Reading LAUJE CIKIN NAƊI by ZAINAB FALALU Chapter 17 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wajen da ƴan'uwa da abokan arziki da zasu zauna daga can gefe.
Mumtaz kam bata gayyaci ko mutum ɗaya ba acewar ta ai biki ɗaya ne.




Tun kafin azzahar me makeup ɗin da zata yi wa mumtaz ta iso, wannan karon babu wani cewa
banaso, da kanta tace "ki tsatso ni infi kowa fita fa"

Yarda tayi maganar seda taba kowa dariya a wajen

Ita kanta seda ga baya taji kunyar abinda tace.

Abun mamaki umma babba itama musaman ta sa aka kira mata me kwalliya har gida.



Ta can ɓangaren yaya faruk shi zamu iyacewa taron shi ya fi na kowa,

Tunda ba ɗaurin aure, shiyasa ya yi gayya sosai wannan karon

Gaba ɗaya abokab shi wankan blue shadda sukayi se baƙin takalmi da baƙar hula

Shikuma yayi wankan farar shadda ƙal da baƙar hula.

Ma sha Allah, ku hango tsarin da kanku ku gani 😊
Biyar saura wajen ya ɗinke sosai da mutane,

shigowar iyayen amarya da ango ake jira sannan shigowar amarya da angon.



Mamace ta fara isowa bayan MC ya sanar da shigowar ta, tana a tsakiyar ƙawayen ta da ko
wacce ka kalla zaka san nera ta zauna ba ƙarya

Gaba ɗaya maman wankan blue black lace tayi ta amsa sunan shi.

Seda suka sami waje suka zauna, sannan MC ya sanar da shigowar hajiya umma babba da
nata tawagar

Ba ƙarya itama itama a tsakiya suka sako ta, bakin nan nata kamar gonar audiga saboda fara'a

Wankan ta itama yayi kyau ba ƙarya, inda ta saka farin lace me ratsin baƙi a jiki
Itama ta samu waje ta zauna.

Seda kowa da kowa ya nutsu ya zauna sannan MC yayi sanarwan shigowar ya faruk da
mumtaz da har yanzu ya faruk ya kasa yarda cewa ita ce saboda yarda shigar fari da baƙi yayi
mata masifar kyau

Da gudu ya sabiha ta ƙaraso da sky blue ɗin net sharara ta rufa wa mumtaz akan goggoron ta,
sannan tace "yes, zaku iya shiga

Tunda suka fara takowa, wajen ya ruɗe da tafi, wasu na guɗa wasu suna sowa

Mama kam ta kasa ɗauke idanun ta akan su, banda murmushi da hamdala babu abinda take

Umma babba kam miƙewa tayi ta tarbosu har seda ta dangane dasu da gujerar su

Tajuddeen me hoto na gaba gaba yana haske su ta ko wace kusurwa.

(ƘANI NA YANA PICS ƊIN BIKI, SUNA, BIRTHDAY, DA KOMI MA, KUMA A KO WANI GARI

👉 😊
KUKE, A CIKIN FARASHI ME SAUKI DA RAHUSA, ZAKU IYA TUNTUƁAR SHI TA WANNAN
NUMBER 09078408747, KU GWADA BABU DANASANI A CIKI )



***TK
Tun da rana da ya leƙa sakina ya aje mata abincin da yayi musu order yace mata "ki shirya
anjima zamu je buɗar kan ya faruk da mumtaz"

A mugun firgice da kuma mamaki ta ɗago, murya a dishe tace "wacce mumtaz ɗin kake nufi?"

Har ya saka kanshi ze fice ya dawo yace "Mumtaz nawa kuke da su a dangin ku?"

Ganin kamar bata fahimce shi ba ya tsaya yayi mata bayanin auren mumtaz da ya faruk dalla
dallah sannan ya fice haɗe da faɗin "kar kuma ki ɓatan lokaci"

yana ficewa sakina tayi jifa da ledar abincin haɗe da gwara kanta da jikin gado

Cikin kuka take faɗin "ya za'ayi ma na ƙare akan TK mumtaz na auren faruk,

Wallahi baze taɓa sakuwa ba"!

Fuuu ta tashi ta fice daga ɗakin

Bata tsaya ko ina ba se kitchen, sharɓeɓiyar wuƙa ta ɗakko ta fito, direct ɗakin Tk ta nufa ido
rufe

Tana shiga tayi kanshi, kwata kwata beyi aune da wuƙar dake hannun ta ba sedai jin shigarta
yayi a cikin shi

Wani wawan ihu ya fasa haɗe da faɗuwa wanwar.

Hmmm

ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR



👹
MAKIRCI
KISHI DA ALJANA
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI

WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg81

Cikin raɗaɗin sukar da tayi mishi yace "sakina wuƙa kika caka min fa"

Ganin yarda jini ke bin jikin shi a lokaci ƙanƙani yasa ta firgice ta fice daga ɗakin da gudu tayi
nata.



A hankali ya fara matsawa inda ya aje wayar shi

Amma da yayi motsi kaɗan zeji kamar wuƙar na sokar wani abu a cikin shi

Yunƙurin da ya rinƙa yi wajen janyo wayar sa yasa jinin ƙara yawan fita

Duhu duhu ya fara mamaye idon shi, amma duk da haka besa ya fasa yunƙurin kaiwa ga inda
wayar shi ke ajiye ba
Cikin yardar Allah ya samu ya ɗauki wayar amma sam baya iya kallon meke ciki saboda yarda
duhu ya mamaye shi

Shafa wayar yayi, ganin ba iya kiran ze ba, ya saketa a wajen

a hankali ɗakin ya fara juya mishi.



A inda ya yasar da wayar yaji kira ya shigo



Duk da ba gani yake ba, kuma hankalin shi na gaf da gushewa ya janyo wayar

Janyowar da yayi ya ɗauka ba tare da ya sani ba

Muryar abokin shi yaji

Cikin fitar numfashi Tk ya ce "Ta caka min wuƙa, kazo, kayi sauri kazo zan mutu"

Daga can abokin Tk ke jin shi cikin mawiyacin hali

A kiɗime yace "Guy me kake faɗa ne wai, ina waje fa, waye ya caka maka wuƙa, kana ina"?

Duk a ruɗe yake zubo mishi tambayoyin haɗe da ƙoƙarin fitowa daga motar



Daidai nan sakina ta fito a kiɗime tayi hanyar titi bako suturar arziki a jikin ta



Juyawa yayi da niyar binta, ya fasa ya shiga gidan da ta barshi a buɗe da gudu haɗe da ƙwala
kiran sunan "TK."



Ɗakin sakina ya fara shiga, began shi ba, sannan ya leƙa ɗayan ɗakin da Tk ke kwance cikin
jini baya numfashi



A kiɗime yayi kan TK da be san a inda kan shi yake ba

Sam be lura da jinin dake fitowaa ta cikin sa ba yayi kanshi ya rarime shi haɗe da jijjiga shi yana
ambaton sunan shi

Maida shi yayi ya aje da niyar kiran uncle Abbas a waya
Se a sannan idon shi yakai ga wuƙar dake cikin shi

A tsorace yaja da baya yana bin jinin dake a ƙasa da kallo

Da ƙarfi yace 'inaaa, wallahi bazan taka sahun ɓarawo ba" yayi waje da gudu ya faɗa motar shi
ya jaa.




*****waje yayi waje fa,

Fuskar kowa ka kalla kasan yana cikin annushuwa da farin ciki

Da ɗan damuwa mummy ke kallon kowa, taga kowa da kowa harda amaren wancan satin da
mazajen su amma bata ga TK da iyalin shi ba

Waya ta ciro tayi dialing no ɗin shi, amma har ta katse be ɗaga ba

A ranta tace "maybe suna hanya, ko wani abun ne ta tsaida su"



Anyi bajinta a wannan taron ba ƙarya, duk da ba'awani shirya mishi ba,

amma kai da ka gani zaka ce an jima ana shirin taron tsabar yarda komi ke tafiya akan tsari da
tsaruwa.



Bayan an gwangwaje, anci an sha, sannan akazo akayi cinikin fuskar amarya a tsakanin dangin
mama da dangin umma babba

Ƙwarai da gaske abun ya ƙawatar, dan an ta zabga ciniki cike da barkwanci har aka daidaita a
kuɗi adadi masu nauyin gaske kafin aka buɗe fuskar amarya kowa ya ganta

Tunda ya sabiha ta ɗaga net ɗin fuskar mumtaz bakin kowa be huta ba wajen faɗin "ma sha
Allah, tubarakallah", shi kan shi ya faruk seda ya furta "Tsarki ya tabbata ga ubangijina me
kashewa da kuma rayawa, tabbas wannan shi ake kira da sakin wawa"!

Hakanan ya tsinci kanshi da murmusawa game da maganar da yayi ta "sakin wawa"



Waigawa ya faruk yayi ta inda su ya sabiha ke zaune, yafito ta yayi da hannu
Da sauri ta taso taje

ya faruk yace "na gaji da hayaniyar nan fa, akwai kuma abinda zanyi kisa ya taƙaita abin pls"

Gyaɗa kai tayi tukun ta sauka zuwa wajen MC dake ta ɓaɓatu yana kwasar nera.

Biyar da kusan kwata abokan shi suka fara mishi sallama suna tafiya haɗe da mishi fatan alkairi
da zama lafia.




😂
A taƙaice aka rufe komi duk da can na hango fuskokin LAUJE FANS ba haka suka so ba, dan
basu gaji da gwangwajewa ba aka katse su LOL

Su o'o da o'o kam kamar su fashe saboda haushi.

Lalubo hannu mumtaz ya faruk yayi ya miƙar da ita tsaye tukun ya ja ta suka fice ta can bata
hanyar da kowa ke fita ba

Seda ya dangane ta da sasan mama tukun yace "zanje na dawo, ki shirya komin dare in sha
Allah yau zamu wuce gidan mu"

Sunkuyar da kai ƙasa tayi tana wasa da stones ɗin jikin kayan ta

Murmushi ya faruk yayi, yatsar shi ƴar manuniya ya saka ya tallafo gemun ta ya ɗago da fuskar
ta sama

Ɗayan hannun yasa ya zunguri hancin ta sannan yace "ko baki shirya hakan ba?"

Da sauri ta ƙwace fuskar ta ta sake yin ƙasa da kai, kunya duk tabi ta cika ta

Daga can ta hango Amal nata nunosu tana kwasar dariya, tana nuna mata irin meye haka take
yi

Murguɗa mata baki mumtaz tayi, shi kuma ya faruk se yayi tunanin da shi take

Folding hannayen shi yayi, still murmushi a fuskar shi yace "eyee harda murguɗa min baki ma
kike?"

Da sauri mumtaz ta dafe baki haɗe da zaro ido tace "Amal ce fa" ta nuna wajen da Amal ke
tsaye

Waigawa yayi daidainan Amal ta juya kamar ba ita ba
Murmushi kawai yayi ya kaɗa kai, sannan yace "Ki taya ni addu'a akwai abinda zan aiwatar a
cikin daren nan in sha Allah"

Kafe shi da ido tayi can tace "me zakayi ya faruk?"

Kallon ta kawai yake yama kasa ce mata komi

Ta sake faɗin "gaba na yana faɗuwa tun ɗazu, bana son yarda nake ji ɗin nan"

Kafe ta da kallo yayi, can ya basar yayi murmushi yace "kazar amarci zan je siyowa fa, wasa
nake maki"

Yana faɗin haka ta rufe fuska ta juya da gudu tayi ciki

Murmushi kawai ya sake yi sannan yace "i have to do this for Abba ƙarami's sake, barin bara
gurbi a cikin zuri'a shi kesa wasu taɓuwa" ya juya ya fice.



Duk sha'anin nan da akayi umma ƙarama bata cikin gidan nan sam,

Har abun ya ba ƴaƴan ta haushi, ganin kowa na nan amma ita bata nan, kuma bata ce ma kowa
ga inda taje ba

A wannan lokacin su suna can suna jiran lokacin da bokan su ya basu ya cika yarda zasu sami
Abba ƙarami su titsiye shi akan maganar hannun jarin da suke da shi a cikin dukiyar sa.




***Tunda abokin Tk ya fice daga gidan saboda firgita da yayi ganin halin da Tkn ke ciki

Beyi nisa ba ya dawo, ya sake komawa ciki

Da ƙyar ya iya saka shi cikin mota yayi rushing zuwa asibiti

Ganin halin da yake a ciki ne yasa suka ce ba zasu karɓe shi ba seda ƴansanda

Hankalin abokin Tk a tashe ya hau kiran uncle Abbas a waya

Haka wayar nan tayi ta ringing amma shiru be ɗaga ba

A ruɗe ya maida akalar kiran ga ya faruk

Ya faruk na zaune a cikin mota yana waya da mus'ab kiran abokin Tk ya shigo
Seda ya faruk ya gama wayar shi, sannan ya amsa kiran

A kiɗime yace "na kawo TK hospital sun ƙi karɓar shi"

Hankali kwance ya faruk yace "nutsu kayi min magana mana, me ya samu TKn? sannan
meyasa basu karɓe shi ba?"



A ruɗe yake mishi bayani

Ido waje ya faruk yace "ɗauke shi maza bari na tura maka address na hospital ɗin dr jamal, zan
kira shi a waya yanzu"



Seda ya faruk ya tura mishi sannan ya kira dr jamal,

Daga nan shiru yayi da bakin shi be gaya ma kowa ba yaja motar shi ya fice.




Sanda sakina ta fice daga gidan bayan aika-aikar da tayi
Gida ta wuce direct

A firgice ta afka ciki, babu kowa a palon se me aiki da ke kitchen

Sakina bata tsaya ko ina ba ta ware ɗakin ta haɗe da rufo ƙofa harda murɗa key

Jin motsin ƙofa da me aikin ta jiyo yasa ta leƙo, ganin bata ga kowa ba ta koma taci gaba da
aikin ta.



Se can wajen magrib mom ɗin sakina ta fito dan taga ko me aikin ta kammala tana son aikenta

Da mamaki tabi palon da kallo ganin jini a ƙasa

Da ƙarfi mom ɗin sakina ta ƙwala wa me aikin kira

Jiki na rawa ta fito, rissinawa

Idon ta akan jinin tace tace "meye wannan daga ina?"
Matswa me aikin tayi, seda ta kalla da kyau sannan tace "jini ne hajiya"

Kafin ta sake magana me aikin tace
"kamar da ƙafa aka tako shi, naga har ta can wajen ma gashi can" ta nuna hanyar da tabi zuwa
ɗakin sakina"



Da mamaki mom ɗin sakina tabi takun jinin, har seda ya dangane ta ga ɗakin sakina

Da sauri ta taɓa ƙofar

Jin ƙofar a kulle kuma ta san bata rufe ɗakin ba yasa tace "waye a ciki?"

Shiru ba amsa

Juyawa tayi da sauri ta koma palon tace "waye ya shigo gidan nan?"

"ina ciki ina aiki banji shigowar kowa ba hajiya"

Fita mom ɗin sakina tayi waje har wajen gate ta ƙwala wa megadi kira ta tambaye shi, nan yake
gaya mata yaga shigowar sakina a firgice ƙafarta duk jini.



Da gudu ta koma ciki,
Ƙofar ɗakin sakina ta tsaya a tsorace take ƙwanƙwasa ƙofar haɗe da kira sunan sakina



Sakina najin ta amma tayi banza da ita

Seda ta gaji da bugawa tukun sakinar tazo ta buɗe

A kiɗime tace "me yasame ki?" ta hau dudduba jikin ta



Ba wani wata wata ko ɓata lokaci sakina tace "Druging ɗina yayi sannan yayi amfani da ni ba a
cikin hayyaci na ba" ta tsaya a nan

Ido waje mom ɗinta tace "se akayi yaya?"

"tsautsayi ya ɗebe ni na caka masa wuƙa"

Da mugun ƙarfi uwar ta aza hannu bisa kai tace "na shiga uku na lalace ni asiya!!! wuƙa fa kika
ce sakina?

A guje ta fita ta koma ɗakin ta, jikin ta na rawa hannun na karkarwa ta janyo wayar ta, uncle
junaid ta danna ma kira daidai lokacin suna tare dukkan su a inda suka saba haɗuwa

Har wayar ta gama ringing be ɗauka ba

Ta kira ya kai sau uku amma ba amsa, da gudu ta sake komawa ɗakin sakina da har yanzu
tana a tsaye abin duniya ya ishe ta "ɗakko gyalen ki mu je"



Daƙilewa tayi a tsorace tace "ina zamuje mom?"

Falla mata mari tayi tace "dan ubanki har kina da bakin tambaya ta, to bari kiji wallahi in har kika
bari akazo aka ritsaki anan to kashin ki ya bushe"



Ba sake cewa komi ba banda fizgar ta datayi suka fice

A guje mom Asiya taja mota suka bar gidan.



*****Ya faruk na zaune a gaban Abba ƙarami call ɗin dr jamal ya shigo wayar shi,

Ɗagawa yayi, daga can dr jamal yace "sun iso fa, case ɗin babba ne wallahi, wuƙar ta shiga
cikin sosai fa"

Murya can ƙasa ya faruk yace "ban fa sanar ma kowa ba a gidan, amma bari na gaya wa su
Abba yanzu"

Da haka suka yi sallama.




******Har aka fito da Tk daga theater ba uncle Abbas ba dalilin shi

Hankali ya tashi ƙwarai da kowa yaji labarin abinda ya samu Tk, dama zargin da ake na sakina
ce tayi hakan, dan labarin bata gidan ya baɗe ko ina,

Ga mom ɗinta a gefe da take ta pretending kamar itama bata san inda sakinar take ba, alhalin
ita ta kaita ta ɓoye ta.
Wajen goma saura su Abba babba da ƙarami dama su goggo safiya, harda su mama da su
mummyn Tk suka koma gida, aka bar Amir ya kwana da shi.



Ta ɓangaren su uncle Abbas kuwa sun ƙagara lokacin ya cika,

miƙewa tsaye umma ƙ tayi, gyara lulluɓin ta tayi sannan tace "zanyi gaba se kun iso, zuwa
yanzu na san sun gama taron shirmen su"

Gyaɗa kai sukayo duka, duk sun bi sun ƙagara

Uncle junaid yace "nan da 30mins muna hanya muma"

Da haka sukayi sallama.




*****
Sanda suka shigo gida daga asibiti ba kowa a baƙi,

duk wanda ka gani ɗan gida ne, kowa sasan shi ya nufa, ga gajiyar hidima ga kuma gajiyar
tsayuwar hospital da sukayi



Abba ƙarami na zaune a palon shi bayan yayi wanka ya kimtsa mama ta kawo mashi tea,

Tana zaune a gefen shi suna firar abunda ya faru da Tk wayar shi tayi ringing

Mama tafi kusa da wayar, yunƙurawa tayi ta ɗakko, sunan Abbas ta gani a rubuce

Da sauri ta miƙa mishi haɗe da faɗin "ƙila se yanzu yaga calls ɗin da akayiyyi masa"

Gyaɗa kai Abba ƙ yayi haɗe da kara wayar a kunne

Duk a tunanin shi maganar Tk ze mishi, se yaji saɓanin haka



Da mamaki Abba ƙ ke sauraron shi, can dai yace "ba matsala ku ƙaraso ina palo na"

aje wayar yayi ya kalli mama yace "ki ɗauki mayafi su Abbas na shigowa"
Babban hijabi ta ɗora akan kaya jikin ta sannan ta koma ta zauna.



Kamar wasu mutanen kirki, uncle junaid da uncle Abbas sukayi sallama suka shigo, ɗauke da
wasu files a hannun su

Amsa sallamar sukayi

Da fara'a Abba ƙarami yace "bisimillah ku zauna mana"

Zama sukayi a kujerar dake kallon tasu

Kafin suce komi ya faruk yayi sallama ya shigo

Da sauri uncle Abbas ya kalli uncle junaid sannan suka kalli ya faruk dake murmushi kanshi
tsaye ya ƙaraso ciki

Basu gama mamakin ganin ya faruk ba se ga uncle ƙasim shima ya shigo goggo safiya biye da
shi a baya



Daga mama har Abba ƙ tsoro ne ya fara kamasu, ganin basu jima da rabuwa ba ai

Baki sake su uncle Abbas ke kallon su

Can suka jiyo ya faruk na faɗin "muna palon saman shi Abba babba"

Miƙewa Abba ƙarami yayi yace "wai lafia?"

Daidai shigowar Abba babba kenan shima ya ɗora da tashi tambayar "me ya faru kuma?"

Uncle ƙasim yayi karaf yace "Ku zauna mana, tunda kuka ga haka ai da magana ne"



A take uncle junaid ya fara jin tsintsinkewar zuciya
se wani mutsu mutsu yake kamar me basir.

Ɗaya bayan ɗaya sauran matan gidan ke shigowa harda manyan ƴaƴan

Kowa ya shigo se yayi turus yabi kowa da kallo kafin ya zauna

Ashe ya faruk ne yabi kowa da kowa ya tura mishi saƙon yana son magana da shi ta sirrin a
palon Abba ƙarami misalin ƙarfe goma da rabi.
Babu wanda yasan da an turawa ɗan'uwan shi saƙon, shiyasa duk wanda ya shigo se yayi
mamaki

Umma ƙarama ce kawai be turama ba, saboda itama yasan zata zo kodan shirin su.




Kowa ya nutsu ya zauna, cikin faɗa Abba babba ya kalli ya faruk yace "kai bana son shashanci,
meye haka ka wani tara mu anan kamar wasu sa'o'in ka?"

Kafin ya faruk yace komi, uncle junaid ya miƙe haɗe da faɗin, "ina jin abun na family ne, nikam
bari naje gobe na dawo muyi maganar data kawoni"

Karaf uncle ƙasim yace "ta shafe ka mana, aikama ɗan gidane, zaka iya zama"

Musu yaso yayi, amma amma ganin mus'ab ya ɗaga labule ya shigo haɗe da sallama yasa ya
tsaya cak, kamar yarda zuciyar shi data uncle Abbas ma ta tsaya.



INA MATUƘAR GODIYA DA ADDU'O'IN KU GAME DA ƁATAN ƘANWATA

ALHAMDULILLAH, KUMA TA DAWO LAFIA

MASU KIRA DA MASU TURO SAƘON JAJE DA ADDU'A ALLAH YA SAKA DA ALKAIRI,
MATSAYIN KU NA DABAN NE,

ALLAH YA BAR ZUƁUNCI

ALLAH YA TSAREMU DA TSAREWAR SA ALFARMAR ANNABI MUHAMMAD

INA MATUƘAR KAUNAR KU ❤️

ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR
👹
MAKIRCI
KISHI DA ALJANA
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI

WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg82

Hannun Abba ƙ na karkarwa ya nusa mus'ab da ya bar ƙasumba sosai a fuskar shi yace
"Mus'ab!"

Cike da rauni mus'ab ya ƙaraso inda Abba ƙ yake ya rungume shi



Kowa mamakin ganin mus'ab yake a wannan lokacin duk da sun san cewa baya ƙasar(in baku
mance ba haka ya faruk ya faɗa ma kowa)



Abba babba yace "saukar yaushe mus'ab?"

Jin abinda Abba babba yace shine ya dawo da tunanin Abba ƙarami shima ya basar



Shigowar mummy(matar uncle Abbas) kenan ta ga uncle Abbas zaune,

Batayi tunanin komi ba ta ce "Dama kana nan nake ta faman kiran ka baka amsa min ba?"



Kallon ta kawai yayi amma ya kasa ce mata komi

Goggo safiya tace "ki zauna mana, ƙila wani abun ne ya tsare shi, tunda Allah ya taƙaita wahala
ai da sauƙi"

Taɓe baki mummy tayi kafin ta samu waje ta zauna.



Ta gefe kuma uncle junaid se zungurin uncle Abbas yake da ƙafa, shima yana zungurinnshi

Duk ya faruk da uncle ƙasim na lura da su.
Cikin ƙagara Abba babba yace "wai meke faruwa? wannan gangankon namene?"



Kai tsaye ya faruk yace "Na uncle Abbas da uncle junaid ne, se kuma umma ƙarama"



Da mamaki kowa ke kallon ya faruk, har da su waɗanda aka ambata ɗin



Cikin faɗa uncle Abbas yace "ohhh rainin da kayi wa kowa shine har ya fara gangarowa kaina
nima?"

Murmushi ya faruk yayi sannan yace "ku gafarce ni da abinda zan faɗa yanzu"

Tsuru kowa yayi yana sauraron ya faruk da ya shafa ma idanun shi toka ya ɗora da

"Abba ƙ ina neman alfarmar ka bar su uncle junaid da uncle Abbas gabatar maka da abinda ya
kawo su kafin akai ga jin komi"



Ɓata rai Abba ƙ yayi yace "meye haka kakeyi ne faruk?"



Kafin ya faruk ya ce komi uncle ƙasim yace "ya kamata su faɗi abinda ya kawosu a gaban kowa
da kowa a irin wannan lokacin"

Nan ma kallon kowa ya koma gareshi.



Cike da tsantsar rashin gaskiya uncle Abbas yace "me kuke nufi da hakan, ko kuna tunanin
wani mugun abunne ya kawo mu?"

Ba wanda yace mishi komi, Abba babba dai yabi kowa da kallo yana so ya tantance abinda ke
shirin faruwa"

Cike da rashin gaskiya ya hau buɗe files ɗin gaban shi, amma rawar da hannayen shi keyi sam
yakasa samun sukunin iya riƙesu da kyau.



Miƙewa tsaye mus'ab yayi, seda yayi ma kowa sallama kafin yace "A dena wani ɓoye ɓoye so
muke su uncle Abbas su fayyace mana meyasa suke cin dunduniyar ahalin Abba ƙarami!"
Mus'ab na gama faɗin haka aka hau kallon kallo

Nan da nan zufa ta rufe su uncle Abbas duk da sanyin aircon dake aiki a palon



Cikin ɓacin rai Abba ƙarami yace "baka da hankali ne mus'ab, waɗan nan ba iyayen ka bane
kake faɗin irin wannan munanan maganganun akan su?"



Shiru mus'ab yayi yana ci gabaa da haɗiyar zuciyar gado



Uncle ƙasim da shima fuskar nan a cukune take yace "tunda ba zasu ce komi ba, bari mu kawo
wanda zeyi ma kowa bayani"



Abu ya fara ɓaci fa, zama na neman gagarar su uncle junaid gaba ɗaya

Umma ƙarama kam saita ƙofa kawai take, dan ba zata taɓa tsayawa ta kunyata ba.



Kafin kowa ya dawo daga duniyar mamakin da suka shiga uncle ƙasim ya shigo da Altine da
idanun ta suka kumbura tsabar kukan data sha



Wiƙi wiƙi su umma ƙarama sukayi

Kunsa mara gaskiya ko a ruwa jiɓi yake.



Tallaƙe ƙeyar ta yayi sannan yace "munafuka faɗa ma kowa abinda kika shuka kafin na fasa
kanki"



Cikin kuka Altine ta kalli mama da gaban ta banda dukan tara-tara babu abinda yake tace
"ku yafe man hajiya, Wallahi duk abinda nayi maku ba da son raina bane, a bisa tirsasawar
hajiya sumayya(umma ƙarama) ne da kuma waɗanda ban sani ba wallahi"

Dafe ƙirji umma ƙarama tayi haɗe da faɗin "ku ji man wani sharri da tsohon daren nan, ina fatan
ba dai ni sumayyar kike nufi ba??"
Ido rufe Abba babba yace "dakata hajiya sumayya!"

Tsit umma ƙarama tayi ta koma zaro idanu

Altine taci gaba "wallahi da zuciya ɗaya na nemi aiki a gidan nan ba dan na cutar da kowa ba,
wata rana ina ƙasa a kitchen mama tace na ɗan fara ɗora mata ruwa a kan gas kafin ta sakko,
sega umma ƙarama ta shigo sasan ta iskoni har cikin kitchen tace min "kizo anjima da daddare
ki same ni, akwai maganar da nake son yi da ke"
tana gama faɗa min haka ta juya ta fice da sauri jin sakkowar mama daga sama.

Ban kawo komi a raina ba naci gaba da aikina, amma can ƙasan raina murna nake ƙila wani
abun zan samu daga wajen ta tunda ta saba min alkairi haka kurum.

Da nagama aiki na, kusan kowa ya kwanta na tashi naje na sami umma ƙarama a ɗakin ta

Maganar data fara min ba ƙaramin gigita ni tayi ba da naji tace aiki zan mata bakin raina

a tsorace nace "wani kalar aiki ne haka hajiya?"

Dariya tayi tace "ba wani aiki bane me yawa, hasali ma ba ze ɗauke ki minti biyar ba kin gama,
amma fa se kin sa kanki"

Kaina a ƙatsa nace "to hajiya, ina jinki"

Wani ƙulli ta ɗakko a takarda ta miƙo min, murya ƙasa-ƙasa tace "so nake ki zuba shi a abincin
Abba ƙarami, shikenan kin gama aikin ki, ba

Please Login or Register in order to submit comment