Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
9 / 12
ransa "A gaškiya babu abinda ya fi yara dadi ina ma nine da wadannan yaran ai da duk inda zani muna tare da su, lallai ma na yarda da rahama ne". Yana komowa gida yana so ya yi ma Sakina zancen yaran da ya gani suka burge shi, yana tsoro kar ta tada balli ta ce ita ma haihuwar take so, ashe bai sani ba ita ta gano a wani wurin sun burgeta tana so ta sanar masa, yana nan zaune sai ta ce "Jamil ka ga kuwa 'yan biyun Yaya Sa'id?" Ya ce "Ina zan gansu?" Ta ce "Ai suna nan sun yi bul-6ul kamar ba 'yan biyu ba, wallahi gwanin ban sha'awa". Ya yi murmushi kawai don ma ya kawar da 106 Kwadayı bar ana Aа Abdullalu Sharada zancen sai ya ce "Wai yaushe kıka ce ana sa ranar kanwarki Ni'ima ne?" Ta ee "Sat jibi". Ya ce "To Allah ya kaımu jıbın" Kwance yake yana ta faman tunani a ransa yana cewa shi yanzu ina zai sami da, ga shi shi kadai ne wurin mahaifansa ba shi da wa ba shi da kani bare in sun haihu ya dauki 'ya'yansu, ga shi su kuma ba kara samun da zai yi ba, yau ya zai yi da ransa A gaskiya ya yi kuskure babba da ya lalata kwayayen haihuwarsa, ai da ace ya san haka ne gara ya hakura yanzu shi ya zai ya sami da? Ga shi ya yiwa kansa. Wannan tunani shi ne yake damunsa a kowane lokaci, yana cikinsa da zarar ya ga yara ko kuma iyaye da 'ya'yansu ana ta raha sai ya dinga jin shaukin abin. A takaice dai tsananin son da ya kamashi ya yin da kuma tsananin nadama ta mamaye shi na abinda ya aikata. "Jamil ya kamata ace munje an duba lafiyarmu domin yau shekara biyu kenan da aurenmu babu ko fatan wata". Kawai ya ji saukar muryar matar tashi a dodon kunnensa, ya dube ta "To maye kuma na wannan maganar ana zaune lafiya?" Inji Jamilu, yayin da ya hantaro mata "To wai ma har yaushe aka yi auran da zaki damu sai an wani haihu? Na ga ana samun shekara biyar da aure babu haihu ba sai daga baya, to ni ba na son irin wannan, ai wannan ma rashin godiyar Allah ne da nuna gazawa akan hakuri". Ta ce "To shikenan ka yi hakuri in ka ji haushi, ni bana fada ne don ranka ya baci ba". Ya ce "Ai ke ce kika ban haushi, kar ki kara yi min irin wannan maganar". Та ce "To na ji insha Allahu ba za a kara ba". Tun daga wannan rana Sakina bata kara cewa 107 Kwadayı harijanal- Auna Abdullahu Sharada komai ba, to amma fa duk yadda Sakina ta ke son ta haihu ba kamar Jamil ba, ba ya so ne ta san matsalarsa domin in ta sani zata iya guje masa kamar sauran matan shi ne ya ke mata wannan kandagarkin. A zaune ya ke bisa gadonsa yayin da ya yaye tattausan bargonsa ya maida shi rabin jikinsa ya yi tagumi yana tunanin halin da ya ke ciki, wannan ba shi ne karo na farko ba da ya fara wannan zaman tunanin ba, wato ya tashi cikin talatainin dare ya yi zaune yana sakar zuci ba, ya saka wannan ya kwance ya saka wancan ya kwance, yana nan zaune yana tunani ya dubi Sakina wacce ta ke kwance tana sharar bacci ya dai zuba mata ido na 'yan muntuna, sannan ya kauda kai ya ce "Shirman banza har da cewa Jamilu muje likita ya duba mu". Ya kwaikwayi maganar ta cikin gatse sannan ya се "Kin damu da son haihuwa, har kya sami idon bacci? Ni da na damu ba gani a zaune ina tunanin mafita ba?" Ya yi tsaki yayin da ya komo cikin tunaninsa da har kusan asuba bai hango mafita ba don haka ya kishingida domin ya d'an rurruma kafin ayi assalatu. Tunanin bacin rai, damuwa, rashin bacci, zancen zuci, babu wanda Jamil baya yi akan matsalar da take addabarsa wacce kuma shi yasa ya tada hankalinsa, ganin duk kudinsa ya kasa magancewa kanshi matsalar da ke takura shi, kuma neman rabuwa da ita, abin ya gagara ga shi yanzu ko abinci ba ya iya ci sosai tun ya nai a boye har Sakina ta sani, amma bata fahimci me yake damunsa ba in ma ta tambaye shi sai ya ce mata ba komai, a yanzu haka suke ita ma kuma ta damu da halin da yake ciki, domi sau da yawa in ta ganshi a irin wannan halin sai ta yi ta kuka don a zatonta ko wani abu ne yake shirin 108 Kwadayı barijana'- Amına Abdullahı Sharada zancen sai ya ce "Wai yaushe kıka ce ana sa ranar kanwarki Ni'ima ne?" Ta ce "Sar jıbi". Ya ce "To Allah ya kaımu jıbin". Kwance yake yana ta ſaman tunani a ransa yana cewa shi yanzu ina zai sami da, ga shi shi kadai ne wurin mahaifansa ba shi da wa ba shi da kani bare in sun haihu ya dauki 'ya'yansu, ga shi su kuma ba kara samun da zai yi ba, yau ya zai yi da ransa? A gaskiya ya yi kuskure babba da ya lalata kwayayen haihuwarsa, ai da ace ya san haka ne gara ya hakura yanzu shi ya zai ya sami da? Ga shi ya yiwa kansa. Wannan tunani shi ne yake damunsa a kowane lokaci, yana cikinsa da zarar ya ga yara ko kuma iyaye da 'ya'yansu ana ta raha sai ya dinga jin shaukin abin. A takaice dai tsananin son da ya kamashi ya yin da kuma tsananin nadama ta mamaye shi na abinda ya aikata. "Jamil ya kamata ace munje an duba lafiyarmu domin yau shekara biyu kenan da aurenmu babu ko batan wata". Kawai ya ji saukar muryar matar tashi а dodon kunnensa, ya dube ta "To maye kuma na wannan maganar ana zaune lafiya?" Inji Jamilu, yayin da ya hantaro mata "To wai ma har yaushe aka yi auran da zaki damu sai an wani haihu? Na ga ana samun shekara biyar da aure babu haihu ba sai daga baya, to ni ba na son irin wannan, ai wannan ma rashin godiyar Allah ne da nuna gazawa akan hakuri". Ta ce "To shikenan ka yi hakuri in ka ji haushi, ni bana faďa ne don ranka ya baci ba". Ya ce "Ai ke ce kika ban haushi, kar ki kara yi min irin wannan maganar". Та ce "To na ji insha Allahu ba za a kara ba". Tun daga wannan rana Sakina bata kara cewa 107 Kwadayı barijana'- Amına Abdullahi Sharada komai ba, to amma fa duk yadda Sakina ta ke son ta haihu ba kamar Jamil ba, ba ya so ne ta san matsalarsa domin in ta sani zata iya guje masa kamar sauran matan shi ne ya ke mata wannan kandagarkin. A zaune ya ke bisa gadonsa yayin da ya yaye lattausan bargonsa ya maida shi rabin jikinsa ya yi tagumi yana tunanin halin da ya ke ciki, wannan ba shi ne karo na farko ba da ya fara wannan zaman tunanin ba, wato ya tashi cikin talatainin dare ya yi zaune yana sakar zuci ba, ya saka wannan ya kwance ya saka wancan ya kwance, yana nan zaune yana tunani ya dubi Sakina wacce ta ke kwance tana sharar bacci ya dai zuba mata ido na 'yan muntuna, sannan ya kauda kai ya cе "Shirman banza har da cewa Jamilu muje likita ya duba mu". Ya kwaikwayi maganar ta cikin gatse sannan ya се "Kin damu da son haihuwa, har kya sami idon bacci? Ni da na damu ba gani a zaune ina tunanin mafita ba?" Ya yi tsaki yayin da ya komo cikin tunaninsa da har kusan asuba bai hango mafita ba don haka ya kishingida domin ya dan rurruma kafin ayi assalatu. Tunanin bacin rai, damuwa, rashin bacci, zancen zuci, babu wanda Jamil baya yi akan matsalar da take addabarsa wacce kuma shi yasa ya tada hankalinsa, ganin duk kudinsa ya kasa magancewa kanshi matsalar da ke takura shi, kuma neman rabuwa da ita, abin ya gagara ga shi yanzu ko abinci ba ya iya ci sosai tun ya nai a boye har Sakina ta sani, amma bata fahimci me yake damunsa ba in ma ta tambaye shi sai ya ce mata ba komai, a yanzu haka suke ita ma kuma ta damu da halin da yake ciki, domi sau da yawa in ta ganshi a irin wannan halin sai ta yi ta kuka don a zatonta ko wani abu ne yake shirin 108 faruwa. Kwadayı barijana'- Amına Abdullalu Sharada Tsaye ya ke ya rataye hannunsa a makarin bene ya zubawa wata bishiya ido kirr, yana kallonta idonsa cike da hawaye domin zafin tunani, Allah ya jarabce shi da son da wannan zamu iya daukarsa a matsayin sakamako ne dangane da abinda ya aikata a baya. Ya fi minti biyar bai dauke ido daga kan bishiyar da yake kallo ba, sai can kamar wanda aka mintsila ko aka zubawa bulala ya zabura cikin gaggawa gami da cewa a fili "Hakika na bar Halima da ciki a wancan lokacin ina cikin ina Hliman ina take? Mc ta haifa?" Cikin sauri ya sauko daga saman gami da shiga matarsa Sakina na cewa "Jamilu ina zuwa haka?" Ya daga mata hannu "Ina zuwa". Har ya kai unguwar su Halima yana kiyasta abinda zai ce da Yalwa in ya je domin hakika Yalwa ba kanwar lasa ba ce, ya san bala'inta sarai bare ga yadda suka rabu. Yana shiga unguwar sai ya yi tsai yana tunanin layin da suke, domin rabonsa da garin yau kimanin shekara goma sha takwas da watanni sai ya ga duk wurin ya sauya masa, don haka ya yanke shawarar ya yi tambaya, nan ya fara tambayar jama'a a gefen hanya har ya sami wadansu suka ce sun san gidan Yalwa suk sa shi a hanya. Ya na zuwa da bishiyar mangwaro a kofar gidan ya gane ya tsaya ya fito ya jingina da motarsa, yana tunanin yadda zai tunkari Yalwa, domin ance tana nan bata mutu ba har ma Babansu wato Malam Usman yana nan da ransa. Wani tunani ne ya fado masa ai ko akwai wata mata makotansu mai suna Gwaggo Hanne, ina ma ace tana nan da a gunta zai fi samun cikakken bayani, can ya dosa domin a gane gidan, saboda katangarsu guda, har yau kuwa haka ne. 109 Kwadayı barijana'- Amına Abdullahı Sharada Yana zuwa ya sa aka yi masa sallama da ita, jim kadan ta lito tana dogara sanda abın ya bashi mamaki ya ce "Lallai tsufa labari, ashe har ta tsufa haka? Koda yake ai abin ba na yau ba ne". Bayan sun gaisa ne Gwaggo hanne ta ce "Samari ban fishshenka ba, daga ina?" Ya ce "Gwaggo na san ba zaki gane ni ba, ni ne Jamilu". Ta ce "Jamilu? Wanne Jamilun fa?" Ya yi murmushí ya ce "Saurayin Haliman gidansu Yalwa?" Ta ce "Af, to to Jamilu kai ne haka?" "Yau wallahi ni ne Gwaggo". Та се "Allah sarki Jamilu ka je ka buya shiru ba amo ba labari?" Ya yi murmushi ya ce "Gwaggo lamarin ne sai hankali dama yanzun ma zuwa na yi in gaishe ku in wuce". Ta ce "Allah sarki ince ko dai kun gaisa da Yalwan, hata jin dadin jikin ma tun kwanaki". Ya ce "A'a ban shiga ba, ai gani nake yi kamar in na shiga zata kore ni". Ta yi dariya ta ce "Haba sai ka ce wani yaro?" Shi ma dariyar ya yi ya sa hannu aljihu ya ciro kudi masu yawa ya bata, ta yi ta godiya sannan ya ce "Wai ni Gwaggo ina Halima kuwa?" Tana jin wannan tambayar sai ta tabe masa baki "Halima ta na can ta auri wani mai kudi sai faman sakar musu kudi yake, suna washe wa". Ya ce "Wai ni ko ya ta yi da cikin nan na jikinta? ta haihu kuwa ko sun zubar da shi'?" Та се "Таa haihu wai ya mace......" Cikin doki ya katse mata maganar da take yi "Ina 'yar?" Ta ce "Ta yadda ita". "Ta yar?" Ya bukata a dan razane, "Eh, wai tana haihuwa sai Yalwa ta ce ta yadda 'yar ina ga ma a kwararo ta haife ta ta yar". nan da nan kamanninsa suka sauya "Ina Haliman ta ke auren?" "Ka ji ka ko? Ni dai kar ka je ka ce ni na haďa ka da ita, na gaya maka komai". Ya ce "Haba (Gwaggo ai babu 110 a Kwadayı barı jana!- Amina Abdullahi Sharada wanda ya san na zo bare a zargi wani abu". Ta ce "A to koda an tambaye ka wa ya gaya maka kar ka be ni ce". Ya ce "Ba ma wani mai tambayata, yanzu a ina ta ke auren?" nan ta ke ta yi masa kwatance, ya gane sannan suka yi sallama akan zai komo bayan kwana biyu. Bai ko kalli gidan Yalwa ba domin ba nan dama ya yi niyyar zuwa ba. *** Y au ce ranar sunan Sameera don haka jama'a an taru makil ko ina mutanen jamus an hallara baki dayansu, Saddik ya zama kato yana rarrafe ko ina abinsa gwanin ban sha'awa ga su Žainab ma an zo da su ibrahim yana ta doki zai ga matar da zai aura a fili, gidan su Alhaji usaini ya cika da baki har Baba Abu ma ta zo a takaice dai an hallara sosai da ya ke Bashir kulle gidan suka yi suka komo gidan Alhaji Usaini wai ayi taron sunan anan don kar a bata musu gida shi yasa baki dayan jama'ar suna gidan hatta harabar gidan ma jama'a ce su kansu gidan su Bashir din wato gidan Hajiya Rukayya nan suka dungumo. Ana cikin tsaka da suna su Halima na ta faman kawowa da komowa ana harabar gidan ana rabon abinci don haka kowa ya nutsu sai cin abinci ake ga abin cin nan iri-iri sai wanda ranka ya zaba, kuma kome ka ce sai an saki maka rabin kazar nan soyayya da tsire mai dadin gaske, ga lemuka nan iri-iri birjik sai wanda ka zaba, ban da na bature na kwali 'yan waje ga na gida nan kuma wanda aka hada da kai kamar su lemon kwakwa da na abarba da dai sauransu wadanda aka dauko masu yi 111 kwaday han jana'- Amına Ahdullaly Sharаdи musamman dama an saha duk sa'anın su sai an barar da kudi shi yasa ma in har sha'anin su ya zo zaka ga jama'a kamar kara turo su aka yi ga kuma kayan rabo nan da za a raba a jibge kala-kala masu rabo na jira a gama sannan a hau rabo Wata bakar motace ta tsaya jeep mai dubun gilasai yayın da sauran 'yan suna su kai mata kallo daya sai kowa ya dauke kansa domin a zatonsu wadansu 'yan sunan ne suka zo sai ga wani farin mutum kyakkyawa ya fito daga motar yana sanye da manyan kaya na alfarma, sai kamshi ke tashi a jikinsa, yayın da ya fito sai ya sami wanı yaro wanda yana daya daga cıkin yaran da aka zo da su sannan ya kkra shi yaro ya ıso da gudu ya durkusa ya ce "Gani". Ya ce masa "Ko ka san wata Halima anan gidan?" Yaron ya ce "Aunty halima?" Ya ce "Eh". Ya ce "Na santa ka ganta can ma waccen mai blue din atamfar wacce ta dauko plate din can ita ce". Ya ce "Yauwa to ka ce ta zo ta yi bako". Yaro ya ruga da gudu yana kiran "Aunty Halima wai kizo kinyi bako" Cıkin tsananin mamaki ta waigo ta kalli yaron tana nanata kalmar bako a bakinta, ta ce da shi "Wanne inin bako kuma?" Ya ce "Wani farin mutum ne". Ya ce "Wai ki zo kin ganshi can". Ya nuna inda mutumın ya ke, Ilalıma bata shaida ko wayc ba, sai ga lHajiya Jamila ta zo ta ce "Wa ye kuma yake kiranki?" Ta ce "Wallahi ban san ko waye ba". Ta ce "To muje mana mu ganı?" Halima ta ce "To". Domin ta ji kwarin zuwa tunda ga Hajiya Jamila, sunje tare ba a ce da alhaji Usaini wanı ya zo ya yi sallama da ita taje ba, don haka sai suka tali babu wanda hankalinsa ya ke kansu kowa nata hidimar gabansa. Suna isa wurin mai kıran Halıma ta tsaya cak tana 112 Kwadayı barıjana'- Amina Abdullahı Sharada dafe da kirji cikin tsananin kaduwa ta ce masa "JAMILU me ya kawo ka gidana kuma bayan ka san cewa ina da aure?" Murmushi ya yi ya ce "Haba lalima ai kya bari mu gaisa tukunna kuma ai na san kina da aure zuwa na yi ki bani 'ya ta da kika haifa!" Wannan magana ta zo wa Halima tamkar harbin bindiga domin saboda razana sai da ta yi baya taga-taga, Hajiya jamila ce at taro ta tana cewa "Wacce 'yar zaki ba shi kuma? ko Zainab?" Da kyar Halima ta girgiza kai ta ce "Ba ita ba ce". Sannan ta dubi Jamilu ta ce "Haba jamilu wannan wacce irin magana ce kuma? ko so kake ka tona min asiri shi yasa ka zo?" Ya ce "No ba nufina ke nan ba, Halima kuma tonon asiri ma ai ke zaki tonawa kanki domin wannan matar da kuka zo tare ai tare an ganku ban san matsayinta a wurinki ba shi yasa". Ta share hawayen da ya gangaro mata ba zato ta ce "Ni dai don Allah ka tafi ka bani wuri, kar Alhaji ya zo ya same ka a nan". Ya ce wanne irin in tafi bayan ga abinda na ce miki?" Ta се "Ai kai kace baka so ni yanzu a ina an samo ta?" Ya ce "to yanzu ina so don haka na baki nan da kwana uku ku gama taron zan komo ku bani 'ya ta don naji ance mace kika haifa". Cikin tsananin fargaa ta dubi Hajiya Jamila, ita kuma Hajiya jamilar ta tabe baki ta juya abinta ta shiga cikin 'yan suna tana ta faman kwazawa jama'a "Kinga wannan mutumin wai wurin Halima ya zo karbar 'yar sa, ko dai dama duk 'ya'yan da halima ta ke haifa bana Alhaji ba ne? To gashi dai ya zo ta bashi 'yar sa duk ta rude ta na cewa wai wani kar ya tona mata asiri". Wasu suka ce "To zancen yaushe ai asiri ya tonu". Ta ce "Ku gane min hanya wai makaho ya so tsegumi". Nan da nan sai zance ya baza gida kaf! 'Yan sunan da baki da 113 Kwadayı barijana- Amina Abdullalu Sharada 'yan gıda babu wanda bai ji wannan magana ba, sai mazan da basu nan kawai. Cikin sanyin jiki da kidimewa Halima ta shige sai la ga anai mata wani irin kallo kamar wadda ta yi gagarumin abu, sai ta wuce cikin gida ta shige dakinta ta rufe kofa ta afka kan agdo tana ta faman kuka, ta ji a rayuwarta dama ta mutu ta huta da wannan bakin cikin ashe Baba Abu bata tafi ba, taan can tana jin yadda gidan sunan ya dauki dumin zancen kowa na fadin albarkacin bakinsa sai ta higa dakin Haliman ta kwankwasa can sai ta taso ta bude, Baba Abu ta tambaye ta "Me yake faruwa ne?" Ta sanar mata cewa "Jamilu ne ya zo wai in bašhi 'yar sa". ta ce "Wa ye kuma Jamilu?" Ta ce "Wannan wanda..." Sai ta kasa fada, Baba Abu ta ce "Kar dai wanda ya yi miki cikin nan?" Ta gyada kai cikin kuka. Baba Abu ta yi salati ta ce "Wannan zuwa ya yi ya tona miki asiri ba zuwa ya yi domin 'yar shi ba, shi da ya ce ba ya so?" Ta ce "To ai ya tona min domin dubu wadannan taron al'umma yadda suka yo caa akan maganar kowa na fadin albarkacin bakinsa". Baba Abu ta ce "to yanzu ya za'ayi?" Ta ce "Z.uwan Alhaji zan jira inji irin hukuncin da zai yanke domin ni na san zamana kuma ya zo karshe a gidan nan don da kyar za a fadi masa iya abinda aka yi sai an yi kari, ta yadda zai ji ya tsane ni!" Ta ce "ki kwantar da hankalinki zama da rashi na Allah ne...." Halima ta katse Baba Abu "Baba kina ganin ko na ci gaba da zama anan zan sami daraja irin ta da?" Ta cе "A gaskiya babu, kai amma wannan yaron ya yi mana rashin mutunci, to Allah dai ya saka miki Halima". Dare ya yi duk 'yan suna an fashe kowa ya tafi da wannan magana a baki, haka ma mai jego mijinta ya zo 114 Kwadayı barı jana'- Amına Abdullahı Sharada ya dauke matars da bind aka tara musu na suna, sun tafi Baba Abu ma sai magruba ta tafi, saboda jimamin abin nan ta yi ta faman kwantar mata da hankali domin hankalın Halima ya yi matukar tashi, can kuma gidan Sameera bayan sun koma sai Sameera ta ke tseguntawa Bashir abinda ya faru yau, ta ce "Yaya bashir ka san me ya faru?"Ya сс "A'а". Та сe "Wai wani ne yau ya zo ya ce wai Aunty Halima ta bashi 'yar sa". Bashir ya kara gyara zama "wacce irin 'ya kuma zata bashi?" "Oho wasu dai suna ta tsegumin wai ko Zainab ba 'yar Abbansu Maryam ba ce". Ya ce "kai haba ai kowa ya ga Zainab ya ga Alhaji har duk sauran 'ya'yan ta ma". Ta ce "A to maye na rudewar da ta ganshi in ta san sharri ya ke mara?" Ya ce "in ma dai akwai wani abu daban to ba maganarsu Zainab ba ce sai dai in akwai abinda ya hada su can daban". Ta ce "Ka san wani abu?" Ya ce "A'a". Та ce "wallahi mutumin suna bala'in kaam da Saddik dan gidan Maryam". Ya yi dariya "Au nan kuma kika koma?" Ta ce "wallahi bani kadai ba kowa ma ya fada". Ya ce "Da Allah ki sake wata hirar daban ni bama na son jin wannan hirar". Ta ja baki ta tsuke kawai. Maryam na tafa hannu a dakinta na gidansu Hajiya Jamila ta dubi mijin yayin da ya ke ta faman yiwa Saddik wasa akan gado ta ce "Faruk ka san abinda ya faru?" Bai ji ba domin suna ta kyalkyalar dariya da Saddik ta dan daka masa duka ya waiwayo yana dariya, ta ce "kai ina son in gaya ma zance kana wasa da da?" Ya ce "Me aka yi?" ta ce "Yau wani mutum ne ya zo wai Aunty Halima ta bashi 'yarsa". Ya ce "Wacce kuma 'ya? Bashi da hankali ne?" Ta ce "wanne irin bashi da hankali? Mutumin lafiyayye ras da shi". Ya ce "to ya akai ya san 115 Kwadayı barıjana!- Amına Abdullahı Sharada ta? Ko dai don 4.1.9 ne?" Ta ce "Anya kuwa? Ai ita ma ta san shi". Ya ce "To kila mijinta ne na baya, ba ance ta taba yin aure ba?" Ta ce "Au ch haka ne kuwa, amma baka ji yadda gidan sunan nan ya dauka ba, wai kila ma duk 'ya'yan Abba ba nasa ba ne, na wancan mutumin ne, wallahi sai da tausayin Aunty ya sani kuka domin kana ganinta dole ka tausaya mata". Ya ce "Ina ma mun same shi mu ci abu ta kazar ubansa don rainin hankali zai zo har gidan mijinta ya ce wani ta bashi 'yar sa?" Та се "wallahi kuwa, wannan rainin hankali ne". Faruk wallahi mutumin nan ya ban mamaki da na leka sai naga suna kama da Saddik". Ya ce "Wanne Saddik kuma?" Та се "Saddik dinmu". Ya ce "Kin faye shirme da yawa". Hajiya Jamila ce zaune a tsakiyar su Hajiya Husna da IHajiya Rukayya da 'yan tsirarun kawayenta, ana ta hira, Hajiya Jamila ce ke ta zuba zance ai kanta ake jiyowa, "Yo in ban da ma Alhaji waye zai yi aure bai yi wani bincike ba? Wallahi Hajiya Husna kannan Halima duk 'yan daba ne, ai ita Hajiya Rukayya munej da ita ta gani. Halima ma bata sani ba, na ja ta muka tafi don ta ganewa idonta, duk sanda kaje gidan nan sai ka tarar da wani abin husuma". Hajiya Husna wato mahaifiyarsu Faruk kenan ta ce "Amman ko in haka ne Halima ta bata wayonta ina ganinta kamar me hankali ashe wayon banza ne da ita?" "Uhum! In na gaya muku ai sai ku ga kamar sharri nake mata, tun da kishiya ta ce". Hajiya Rukayya ta ce "Ai ni dama tuni naji labarinta har cikin shege ta taba yi ko zubar wa aka yi ne oho? Shi ne dalilin da ta koma gidan wannan kanwar uwar tata ta Gwale". Hajiya Jamila ta ce "Ammashi ne ko ki sanar min?" Ta ce "to ai in kaji 116 Kwadayı harı jana'- Anına Abdullahu Sharada irin wannan baka lada lajiya Jamila kın san dai irin son da Alhajı yake mata in ya ji ba lallai ne ya yarda ba". Tа сc "Hakika ba ya son laifin ta bara ki ga yanzun ma ba lallai ne ya yarda ba, in ma ya tan yaushe za'a taushe bakinsa da malamai". Inji Hajiya Jamila "Ai wannan son da yake mata bana Allah ba ne". Nan dai suka yi ta faman hirar har kusan goma na dare, sannan Alhaji Usainı ya komo, Hajiya Jamila ta tafi dakinsa domin ita ce da girki a wannan ranar. Kusan sha biyun dare kowa ya yi bacci, amma Halima na kwance idonta biyu duk ya kumbura, saboda kuka ga yaranta nan a kwance suna ta bacci kusan ukun ita kuma ta hada kai da gwiwa sai ta ji an turo kofa a hankali an shigo. Cikin sauri ta dago kai ta ga Alhaji Usaini ya shigo, daga shi sai singileti da gajeran wando ya sami gefen gadon ya zauna yayin da ita kuma hantar cikinta ta ci gaba da kadawa domin razanar ganinsa da tayi ta fara rawar sanyi dama kuma zazzabi ne a jikinta, saboda kukan da ta sha. "Hajiya Sadiya ance yau kinyi bako ko?" Nan take gabanta ya kara faduwa ta rasa ya ma zata amsa masa wannan tambayar, sai hawaye kawai ke zuba, ya ce "Da ke nake fa?" Ta dago kai ta kalle shi ta ce cikin shesshekar kuka "I na yi". "To me ya zo yi?" "Wai cewa ya yi in bashi 'yarshi?" Saı ta karashe zancen cikin kuka, ya ce "Wacce 'ya ya ke da ita a wajenki?" Ta ce "Ai ba yanzu ba ne zancen ya jima". Ya ce "Tun yaushe ne?" Ta ce "tun

Chapter 9 of 12