kira uku bata ɗaga ba, kuma ta kasa shiga kasuwar sam

Sosai zuciyar ta ke ingiza ta, amma wani sashi na zuciyar yana dakatar da ita



Kome ta tuna oho, jikin ta har yana rawa ta tsaida wani me keken ta hau



Ya faruk na ganin haka ya juya yabi bayan ta again
Mugun mamaki ne ya sake kamashi ganin sun ɗauki hanyar gida

A fili ya furta

"bata da gaskiya, wani abun tayi niyar shukawa"



Kafin a kai gate ɗin gidan ya sauke ta taƙarasa da ƙafa.




Seda ya faruk ya bada tazara sosai kafin ya shiga gidan shima



Direct side ɗin mamar ya nufa, seda ya duba ta da jiki tukun ya fito



Sakina na zaune ana mata kitso yace

"ina mumtaz"

fuska a ɗaure tace

"ƙila tana ɗaki"



Kai tsaye ɗakin ya nufa, seda ya ƙwanƙwasa kafin ya shiga



Zaune ya iske ta gaban mudubi comb a hannun ta ga gashin nan buzu-buzu kamar mahukaciya
sabon kamu, ido sharɓe da hawaye

Jin shigowar mutum yasa ta waiga da sauri tana tashi tsaye, ita duk a tunanin ta mamar ce ta
dawo kamar yarda tace



Ganin ya faruk ne yasa ta ja baya ta ɗauki hijabin ta zata saka



Yasan sarai me take wa kuka, sam bata ƙaunar kitso tun tana ƙarama,

Taɓe baki yayi sannan yayi ƙasa da murya yace
"wajen ubanwa kika je ɗazu, me ya fitar dake?"



Firgicin jin tambayar da yayi mata ne yasa ta saki comb ɗin hannun ta, ido a waje tace



"wallahi ba inda naje fa"

Cable ɗin wayar ta da ya gani a kan mudubi ya ɗauka, shima zaro mata nashi manyan idanun
yayi yace



"kin iya rantuwa akan ƙarya ko?, me kika je yi a kasuwa?" ya sake maimaita tambayar yana
ɗaga cable ɗin kamar ze tsula mata



Bata mance da haɗuwar su ta rannan ba, jiki na rawa tace

"wallahi abu naje siya, kuma ban shiga kasuwar ba na dawo"



Ƙara matsowa kusa da ita yayi, kamar ze shaƙeta yace



"ƙarya kike, abun wani kika sata halan zaki je ki ɓatar da shi?"



kasa magana tayi, se girgiza kai kawai tana sake ja da baya, murya na rawa tace wallahi ban
ɗauki abun kowa ba"



Jin muryar mama na kwala kiran sunan ta yasa ya shige toilet ɗin ɗakin da sauri, yana shiga
tana turo ƙofar



Tsaye tayi tana ƙare mata kallo ganin yarda take sharar hawaye wani na korar wani

A mugun fusace tayi kanta da faɗa

"Kitson kike ma wannan kukan mumtaz, saboda baki san darajar mutum be shine kika shanyata
tun ɗazu tana jiran ki?
To wallahi ko kukan jini zakiyi bazamu tafi dake a haka ba kai kamar na mahaukata, ni wlh
dama gashin ze kakkaɓe uban kowa ma ya huta ni kaina na huta da ciwon kan da kike sakani
duk sanda za'ayi miki kitso"



Tsaye mumtaz tayi bata ko motsa ba, ganin mamar tayo kanta ta fice da gudu hada ɗan
haɗawa da ihu



Haka mama tayi ta sababi kamar zata ari maki saboda takaici.



Ya faruk najin fitar su ya fito, ba komai ya sakashi ɓoyewa ba se sanin halin mama da yayi

Tsab zata zargi da wani a bu a ƙasa, shi kuma be shiryawa tambayoyin ta ba



Wayar mumtaz da ya gani akan mirrow ya ɗauka

tas ya bincike wayar ko da zega wani abun, amma bega komi ba, haka ya maida ya ajiye

Can ta ƙofar baya yabi ya fice ba tare da kowa ya lura da shi ba.



Seda mumtaz tasha faska a wajen mama kafin me kitson nan ta gama.



Ya faruk tunda ya shiga ɗaki yake saƙa da warwara,

tun lokacin da ya kama mumtaz da fara ɗauke-ɗauke yake shawara da zuciyar shi, se yau yaji
kwarin zuciya inda yayi alƙawarin zuwa bayan sallah in sun dawo daga umara ze faɗa ma
iyayen nashi dan a tunanin shi shine babban mafita, gwara duk a aurar da su kowa ma ya huta.



SHARE PLS

ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
IN SHA ALLAH SE ZUWA BAYAN SALLAH ZAMU ƘARASA

ALLAH YASA MU FARA AZUMIN MU GAMA A SA'A, UBANGIJI YASA MUNA DAGA CIKIN
ƳANTATTUN BAYIN DA ZA'A ƳANTA

YA RABBI YA ZAƁA MAMU SHUWAGABANNI NA ƘWARAI
ALLAH YASA MU CIKA DA KYAU DA IMANI.

LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR



👹
MAKIRCI
KISHI DA ALJANA
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI

WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg-26-27

Ko second goma beyi ba ya ɗauke kanshi yaci gaba da wayar shi kamar be ganta ba.



Mumtaz kam tunda ta ja ta tsaya bata sake motsi ba seda taji maganar khalid daf da ita tukun ta
dawo hayyacin ta

Da mamaki khalid yake tambayar ta

"Are u okay?"



Ko kallon khalid bata tsaya yi ba ta ɗiba tayi ciki, ƙiris ya hana ta kwasa da gudu, tana kaiwa
ƙofar ɗakin su jikin ta na ɗan rawa ta ciro katin ɗakin ta kara a jiki, yana buɗewa tayi wuf ta
shige dan har seda ta ba Amal dake zaune tsoro



Ido a waje Amal tace "Mumtaz ina kika je?"



Banza da ita tayi, cire hijabin jikin ta tayi ta wuce toilet

Gaf da zata shige toilet ɗin Amal ta sake cewa
"Tunda bani da matsayin da zan tambaya ki bani amsa se ki tanaji amsar da zaki ba ya faruk da
su Abba ƙ"

Tana gama faɗin haka ta juya tayi kwanciyar ta mamakin mugayen halin mumtaz na daɗa cin ta
a ciki



Duk da mumtaz ta ɗanji tsoro da Amal ta ambaci su Abba, amma ji tayi zuciyar ta dake sam
tsoron babu shi,

Ƙaramin tsaki taja bayan ta watsar da komi hankalin ta gaba ɗaya ya ɗugunzuma ga agogon
hannun khalid, tunani take na yarda zata raba shi da shi har ta shiga toilet tana saƙe-saƙen ta.



Cikin farin ciki da zumuɗi khalid ya koma masauki, sedai murnar shi ta koma ciki, inda yayi ta
kiran layin Mumtaz amma shiru bata shiga

Ta ɓangaren mumtaz kuwa kashe wayar tayi, dan kar Abba ƙ ko ya faruk su nemeta.




Sam kasa rintsawa ya faruk yayi a cikin wannan dare, da ya tuno fuskar khalid se gaban shi
yayi mummunar faɗuwa

Sam kwanciyar ma gagarar shi tayi ya tashi zaune, duk da sanyi air con dake ɗakin hakan be
hanashi zufa ba

Zazzafan huci ya fesar, cike da kokwanto ya furta

"Allah yasa yarinyar nan bayan ɗauke ɗauke bata bin maza!"



Shi kanshi seda ya runtse ido da ya faɗi kalmar "neman maza" da yace

da sauri kuma ya koma faɗin "a'uzubillahi minashshaiɗanirrajim"

A haka har dare ya raba yana saƙe saƙen abubuwa a ranshi.



******

Hafsa ce ɗaure da towel zaune a gefen gado tana shafa mai, kunnuwan ta gaba ɗaya ta miƙa
wa najwa dake ta fama fallasa mata sirrin dake cikin zuciyar ta akan ya faruk
Seda hafsa tagama jin komi daga bakin najwa tukun tace

"Danƙari, lallai najwa zuciyar ki batai miki adalci ba wallahi, tunda muke dake kin taɓa ji ance ga
budurwar ya faruk?"

Bata jira cewar hafsa ba ta ɗora da

"To wallahi na taɓa jin ance aljanar dare ta aure shi da daɗewa, dan haka ki shafa ma kanki lafia
ki lallaɓa da ɗan sadik ɗin ki, in kuma baki ji ba kyaji da wulaƙancin shi ba ruwana"



Murmushi Najwa tayi ta matso kusa da hafsa da har a fuskar ta zaga gane batayi na'am da
maganar ba tace

"Haba hafsa, ke da zaki bani shawarar yarda zan fara tunkarar shi amma ke ce ma sage ni,
koma dai menene zaki fini sanin abinda yafi so tunda ciki ɗaya kuka fito dashi"



Taɓe baki hafsa tayi kafin tace

"To ko umma data haife shi ba zata iya tantance abinda ya faruk ya fi so ba wallahi, dama dai
mamace ko kuma warcan data ɗakko ma kanta dala ba gammo(tana nufin mumtaz) ƙila ki samu
wani abu da ze amfane ki"



Shiru Najwa tayi tana sauraran hafsa, can Najwa tace

"zan san yarda zanyi dai"



Sake taɓe baki hafsa tayi, taci gaba da shafe+shafen ta



Seda ta gama shiryawa tsaf tukun ta sake cewa

"Yanzu ya zakiyi da sadik da ya mutu a kanki najwa?"



Kai tsaye Najwa tace "haƙuri zeyi"
Bilhaƙƙi da gaskiya hafsat ta fuskanci najwa tace

"Ki bi a hankali najwa, karki fara da bawa sadik haƙuri baki damƙi dahir ba, wallahi tallahi zakizo
kiyi danasani nan gaba"

Tana gama faɗin haka ta ɗauki wayar ta da ƙaramar jakar hannun tace "mu wuce kar mu
makara sallah".




******

Kamar kullum yauma mumtaz wajen ta daban ta zauna, gaba ɗaya ta rasa sukuni ta rasa me ke
mata daɗi a cikin zuciya



Hand bag ɗinta ta buɗe ta zaro wayar ta da tun jiya take a kashe ta kunna

Few seconds ta gama booting, seda ta kalli wayar taga ashe data a kunne ne ma ta kashe
wayar jiya



Kamar jira khalid yake ta kunna wayar, nan calls ɗin shi sukai ta sintiri, mumtaz na kallon kiran
tana ignoring

Sam ta kasa samun courage ɗin amsa shi

Sauka tayi da niyar kashe data, kafin ta kashe message ɗin shi ya fito a saman notification,

"Dan Allah ki amsa mumtaz"

Hakanan ta samu kanta da replying shi "muyi chat, i cn't answer ur call now"



Cikin damuwa khalid ya ce

"kina ina yanzu, ina so in ganki pls".



Da ƙyar da jiɓin goshi mumtaz ta tura mishi live location ɗinta, ko minti shabiyar beyi ba ya
ƙaraso,
Abu na farko da mumtaz ta fara kai idonta kai shine hannun shi,

Ganin babu agogon data ƙwallafa rai akai taji ranta ya ɓaci, ɗan sakin data yi wa fuskar ta ma ta
koma ta ɗaure tamau



Da ƙyar mumtaz ta ɗan fara sakin jiki da shi, suka fara fira sama-sama



Cike da ƙwarewa khalid ya fara kafa gwamnatin soyayyar shi a zuciyar ta.



Sosai khalid ya saki jiki ya fara bata labarin shi

"Ni haifaffen ɗan kano ne, ɗa ɗaya tilo a wajen iyayen shi, babana tun ina secondry aji biyu ya
rasu, ya barmu daga ni se mamina taci gaba da kula dani

a yanzu haka ina aiki da A.S.K textile company"



Da sauri Mumtaz tace "A S.K company fa kace"?



Gyaɗa kanshi yayi kafin yace

"kin san wani a wajen ne?"

Murmushi kawai tayi, bata ce komi ba

A.S.K, textile company na Abba ƙ ne, shine kampani na farko kuma mafi girma a dukkan sauran
kampanonin shi guda takwas, shiyasa tayi mamaki jin a can yake aiki



Jin bata ce komi ba shi ya ɗora da

"Saura ke ranki shi daɗe" ya ƙarashe maganar yana murmshi



kan mumtaz a ƙasa tace

"nima ƴar kano ce, a sharaɗa phase 2, ina a 200lv a jami'ar bayaro ina karantar mass com"
Daga nan tayi shiru taci gaba da wasa da yatsun ta.



Girar shi biyu ya ɗaga haɗe da kallon yatsun ta datake wasa da su yace

"ma sha Allah, sauran abu ɗaya ne banji na"

Ɗan ɗagowa tayi kaɗan, tana sauraren shi

yace "Ni na gaya miki nine tilo, nine ɗan fari nine kuma auta"

The way ya ƙarashe maganar se ya baka dariya

Ilai kuwa seda mumtaz ta ɗan dara, tukun tace

"muna da yawa sosai a gidan mu, but a wajen Abba da mama nice ta uku, ina da yayu maza
guda biyu, se ƙanwa mace ɗaya, mama tace bata wuce 6month ba ta rasu"



Dariya khalid yayi yace 'kawai malama kice min kema autace"

Murmushi kawai mumtaz tayi, tana ɗan waigawa gefe, akwai wani feeling datake ji a jikin ta in
har ana kallon ta

Ɗayan gefen ta sake waigawa caraf suka sake yin ido huɗu da ya faruk dake kallon ta ko
ƙyaftawa babu, fuskar nan tashi a murtuke ba wani alamar sassauci



Da sauri ta waiga ta dena kallon side ɗin da yake

A ɗan tsorace, bama lale ka gane a tsoracen take ba tace

"ehnmm, tun da mun gaisa ka tafi, nima zan tafi ne yanzu"



Da kyau khalid ya kalleta, kafin yace

"ke dawa kukazo ne nake ganin ki ke kaɗai?"



Seda ta miƙe tsaye ta gyara hijabinta tukun tace

"muna da yawa sosai, kusan duka gidan mu"
Ganin tayi gaba da sauri ya sashi bin bayanta,

A ɗan ƙage ta juyo tace

"Kar ka biyoni pls, zamuyi waya kawai"

Sototo khalid ya tsaya ganin yarda mood ɗin ta ya sauya gaba ɗaya

Har ta ɓace wa ganin shi be motsa daga wajen ba.




***Ran ya faruk a ɓace ya ɗaga waya ya kira guy ɗin da yake sawa yana siyen mishi tickets duk
sanda tafiya haka me yawa ta taso



Sallamar shi kawai ya faruk ya amsa, ko ta kan gaisuwar da yake mishi be bi ba ya ɗora da

"sagir dan Allah date ɗin komawa gida nake so a sauya ma wasu daga cikin yaran gida"

Daga can ɓangaren wanda aka kira da sagir yace "to yallaɓai, yaushe za'a maida kuma da wa
da wa?"



Ya faruk yace "in har za'a samu jirgin zuwa anjima ma yayi, zan tura maka sunayen su yanzu"

"okay sir".




*****Mamace kaɗai zaune a masaukin su tana waya da yayan ta(baban sakina) mumtaz tayi
knocking ƙofar



Still wayar na a kunnen mama ta tashi ta buɗe mata ƙofar,

Da sallama mumtaz ta ƙaraso ciki, tana shigowa ta cire hijabi ta haɗa da hular kanta tacire,
agogon ɗakin ta kalla taga shida saura, ɗan tsaki taja ta zame a wajen ta kwanta, dai dai nan
mama ta gama wayar, kallon mumtaz tayi ganin yarda tayi ɗai-ɗai kamar wata mara lafia tace

"Ya dai? garin ko jikin?"
Turo baki gaba tayi kafin tace

"wallahi muguwar ƙishirwa nake ji mama, gashi yau lokacin baya gudu sam"



Kallon agogo mama tayi, tukun tace

"saura kaɗan ai"

Kamar an zunguri mumtaz ta miƙe zaune tace

"Mama Abayar dana ƙwallafa

Please Login or Register in order to submit comment