Reading LAUJE CIKIN NAƊI by ZAINAB FALALU Chapter 11 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

auren nan ko ya samu
nutsuwar zucia.




*****
A mugun fusace uncle Abbas ya sauke ma Tk mari a duka kumatukan shi

Cikin zafin rai yanuna shi da yatsa yace " Har kai ka isa ka nuna min ga yarda zanyi a al'amura
na? tun jiya nake lallaɓa ka akan ka bari ina da shiri na amma ka ƙi ji, na faɗa na kuma faɗa
mumtaz bata da wani miji da ya wuce kai a yau ɗin nan saboda ina da tabbaci daga majiya me
ƙarfi, ohhh shine zakazo kana min barazana da zaka faɗi gaske cewa ni na saka ka danne
Abubakar(Abba ƙarami) ka kashe shi, ko kuma ka sanar mu muka saka a tsinke wayar burkin
motar shi?"

Cikin zafin rai ya ƙara matsawa kusa da TK dake ja da baya ya ɗora da "to da kayi babban
kuskure a rayuwar ka, kallo na kawai kake a matsayin mahaifi amma kai kanka kawar da kai ba
wani abu me wahala bane a waje na, sakarai shasha"

Still a cikin fushi ya juya gefen gadon ɗakin hotel da ya kama saboda cinkoson mata a cikin
gida, ya janyo babbar farar leda me ɗauke da farar shadda aciki

Wirga mishi ledar yayi kafin yace "kaje ka shirya, kuma karkayi wasa da turaren da na baka ka
tabbatar da seka hango Abubakar(Abba ƙ) tukun zaka shafa a hannun ka, ka tabbatar da ko
yaya ne hannun ka ya taɓa jikin sa kafin a ɗaura auren, daga nan ka gama naka se kaja gefe
kayi kallo"



Duk da ya TK yaji marin da uban nashi yayi mishi amma jin wannan bayanin ya wanke mishi
zuciya, ko ba komi yanzu ze nuna ma ya faruk yafi kusanci da Abba ƙ da kuma duk wani abu da
ya mallaka



Seda TK ya ɗauki ledar tukun yace "sorry dad, nima ba da son raina nayi maganar ba" yana
gama faɗin haka ya juya ya fice ranshi fess.
KHALID

Ɗaya da kusan rabi ya shiga cikin gidan nasu inda shima a cike yake danƙam da mutane

Tunda ya shigo yaje gaishe gaishe

Guɗa ta ko'ina se tashi take

Mami nadaga can ta jiyo guɗar mutane, da sauri ta tawo dan ta san be wuce kalid ɗin ne ya
shigo

Tana zuwa kuwa ta rungume shi haɗe da fashewa da kukan murna da kuma tunowa da
mahaifin shi

Shi kanshi dauriyace kawai ya ara ya yafa ma kanshi, amma ƙiris da ya fashe da kukan

Mami na rungume da shi ta rinƙa jeho mishi addu'oi mutanen kusa da ita suna amsawa

Ta jima a haka, kafin kamal ya matso kusa da ita yace "mami time ya kusa wallahi, 2pm ne
ɗaurin auren fa"

Da ƙyar dai ya zame kanshi daga wajen ta suka ɗunguma zuwa babban masallacin dake
manne a jikin gidan amaren.




Fotowar mumtaz kenan taji ana ta guɗa a palon ƙasa, kamar ta fasa sakkowa take ji

Badan calls ɗin da ƙawayen su keta auno mata ba da bazata sakko ba

ISMAT ƴar ƙawar mama da bata jima da isowa ba, dataga alamun juyawa mumtaz zatayi yasa
ta taro ta, galla mata harara tayi kafin tace "Halin ki sak da na yaya mardiya wallahi, kuyi ta abu
kamar baku da gaskiya"

Mumtaz bata ce komi ba, dan tasan musu da ISMAT ɗin Ummu ba riba shiyasa ta lafe a jikin ta
suka fara takowa

Tana sakkowa daidai nan taga mama ta rungume ya faruk da yasha galleliyar farar shaddar shi
da ta amsa sunan ta

Yarda yake sheƙi da walwali kwa rantse da Allah shine angon
Sakato Mumtaz tayi tana kallon su

Sam fara'ar fuskar mama taƙi ɓoyuwa, gefen kumatun shi ta mangara tukun tace "ka kyauta
daka dawo yarona, a jiki na naji kamar wani abu da na rasa ya dawo"



Dariya yayi yace "wallahi saboda ke na aje komi mamana nazo, daga tafiyata na gane baki so
hakan ba, shiyasa ni kuma nace dole nayi suprising ki"



Kafin mama ta sake magana ta hango mumtaz, da sauri ta kamo hannun ta

Tsakiyar ita da ya faruk ta shiga sannan tace wa me hoto ya ɗauke su

Haka camera man ɗin nan yayi ta kashe su da hotuna

ISMAT kam wayar ta kunna itama tayi ta kashe su



Tajuddeen(me hoton) yace "Hajiya ɗan fita a yi musu au biyu"



Fita mama tayi, nan kuma tsakanin ya faruk da mumtaz aka tsaya kallon kallo

Ko a jikin Tajuddeen ya matasa kusa da su sannan yace
"yallabai matso kayi haka" ya nuna mishi ya dafa ta

Ganin zasu ɓata mishi time yasa ya ɗauki hannun ya faruk da kanshi ya ɗora a kafaɗar mumtaz
data ɗan sunkuyar da kanta

Ganin da sauran space a tsakanin su yasa ISMAT matsowa da sauri ta tura mumtaz jikin ya
faruk

Da yake Tajuddeen mayen hoto ne tuni ya samu ya hashaska su, kai kace shine mijin



Bayan ya gama ɗaukan su, ya faruk ya juya ya fice da sauri dan gaf ake da fara ɗaura auren

Ɗago kan da Tajuddeen zeyi yace "Kai ban taɓa ganin angon da sukayi mugun dace da
amaryar sa ba irin wannan"
Daga mama har mumtaz seda suka ji wata faɗuwar gaba dajin furucin Tajuddeen me hoto

Ganin ba wanda ya bashi amsa yace "next, se suwa za'a ɗauka"



ISMAT na dariya tace "muje ta can" sannan taja mumtaz suka ƙarasa ficewa zuwa babban
palon da amaren da kuma ƙawayen su suke.



Tunda ya Tk ya iso wajen yake kutsawa ya samu ya dangane da cikin masallacin

Duk inda ya saƙa be yarda Abba ƙ ya ɓace wa idanun shi ba

Cunkoso ne sosai a wajen, amma haka ya kurkurɗa har ya dangane da gaba gaba inda wakila
duka angwayen ke zaune

Can ta gefe ya hango Abba babba da Abba ƙarami se kuma uncle junaid yayan mama

Ta ɗayan ɓangaren uncle Abbas da uncle ƙasim se ya faruk a gefen su da kuma dr jamal a
kusa da ya faruk

Kusa da Abba ƙ ya matsa mutum ɗaya ne a tsakanin su, daga can uncle Abbas na kallon shi
ganin ya dangane da Abban yasa shi lumshe idanun yana sauke ajiyar zuciya

Cike da kula ya Tk ya sunkuyar da kanshi tukun ya zaro kwalbar turaren daga cikin aljihun shi,
da ƙyar ya kwance ledar duk dai yana bi a hankali kar ya tama kayan shi

Yana samu ya kwance ledar ya buɗe murfin shima da ƙyar tukun ya tsiyaya turaren a tafun
hannun shi, ya riƙe kwalbar da ledar da kuma murfin a hannu ɗaya

Tsabar mugunta seda ya wani runtse idanu tukun ya matsa a inda yake tunanin Abba ƙ ɗin na
zaune, a wayance ya shafe wannan turare da ya zuba kaf a jikin uncle junaid, wanda a tunanin
Tk a jikin Abba ƙ ya saka

Buɗe idon da zeyi ya hango Abba ƙ ya matsa can wajen da liman ke sallah yana amsa waya

A mugun tsorace ya ja baya, tsautsayi da baya wuce lokacin shi, aikuwa sauran turaren ya kife
a jikin ya Tk

Tsaf akan idon uncle Abbas da hankalin shi yafi na Tk tashi



A mugun tsorace uncle Abbas ya miƙe tsaye, har uncle ƙasim na tambayar sha da "lafia?"
Ko amsa be bashi ba, yafara ƙoƙarin cinma Tk dayayi mutuwar tsaye anan inda yake

Kafin uncle Abbas ya ƙarasa wajen Tk ya fara jin juyawar kai da kuma ɗarsuwar abu a zuciya

Ko tunani na biyu beyi ba ya matsa can kusa da Abba babba

Abba Abba na ganin shi yace "ya akayi ne Tk?"

Kanshi a ƙasa yace "Inaso ka nemar min auren sakina a hannun mahaifin ta uncle junaid Abba
b"



Da mamaki Abba b ke kallon shi, bama shi kaɗai ba har sauran dake gewaye a wajen ma sunyi
mamaki

Uncle junaid na gefe idon shi sun kaɗa sunyi jajir, ga wata muguwar azalzala da yake ji a cikin
ranshi



Uncle Abbas na ganin an tsaya saurarar Tk ya koma kawai ya zauna, dan yasan tunda
tsautsayi yasa har turaren ya taɓa shi to ba makawa se an ɗaura auren

Amma inda zaku duba kuga a wani irin yanayi zuciyar shi ke a ciki se kun firgita da mugun
baƙin da zaku gani.



Wasa-wasa magana ta zama babba,

Uncle junaid da kanshi ya amsa da ya ba Tk auren sakina

Ya faruk da gayya ya cire sadaki ya biya ma Tk

Har aka ɗaura auren Tk da sakina mamaki be bar zukatan kusan kowa dake wajen ba

Da gangan ya faruk yace a fara ɗaura na Tk dan ba'a san abinda ubangiji ya ɓoye a ciki ba



Aikuwa nasun aka fara ɗaurawa, sannan aka ɗaura na hafsa se Bilkisu sannan Amal se najwa
Kafin a ɗaura auren mumtaz ya faruk ya saɓar ya bar wajen cike da ƙunar zuciya da rashin
sanin abun yi kuma.
ALHAMDULILLAH aure ya ɗauru tsakanin khalid safwan da amaryar sa mumtaZ Abubakar

Haka maroƙi yayi ta kururuwar faɗar sunayen angwayen da kuma amaren

Khalid da suke tsaye ta can ya lumshe ido haɗe da godiya ga ubangiji jin anɗaura

Jikin shi har rawa yake wajen ciro wayar shi yayi dialing no ɗin mumtaz.



HMMMMM, AKAWAI FA LUKUTAR MASIFA JAMA'A!!!!!!



ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR



👹
MAKIRCI
KISHI DA ALJANA
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI

WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg55-56



Mummy na cikin jama'a taga uncle Abbas ya shigo fuuuu kamar ze tashi sama

gaisuwa da mutane ke masa ko kallo basu ishe shi ba yayi ciki

Da mamaki mummy tabi bayan shi, sanda ta je har ya kulle ƙofar bedroom ɗin shi

Tsaye tayi a bakin ƙofar tana so ta gano abunda ya ɓata wa mijin nata rai har haka



A hankali ta fara kiran sunan shi tana ƙwanƙwasa ƙofar ya buɗe
Cikin tsananin fushi da hargowa uncle Abbas yace

"Wallahi da zaran kin ƙara taɓa ƙofar nan a bakin auren ki!!!"

A mugun bazata mummy taji furucin

Sakato tayi tana jin yarda bugun zuciyarta ya ƙaru daga jin furucin sa

Da yake tasan halinn zuciyar shi, a ranta tace "yanzu haka abinda akayi mishi be taka kara ya
karya ba yake wannan ɓacin ran," dawayewa tayi ta ja ƙafafuwanta ta bar wajen ta koma wajen
mutanen ta.



Tunda uncle Abbas ya kulle kanshi a ɗakin yake buga number malamin nasu,

Busy kawai ake ce mishi, amma ya ƙi haƙura ya manne wuta, da ta tsinke ya maida wani, daga
ƙarshe ma akace wayar akashe take.

Wurgi yayi da wayar sannan ya dafe kanshi da hannu bibbiyu ya kifa goshin shi a jikin bango ya
runtse idanu

Da ƙarfi ya ce "no! bazeyuwu ba billahillazi, ba zan ɗauki asara ba ban kuma santa ba" the way
yake magana da ƙarfi badan hayaniyar ƴan biki ba da babu abinda ze hana a ji shi.

Ganin yana neman zarewa a ɗan ƙanƙanin lokaci yasa ya janyo drower gefen gado ya zaro
kwalin sigari ya buɗe ya hau kunna musu wuta yana zuƙewa

A ƙanƙanin lokaci ya zuƙe kwalin tas sannan ya fara samun ɗan sukuni a ranshi.




Amare da ƙawayen su suna a nan anata shewa

Amal ta shigo palon da gudu tana haki

Kusan kowa kallon ta yake da mamaki

Hafsat ce tayi tsalan tace "oh Allah ya kyauta miki kedai, kar ki manta kin dai zama matar aure
tun ɗazu"

Dariya da shewa sauran suka saka, banda mumtaz data kafe ta da ido
Seda Amal ta zauna ta mayar da numfashin gudun data kwasa tace "Gulma da ɗumi ɗumin ta
na kwaso yasin"



Bata jira amsar su ba ta ɗora da "Ya TK shima ya angonce"



Ido a waje Najwa tace "Amma ba ya Tkn da na sani ba ko?"



Dariya sosai Amal keyi bayan ta kalli sakina dake ta wani taɓe baki irin ko'ajikin nan nata



Cike da son tabbatar da gaskiyar zancen mumtaz tace "a ina aka bashi auren tunda dai naga
alama kin koyo gulma kema"



Dariyar ta kawai take kwasa, lukutar masifar data hango a fuskokin mutanen gidan kawai ya
isheka sanin cewa AKWAI LAUJE A CIKIN NAƊI!



Ganin Amal taƙi basu amsar tambayoyin su ne yasa suka shareta dan maganar dama batayi
kama da warce za'a yarda da ita ba.




A waje kuwa, ana gama ɗaurin aure uncle junaid ya bar wajen saboda yarda yake jin kan shi na
jujjuyawa.



TK kam ya shiga sahun angwaye bakin nan nashi har kunne yake gaisawa da mutane ana
masa murna da sam barka.



Wurin a hautsine yake bama ka iya gane inda kowa yake

Ɗaurin aure ne ba na mutum ɗaya ko biyu ba

Shiyasa cinciridon jama'ar yayi yawa.

A haka dai aka rinƙa ragewa ana watsewa
Duka angwayen ko wanne tawagar shi sun bishi zuwa reception da suka shirya



Sam khalid beso tafiya ba, yaso se yaga fuskar amaryar tashi, bata samu amsa wayar shi ba,
ga gidan kuma ba ze shigu ba a yanzu, haka nan ya shige mota kamal yaja suka nufi wajen
reception.




Ba abinda mama ke maimaitawa se kalmar "innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"

Da damuwa a fuskar tace "An dena irin wannan auren fa Abban mus'ab, ni a iya zuwa gidan
nan da sakina keyi ban taɓa ganin wani abu ya haɗa ta da TK ba in ba gaisuwa ba, amma rana
tsaka ace an ɗaura aure"



Abba ƙ da shima haryanzu be fita daga mamakin al'amarin ba yace "To tunda mahaifin yarinya
yaji ya gani ai mu bamu data cewa zahra'u, in kika ga yarda junaid ya amsa ma Tkn ma zaki
sha mamaki wallahi, nasha Abbas zeyi magana shima naga yayi shiru daga baya ma ya bar
masallacin gaba ɗaya
Shi kuma junaid kafin na gama gaigaisawa da mutane na nemesa na rasa, kuma ya tashi ya
kashe wayoyi gaba ɗaya"



Ajiyar zuciya mama ta sauke sannan tace "Danƙari, tabbas akwai wani abu a ƙasa wallahi"



Goge zufar goshin shi yayi kafin yace "Yanzu abinda nake so dake shine, ki san yarda za'ayi ita
hajiya Asiyan kiyi mata magana ta fahinta kafin taji daga sama, daga nan se asan yarda za'a
ɓullo wa sakinar itama"



Jiki a mace mama tace "toh, bari naje"
Ta hauro sama, shi kuma ya fice ta ƙofar sirrin sa.



Mama na fitowa sukayi kiciɓus da hajiya Asiya data shigo a ruɗe

Da sauri mama ta tarbeta, bata jira komi ba gudun jan hankalin mutane garesu taja ta zuwa
bedroom ɗinta da ba kowa

Suna shiga ta danna key a ƙofa, kafin mama tace komi hajiya asiya tace "Ga dukkan alamu kinji
abinda na jiyo ko hajiya zahra?"

Jiki a sanyaye mama ta kamata ta zaunar da ita a gefen gado tace "Ki nutsu muyi magana haj
Asiya"



Da sauri maman sakina tace "Da gaske ne kenan?"



Cike da hikima mama tafara magana "Karki ɗaga hankalin ki akan abinda kika ji pls, Ya junaid
ba ze taɓa cutar da ƴarshi ba, ki riƙe zuciyar ki har sanda zakiji daga bakin mijin ki, nasan zaki fi
fahimtar zancen"



Fashewa da kuka tayi tace "wannan wani irin ƙaddara ne, aure ba shiri ba sanin uwa balle ƴar,
yanzu ya zanyi da sakina in taji wannan maganar bayan tana da wanda take so yake sonta,
innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"



Miƙewa da sauri mama tayi tace "ki zauna a nan kuma ki share hawayen nan, bari inje in tawo
da sakinar"
Ta fice da sauri har tana ɗan cin tuntuɓe.




Tun bayan shigowar Amal a gujen nan sakina taja can gefe tana amsa call ɗin saurayin ta dake
hanyar zuwa

Matsawa kusa da ita Amal tayi, seda tayi ƙasa da murya tace "wayar nan da kikeyi fa ta saɓawa
addini malama"
Ta ja gefe kamar ba ita tayi maganar ba

Seda sakina ta gama masa kwatancen gidan ta aje wayar kafin ta waiga inda Amal ke zaune
tace "Me kikace uwar ƴan shishshigi?"



Banza Amal tayi da ita, duk da taji me tace, amma tayi pretending kamar bata ji ba taci gaba da
firar ta

Ƙwata sakina tayi ta miƙe da niyar jan mumtaz zuwa sauya kaya mama ta faɗo ɗakin itama

Sama-sama ta amsa gaisuwar su kafin ta wurga idon ta can inda sakina ke tsaye tana wa
mumtaz magana
Da hanzari mama ta ƙarasa can, hannun sakina kawai ta kamo ta janyota suka fito daga palon
zuwa can sasan maman.



Suna fita Amal ta saki guɗa haɗe da karkaɗa jiki tana juyi

Kallon ta mumtaz tayi ta yafitota da hannu

Amal na dariya ta matso kusa da mumtaz

Kafin mumtaz tayi magana Amal tace "muje mu sauya kaya"

Mumtaz ta gane me take nufi, ba musu suka fice daga palon

Tacan bayan ɗakin ya faruk Amal taja mumtaz,

ido cikin ido Amal ta kalle ta tace "kin san wa ya Tk ya aura?"

Tsaki mumtaz taja kafin tace "wai wani ya Tkn kk magana akai?"



Cike da gulma Amal tace "Ya Tk na nan gidan, to wallahi na shiga ɗakin umma babba naji tana
waya da Abba b yana faɗa mata an ɗaura aure harda na ya Tk da sakinar uncle junaid"



Ido waje mumtaz ta dafe ƙirji tace "jakar ubancan kayyasa!!
Sakina fa kikace?"

Rai fess Amal tace "Rass sakinar da kika sani, kuma daga majiya me ƙarfin gaske naji"



Ai mumtaz bata gama tsayawa jin ta ba tayi hanyar sasan su da sauri kamar zata kifa

Direct bedroom ɗin mama ta nufa,
Murɗa ƙofar tayi tajita gam a rufe

Ƙwanƙwasa tayi, daga ciki mama tace "waye?"

"nice mama"

Sakina ce ta buɗe ƙofar duk tabi ta firgice
Mumtaz na shigowa tace "mama wai da gaske ya Tk an ɗaura mishi aure da sakina"

Dakatar da ita mama take, saboda sun kasa gaya ma sakinar, amma ina seda ta kai ƙarshen
tambayar ta kafin ta tsaya



A mugun firgice sakina tace "wai wace sakinar kike nufi?"



Shiru mumtaz tayi, ta nemi waje ta zauna ganin ɓallo ruwan datayi.



A tsorace sakina ta kalli maman ta dake kuka sannan ta waiga ta kalli mama itama tayi
zuru-zuru tace

"Dan Allah da gaske ni sakinar ake nufi wai?"

Yarda tayi magaanar mama taji wani mugun tausayi ya kamata,

Kamota tayi ta zaunar da ita tukun ta runguneta sannan tace "ki kwantar da hankalin ki sakina,
Dad ɗin ki kawai muke saurara muji tabbaci amma ba wani abun da zaki ɗaga hankalin ki bane
akai"



Da ƙarfi ta ture mama ta miƙe tsaye, cikin hargowa da rawar jiki tace "ku faɗa min gaskiya kafin
zuciyata ta buga, da gaske ni sakinar ake nufi ko wata ce daban?"

gyaɗa kai mama tayi sannan tace "ki nutsu abi komi a hankali sakina"



Wage baki tayi ta kurma ihun da seda ya janyo hankulan mutanen dake zaune a palo.



ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR

MAKIRCI
KISHI DA ALJANA 👹
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI

WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg57-58

A guje mama da mamar ta suka tare ta ganin zata buga kanta a ƙasa

Kafin ta kai ƙasa suka tare ta

Cikin kuka maman ta ke jijjiga ta tana kiran sunan ta

Mumtaz dake tsaye jiki na ta kerma mama tace "kawo ruwa da sauri suma tayi"



Gaba ɗaya mumtaz ta ruɗe ta manta sam akwai toilet a ɗakin ta buɗe ƙofa ta fice a ruɗe zuwa
neman ruwa

Buɗe ƙofar data yi ne ya ba wasu daga cikin ƴan'uwan maman shigowa ɗakin

Ƙanwar mahaifiyar su maman ce tace "me ya same ta ne ni hassu, ina yanzun nan naga
gilmawar ta?"



Cike da kuka sa kuma ɓacin rai da ya fara bayyana a fuskar mum ɗin sakina ta waiga ta kalli
matar tace "inna hassu wallahi in dai junaid yayi sanadiyar rayuwar ƴata sena maka shi a kotu,
na san ba wanda ya isa ya gaya mishi yaji, amma ke tunda ƙanwar uwace a wajen shi ƙila yaji
taki maganar"
Bata ƙarasa ba inna hassu ta dakatar da ita cikin sauri tace "Kiyi ki kaini inda nake son zuwa kin
tsaya kina ta mana jaye jayen lukutar masifa"



Mama tayi caraf tace "ayi a hankali dan Allah, kunga akwai baƙin kunya a gidan"

Inna hassu tace "ku faɗa min me junaidun yayi?

Mama tace "aure ya ɗaura mata da ɗan gidan ƙanin megidana"



Kusan gaba ɗaya ɗakin aka hau salati da tafa hannuwa
Riƙe baki inna hassu tayi tace "shine wai abin ɗaga hankali harda suma?"

Sakatoo mum ɗin sakina da mama sukayi suna kallon ta da mamaki

mum ɗin sakina tace "aure fa ba shiri, babu jituwa ko wata sanayya tsakanin ta da yaro fa inna
hassu"



Ɗaya bayan ɗaya inna hassu tace kowa ya fita

Kowa ya fita ya rage daga ita se mama se mum ɗin sakina,
Se sakinar dake kwance ido rufe bayan ta farfaɗo daga suman wucin gadin data yi



Inna hassu ta kalle su duka tace "waye ke da haƙƙin aurar da ƴarsa?"

Ba wanda yace komi, da kanta ta ba kanta amsa tace "ina ubane ke da wannan haƙƙin"?

Ta ɗora da "mujira shi muji hujjar shi ta yanke wannan hukuncin da yayi ba wai ku zauna ku
ɗaga hankalin ku ba itama yarinyar ku ɗaga mata nata.

Yanzu abunda za'ayi shine, ke Asiya kamo ƴarki mu tafi can gidan naku ayi komi a can gudun
surutun mutane"



Ba yarda suka iya haka mum ɗin ta kamo sakina da banda kuka babu abinda takeyi, duk uban
kwalliyar da aka ɗauka ta caccaɓe da hawaye da majina, suka yi waje.

Kun san gidan biki, nan aka koma maganar da yarda abun ya kasance.



Mummy kam data ji batayi mamaki ba, dan ta san a halin mijin ta ze iya aikata komi ba tare da
sanin ta ba

Da Tkn ya shigo gidan ma rungume ta yayi yana murnar shima ya zama ango

Zaunar da shi tayi ta tambaye shi ra'ayin shi ne ko kuwa na iyayen shi ne

Da bakin shi yace mata ra'ayin shi ne, harda ƙarin cewa, daga tambayar baban ta yace kawai a
ɗaura yanzu.

a haka ya barta, ko ajikin ta taci gaba da sabgar jama'ar data gayyata.
Tsegumi na can sasan umma babba tunda ita ta fara jin maganar auren

Tayi-tayi taji wani abu game da auren a bakin ya faruk, amma yace mata be san komi ba akan
lamarin.



Inna hassu suna isa gidan suka iske uncle junaid baje yana bacci

Da mamaki sakina da mum ɗinta suke kallob shi,

Cikin kuka sakina tace "Gaskiya ba lafia ba mum, kalli a yarda dad ke bacci fa"



Ita kanta hajiya Asiyan jiki a sanyaye ta matsa kusa da mijin ta,
Ƙafar shi ta kama ta jire mishi takalmi sannan ta cire mai hular kanshi, da ƙyar suka haɗu su
ukun suka cire mishi malum malum

Inna hassu ta kalli haj Asiya tace "anya lafiar shi ƙalau kuwa?"



Shiru hajiya asiya tayi, tama rasa wani kalar tunani zatayi.




A gidan biki kuwa an ci gaba da shagali, masu janjanin magana nata yi, a haka ma wasu basu
san da maganar ba ana ta sha'ani



Wajen biyar da rabi na yamma masu ɗaukar amare suka fara isowa

Kaf amaren sun bar palon da suke zaune, ko wacce ta koma sasan su



Ya sabiha ta sasu Amal yin wanka kafin su Abba babba su ƙaraso

Haka Najwa itama ƙanwar mummy ta haɗa mata ruwan wanka da yaji turaruka masu ƙamshi.



Mumtaz kuwa tunda aka fitar da sakina jikin ta ya sake yin sanyi, ga azababbiyar faɗuwar
gaban da ta ƙaru fiye da na baya
Maman kanta dauriya kawai take wajen sallamar mutane dan kalli ɗaya zakai mata kasan duk a
firgice take, bata da sukunin zuciya

Mumtaz na nan kwance a kan gadon mama ta sake shigowa ɗakin

cikin faɗan dabata san daga ina ba tace "yanzun ma se nace kiyi wankan ne?"

Murya na rawa tace "a'a mama"

Mayafin ta tafara cirewa sannan ta cire sauran kayan

Ɗaya daga cikin akwatunan ta da ta haɗa ta buɗe, towel ta ɗauka sannan ta shige toilet tana
share hawayen da suka sakko mata.

Ta jima a ciki tana kuka kafin tayi wankan ta fito

Mai kawai ta shafa, se kayan ƙamshi, amma ko kwalli babu a idon ta

Wannan karon blue black ɗin atamfar me ratsin fari a jiki ta saka
Masha Allah, sosai ta fito a cikin ɗinki tayi ɗass abinta shigar ta dace da kalar fatar ta ƙwarai.



Buɗe jakar da ƴankunnaye ta ke aciki tayi har ta ɗauki ƴan kunne masu kyau zata saka ta fasa,

ƙananun barima ta ɗauka ta manna a kunnen ta, har zata rufe jakar ta hango wannan ɗan abin
hannun da ta sata ta, da sauri ta kai hannu ta ɗauke shi ta saka a hannun damanta,

first time da ta saka abun hannun kenan, shiru tayi ta tsaya tana kallon yarda ya dace da
hannun ta da kuma shigar data yi

Haka kawai ta tsinci kanta da yin murmushi.



Maida komi tayi ta rufe bayan ta cire sabon farin hijabi ƙar daga cikin kayan

Sassauke akwatunan tayi ƙasa, tukun ta haye gefen gadon tayi kwanciyar ta.



Gab da magariba su Abba b suka sallami ƴaƴan nasu bayan doguwar nasiha da suka sha

Tun ana jiran uncle Abbas har suka gaji suka sallami yaran .
Tabbas gida yana da daɗi, koda kai kaji kana son auren, amma ranar tafiya gidan miji se an
ɗaure

gaba ɗayan su kuka suke, kar ma kuzo kuga mumtaz, duk irin dauriya da kawar da kai irin na
Abba ƙ, kasa daurewa yayi, be bari an gama ba ya bar palon

Mama kam dama ko da aka kira ta ƙin zuwa tayi, da goggon safiya ta dameta se cewa tayi "ai ni
na gama mata faɗa, duk abinda taga inayi tayi shi bazata taɓa taɓewa ba"

Ba yarda goggo safiya ta iya, haka ta rabu da ita.



Ya faruk na cikin RANGE ROVER shi ƴar yayi, gab da babban palon,

Ko wacce an riƙota fuskar ta a rufe zuwa wajen motar

Duk da ba da son ranshi ze kaisu gidajen nasu ba ya sakko yace "Iya su biyar ɗin zan ɗauka,
ko wacce ta shiga wata motar"

Goggo safiya tayu caraf tace, "a ina ka

Please Login or Register in order to submit comment