Reading LAUJE CIKIN NAƊI by ZAINAB FALALU Chapter 14 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

matso kusa da ita ya tsaya ta bayanta

Da hannu ya zungureta, aikuwa a firgice ta juyo jikin ta na ɗan rawa

Da baki ya nuna mata inda takalmin ya shige

Da sauri ta janyo shi tayi hanyar fita har tana cin tuntuɓe da ƙafarshi

Karkaɗa kai kawai yayi tukun ya bi ya kashe wutar gidan sannan yaja ƙofar ya rufe ya ƙarasa
motar

Ganin mama zaune a gaba yasa ya ɗab waiwaya baya, can ya hango mumtaz maƙure a gefe

Be san sanda murmushi ya suɓuce mishi ba,
Duk abinda yake ta gefen ido mama ke kallon shi,

Farin cikin da take ji be misaltuwa dan rabon dataji irin haka ta mance.



Motar tayi tsit baka jin motsin kowa, dukansu da saƙe-saƙen da suke

Sun ɗanyi nisa kaɗan, jin shirun yayi yawa ya faruk ya kunna radio, rabi idon shi na titi rabi
kuma yana kan radio
Canza radion yayi da bluetooth sannan yayi searching waƙar Naziru "IN RABO YA TSARO DA
KAI, KUMA ABUN YA TABBATA DA KAI, RABBI NE YACE SE DA KAI EM SE DA KAI KAWAI
SEDA KAI...." har ƙarshe

Cikin shauƙi da annushuwa yake bin waƙar duk da a hankali yake bi amma hakan be hana
mama jin shi ba

Murmushi sam yaƙi barin fuskar ta.

Suna zuwa ƙofar gida yace "mama ba zan shiga ba nan zaku sauka akwai inda nake son zuwa"

Agogon motar mama ta kalla tukun tace "its late fa faruk"

Murnushi yayi tukun yace "Bazan jima ba ai"

Ganin mumtaz na son riga kowa fita yasa shi saurin faɗin "Mumtaz tsaya ke ki wuce da
wannan" yayi maganar yana wani faskewa

Ranƙwashi goggo safiya ta kai mishi haɗe da faɗin "algungumi, kaji dashi dai" ta fice, mama ma
na dariya ta fice

Suna fita ya saka lock a motar

Idin shi na kansu mama har suka shiga gate, sannan ya waigo ya kalle ta

Daga sama har ƙasa yake kallon ta, itakam taƙi yarda ko sau ɗaya ta kalle shi, ta takure a waje
ɗaya

Seda ya gama kallon ta tas tukun yace "Da kin shiga gida ki tabbatar da kin cire waɗan nan
kayan jikin naki, ki ɗauki naki na gida ki saka, ko da wasa kar in sake ganin ki da kayan da
wancan guntun ya kawo"
Mancewa ma tayi da tsoron ta saki baki tana kallon yarda ya faruk yasha mur yake bata umarni



Hannu ya kai ya tsokale mata manyan idanunta da sauri ta rufe idon da hannu haɗe da faɗin
"wayyo Allah"

Murya ƙasa-ƙasa yace "nan gaba ƙwaƙulo daƙwa daƙwan idanuwan zanyi tunda baki iya amsa
ni ba sedai ki kafe ni da idanu kamar ansoya tasoyu"

Murza idon take, amma hakan be hanata zumɓuro mishi baki ba

Murmushi yayi ya kauda idon shi tukun yace "jeki, shine saƙon dama"

Ko ƙarasa rufe baki beba tayi wuf ta fice, ki waiwaye batayi ba, tana tafe tana faɗin "daɗin abun
ma ai idanun ka sun fi nawa girma"

Seda yaga ta shige tukun yaja motar yayi gaba.

Wayar shi tayi ringing ya ɗaga yace "on my way" ya sauke yaci gaba da tuƙi.



A parking lot na gidan dr jamal yayi parking, direct ciki ya shiga inda ya iske mus'ab da dr jamal
na zaune ko wanne da yana ɗauke da mug me ɗauke da coffee a ciki

Yana shiga toilet ɗin palon ya shiga ya ɗauro alwala sannan ya fito

Anan palon ya kabbara sallar shi,

Ya jima yana addu'ar neman sassauci daga wajen ubangiji akan umman shi, haɗe da godiyar
kyautar da ya bashi a sanda ya riga da yacire rai gaba ɗaya

Seda ya gama tukun ya dawo palon ya zaune haɗe da cire hular kanshi yana faɗin "wash"

Cike da damuwa mus'ab yace "kun mayar da mumtaz ɗin ne?"

Karkaɗa kai yayi haɗe da kallon dr jamal ya ce "guess what?"



Girar shi biyu dr jamal ya ɗaga sannan yace "kasan im not a good a guessing abu, kawai mlm
ka gaya mana"



Murmushi ya faruk yayi yace "Da gaske nima yau ango ne"
A mugun bazata suka ji maganar, sedai basu yarda ba

Dr jamal tsaki yaja yace "karo na farko da naji kayi ƙarya kenan wallahi, Halan tsinko matar
akeyi a bishiya?"



Dariya kawai ya faruk keyi



Mus'ab da yasan waye yayan nashi yace "Sunyi galaba akan mu ko mu mukayi ya faruk?"



Tashi ya faruk yayi, ya zagaya ta side ɗin mus'ab yace " akoda yaushe Allah na bayan me
gaskiya mus'ab, a yau Allah ya mallaka min mumtaz a matsayin matar aure"

Da gudu mus'ab ya rungume ya faruk, tsabar murna da yarda yake ji ya hana shi magana,
banda "Alhamdulillah, Alhamdulillah" babu abinda yake faɗa, dan ya san babban burin yayan
nashi kenan, kuma babban burin iyayen shi.



Tasowa dr jamal shima yayi baki buɗe yace "are u for real guy?"

Gyaɗa kai ya faruk yayi, shauƙin abun na daɗa tasiri a ranshi.



Ɗakin da Tk yake kwance suka nufa

Yana nan a kwance kamar yarda suka aje shi
Ya faruk yace "Ina ganin ba zamu bari se da safe ba, kawai mu fitar da shi tunda abun yazo da
sauƙi"

Mus'ab yace "hakane, ina ta ganin calls ɗin uncle Abbas harda na uncle junaid ma, amma ba
wanda muka ɗaga daga baya ma kashe wayar muka yi"

Murmushi ya faruk yayi yace "su ya shafa wannan, mu saka shi a mota mu maida shi"

Su ukun suka cinciɓe shi sukayi waje da shi

A bayan motar da mus'ab ke basaja da ita aka saka shi

ya faruk ya shiga tashi motar, mus'ab da dr jamal suka shiga motar mus'ab ɗin suka fice kusan
a tare.
a inda suka ɗaukeshi nan suka koma, mus'ab ya ciro key ɗin motar TK ya buɗe, sannan suka
kamo shi suka saka shi a motar shi

Dr jamal yayi mishi allurar da zata dawo da shi hankalin shi cikin minti biyar, sannan suka bar
wajen gaba ɗaya.




****** Tunda su mama suka shiga gida goggo safiya ke rafka guɗa a tsakar gida

Irin guɗar nan me shiga kai har ƙwaƙwalwa

Da kusan gudu mama ta shige sasan ta dan ta san jan maganane goggo safiyar ke ƙoƙarin yi



Jama'ar gida jin guɗar taƙi ƙarewa yasa aka hau firfitowa, abinka dama da gida na a cike da ƴan
biki

Dangi su goggo safiyar ma tun kafin suji komi suka hau tayata da guɗar



Umma babba na ɗaka tana ba su ya sabiha labarin abinda ya faru a gidan su kalid suka jiyo
hayaniya gidan gaba ɗaya ya ƙaure da iface iface da guɗoɗi

Su ya sabiha hankalin su a matuƙar tashe jin mummunan labari daga mahaifiyar tasu suka
mimmiƙe, dan a yarda suke jiyowa kamar ma faɗa ne aje a wajen

Ya maryam ce ta banko ɗakin da gudu, ta ƙanƙame umma babba tace "Allah mun gode maka,
Allah ya kiyashe mu jin kunya duniya da lahira, ga goggo safiya can na faɗin an ɗaura auren ya
faruk da mumtaz yanzu"!



Wata wawiyar hankaɗa umma b tayi ma ya maryam har seda ta kusa wuntsilawa, a mugun
firgice tace "Na shiga uku na Nabila, waye ke shirin ganin bayana"!

Tayi hanyar fita da gudu!

ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR



👹
MAKIRCI
KISHI DA ALJANA
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI

WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg67-68

Cikin zafin nama ya sabiha ta tare umma babba da gaba ɗaya idanun ta sun rufe tsabar tashin
hankali



Jiki na rawa ya sabiha tace "Dan girman Allah umma ki nutsu kar kije kiyi abinda zaki zo kina
nadama daga baya"

Ya maryam itama tace "ga gida bamu kaɗai ba, baka san waye ze tafi da kai a baki ba umma"



Ya fa'iza kam na ganin umman zata fice tayi wuf ta fice ta rufe main ƙofar palon da key tayi
gaba.



Cikin tsananin fushi umma b tace "sakeni sabiha kafin kiji mugun furuci daga bakina wallahi"

A hankali jiki a saɓule suka ja baya suka zuba mata ido

Yarda ta fito da zafin ta tana zuwa ƙofar palon taja tajita a garƙame

Kallon ƙofar tayi taga ta waje aka rufe

Fuuu ta koma ciki, a yarda ta barsu a haka ta iske su, zazzare musu ido tayi ta hau nuna su da
yatsa tace "ubanwaye a cikin ku yasa aka rufe ƙofar?"

Kusan a tare sabiha da maryam suka sauke ajiyar zuciya, sanin aikin fa'iza ne

Cikin tsawa umma tace "ba magana nake muku ba wai"

Nan ma a tare suka haɗa baki wajen faɗin "bamu sani ba umma"



Yaraf ta faɗa a kan kujera, tama rasa me zatayi, can ta zabura tace "Ku miƙo man wayata"



Sanin zata nemi wayar yasa suka kasheta suka ɓoye"



Kamar da gaske suka hau neman wayar

Sama ko ƙasa ba'a ganta ba, duk suka yi tsuru-tsuru ganin kallon da umman ke musu

Seda ta gama kallon su tsaf tukun tace "na gama gane rainin hankalin ku, to ku rubuta ku ajiye
ba zan taɓa yarda da wannan abun da akayi man ba, dama sun mallake man ɗanne dan sun
san abinda suka shirya ko?"



Da sauri ya sabiha tace "karkice haka umma, dan girman Allah ki nutsu kar ki kawo wani abu
can da be da alaƙa da wannan"



Da ƙarfi umma b tace "ku dakata man dan ubanku, na lura kallon mahaukaciya kuke man a
gidan nan, to bari kuji na jima da sanin faruk yana son mumtaz shiyasa tun wuri nayi ma tufkar
hanci na gargaɗe shi, da yake munafuki ne shima se yayi man wasa da hankali ya nuna min
bema san wacece mumtaz ba da har ze so ta

ohhh shine yanzu dan su nuna min ban isa ba yasa aka tafi can aka gama ƙulle-ƙullen tukun
zanji, banma ji daga matushiya me ƙarfi ba se a saƙar gari"



Gefe da gefen ta sabiha da maryam suka zauna

Cike da lallami suka fara nusar da umma b da gaba ɗaya ta gama haɗa zufa tsabar bala'i

Ya sabiha tace "Umma kar muyi ma ubangiji shishshigi a cikin ikon sa fa, wallahi tsanani akan
abunda akwai rabo yakan kai mutum ga kushewar sa fa"
Wannan maganar da ya sabiha tayi ta sake tunzira umma b,

Dole suka haƙura suka rabu da ita, haka tayi ta surfa bala'i a cikin ɗaki, su kuma suna gefe sun
zuba wa sarautar Allah ido

Amma fa sunyi babakere sun hanata fita ko nan da can.




****Da mamaki Tk ke kallon gari yarda yayi duhu

Da sauri ya janyo wayar shi dake yashe a kusa da shi ya danna yaga har sha biyu na dare ta
kusa



Da mamaki yace "Ahh gari da sauran haske fa na tsaya a wajen nan,
To bacci nayi ko me?

Bashi da me bashi wannan amsar,

Missed calls ɗin uncle Abbas dana uncle junaid har ma dana mummyn shi da ya gani tururu a
wayar shi ƙara bashi mamaki

Da sauri yayi dialing no ɗin uncle Abbas,

Kamar jira yake, ringing ɗaya tayi ya ɗaga, cike da zafin rai uncle Abbas ya fara surfa mashi
banbamin bala'i, shiru Tk yayi yana sauraron shi yana wani ɓata rai

Daga can uncle Abbas yace "To gidan ubanwa kaje ka ajiye wayar ina ta neman ka, kai duk
abinda aka haɗa da kai suka ba mutane matsala, kazo hotel ɗin da nake ka same ni yanzun
nan shashashan banza" be jira cewar shi ba ya kashe wayar shi.




A guje TK ya taka motar ya bar wajen, cikin ƙanƙanin lokaci ya isa hotel ɗin.



Ƙwanƙwasa ƙofar yayi, ko cire hannun shi beyi daga ƙofar ba akace "shigo"



Tura ƙofar yayi ya shiga, kanshi a ƙasa dan be san da wacce kuma uncle Abbas ɗin ze tarbe shi
Still kanshi a ƙasa ya samu waje ya zauna, muryar uncle junaid da yaji ne ya sashi saurin ɗaga
kanshi

Fuska a ɗaure Tk ke kallon uncle junaid da sam shima babu alamun rahma a tattare da shi



Ɓata rai Tk yayi yace "Banji me kace ba"



Miƙewa tsaye uncle junaid yayi, cike da hargowa yace "Ka sakar min ƴa nace!"



Dariyar gefen baki Tk yayi sannan yace "shine kiran dama?"



Daga gefe uncle Abbas yace "Dole ka saketa yanzun nan kafin mu fuskanci matsalar dake
shirin tunkaro mu"



Cike da hargowa uncle junaid yace "ni kam yanzu na haƙura da komi, kawai ka saka ɗanka ya
sakar man ƴa daga nan ku ƙarata can ku kuka sani, shekara da shekaru muna akan abu ɗaya,
har yau ba nasara, da munga alamun nasara lokaci kaɗan kuma muga akasin haka,

To ni na janye na fita a ciki tunda har abun na neman taɓa min gida"



Daga can gefe umma ƙarama ta cire nose mask ɗin fuskar ta, ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya tace
"Baka isa ba Junaid, tunda aka soma da kai to tabbas da kai za'a gama"!.



Bani kaina ba har Tk da ke zaune seda ya miƙe ganin warce betaɓa zato ba, da mamaki ya
nuna umma ƙarama yace "umma ƙ!"

Gira ɗaya ta ɗaga mishi kafin ta miƙe tsaye, dariya tayi tace "kayi mamaki ko Tk?"

Murmushi ta sake yi sannan tace "anmin shigar sauri ne da tuni nice mahaifiyar ka"

Da ƙarfi uncle Abbas yace "Stop it sumayya"

Cikin salo da ƙwarewa a bariki umma ƙarama ta juya kaɗa mishi idanu tayi kafin tace "We will
come back to that my Abbas"
Daga can inda ya faruk da mus'ab ke zaune suna sauraron su ta wayar Tk ɗin,

Tsabar tashin hankali ya faruk kasa ci gaba yayi da saurare jin muryar umma ƙarama ƙurukuru
cikin gang ɗin su uncle Abbas

Sunan Allah kawai yake ambata dan tabbas ya shiga ruɗu, anan take maganar umma babba ta
faɗo mishi inda take cewa "Allah ka rabani da zama mutum me kan maciji"

A bayyane yace "La haula wala ƙuwata illa billah"



Murmushi mus'ab yayi yace "Anjima ana ruwa ƙasa na shanyewa".




Tk be gama fita a mamakin da ya shiga ba uncle junaid yace " Kai nake jira Tk, bani takardar
ƴata kafin ran kowa ya ɓaci a wajen nan"



Dariya Tk yayi ya hau tafa hannaye yana nuna su ɗaya bayan ɗaya, kafin yace "wallahi ba zan
sake ta ba, babban kuskuren da kuka yi shine bari a ɗaura auren, oh kuna nufin in sake ta
shikenan nayi biyu babu?"



Kanne musu ido uncle Abbas yayi, sannan ya matsa kusa da Tk ya dafa kafaɗar shi yace

"Baka yarda da baban ka ba kenan?"

Shiru yayi ya hau hura hanci

Cikin dabara uncle Abbas ya ɗora da "mu gata muke maka baka sani ba, taya za'ayi a baka
auren mumtaz bayan kana auren ƴar ɗan'uwan mahaifiyar ta?

Kai sakarai ne, kayi tunani akai"



Shiru Tk yayi yana nazarin maganar uncle Abbas, can yace "Kasan faruk ba ze taɓa sakin
yarinyar nan ba tunda ya samu ya dafe ta, balle na aure ta, kuma kowa yasan sarai yana sonta
dama"



Tsaki umma ƙarama tayi tace "Lallai da gaske sakaran ne kai, yanzu kai kana tunanin
mahaifiyar faruk zata yarda ya zauna da yarinyar da aka saketa a ranar da aka kaita gidan miji
ɗanta ya aura?

Har yau kenan baka gama fahimtar wacece hajiya Nabila ba, macece da bata son wani aibu ko
kaɗan ya shafi ƴaƴan ta, kuma kar ka mance a dalilin sata ne aka sako mumtaz har aka maye
gurbi da ɗanta, daɗin daɗawa ma a gaban ta akayi case ɗin komi"



Shiru Tk yayi, tabbas ya yarda da abinda umma ƙ kefaɗa,

Ajiyar zuciya ya sauke sannan yace "na yarda in har faruk ya saki mumtaz to nima zan saki
sakina" yana gama faɗin haka ya fice



Zama suka yi gaba ɗaya kowa da saƙe-saƙen da yake a rai

Umma ƙarama ta katse shirun da "mu sake haƙuri mugani, muka yi haƙurin shekaru ma balle
yanzu na ɗan taƙin lokaci"

Tsaki uncle junaid yayi yace "Baki san taurin kai da tsaurin ido irin na faruk ba wallahi,
Shiyasa nayi mugun tsanar yaron nan"



Murmushi uncle Abbas yayi yace "Dole daman sedai a ɓullo mashi ta bayan gida"



Umma ƙarama tace "to ta yaya kenan"?

Uncle Abbas yace "habaici zaki koma ki rinƙa saƙa mata a fakaice, tunda har mun san inda
weakness ɗin ta yake, dole zata hasala tace zata yi mishi baki in be sake ta ba, shi kuma in ba
wawa bane ai ba ze yarda ya ɓalɓance a banza a wofi ba, daga nan ze sake ta, kuma at the
same time mun karya ƙwarin gwiwar iyayen da kuma ita kanta ƴar"

Dariya suka kwashe da ita duka, umma ƙarama harda kwanciya a kafaɗar uncle Abbas tana
wanu jinjina mashi.

Tas plans ɗin da suka shirya a kunnen ya faruk da mus'ab, seda suka gama naɗar komi kafin
suyi saving

Dialing no ɗin dr jamal ya faruk yayi, yana ɗagawa yace "na gama ji aboki, saura abu na gaba
kuma".



KUN SAN YAU INA HUTU, AMMA HAKA NAN NA DAURE NAYI MAKU
ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR



👹
MAKIRCI
KISHI DA ALJANA
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI

WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg69-70

Duk wata hanya da ya faruk yasan ze haɗu da umma b ya kauce mata

A daren suka yi waya da ƴan'uwan shi suka ji dahir ɗin zancen auren a bakin shi, kuma suka
sanar da shi jiran da umma b ke masa,

Sosai suka taya shi murna, bama kamar ya sabiha datafi kowa sanin shi.



***MAMA

Murnar data ke ciki bata musaltuwa, ƴan'uwan ta kaf da suke gidan kowa yaji abunda ya faru na
auren mumtaz da ya faruk,

Da mamaki da yawansu ke tambayar ya akai hakan ta kasance

Kafin mama tayi magana goggo safiya tayi caraf tace "sauyin ubangiji mana, a daren tun kafin
mu kai ga isa da ita mijin ya kira yace ya sake ta akan dalilin shi mara tushe,

Aikuwa a cikin daren jiya iyayen ta suka ɗaura mata da wanda yafi shi komi"

Al'ajabin maganar kowa yake,
Sedai maganar data ke fitowa daga sasan umma babba daban da warce goggo safiya ke faɗa

Yawanci da magana biyu a zuciya suka bar gidan.




Tun a daren jiya da aka ɗaura auren ya faruk da mumtaz Abba babba ke neman umma babba a
waya amma wayar a kashe

Se kawai yayi la'akari da ƙila ta shiga ribibin mutane ne ya haƙura zuwa wayewar garin Allah

besan tana can tana tafasa ba.



Mutane na nesa nata shirye shiryen tafiya gidajen su ta ɓangaren mummy da aunty, tunda su
acewar su sun gama nasu bikin.



Mama kuwa a wannan safiyar tana tashi ta bada umarni a ɗora manyan tukwane a wuta

Inna hassu da ta baro gidan uncle junaid tun a daren jiya tace "anya basuyi yawa ba zahra'u?"

Murmushi mama tayi annushuwar fuskar ta na daɗa yalwatuwa tace "Basu yi ba inna, so nake
akai gidan marayu sannan a raba wa almajirai "

Gyaɗa kai inna hassu tayi, kafin tace "kice mu yanzu muka fara hidamar tamu"

Mama tace "ƙwarai kuwa, sabon ango sabuwar hidima"



Gaba ɗaya wajen suka saka dariya da guɗa

A hankali Altine tayi ƙasa da murya tace wa ɗayar me aikin da suke aikin hidimar bikin tare tace
"Rabon da naga baiwar Allah n nan a cikin farin ciki haka na mance wallahi,
Ki kalle ta da kyau ki gani, tunda aka fara hidimar bikin nan bata a cikin walwala sam, amma
daga jiya da daddare zuwa yanzu ko aljihun ki ze sheda da tana cikin murna"



Dariya matar tayi ta dafe lalitar ta taji zam kuɗin ta na nan, sannan tace "kyauta me tsoka fa
mun shata, mukam gaba ta kaimu wannan sauyin tunda ko ba komi mun sami alkairi"

Suna aiki suna hirar su, ko irin su nuna gajiyar nan, amma daka gansu zaka san cikin nishaɗi
da walwala suma suke aikin.
*****
Sha ɗaya da kusan rabi na safe yaya faruk yayi parking a harabar gidan nasu



Tunda ya tsaya be fito ba, yana ciki zaune yana ƙare wa jama'ar dake harabar gidan kallo ta
cikin baƙin gilashin motar shi

Seda ya gama kallon kowa tukun ya kwashi wayoyin shi dake ajiye a gefe sannan ya saka ƙafa
ya fito

Ma sha Allah! koni kallo ɗaya nayi mashi na tabbatar da lallai ya faruk ya zama ango da gaske

Banda baza ƙanshi da sheƙi ba abinda yake

Duk da faɗuwar gaban da yake ji hakan be hana shi murmushi ba



ya fauza dake ta kai kawo a harabar gidan ita ta fara hango shi

Ihu ta fasa tace "Angooooo"

Aikuwa akayo mishi caaa

Abokan wasa kowa na yagar shi, hatta da ƙannin shi yau basu barshi ba

Ba abinda yake se aukin murmushi da saɓa babbar riga



Ta window umma babba ke hango shi, ta ƙara ciki tayi fam ganin yarda yake wani zuba
murmushi yana amsa addu'o'in da ake mishi.



Da ƙyar ya kufce musu ya shige ciki wajen umma b

Zaune a palo ya iske umma ƙarama da wasu daga cikin baƙi

Be nuna komi a fuska ba yace "barka da safiya umma ƙarama"
ya gaishe da sauran sannan ya shige ɗakin umma babba
Tana tsaye jikin window dake kallon harabar gidan

A ɗan ɗarare yayi sallama ya shigo ɗakin

Ciki-ciki ta amsa, bata waigo ba bata kuma nuna tasan ya shigo ba

Gefen kujera ya ɗosana ya zauna, kanshi a ƙasa yace

"Ki yafe min umma na, wallahi tallahi ba'a tambayi ra'ayi na ba nima akan maganar"

Jin rainin da yake ƙoƙarin kawo mata yasa ta waigo a fusace tace "Dakata faruk, yanzu na sake
tabbatar wa da bani da wani matsayi me girma a wajen ka kai da mahaifin ka,

Na sha komin lalacewa ta tunda har ni na tsugunna na haife ka za'a nemi shawarata koda kuwa
ba zan yarda ba, nasan an fita haƙƙina an gaya min

Amma abun haushin sedai naji a gari, har wasu su sami damar yi min gori da habaici"

Tana faɗin haka ta hau share hawaye tana tuno da kalar habaicin da umma ƙarama ta yayyaɓa
mata ɗazu da safe



Gyaɗa kai ya faruk yayi, a ranshi yace "Tabbas sun gama sanin laggon ki umma na"



Jin bece komi ba yasa taci gaba da faɗin "wai kamar ni ace ɗan da shi kaɗai ne ɗa namiji dana
haifa ya ɓige da auren ɓarauniya, kai abin da ciwo wallahi"

Jin ta ɗan fara ɗaga murya, ga kuma mutane dake ta kai kawo yasa ya miƙe a hankali ya
sakaya ƙofar sannan ya dawo kusa da umman da ke ta sharar ƙwalla ya zauna



Kama hannayen ta yayi sannan yayi ƙasa da murya cike da ladabi da kuma sanin haƙƙin
mahaifiya yace

"Ki yafe min kuma ki yafe wa Abba na umma, wallahi tallahi muna sonki kuma kina da daraja a
waje na fiye da kowa a duniyar nan umma, kece kawai kika kasa fahimtar hakan"



Muryar ta na rawa tace "Yanzu kai kaji ka amince da auren yarinyar nan? wallahi faruk karka so
kaga wulaƙanci da cin kashin da mutanen can sukai mana saboda halin yarinyar nan

Ganin bazasu ɗaukar wa kansu jidali bane yasa ya sauwaƙe mata amma kai se ka kwaso mana
ita?"

Nutsuwa sosai faruk yayi yace "umma ke da akace maki mumtaz na ɗauke-ɗauke ya kika ji
zancen?"
Ya kafe ta da ido yana jiran jin amsar ta.



Shiru tayi can tace "gaskiya daga farko ban yarda ba"

"good" ya faruk yace sannan ya sake cewa "Tsakanin ki da Allah kuma baki ɗarsa komi a cikin
ranki ba, duba da ynayin yarda kuka bamu tarbiya daidai gwargwadon iyawar ku?"



Gyaɗa kai tayi tukun tace "Da wannan dan wannan kuma"

Murmushin gefen baki yayi ganin tun ba'aje ko ina ba matsalar shi ta kusa warwarewa.

Gyara zama sosai yayi sannan yace

"Umma in kika duba gatan da iyayen ta ke mata,

dan ban manta ba har maganar kin taɓa yimin cewa gatan da suke mata yayi yawa, kar su saka
mata girman kai a abubuwa, har kike cewa hakan yana da nasaba da ƙin kula samari da takeyi
saboda tana ganin ta wadatu da komi ta fi ƙarfin su"

Gyaɗa kai tayi tace "anyi haka"

Sannan yace "To umma kina ganin wanda ya wadatu da wannan gatan shine har wani abu na
wasu ze birgeta ta ɗauka?"

Ajiyar zuciya ta sauke a wannan karon, taci gaba da sauraron shi

Jin bata ce komi ba ya ɗora da " Tabbas in hakan da gaske ne to AKWAI LAUJE CIKIN NAƊI
umma"

Shiru umma babba tayi tana nazarin maganar ɗan nata

a karo na farko da taji wani abu me kama da tausayi tausayi na son kamata game da ahalin
mama.

Cikin ido ya faruk ya kalli mama yace "Kiyi nazarin maganata umma, in har baki gano komi ba
to ina me tabbatar miki da a gaban ki zan saki mumtaz!."
Yana gama faɗin haka ya miƙe yace "na barki lafiya umma" ya fice.



Yana fitowa yaga juyawar umma ƙarama da gudu

Karkaɗa kai kawai yayi a ranshi yana faɗin "Baƙar macijya me kan mutum".



ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR



👹
MAKIRCI
KISHI DA ALJANA
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI

WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg71-72

Yaso ya shiga sasan mama amma ya kasa, dan yau sasan nata yafi na kowa cika, a yarda yake
gani ma kamar sake yin wasu baƙin akai

Mota ya koma ya zauna, so yake yaga mama ya shawarce ta kafin ya aiwatar da ƙudirin shi

Wayar shi ya ciro yace "bari nagwada kira ƙila na same ta yanzu"



Mumtaz na kwance taji wayar maman na ringing

Calls ne ke ta shigowa na mutane daban daban

Jin wayar ta sake ringing yasa taja tsaki a gajiye ta kara wayar a kunne ko saurarawa bata yi

Please Login or Register in order to submit comment