Reading LAUJE CIKIN NAƊI by ZAINAB FALALU Chapter 12 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

taɓa ji amare sun tafi ba ƴan rakiya?"

Fuska ba yabo ba fallasa yace "bance kar kuje ba ai, ina nufin motar bazata ɗauke ku ku duka
ba"

Uncle ƙasim ya ƙaraso yace "su shiga mu gani"

Hafsat ta fara shiga, se najwa, sannan bilkisu, se Amal, kujerar
Bayan ta cika, uncle ƙasim ya rufe musu ƙofar



sannan ya buɗe ƙofar gaba yace "zo ki shiga nan mumtaz" tana shiga yace "matsa" sannan
yace "ya safiya shiga" ta shige tukun ya rufe ƙofar.



Tun kafin dama a fito da amaren, ƙawar ko wacce tabi motocin angon ƙawar ta

Haka dangi ma, wasu suce can zasu wasu suce nan zasu

Haka angwayen suka kwashe su tas

Tun farko sun san dama daga gida za'akai musu amaren nasu.
Ya faruk ya daidaita motar akan titi tukun ya kalli goggo safiya yace "gidan wa za'afara zuwa"?

Tana kallon hanya tace "a fara kai babba se ƙaramar ta zama ta ƙarshe"

Mumtaz najin haka ta sake lafewa a jikin goggo safiya tana sauke ajiyar zuciya, tun jiya dama
take roƙonta kar a fara kaita, kuma a al'adance in biki ya haɗe haka, ƙarama ake fara kaiwa
sannan babba.



Hakan kuwa akayi, hafsat naji na gani aka fara kaita,
Sannan bilkisu

Gidan najwa da Amal ba nisa tsakani, se anje gidan najwa kafin na Amal,

Nan ma seda aka kai najwan tukun aka zagaya da Amal, rungume juna suka yi da mumtaz
suna ta kuka, da ƙyar aka raba su tukun aka wuce da mumtaz

Kukan da mumrtaz keyi a yanzu yafi na ɗazu

Gaba ɗaya ya faruk na neman rasa nutsuwar shi

A cikin zuciyar shi yake jin kukan ta

Jiki a mace ya kai hannun shi jikin radion motar ya kunna karatun ALARAMMA AHMAD
SULEIMAN wanda yake karanta suratul mulk

Tun sautin kukan na tashi da ƙarfi har ya koma yayi ƙasa sosai

Shi kanshi karatun ya saka shi nutsuwa ƙwarai

Yarda suke tafiyar har yaso bawa goggo safiya mamaki

Laƙaƙai laƙaƙai haka suke tafia, da na kalla da kyau naga a 40 yake tafiyar

Kasa haƙuri goggo safiya tayi tace "wannan tafiya haka faruk, kamar baka so mu kai"

Se a sannan ya farga da yarda yake tafiyar
Duk haushin kanshi ya kama shi



Sunyi nisa sosai goggo safiya tace
"na mance, gidan sirikanta Za'a fara kaita kafin mu wuce gidan ta".



Cike da ƙosawa ya faruk yace "mijin ya kaita da kanshi, ina da abun yi ni kam"



Da sauri goggo safiya tace "wallahi baka isa ba, al'adar suce, kuma tunda har suka sanar mana
to ba zamuyi ƙaranta ba, dole muje"



Rai ɓace ya faruk yace, "nifa ban san gidan ba"

Itama rai a ɓace tace "bari na kira yayi maka kwatance"



Be sake cewa komi ba, se muryar kalid da yake saurar ta wayar goggon yana musu kwatance.

Har ƙofar gidan suka je, a can suka iske mota biyu ɗauke da mutum uku-uku a ciki, ciki harda
umma babba suna jiran ƙarasowar su.



Suna zuwa suka ɗunguma zuwa ciki inda ahalin mami ke jiran ƙarasowar su



Mami da kanta ta tarbi mumtaz da ƴan rakiyar ta har zuwa ciki



Tana rungume da mumtaz data lafe ajikin mamin, itama ta taro bayan mami da hannun ta na
dama ta riƙe ta

A haka suka taka zuwa ciki, ana ta ɗaukar su hotuna, ga guɗa nata tashi ta ko wace kusurwa

Da dai mumtaz taji ana ƙoƙarin yaye mata rufin fuskarta ta saka duka hannayenta ta riƙe hijabin
ƙam
Har seda mami ta aje ta a babban palon gidan, tukun ta kalli su umma babba tace, "marhabun
ku zauna bari nazo"



Hannun daman ta mumtaz tasa ta taɓo goggo safiya dake gefe,

Ɗiyar ƙanwar mami nata ɗaukan hotunan ta,
Khalid ya saka ta dama, seda ta ɗauka sosai duk da ba wani ganin fuskar ta ake ba tukun ta
fice
Ɗakin da sauran take takoma, sannan ta danna ma number khalid ɗin kira

Yana ɗagawa tace "duba whatsapp yanzu zan antayo maka pic ɗin, dan ma taƙi bari muga
fuskar ta"

Cike da jin daɗi khalid yace "Thank you, yanzu kuwa zan duba"



Babbar yayar mami da ke zaune kan dadduma tace "muga hotunan"

Miƙa mata wayar tayi ta ce "gama gani kafin na zo"

Aunty hajara(yayar mami) ta rinƙa duba pics ɗin da ƴar tata ta ɗauka

Tana ta scrolling taci karo da hoton da mumtaz ta miƙa hannu ta taɓo goggo safiya

Har ta wuce ta dawo da sauri,

kafe hannun mumtaz da ido tayi tana kallon abun hannun ta, daidai nan mami ta shigo da sauri
cike da annushuwa tace "ya hajara muje mana sun iso fa"



Yafito mami da hannu tayi, tace "zo kiga, kodai idona ne kemin bishi-bishi?"

Ɗan ranƙwafowa mami tayi ta amshi wayar ta kalli hoton

Dariya tayi tace "amaryar ce ai, muje ki ganta a zahiri"

Aunty hajara tace "ki kalli hannun ta, kamar abun hannun da inna ta baki ne"

Dummmm, haka mami taji gaban ta ya faɗi yin tozali datayi da shi.

Zooming hannun tayi da kyau, tana kallo ƙirjin ta na dukan uku-uku,

Da sauri ta fice daga ɗakin ta nufi nata,
itama aunty hajarar da sauri ta bita a baya tana ƙwala mata kira,

Tana shiga ta janyo laptop ɗin ta ta hau binciko videon data yi mushi ajiya me kyau

Tare da aunty hajara suka kalli ɗan gutun videon da fuskar mumtaz ce ɓaro ɓaro
Tsayar da videon tayi, a tare suka nufi palon da aka sauke su

Fuska ba yabo ba fallasa aunty hajara tayi musu sannu da zuwa ta tsallake su ta nufi mumtaz
dake ƙudindine a hijabi

Su goggo safiya sun sha duk a cikin al'adar su ne hakan

Ido suka zuba wa aunty hajara data ɗaga hijabin mumtaz fuskarta ta bayyana ma kowa.

BA LALE KU JINI GOBE BA, SHIYASA NAYI PAGES BIYU

ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR



👹
MAKIRCI
KISHI DA ALJANA
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI

WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg59-60

Aunty hajara na buɗe fuskar mumtaz ta waiga ta kalli mami dake tsaye a bakin ƙofar palon
hannayen ta harɗe a ƙirji

Da ido tayi mata alamar itace

Gyaɗa kai mami tayi ta juya ta fice
Gaba ɗaya ranta a mugun ɓace,

Fuska ba yabo ba fallasa aunty hajara tace

"kuyi sallah se ku ci abinci muna zuwa"
Goggo safiya tayi caraf tace "a'a tafiya mu kam zamuyi, anan zamu bar muku ita ko kuwa zamu
dangane ta ga ɗakin ta?"



Ɗan taɓe baki aunty hajara tayi kafin tace "ku jira ku wuce da ita muna zuwa"



Gaba ɗayan su jikin su yayi sanyi ganin yarda fara'ar su ta ɗauke lokaci ƙanƙani ta koma yaƙe



Farat ɗaya umma babba ta fara hasashen akwai matsala tsabar ƙwarewarta asa ido



Suna nan a zaune babu wanda a cikin su yayi yunƙurin yin sallar balle har su taɓa kayan
ciye-ciyen da aka jera musu

Mumtaz kam kanta na a cikin hijabi, gaba ɗaya ta nemi nutsuwarta ta rasa, tsananin faɗuwar
gaban datake ji ya zarce na ko wani lokaci gaba ɗaya ra kasa sukuni.



Aunty hajara da wata ƙanwar su suka iske mami a a ɗaki ta haɗa goshin ta da bango
Idon nan nata ya kaɗa yayi jajir

Kallon su kawai tayi tama kasa cewa komi

Amma kallo ɗaya zakai mata ka gane tana cikin tsananin ɓacin rai

Dafa kafaɗar ta aunty hajara tayi tace "Meye mafita?"



Cikin karayar zuciya tace "ban sani ba aunty hajara, gaba ɗaya tsanar yarinyar ta gama rufe ni,
banji ko ta zauna da khalid zanso ta ba, kuma ba zan taɓa sakin jiki da ita a cikin zuri'ata ba"



Gyaɗa kai aunty hajara tayi, tana ƙara jinjina wannan al"amari a cikin ranta



Can mami ta sake faɗin "Ɗa ɗaya tilo da Allah ya bani nake saka ran samun zuriya me yawa
daga tsatson shi kuma ya jarbce shi da auren ɓarauniya, wasu kalar ƴaƴa zata haifa mishi
kenan ni ƴasu?"
Ta fashe da kuka tana sake hango yarda mumtaz ta ɗauki abin hannun nan
Cike da jimami aunty hajara tace "dole khalid ya san wa ya aura gaskia, kuma tun farko inda
ansan haka halin ta yake bazamu tama yarda ya aure ta ba, kuma in kika kalli yarinyar bazaki
taɓa cewa zata aikata ba"



Zama mami tayi haɗe da dialing no ɗin khalid

Ringing biyu ya ɗaga,
Kafin yayi magana tace "kazo yanzun nan ka same ni"

Har ya buɗe vaki yace "lafia mami?" yaji ta tsinka

Da ɗan mamaki a fuskar shi ya kalli kamal yace

"Muje, mami na kira na"

Suna a mota dama, daga inda suke zuwa gidan ba wani tazara, cikin minti biyar suka ƙarasa
ƙofar gidan

Gab da ze shiga gidan ya faruk yayi mishi fitila

Dawowa khalid yayi, saitin ƙofar ya tsaya,
A hankali ya faruk ya sauke glass

Cike da fara'a khalid ya miƙa mishi hannu suka gaisa, sannan ya faruk yace "In ka shiga kace
musu muna jira fa suyi sauri"



Still da fara'ar shi yace "yanzu kuwa, ai yakamata ace sun gama komi zuwa yanzu, ina zuwa"
ya juya zuwa cikin gidan.



Direct ɗakin mami ya nufa, yana shiga yagan su wani iri

Da fara'ar shi ya shiga, amma ganin yanayin da mamin shi ke a ciki yasa jikin shi yin sanyi

Jiki a mace ya samu waje ya zauna haɗe da faɗin "me ya faru mami?"

Ganin shi da mami tayi yasa idanun ta sake cikowa da ƙwalla dan bata so yaji kalar ɓacin ran
da take ji a yanzu, kuma abu ne da bazata taɓa iya ɓoye mishi ba sam

Cikin ƙagara sa kuma tsoro da yafara kama shi yace "Dan Allah ku faɗa min meke faruwa, na
fara jin tsoro wallahi"
Kasa magana kowa yayi, se can mami tace "Ina zuwa" ta tashi ta fice

Palon da aka aje su mumtaz ta nufa

Ciki-ciki tayi sallama, tukun tace "zaku ɗan bani aron yarinyar ku pls"

Rassa, haka mumtaz taji a ƙirjin ta, bama ita kaɗai ba har su goggo safiya seda suka ji maganar
mami wani banbaraƙwai da ita, ba kara sam a maganar ta

Jin kowa yayi shiru ne yasa umma babba tace "Tashi mana mumtaz" ta yunƙura ra kamota
kamar da gaske

Ganin umma babban zata taso mumtaz yasa mami tace "Da kin zauna hajiya, ita kaɗai muke
son gani"



Baki sake kowa ke bin mami da kallo, gaba ɗaya ta sauya ba kamar da suka shigo ba, yanzu
har wani hare-hare take da kuma maganganu na gadara



Cak mumtaz ta tsaya taƙi yarda ta bi mami, gaba ɗaya tsoro ya gama rufar mata

Ba ganin fuskar ta take ba, amma ji take kamar ta san muryar kuma ta rasa a inda tasan
muryar.

Mami har ta kai ƙofa ta waigo jin mumtaz bata biyo ta ba

Ganin haka yasa ta dawo da baya tace "wanda suka fi kusanci da ita mutum biyu suzo muje



A fili umma babba tace "yau ko mun kawo kanmu gidan iko"

Goggo safiya da itama zuciyar ta na gaf, kawai tana basarwa ne ta miƙe tace "muje to"

Umma babba tayi tsalan tace "ai ba kyaje ke kaɗai ba yaya safiya, muje na rakaku nima"



Suka saka mumtaz a tsakiya suka bi bayan mami da tayi gaba

Har cikin bedroom ɗinta taja su

Khalid na ganin mumtaz a tsakiyar su goggo safia ya miƙe tsaye, da fara'a yace " sannun ku
gaggo, bisimillah ga waje"

Ya tashi daga kujerar da yake umma b da goggo safiya suka zauna

Ganin an bar mumtaz a tsaye yasa ya janyo mata kujerar gaban mudubi

Ganin taƙi zaman, kuma a cikin iyayen nashi ba wanda yayi yunƙurin cewa ta zauna yasa ya
rufe idon shi ya kama hannunta ya zaunar da ita,
Sannan ya tsaya ta ɗan saitin ta, da gangan ya rinƙa taka mata ƙafa yana mata waiwayi.



Jin shuru kowa ya kasa magana yasa goggo safiya faɗin "To mu kin ƙira mu bakuce komi ba ga
lokaci na tafiya dare na daɗa yi"



juyawa mami tayi ta kalli aunty hajara tayi mata signal da ido ta fara magana

Gyaran murya aunty hajara tayi kafin tace " faruk da kai zan fara"

Gyara tsayuwa yayi ya fuskance ta da kyau, dan wannan abun sabo ne a idon shi shikam

Shiru ta ɗanyi sannan tace "ku gafarce ni akan abinda zan faɗi hajiya, amma gaskiya an ha'inci
ɗanmu da ba'a sanar da shi cikekken halin ƴarku ba!"



Duuuuuum, haka ƙirjin mumtaz dana khalid da goggo safiya kai harma dana umma babba ya
bada wannan sautin a kusan tare



Da sauri khalid ya kalli yayar baban nashi yace "Wannan wace irin magana ce aunty"?



Goggo safiya ta ƙanƙance idanun ra tace "Me kike nufi da an ha'inci ɗanku??"



Gyara zama sosai ta sake yi sannan tace "eh hakan dai nake nufi, an ha'inci ɗanmu, kun san
sarai ƴarku na ɗan hali,baku faɗa mana ba, da akazo neman auren ta ai se ku faɗi ba wai ku
ɓoye ba, daga baya se anyi abu ta yi halin a inda ze tonu azo ana kai ruwa rana, ana wallahi
tallahi"



Bama ta kai ƙarshe ba mumtaz ta buɗe fuskar ta tana bin kowa dake palon da kallo har idonta
ya sauka akan mami da se a yanzu ta tuna da inda ta santa
Goggo safiya da umma babba kuwa a kusan tare suka miƙe tsaye,
salati suka hauyi haɗe da kallon aunty hajara da mugun mamaki da al'ajabi

Rai a ɓace goggo safiya tace "wannan wani kalar sharri ne daga kawo yarinya?

Umma babba tayi caraf tace "bayan sharri harda cin fuska ma wannan ai"



Khalid kam jin mugun kalamin bakin auntyn nashi yasa shi ƙamewa a wajen, ido jajir yake
kallon mamin shi da sauran, sam ya kasa cewa komi banda rawar leɓe dayake faman yi



Jiki a mace mami ta kalli mumtaz da gaba ɗaya bata san a wani kalar yanayi take a ciki ba tace

"Ya kike da suna, muga abun hannun ki"

Gaba ɗaya kallo ya koma kan mumtaz datake ta muƙumuƙu da hannuwa a cikin hijabi

Da sauri ɗayar ƙanwar mamin tace "zata cire ne fa"

Tsabar zuciya yasa goggo safiya matsowa gaba mumtaz ta yaye hihabin ta,

Aikuwa se gashi tana ƙoƙarin cire abun hannun



Khalid na tozali dashi yayi baya baya kamar ze faɗi, Allah ya temakeshi bango yayi mishi waigi
da ya sha ƙasa

Finciko abin hannun goggo safiya tayi kafin tace "wannan abun kike nufi ko me?"



Gyaɗa kai mami tayi, hannu ta miƙa da niyar karɓa ta fasa, can tace

"Kaf ƙasar nan ciki da kewayen ta wannan abun hannun ne kawai, ba zaki taɓa samun kalar shi
ba,

kai ko irin shi banjin zaki samu ba

Gaɗon shi naci daga wajen mahaifiya ta, itama daga wajen tata mahaifiyar ta gajeshi,

Bama wannan ba,
har sanda ƴarku ta saci abin nan ina da videon ta,

maganar gaskiya inda na san wannan ce yarinyar da ɗana ze aura bazan taɓa bari ba,

ba wai dan yana da muhimmanci a waje na ba,
se dan ba zan taɓa bari na haɗa jini da jinin sata ba"



Dafe ƙirji umma babba tayi

A yayin da goggo safiya kuma ta saki abin hannun a ƙasa tana wa mami kallon tuhuma da
kuma tsantsar rashin mutunci



Idon mumtaz kam ya gama soyewa, bakin nan ya bushe tsabar rashin isheshshen miyau a
bakinta



Khalid kam gaba ɗaya ya lula tunanin maganar da sakina ta faɗa mishi akan mumtaz kwanakin
baya.



Ido jajiri goggo safiya ke kallon videon da mami ke nuna mata

Umma babba ta gama yarda da sadaƙarwa, tunda har ga Allah bata yarda ba daga farko seda
taga videon tukun



Mumtaz na nan zaune idon ta a ƙasa tana kallon abun hannun da goggo safiya ta wurgar

Jiki a sanyaye ta duƙa ta ɗauki abin hannun ta matsa har gaban mami ta tsugunna

Se a sannan idanun ta suka kawo ruwa, murya na rawa tace "ki gafarce ni mami, kuma ki yafe
min, sannan dan Allah ku bani dama ta biyu karki yanke hukunci cikin ɓacin rai, wallahi sata ba
halina bane, haka nan na tsinci kaina da kwaɗaituwa da abun mutum in na gani"



Wani mari me raɗaɗi goggo safiya ta yarfa mata da ya hanata ƙarasa maganar data faro

Cikin tsananin fushi tace "Da gaske bayan wannan ma kin taɓa ɗaukar abun wasu mumtaz?"

Kafin tace komi khalid shima cikin tsananin ɓacin rai yace
"Munafuka halinta ne wallahi, ni kaina tamin sata amma na kasa yarda cewa itace saboda
yardar dana mata, sannan banyi mamakin satar da kike ba tunda dama duk me bin maza
bazaka taɓa rasa shi da ƴan ɗauke -ɗauke ba"



Ido a waje kowa ke kallon khalid jin abinda yace



Ita kanta mumtaz jin maganar khalid ba ƙaramin ƙaraa saka ta wani mawuyacin halin yayi ba

Amma kalmar bin maza da yace yasata saurin faɗin "Kar kayi min sharri khalid, eh tabbas
nasan ni na ɗauki agogon ka a airport, amma kar ka ƙara da abinda baka da tabbas akai"

Kamar ze maketa ya matso, da sauri mami ta riƙe shi, yace "Tunda baki da kunya ai zaki faɗi
hakan, kuma in kowa yayi maki ƙarya ina jin jinin ki SAKINA bazata munafurce ki ba"!



Mumtaz tace "SAKINA"!

Fashewa da kuka khalid yayi ya rungume mami da itama gata nan dai

Cikin kuka yace "wallahi mami bayan sata har maza take bi, ƴa'uwar ta musamman takirani ta
sanar dani amma ban yarda ba se yanzu, wallahi mami ba zan yarda da rufa-rufar da akayi min
ba se na bi kadi na"



Goggo safiya da umma babba kam basu da bakin magana tunda har mumtaz ta amsa da bakin
ta

Kunya kam ta gama saka su a cikin ta, dan ji suke ina ƙasa take su shige



Jiki a mace umma babba tayi hanyar ƙofa ta fice, goggo safiya bata da wata mafita itama tabi
bayan ta

Suka bar mumtaz a ɗakin a tsugunne riƙe da ƙirji.



Waigowar da khalid zeyi ya ganta durkushe, a mugun fusace yace

"Ki tashi ki bisu kafin su bar gidan nan, dan wallahi bazaki kwana a gidan nan ba"

Da sauri mami tace "kull kalid, bana son ka sake furta komi"
Da ƙyar mumtaz ta lallaɓa ta miƙe itama ta fice



Umma babba cikin ƙarfin hali tace ma sauran mutanen da suka zo tare su taso su tafi

Goggo safiya kan waje tayi tana kuka kashirɓan.



Ya faruk na hangota ya sakko ganin yarda ta fito a firgice ga kuma kuka

Gaban mota ya buɗe mata ta shiga, kafin yace "Halan haka kika barota itama tana ta kukan
ko?"

Bawan Allah besan abinda ke faruwa ba 🥹
ALLAH KASA ANNABI YA CECE MU 🤲
LAUJE CIKIN NAƊI

NA
ZAINAB FALALU(MRS SULAIMAN)

MARUBUCIYAR



👹
MAKIRCI
KISHI DA ALJANA
WANI HANIN GA ALLAH
ƘADDARAR MU
LAUJE CIKIN NAƊI

WATTPAD@ZAINABFALALU8

Pg61-62

Kukan goggo safiya yaso ba ya faruk dariya,

Yarda ta aza hannuwan ta duka biyu a kanta ka rantse da Allah wata gagarumar mutuwa akayi
mata

Ganin bata da niyar magana ga kukan dake ƙara yawa yasa shi ficewa a motar, haɗi da hango
su umma babba da fitowar su kenan.



Ganin jikin umma b a sanyaye itama kamar warce ta yi kuka yace "lafiya dai ko umma"



Murmushin takaici tayi tace "da sauki dai"



Bata gama rufe baki ba suka ga fitowar mumtaz da gudu tayi hanyar titi



Daga cikin mota goggo safiya ta hangota, a guje ta fito itama



A ruɗe goggo safiya ke faɗin

" ku bita kar tayi wani wajen, faruk ku bita, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! ku bita bata cikin
hayyacin ta"



Shima a kiɗime yace "wacece me akayi mata"
Kwata kwata beyi tunanin mumtaz bace tayi wannan fecewar



Umma babba ma a ɗan ruɗe tace "mun shiga uku, muntaz ce fa"



Umma b bata kai ga rufe baki ba ya faruk ya kwasa da gudu yabi bayan ta.

Kamal abokin khalid dake jiran shi a mota, jin ana a bita mumtaz ce, yayi saurin fitowa ya mara
ma ya faruk baya a guje shima.



Sauran matan da suka zo tare ɗaya daga cikin su ta kalli ɗaya tace "anya lafia kuwa, akwai dai
wani abun a ƙasa nake ji, wannan baza'a ce kukan rabuwa da gida bane gaskiya.



Da ƙyar ya faruk ya dafe mumtaz da saura ƙiris mota tabi ta kanta

Da wani irin speed ya damƙo ta gam ya fincikota baya

Allah yasa me motar ya ankare da yarda ta shiga titin ya taka birki da sauri
Ganin fizge-fizgen da take ne yasa ya haɗeta da jikin shi,
Shi kanshi jikin shi rawa yake dan ya sadaƙar da me motar nan ya take ta



Da ɗan fushi-fushi ya fara mata faɗa yace "Da hankalin ki da komi zaki je ki kashe kanki, inace
ke kika kawo mijin kika ce kina so ba dole akayi maki ba? to shine dan ankawo ki kuma bazaki
zauna ba se kiyi ta wa mutane hauka?"



Ƙanƙame shi tayi ta fashe da wani irin kuka me taɓa zuciya

Shuru ya faruk yayi, shi be tafi ba shi kuma be sake ta ba

Yarda ta ɓoye kanta a jikin shi yake jin yarda hawayen ta ke taɓa jikin shi yasa jikin shi sake yin
sanyi ga matsanaiciyar faɗuwar gaban dake damun shi



Tunda kamal ya hango ya faruk rungume da ita ya tsaya,
Wayar shi ya ciro ya danna wa kalid kira

Wayar tayi ta ringing be ɗaga ba,
Shima jikin shi yayi la'asar be ma yarda ya ƙarasa wajen ba ya juya.



Hangowa da ya faruk yayi
Ganin kowa jiran su yake yasa ya cireta daga jikin shi ya kama hannun ta ya fara janta

Tirjewa ta hau yi, taƙi yarda ta sake koda taku ɗaya ne

Da mmaki ya faruk ke kallon ta, beyi niyar cewa komi ba jin yarda kanshi ke mugun sara mishi,
duk saboda firgicin daya shiga

Amma ganin tirjiyar da take yasa ya tsaya yace "Talk to me menene mumtaz?"

Cikin kuka tace" na shiga uku ya faruk, wallahi ba da son raina nake sata ba, nima bana so,
kuma wallahi bana bin maza"



Kalmar farko ta sata data ce ba ƙaramin dukan zuciyar shi tayi ba

Ya tsorata ainun, duk da besan me ya faru ba
Dan ya kawar da kokwanton shi yace
"Nasan ba da son ranki bane ai, nutsu kiyi min bayani yarda zan fahimce ki"

Kasa cewa komi tayi taci gaba da kuka kamar ranta ze fita

Jin taci gaba da kukan kuma taƙi cewa komi yasa ya jata zuwa inda su goggo safiya da kuma
sauran mutanen suke

Amma deep down him yasan akwai matsala, ko daga ganin yanayin fitowar umman shi da
kuma goggo safiya da kukan ta yayi kala dana mumtaz.



Yana ƙarasawa inda ya aje motar shi yace "nan gidan za'a barta ko kuma gidanta zamu?"



Murya a dishe goggo safiya tace "ba wannan maganar ai, muje gida kawai kafin mu tara wa
kanmu jama'a"

Baki sake yace "kamar ya goggo, ban gane ba, kina nufin mu koma da ita gida wai?"

Muryar ta bata fita sosai tace "eh muje" kafin ma ta gama rufe baki mumtaz tayi wuf ta shige
mota

Ƙin shiga mota ya faruk yayi, kusa da umma da ke ƙokarin bude front seat ta zauna ya matsa,
da dan tsoro a fuskar shi yace "umma wai menene ke faruwa dan Allah"

Taɓe baki umma b tayi sannan tace "ai yau kunya da ƙasƙanci babu kalar wanda bamu gani ba,
ni wallahi ko maƙiyi na ba zanso ace an mishi kalar tozartar da ƴarnan tasa akayi mana ba"



Tsabar faɗuwar gaban da yake ji sam ta hana shi magana,

Kamar wanda beda lakka ya zagaya ya shiga motar

A cikin zuciyar shi yake jin sautin kukan ta, be waiga ba, murya na rawa yace "Seda kika bari
asirin ki ya tonu ko mumtaz"?



Daga umma b har goggo safiya sakin baki sukayi suna raba kallon su a tsakanin su.



Ba wanda ya sake cewa komi ya tayar sa mota yaja suka yi gaba
Baki a sake kamal yabi motar da kallo, ganin sun tafi da mumtaz,

Daga baya ya tuna ƙila gidan ta zasu kai ta kafin su wuce.




***UNCLE ABBAS

Tun baccin daya kwashe shi bayan ɗaurin auren sakina, se da akayi sallar magariba ya farka

Ganin shi kwance a gida yasa ya sauke ajiyar zuciya haɗe da hamdala, shi duk a tunanin shi
mafarki yake

Be kai ƙarshen tunanin da yake ba yaji muryar maman sakina bisa kanshi tace

"Tunda har ka farka se kazo muji da sakina, gata can jikin ta ya ɗume da zazzaɓi"



Da ƙyar ya miƙe zaune, dafe kanshi yayi kafin yace "Zazzaɓi kuma? ko daga gidan bikin ne ta
kwaso shi?"



Galla mishi harara haj Asiya tayi, ta cika kamar ta fashe dan takaici, tace "Hmm ka gama
kewaya-kewayar ka, kana nuna kamar babu abinda ya faru alhalin kasan silar zazzaɓin nata"



A ƙasan ranshi yace "da gaske ne kenan ba mafarki nake ba"



Hular shi ya ɗauka, se waya sannan makullin mota ya miƙe

Kai tsaye hanyar fita yayi, yana tafe yace "Ku jira ni, zanje na samu Abbas yanzun nan"



Ƙwata hajiya Asiya tayi ta koma ta zauna ta zabga uban tagumi

Fitowar inna hassu kenan daga sallar magrib, itama ta samu gefe ta zauna sannan tace "Fita
yayi?"

Haj Asiya tace "yaje warware abinda suka haɗa ne, ai kowa yaga abunnan yasan akwai wata a
ƙasa, anyi auren so da ƙauna ma ya aka ƙare ballantana auren haɗi"
Tana gama faɗin haka ta tashi tayi shigewar ta ɗaki.




****MAMA

Tunda aka saka ƙafa aka tafi da mumtaz t shige ɗaki ta kulle kanta, haka nan take son tayi kuka
ƙila Allah ya temake ta abinda ya tokare mata maƙogwaro ya wuce.



Mama bata fito ɗakin ba seda tayi sallar isha sannan ta sakko



akwai ƴan'uwan ta sosai a palon, ana ta fira da yaba ɗakuna

Nan mama take ji har suka baro gidan mumtaz ba'akaita ba

Ɗaya daga

Please Login or Register in order to submit comment