Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
9 / 12
kama da walkiya sai kawai aka ga SADAUKI DURZASU ya finciko takobinsa ya sokata a tsakiyar Kan shugaban birirrikan, nan take Takobin ta lume cikin Kan tamkar an soka allura a cikin katifa. Nan take DURZASU ya zare takobinsa daga cikin Kan shugaban birirrikan, sai ga jini da kwanya na Malala da fantsama a sama tamkar teku ce ta balle. Kawai sai dai akaga Gawar shugaban birirrikan nan ta fadi can gefe guda jini na zuba ko shurawa Bai Kara Yi ba. Cikin tsananin razana sauran birirrikan suka ruga izuwa cikin Dajin da nufin guduwa. Ai kuwa sai SADAUKI DURZASU ya falfala da matsanancin gudu ya rinka kurewa birirrikan Nan gudu yana tsalle ya tsinko kansu suna faduwa Kasa matattu. Kafin cikar dakika Dari da saba'in duk ya Karar da su, babu dayansu da ya tsira da rayuwarsa. Yana gama kashe birirrikan sai ya fadi Kasa sumamme saboda jinin da yayi ta zuba daga cikin raunikan da yayi. Sai da shafe dakika Dari uku a kwance Bai farfado ba, sannan ruwan sama ya gangamo kamar da bakin kwarya Wanda ya zama sanadiyyar farfadowar shi. Nan take SADAUKI DURZASU ya doddagara takobinsa ya shiga cikin Dajin ya karyo magungunan da zai sanyawa raunikansa domin tsayar da jinin Dake zuba. Bayan ya samo su ya samu Dutse ya dandankasu sannan ya rinka shafawa a jikinsa, har sai da yayiwa Kansa magani tsaf. Daga bisani Kuma ya rinka samo 'yayan itatuwa Yana ci har tsawon kwanaki goma, a wannan lokaci karfin jikinsa ya dawo Kuma raunikan jikinsa duk sun warke. A Rana ta goma Sha uku ne, ya tashi ya fita daga wannan Dajin da ya fafata da birirrikan Nan. Bayan kwana biyar ya iso daji na biyu. Da shigarsa wannan daji sai ya fara cin karo da wasu zarkala-zarkalan dabbobi masu zureren wuya, sannan suna da rafkeken Kai Wanda duk abinda suka maka mawa sai abun ya rugurguje tamkar an Nika hatsi. Su dai wadannan dabbobin adadinsu yakai dubu arba'in. Sannan Kuma duk halittar da tsautsayi ya kawo ta wannan Dajin, Nan take suke yi Mata Taron dangi sannan su kashe shi su fasa tumbin mutum su cinye kayan cikin gaba Daya, sai su bar Gangar jikin Nan ya rube a Kasa. Wannan dalilin ne yasa Dajin ya yawaita da kwarangwal din Kasusuwan bil'adama a ko'ina. Koda Sadauki DURZASU yayi arba da wadannan dabbobin sai ya tsaya yana Mai nazarin yadda zai yake su. Kafin yayi wani yunkuri tuni wadannan dabbobin sun rugo gareshi gaba dayan su da nufin gamawa dashi. Koda ganin rundunar wadannan dabbobin ta tunkaro shi, sai ya daka tsalle ya makalkale wata Katuwar bishiya Sannan ya ruga izuwa Saman bishiyar da gudu har yaje karshen bishiyar. Koda wadannan dabbobin suka zo gindin wannan bishiyar da DURZASU ya hau, sai Daya daga cikin dabbobin ta jin-jina kanta iyakar karfinta ta makawa wannan bishiyar, nan take Kasan bishiyar ya ratattake tamkar an zubawa katako acid, sai gashi gaba dayan bishiyar ya surmuyo Kasa. Karar karyewar bishiyar ya cika Dajin gaba Daya, Nan take dabbobin sukayi Shirin Afkawa SADAUKI DURZASU da zaran ya fado.... Mu hadu a GASAR JARUMTAKA na bakwai part B don Jin cigaban wannan Kasaitacce Kuma Kayataccen labari Mai dadi da debe kewa✍️✍️✍️👆👆🙏🙏❤️❤️🥰🥰**GASAR JARUMTAKA** LITTAFI NA BAKWAI 7 ✍️ PART B ✍️💯 AUTHOR: NAJIBULLAH MUHAMMAD ✍️✍️ POSTING: NAJIBULLAH MUHAMMAD ✍️🥷🥷🥷 Koda wadannan dabbobin suka zo gindin bishiyar da DURZASU ya hau, sai daya daga cikinsu ta jin-jina kanta iyakar karfinta ta makawa wannan bishiyar, nan take bishiyar ta ratattake tamkar an zubawa katako acid, sai gashi gaba dayan bishiyar ta karyo ta sumuryo Kasa. Karar karyewar bishiyar ta cika dajin gaba daya. Nan take sama da dabbobi dubu uku suka yiwa bishiyar nan Kawanya suna jiran fadowar DURZASU daga Saman bishiyar su tumurmusheshi. Ba shiri SADAUKI DURZASU ya taho luu daga Saman bishiyar zai fado Kasa, tazarar Saman bishiyar da Kasa Nisan kamu dari da tamanin ne. Saboda haka sai da ya shafe dakika hamsin yana tahowa amma bai iso Kasa ba. Nan fa yaga yadda wadannan dabbobin kowace tayi mummunan Shirin gamawa dashi da zarar ya fado. Koda ya rage bai wuce taku biyar ba ya fado Kasa, sai sama da dabbobi dari biyar suka daka tsalle sama suka kawo masa mugun duka da wannan rafkeken kan nasu. Cikin tsananin zafin nama DURZASU yasa kafarsa guda ya taka kan daya daga cikin dabbobin, kawai sai yaji ta cillashi sama, sai da yayi nisan da ya kere gaba dayan bishiyoyin sannan ya fado a saman wata bishiyar. Su kuwa wadannan dabbobin Koda sukayi sama da nufin mako DURZASU, sai ya goce. Nan take sama da dabbobin dari biyar suka makawa junansu kawunansu, sai gashi gaba dayan kawunan nasu sun fashe sun tarwatse jini ya rinka Malala da fantsama a sama, kafin cikar dakika hamsin sun gama shure-shuren su sun zama gawa. Koda sauran dabbobin suka ga haka, sai suka Kara rugawa bishiyar da DURZASU ya maƙale, suka kara mako shi ya taho, sai ya kara taka kan daya daga cikinsu, nan take suka Kara gwara kawunansu. Nan ma sama da guda dubu ne suka mutu. Nan fa DURZASU ya rinka tsalle-tsalle daga wannan bishiya zuwa waccan, Kuma da zarar sun mako shi da kawunansu don ya fado su tumurmusheshi, sai ya taka kan daya daga cikinsu ya canza wata bishiyar, su kuwa su gwara kawunansu su fashe. A bisa wannan dalili ne yasa dabbobin suka rinka yin mummunar mutuwa saboda irin mugun kisan da sukewa junansu. A cikin abinda bai wuce sa'a guda ba, sai da sama da dabbobi dubu tara suka mutu. Bugu da Kari a wannan lokacin sun kusan Karar da gaba dayan bishiyoyin Dajin, saboda tsabar dukan Kasan bishiyar da kawunansu da sukeyi. Duk Inda mutum ya duba a cikin dajin sai dai kaga gawarwakin dabbobin nan kwance a Kas fululu tamkar an shimfida su. A wannan lokaci Sadauki DURZASU ya gaji ainun da tsalle-tsalle Saman bishiya, Kuma daman saura bishiya uku kacal a cikin dajin wadda dabbobin nan basu ratattake ta ba. Koda ya gama hawa sauran bishiyoyin Suma wadannan dabbobin suka ratattake su, sai ya fado bisa turba ya rinka falfalawa da matsanancin gudu tamkar na tauraruwa Mai wutsiya don gujewa dabbobin nan. Nan fa aka Kasa mahaukacin tsere a tsakaninsa da wadannan dabbobin. DURZASU gudu yake iyakar karfinsa Amma da zarar ya waigo sai yaga a kowane lokaci dabbobin nan zasu iya makoshi da wannan rafkeken kan nasu. A halin yanxu yawan dabbobin bai wuce dubu uku ba. Sai da SADAUKI DURZASU da wadannan dabbobin suka zagaye gaba dayan dajin suna tsere amma basu samu nasarar buge shi ba. Koda DURZASU ya duba sai ya ga Ashe gaba dayan wadannan dabbobin sun rugurguje duk Duwatsun Dajin da kawunansu. A lokacin da suke gudun Koda sun iske dutse a gabansu sai dai kaga sun wurwura kansu sun maka Masa shi, Nan take yake ratattakewa ya zama toka. Wannan yasa gaba dayan Dajin ya koma Fili fetal Wanda babu sauran bishiya daya a tsaye ko Dutse. Hatta bishiyoyin da suke kwance a Kasa, gaba dayansu sun zama tamkar garin magani saboda tsabar gudun da dabbobin sukeyi a kansu. A wannan lokacin tuni DURZASU ya gaji ainun domin har sassarfa yake kamar Wanda yasha giya. Nan take ranshi ya baci ainun, ya tuna cewa shi ne fa gagarumin SADAUKIN da yake tunkarar mazaje sama da guda dubu Kuma yayi nasara a kansu. Nan take ya tuna da duk irin tsananin Jarumtakarsa da Kuma irin yake-yaken da yasha yi a rayuwarsa. Yana gama wannan tunani ne, sai ya tsaya cak, sannan ya juyo ya fuskanci wadannan dabbobin. Tsayuwarsa keda wuya wai wata shegiyar dabba Mai mugun naci tayo tsalle sama ta kawo masa mummunan duka aka, cikin zafin nama ya durkushe Kasa ya goce harin nata, sannan yasa takobinsa guda ya soka mata ita a ciki, take Takobin ta lume sai gashi ya tsarge dabbar gida biyu. Nan take wasu dabbobin suka sake rugowa suka sake kawo masa mummunan hari da kawunansu, cikin tsananin zafin tamkar walkiya sai ya Suri Gawar wannan dabbar da ya tsarge gida biyu ya maka masu kanta a duka kawunansu. Faruwar hakan keda wuya sai akaga gaba dayan kawunan dabbobin sun rugurguje kwatsa-kwatsa tamkar an kwankwantsa garin magani da Dutse. Haka DURZASU ya kasance yana amfani da wasu daga cikin gawarwakin dabbobin yana tare harin su Kuma yana mayar da martani. Kafin cikar dakika dari biyu da arba'in ya kashe sama da guda dubu biyu da Dari bakwai da saba'in. Nan fa 'yan tsirarun dabbobin da suka rage, suka zage dantse sosai wajen hallaka DURZASU ta kowane hali amma abu ya gagara. Saboda tsananin zafin naman kawo harin dabbobin ne yasa har takubbansa suka subuce daga hannunsa. Faruwar hakan keda wuya sai daya daga cikinsu ta daka tsalle sama sannan ta banke DURZASU a kirjinsa. Saboda karfin dukan har da yayi sama tamkar an cilla shi, sannan ya fado a cikin wani rami yana aman jini, kafin cikar dakika goma ya Suma. Ramin yana da matukar zurfi da fadi, saboda haka a lokacin da DURZASU ya fada cikin ramin ya fara gangarawa cikin ramin sai wata Katuwar saiwar bishiya ta sargafo shi, ya maƙale a jikinta ya Kasa fadawa can Kasan ramin. Ala'marin ragowar dabbobin kuwa, Koda suka ga abun harinsu ya fada wannan ramin sai gaba dayansu suka rugo cikin ramin domin karasa shi. Zuwansu keda wuya sai suka rinka Afkawa cikin wannan wawakeken rami, har sai da gaba dayansu suka fada ramin. Zurfin wannan ramin ya Kai kamu dubu uku, saboda haka tun kafin dabbobin su kai karshen Kasan ramin suka sume saboda tsabar iska da Kuma gwaruwa da bangwayen ramin da sukeyi. Kafin cikar dakika dari da arba'in gaba dayan jikinsu yayi kaca-kaca da jini saboda tsabar gwaruwa da duwatsu da itace masu tsini. Sai da suka shafe dakika dari biyu suna lilawa cikin ramin sannan suka fado Kasa, ai kuwa Nan take gaba dayansu suka dagargaje suka zama gawa. Ala'marin SADAUKI DURZASU kuwa sai da ya shafe dakika hamsin a maƙale jikin saiwar nan, sannan ya farfado. Koda ya farfado sai yaji kirjinsa jingim tamkar Kasusuwansa sun kakkarye. Nan fa ya takarkare ya rike wata zungureriyar saiwar bishiya da ta har Kasa, ya rinka kamawa Yana hawa Sannu a hankali har yaje karshen ramin. Yana Isa Saman ramin sai ya baje a Kasa yana ta numfashi sama-sama kamar ransa zai fita. Cikin matukar karfin hali, ya rinka tafiya da rarrafe yana tsinko ganyayen bishiyoyi Yana mutsittsike su Yana Sha Kuma ya shafa a kirjinsa. Sannu a hankali har ya fara samun kwarin jikinsa, ya iya mikewa da Kafarsa Yana tafiya dakyar. Amma har a sannan bai dena Jin Zogi da radadin wannan ciwo ba. A bisa wannan dalili ne yasa ya Kafa tantinsa anan ya rinka jinyar Kansa har tsawon kwanaki bakwai. Tsawon wadannan kwanakin yana ta bawa kanshi horon yaki da tseren gudu, har sai da yaji karfin damtsensa da Jarumtakarsa sun ninka na da sau goma. Bugu da Kari Kuma yanzu zai iya yin gudun wuni biyu batare da ya gaji ba. Koda yaji lafiyarsa ta dawo sosai, sai ya dauko takubbansa sannan yaci gaba da tafiya. Sai da yayi tafiyar kwana uku sannan ya iso daji na uku. Da shigarsa wannan Dajin sai ya cika da tsananin mamaki Kuma hankalinsa yayi mummunan tashi sakamakon abinda yayi arba da shi. Ba wani bane SADAUKI DURZASU ya gani a wannan daji ba, face wadansu jibga-jibgan SAMUDAWAN MARIDAI wadanda adadinsu yakai dubu arba'in. Ashe daman tun kafin isowar DURZASU da kusan tafiyar sa'a biyu sukaji kamshinsa ya addabesu. Wannan yasa sukayi gagarumin shiri domin jiran zuwansa su cinyeshi. Sudai wadannan MARIDAI sun kasance manya-manya masu matukar tsawo da kauri, domin kowannensu ya ninka SADAUKI DURZASU girma sai biyu. Kuma dukkaninsu suna sanye ne da benta Wanda aka dinka da fatar damisa. Rike a hannayensu wadansu zabga-zabgan sanduna ne masu matukar girma tamkar manyan rassun bishiya. Gaba dayan jikinsu a murde yake tamkar dunkulallen Dutse ne aka cusa a jikkunansu.. Bayan anyi kallon kallo tsakaninsa da wadannan MARIDAI sai ya zare takobinsa sannan ya falfala da matsanancin gudu ya tunkari wadannan MARIDAI, Koda ya rage saura taku goma su hadu sai ya daka tsalle sama tamkar an cillashi. Ba zato ba tsammani sai daya daga cikin MARIDAN ya cafko wuyan DURZASU da hannu guda, sai gashi yana wutsil-wutsil da kafafu. Nan fa idanunsa suka zazzaro sukayi kwala-kwala saboda tsananin wahala. Koda yaji numfashinsa na niyyar daukewa sai daga takobinsa sama, sannan ya Kaftawa hannun MARIDIN Nan Sara, kawai sai gani akayi hannun MARIDIN nan ya tsinke ya fado Kasa tare da SADAUKI DURZASU. Nan fa jini ya rinka fantsama a sama Yana Malala a Kasa daga jikin Dungulmin hannun wannan MARIDIN. Koda sauran MARIDAN suka ga abinda ya faru gaba dayan su suka kwarara uban ihu Mai tsananin razanarwa sannan suka rugo suka afkawa SADAUKI DURZASU gaba dayansu. Nan fa aka kacame da masifaffen azababben yaki mai matukar tashin hankali, gumurzu, ban tsoro Wanda a kowane lokaci lahira na iya yin Bako..... SU WAYE ZASU SAMU NASARA A WANNAN YAKI? SHIN YARIMA DURZASU YANA SAMUN NASARAR ISA KOGON DUTSEN DA ALJANI GAMJAHUL FUTUL YAKE? INA LABARIN YARIMA ZULDARI, ME YAKE SHIRYAWA? WANENE ZAI MALLAKI KARAGAR MULKIN SARKI GURBASU A TSAKANIN SU YARIMA DURZASU DA ZULDARI. Mu hadu a GASAR JARUMTAKA na takwas don Jin cigaban wannan Kasaitacce Kuma Kayataccen labari ✍️♥️🥰🥰**GASAR JARUMTAKA** LITTAFI NA TAKWAS 8 PART A ✅♥️ AUTHOR: NAJIBULLAH MUHAMMAD ✍️✍️ POSTING: Najibullah Muhammad 🥷🥷 Whatsapp Num..08112778656. Lokacin da aka kacame da masifaffen yaki mai tsananin ban tsoro a tsakanin SADAUKI DURZASU da Kuma wadannan MARIDAN, sai ya zamana cewa maridan suna iyakar kokarinsu wajen cafko DURZASU shi kuwa Yana zillewa, sannan ya Amfani da takobinsa guda Yana saran maridan a dayan hannun nasa kuwa ya rinka Amfani da Dungulmin hannun maridin nan Yana dukan Kafafunsu. Duk Wanda DURZASU ya makawa wannan MARIDIN sai dai kaga kafarsa ta karye Kararas... Tamkar an kaya busasshen icce. Nan fa maridan suka Kara kaimi ainun wajen kokarin cafko DURZASU Amma Abu ya gagara. Koda wannan Ala'mari sai ran Shugaban maridan ya baci matuka, kawai sai akaga ya banke sama da MARIDAI dubu da suka yanyame DURZASU, da zuwansa bayyi wata-wata ba sai yasa kafarsa guda ya harbar da DURZASU. Saboda karfin Harbin sai da yayi sama tamkar an zuro Kugiya daga sama an janye shi. Sai da yayi doguwar tafiya a sama har sai da Kansa ya fara tabo giza-gizai sannan ya juyo Kasa. Nan fa sama da MARIDAI dubu sukayi cincirindo a inda zai fado gaba dayan su suka wangame tafkeken bakinsu da nufin ya fado cikin bakunansu su cinyeshi. Sai da DURZASU ya yayi tafiyar dakika dari biyar a sama Yana shillowa Kasa, sannan ya iso dai-dai saitin bishiyoyin Dajin. Fadowar sa keda wuya sai akayi akasin hannunsa na hagu ya maku a jikin wani Katon reshen bishiya, Nan take hannunsa ya karye Kararas... Ba shiri ya kwarara uban ihu, sannan ya rikito Kasa daga jikin reshen da ya maƙale.. A wannan lokacin tuni DURZASU ya fita daga hayyacinshi saboda tsananin wahalar da ya Sha, fadowarsa keda wuya sai shugaban maridan nan ya bude wangamemen bakinsa DURZASU ya fada cikin bakin ya hadiyeshi.. Nan fa gaba dayan maridan nan suka rinka yiwa Shugabansu jin-jina akan wannan nasara da ya samu. Sai da SADAUKI DURZASU ya shafe dakika dari da tamanin a cikin bakin wannan MARIDIN sannan ya farfado daga dogon suman da yayi, farfadowar sa keda wuya sai ya jawo takobinsa ya rinka sarar hanjin cikin maridin nan. Faruwar hakan keda wuya sai akaga wannan jibgegen maridin ya kame Kam.. Kafin wani daga cikinsu yayi wani yunkuri tuni DURZASU yasa takobinsa ya Burma tumbin wannan MARIDIN sai gashi ya keto cikinsa ya fito jikinsa kaca-kaca da jini. A wannan lokaci tuni hannun DURZASU ya fara kumbura saboda karayar hannunsa, Nan take ya yago wani kyalle Dake jikinsa ya daure hannun tamau. Sannan ya jin-jina hannunsa Mai lafiyar ya Suri takubinsa ya afka cikin maridan nan, ya wanzu Yana masu Kai masu mugun Sara da suka cikin tsananin zafin nama juriya da bajinta. Nan fa DURZASU ya wanzu a tsakiyarsu Yana saransu tamkar ana sassabe a gona. Duk Wanda ya laftawa rasa da takobinsa sai dai aga ya cisge Masa Hannu ko Kafa jinin na Malala daga jikin Dungulmin jikkunansu. A zahiri gashi dai Yana ta kashe maridan Amma kamar karo wasu akeyi saboda tsananin yawansu. Amma duk da haka sai Kara kaimi sosai wajen lahanta maridan nan, bugu da Kari da hannu daya yake yakarsu Amma Kuma duk Wanda yake ganin wannan Yakin sai yayi zaton mutum dubu ne suke yakar wadannan MARIDAN saboda tsananin zafin nama da tsalle-tsallen da yake a Saman maridan nan. Kafin cikar sa'a guda da rabi ya kashe gaba dayan maridan nan, ya zamana cewa babu sauran dayansu da yayi Rai. Duk Inda mutum ya duba sai dai yaga gawarwakin maridan nan fululu kwance a Kas.. Haka Kuma jinin maridan nan ya gauraye tur6ayar Kasar Dajin daga ainihin launinta izuwa jaaa. Koda DURZASU ya kammala kashe gaba dayan maridan nan sai fadi a Kasa sumamme saboda matukar galabaitar da yayi. Sai da ya kwashe dakika dari biyu Sannan ya farfado daga dogon suman da yayi, farkawarsa keda wuya sai ya kwance daurin da yayiwa hannunsa. Nan take ya shiga gyara karayar da yayi, sai da ya Kara shafe dakika dari da tamanin Yana kwarara uban ihu a kokarin gyara karayar hannunsa sannan ta gyaru, ai kuwa yana gamawa ya Kara faduwa Kasa sumamme. Bayan lokaci ya farfado, sannan ya rinka Jan kafafu Yana zagaya Dajin Yana samo wasu ganyayen magani tare da kwakulo sauyoyin wasu bishiyoyin Yana dandakawa, ya rinka jikawa a cikin ruwan battarsa Yana Sha tare da shafawa karayar hannunsa, sannan ya dena Jin Zogin da takeyi. A wannan daji DURZASU ya yada zango tare Kafa tantinsa ya rinka shiga cikin Dajin Yana samo 'yayan itatuwa da ruwansha Yana ci Kuma Yana jinyar Kansa, har tsawon kwanaki Ashirin da biyar.. A wannan lokaci ne karayar hannunsa ta warke sumul yaji tamkar Bai taba karyewa a ba. Koda yaji jikinsa yayi kwari sosai, sai ya tashi daga wannan Dajin ya tunkari daji na hudu. Nan fa ya rinka tafiya ba ji ba gani ya wanzu Yana Mai keta dazuzzuka da koramai masu matukar hadari, har ya iso daji na hudu. Tun sa'adda ya shigo wannan Dajin yasha jinin jikinsa, domin gaba dayan siffofin bishiyoyi da Duwatsun Dajin siffar ababen tsoro garesu. Duk bishiyar da ya Kalla sai ya ga tana kama da wata mummunar Dabba. Gaba dayan bishiyoyi da Duwatsun Dajin siffar dabbobin daji gare su, Kuma gani kamar a kowane lokaci zasu iya rikidewa su afka Masa. Sai da DURZASU ya shafe dakika arba'in Yana yawo cikin wannan Dajin lungu da sake batare da ya ji motsin komai ba. Yana zuwa dai-dai wani wuri a cikin dajin masu zungura-zunguran bishiyoyi kawai sai yaji dudufniyar takun sawaye ba adadi ya tunkaro inda yake. Kwatsam ba zato ba tsammani sai ya ga wadansu jibga-jibgan KARNUKAN DAWA HADE DA DAMISOSHI masu matukar yawa tamkar ruwansu akayo sun rugo gareshi. Kafin yayi wani yunkuri tuni sunyi Masa Kawanya suna dallo harshe hade da wani gurnani na musamman Wanda ka iya sa mutum ya tsure da gudawa saboda tsananin razana. Kafin ya Ankara tuni wadannan dabbobin sun afka Masa da dukkan karfinsu da nufin kowa ta yagi rabonta. Cikin tsananin zafin nama ya rinka Amfani da karfin damtsensa Yana bankesu suna zubewa Kasa tamkar ana zubar da karmami. Nan fa wuri ya yamutse aka rinka dauki ba dadi, babu abinda mutum ke ji dudufniyar kafafun dabbobin tare da gurnaninsu. Kafin cikar dakika tamanin, ya kashe sama da dabbobi dubu uku. Ana cikin hakane wata Mai naci daga cikin DAMISOSHIN Nan ta samu nasarar bankeshi da kirjinta. Nan take DURZASU yayi baya luu yaje ya gwaru da wata Katuwar bishiya Sannan ya fado Kasa a matukar galaibace, faruwar hakan keda wuya sai gaba dayan dabbobin suka daga tsalle sama da nufin daka Masa Wawa..... Ana cikin hakane nikuma na gaji ainun. Mu hadu a GASAR JARUMTAKA na takwas part B don Jin cigaban wannan Kasaitacce Kuma Kayataccen labari ✍️♥️🥰 Najibullah Muhammad legends ✍️✍️🥷🥷🥷**GASAR JARUMTAKA** LITTAFI NA TAKWAS 8 ✍️✅ PART B ✍️💯♥️ AUTHOR: NAJIBULLAH MUHAMMAD ✍️✍️ POSTING: NAJIBULLAH MUHAMMAD 🥷🥷 Whatsapp Num.. 08112778656. Idan baku manta ba, a baya mun tsaya ne inda SADAUKI DURZASU yake fafata kazamin yaki da wadannan KARNUKAN DAWA HADE DA DAMISOSHI. Ana cikin hakane wata Mai naci daga cikin damisoshin nan ta samu nasarar bankeshi da kirjinta. Nan take DURZASU yayi baya luu tamkar an janye shi da Kugiya yaje ya gwaru da wata Katuwar bishiya Sannan ya fado Kasa a matukar galaibace, faruwar hakan keda wuya sai gaba dayan dabbobin suka daka tsalle sama da nufin su daka Masa Wawa.. Anan muka tsaya wancan Karon Kuma a halin yanxu zamuci gaba... Cikin tsananin zafin nama da nuna Jarumtaka ta gaban kwatance, DURZASU ya soka hannunsa a karkashin Kasa sai gashi hannunsa ya lume a ciki tamkar a Kan katifa ya soka shi, kawai sai akaga ya finciko wata zabgegiyar jijiyar bishiya Mai tsananin girma da kauri, saboda karfin fincikowar da yayi mata har sai da bishiyar ta fadi Kasa duk da kasancewarta Mai tsananin kwari. Nan take yayi Amfani da wannan murtukekiyar jijiyar ya rinka mako dabbobin nan daga sama tun gabanin su fado Kasa. Nan fa ya rinka kado su suna fadowa Kasa wasu matattu wasu sumammu tamkar ana girgiza bishiyar da 'yayanta suka rube. Tsananin zafin naman da yake Amfani da shi, da Kuma karfin bugun da yake kaiwa ya wuce misali. A duk lokacin da ya Kai duka da wannan jijiyar yana iya mako dabbobi dari da arba'in da ita. Kafin cikar dakika dari da tamanin ya kashe kaso biyu daga cikin ukun dabbobin, a wannan lokacin gaba dayan jijiyar bishiyar tayi fata-fata ta kakkare saboda tsabar Kai hari da dukan dabbobin da yake da ita. A dalilin haka ne yasa dabbobin suka rinka samun nasarar kawo masa cizo da yakushi da Kuma bangaza, saboda Koda ya wurga jijiyar izuwa garesu Bata kaiwa can. Sannu a hankali har dabbobin nan suka fara samun nasarar yakushin jikinsa, jini ya fara zuba. Kafin cikar dakika hamsin jiri ya fara dibarsa Yana layi. A wannan lokaci DURZASU ya gaji ainun bugu da Kari ga jini na zuba a jikinsa Wanda ya haifar Masa da gani dishi-dishi. Ana cikin hakane wani jibgegen Karen dawa Mai wawakeken Baki ya shammaci sauran ya dako mugun tsalle sama da nufin ya cizge kan SADAUKI DURZASU ya cinye, cikin tsananin zafin nama ya gocewa harin nasa Amma duk da haka sai da kafar Karen ta dama ta yakusheshi a kumatu, Nan take wurin ya dare jini yayi feshi tamkar takobi aka sa aka yankeshi. Cikin tsananin zafin Karen ya Kara juyowa da baya, ya sake dako wani tsallen a karo na biyu tare da wangame bakinsa. Ba zato ba tsammani sai akaga DURZASU ya finciko takobinsa Sannan ya daka wawan tsalle sama ya soka takobin a cikin bakin wannan Katon Karen, sai gashi takobin ta lume a cikin bakin Karen, sannan ya finciko ta, sai gashi jini na malala a Kasa Yana fantsama a sama a haka dai ya gama shure-shurensa ya mutu. Koda sauran dabbobin suka ga haka sai, suka rugo gaba dayansu suka afka Masa, Nan fa Shima ta tare su da dukkan karfinsa yana shawagi a samansu tare da soka masu zureriyar takobinsa a cikin kawunansu. Nan fa ya rinka kashe dabbobin suna faduwa Kasa matattu tamkar kanyar da babu dadi, sai dai aga kwanya da jini na Malala a Kasa. A wannan lokacin idanun DURZASU suna lumshewa da budewa saboda tsananin galabaitar da yayi, Amma saboda juriya da naci irinta manyan mazajen kwarai, yaki yarda ya fadi, domin yasan cewa kuskure kadan zai iya jaa Masa mutuwa, Idan kuwa ya mutu shikenan burinsa ya Yanke Kuma Kasarsu zata fada hannun Dan uwansa ZULDARI Wanda babu abinda yasa a gabansa sai bakin zalunci da cin Amana. Haka dai DURZASU ya daure ya ci gaba da wannan Yakin har ya Karar da gaba dayan dabbobin, Yana gama kashe su ne sai ya fadi Kasa sumamme. Faduwarsa keda wuya sai akaga wata guguwa Mai tsananin karfi ta yayibe shi tayi sama dashi ta luluka sama a cikin gajimare, sai da tayi tafiyar dakika arba'in sannan ta sauko dashi a wata korama wadda ruwanta ke gudana garai-garai, a gefe guda Kuma ga 'yayan itatuwa nan iri-iri na musamman babu kalar da babu a wurin. Haka Kuma wata sassanyar iska Mai matukar dadin gaske, na kadawa a wurin wadda Nan da nan zata iya sa mutum barci saboda dadinta. Ajiyeshi wurin ke da wuya, sai wannan Guguwar ta rikide ta zama wani Dan mitsitsin Aljani Mai fuka-fukai shida, sannan Yana da rafkeken Kai tamkar Katon Dutse ne aka lika Masa, bugu da Kari bakinsa na da tsawo tamkar na Zalbe, Yana da zabtara-zabtaran hakora irin na damisa. Jikinsa madai-dai-ci ne baya da wani girma sosai. Bayyanarsu wannan wuri keda wuya sai wannan Aljani ya busa wa DURZASU wata siririyar iska Mai tsananin sanyi a

Chapter 9 of 12