ya hadu. Falon shi ya sa su a tsakiya
6angaren, shigo sai ka ratsa falon sannan za ka kowane
a girke da
kuma anan falo daga gefe dinning table ya ke kujerunsa abin dai gwanin ban sha'awa.
cewa dai
Kowa ya fashe an bar Amarya da Angonta, duk da
ana Angwanci,
Angon bai shigo ba, ya na can tare da abokansa
dakin Amaryarsa, kusan sau goma suka taho rako Ango domin garin ya fara nuna alamun hadari zai taso, ana ta faman walkiya da ya ke damuna ne.
bakinsa, Sunyi
anyiwa
raha sosai da sosai kowa ya fadi albarkacin
zaman lafiya, daga
Ango da Amarya addu'a ta neman nan kowa ya kama gabansa saboda hadarin da ya taso, shi kuma Bashir ya raka su ya rufo kofa ya komo, a lokacin nan Sameera ta na nan zaune, ban da fargaba ba abinda ta ke yi, don Bashir ba ya sonta aka yi wannan auren har kawo yau da aka gama biki bai ce ma ta kala ba yanzu ma da ya shigo fangarensa ya shige abinsa.
Ta na jira ko zai fito, kusan awa biyu bai fito ba har ta fara bacciba ta san shi tuni ya yi baccinsa ba ma, 42
Kwadayı barı jana!- Auna Abdullahı Sharada
bangaren dakinta ta tafi ita ma ta kwanta ba tare da ta
rufe kofar da key ba, nan ta ke bacci ya yi awon gaba da
ita, don ta gaji sosai.
Kashe gari tunda wuri ta tashi, ta yi sallah, bayan ta
idar ta fito falo, ta shiga kitchen don ta hada musu abin
karyawa ba ta fito ba sai bakwai saura, ta same shi a falo
ya na zaune ya kunnan kallo har kasa ta durkusa ta
gaishe shi, amma ko kallon inda ta ke bai yi ba, cikin
sanyin jiki ta shige dakinta, yayinda hawaye ya zubo ma
ta, ta ce "Yau na shiga uku, ya zanyi? Bashir ba ya so na
da gaske!"
Fitowa ta kuma yi, ta shiga kitchen ta hada musu
break fast ta kawo bisa dinning table ta shirya sannan ta
komo ta durkusa ta ce ma sa "Yaya na gama shirya mana
break ka zo muje mu karya". Ta na maganar ne gabanta
na faduwa. Ko kallonta bai yi ba, nan ma sai ta koma
gefe daya ta zauna, ta yi tagumi hannu biyu, jarida ma ya
dauka ya na karatu abinsa, bai ko kalleta ba, can kuma
sai ya ajiye jaridar ya haura takalmansa ya fice abinsa.
Ta bishi da kallo har ya kule, wasu sabbin hawaye masu dumi suka zubo ma ta.
Nan ta ke tunanin iyayenta da 'yan uwanta ya fado
ma ta a rai, duk da cewa suna nan basu koma ba, amma
ai gobe za su tafi, ya za ta yi in sun ta fi?
Gashi wanda ta ke so din ta zauna domin shi ba ya
kaunarta? Hawaye ya sake zubo ma ta a fuska, ta na
cikin gogewa, sai gashi ya shigo ya na dauke da wata
kula, ashe abin karyawa ya je ya sayo a wani restaurant
da ke nan ku sa da su, nan ma ran ta ya sosu, ta hana
idonta bacci ta yi don ta burge shi amma ya je ya sayo a
wani wuri, kuma abinda ya sayo din ma bai kai dadin
43
Kwadayi barijana'- Auna Abdullahu Sharada
nata da tsafta ba.
Don ita ko abinda ta zuba musu abin karyawar ma
abin sha'awa ne, ga wani ado da ta sshirya musu kun san
turawa da adonta abinci, kamar daurawa za'ayi ba ci bа,
tashi ta yi ta nufi inda aka girke musu kayan kallo ta ciro
wani faifan sidi na audio wakar Ramla ta labbaika
rasulullah ta sanya, wakar na tashi a hankali ta koma ta
kwanta bayan ta rage rediyon ta na sauraron wakar.
Zuciyarta cike da shaukin bege na manzon Allah
(S.W.A), shi kuma ya na gama cin abinci ya yi waje
abisa, ya bar kular a wurin.
Tsam! Ta mike ta je ta duba, ashe ma har ya cinye,
ta dauki kular ta wanke, sannan ta komo da ita ta ajiye
ma sa can sai gashi ya zo dauka, ya na budawa ya ga an
wanke, amma duk da haka bai yi magana ba ya ficce
kawai abinsa.
Murmushi ta yi ta ce "Duk lalacewar zuciyata na
san mai kyautata ma ta".
Ya na ta faman sauri ya shirya zai ficce ya fito da
wankinsa daga daki, zai tafi da su ya kai wanki, ya zube
a falo ya fice ya manta su don ya na ta sauri, kuma har ya
ficce bai tuna cewar ya mance wankin ba, nan da nan ta
kwaso bahunna ta zagaya can famfon baya ta dauki
wankin da sabulu, ta wanek ma sa su tas.
Set takwas ne ban da gajerun wanduna da best da
kuma hankici kala biyar a cikin aljihunnan wandon ne ta
sami takardu da 'yan tsirarin canji da dan abinda ba'a rasa
ba, ta kwashe ta kai ma sa daki ta ajiye don ba ya nan,
har wankin ya bushe bai dawo ba, ta kwaso ta zo ta zube
ta fara guga gashi kuma kayan sun fi ta kal.
Ta gama gugar ta ciro zani daga cikin zannuwanta
Kwadayı barı jana'- Anuna Abdullahi Sharada
ta nade gugar nan ta ajiye a inda ya ajiye kafin ya fi ta,
sannan ta dora musu abinci duk da cewa ba ci zai yi ba,
to amma dai in bai ci ba na sa rabon ta ke ci da daddare
in ta abshi da daren ma ya ki ci.
Bai dawo ba sai ku san takwas na dare, to ta na jin
ya shigo ta mike ta nufi inda ya ke, ta yi masa sannu da
zuwa, ko kallon inda ta ke bai yi ba, ya wuce inda ya
ajiye wankinsa, don bai tuna ya mance ba sai da ya yi
nisa sannan ya tuna ya bar wankinsa, to amma gobe ya
kai.
a Duk da ba haka ya so ba, ya fi son a wanke su
yau din nan don akwai wata shadda da ya ke son sa ta
gobe, ya na shirin dauka ya ga zanin mace an nade su, ya
ware zanin ya ga kayanshi a wanke, a goge, a tsaftace,
gashi an gaam shirya su kamar yadda ya kamata, layin
gajerun wandunansa daban, layin hankicinsa daban, ga
wani kamshi mai dadi ya na tashi, a jikin kayan, ashe
turaranta ta fesa musu.
Cikin sauri ya waiwaya inda ta ke, ya ga ashe ba ta
wurin ma, sai zuwa can ya ga ta fito ta nufo inda ya ke,
ta durkusa ta mika masa canjinsa da ta tsinta a aljihun
wando, kuma ta abshi sauran takardun ta ce ma sa "Yaya
da ina yi maka wanki ne na gansu a aljihun wandonka,
shine na dauke na ajiye ma ka".
Shiru kawai ya yi gami da mika hannu ta bashi, ya
cire zanin da ta yi masa wankin ya ajiye, sannan ya shige
dakinsa abinsa, ya rufe kofa ya barta anan a tsaye, dama
ba ta sa ran zai kula ta ba, don haka sai ta juya abinta ta
shige dakinta.
45
Vma am sane, duns Ahhilbahı Sharnda
Amaday AnC une odullahı Shaada
***
A
Famarin su Maryam kuma, abin ba magana domin
faruk ya shiga tsaka mai wuya game da Maryam,
sam zama ya ki dadi, duk abinda ya kamata ya yi don a
zauna laliya ya yi, amma bai samu nasarar shawo kanta
ba. Gashı iyayensa sun dauki laifi sun fora mishi saboda
sharrin da ta ke-masa, wai cutar ta ya ke, dukanta ya ke,
kuma ya shiga neman mata, wannan sharri shi ya janyo
wata matsala a wurin iyayensa domin sun yi fushi da shi
sosai, su a ganınsu wulakanta matarsa ya ke, fargabarsu
daya kar ta sanarwa iyayenta domin abin ba zai musu
dadi ba, ga gari ba kusa ba, har ta kai yanzu daga Mum
har Abba da sauran kannan Faruk wato Ibrahim da
Zainab ba ya jin dadinsu, zaune ya ke a gidan kowa ya
tsane shi, amma ita Maryam ko a jikinta, yadda abın ko
ya fara, shi ne:-
Lokacin da suka tafi bikin Samecra gida ya rage daga Faruk sai Maryam, to ga laifin Bashir zai auri kuma Kanwar Faruk zai aura sai ta kara hasala, ta kuma dora
masa karan tsana shi kuma ganin su kadai ne a gidan sai ya zamana duk lokacin da ya bukace ta sai ya ida bukatarsa komai ihunta, hakan ne ya kara rura wutar Kiyayya a tsakaninsu, ya zamana ba ta ko son ta dube shi, bare ta saurare shi, gashi har yau ba ta jin dadin jıkinta ba, bayan sun dawo ne suka samu duk ta rame, suke tambayarta ko har yanzu jikin nata ne?" Ta сe "Ba komai, ita ba ta san abinda Faruk ya ke yi ba, sai ya dinga kawo mata gidan, ta yi masa magaan
46
hwadayı hanjana' Amuna Abdullalu Sharada
ya yı ma ta duka" Ai jin abinda ta fada ya harzuka
Zuciyar su Mum suka kira shı, ran Abba a bace suka yi
masa lada sosar, to tunda nan sar Mum ta tambaye ta ko
ya daına balinsa?" Sai ta ce "Bai daina ba". To fa nan
suka kafa masa karan-tsana ko ya gaischsu ba sa
amsawa, yayi-yayi lyayen su fahimta ba su fahimta ba,
don haka sai kawai ya kyale su ya zuba musu ido kawai
ya na kallonsu don shi ya san wannan duk hadin na
Maryam ne ba wani ba.
Yawan tunani da zancen zucin da sauran su su suka
haddasawa Paruk shiga bacın rai da sauransu, har ya dinga jin babu dadi a 'ransa, a kullum shi ke nan yawan
tunani da abin ya yi tsananı ma sai ya dinga jm rashin
dadi a jikinsa, yau a lafiya, gobe babu, amma babu wanda ya san halin da ya ke cıki, sai shi daya, sannusannu har ciwo ya fara damunsa, tun ya na kokari akan
wannan har ya zamana ba ya iya aıkin komai, yawan kwanciya da yawan tunani wannan lamari ya sa iyayensa
sun hassala domin su na zaton ko halayya ya sauya.
Yau ma ba inda ya je, don jikin nasa na matsa
masa, ga ciwon kirji da ciwon kai duk ya bi ya rame, ya
na nan a kwance sai ga Mama wato Mum ta shigo, ranta
a bace ta sameshi akwance ta ce "Wai kai me ka ke nufi
ne?" Cikın karlin hali ya taso ya ce "Me na yi kuma Mum?"
Ta ce "Ban sani ba, ka ga in baka san yarinyar nan
ka saketa kawai shi ya ti sauki". Y ace "Mum me ta ce
kuma na yı ma ta?" Ta ce "ban sani ba, ai komai ka ke yi
ma ta ka xani ba sai an fada ba, ka fi kowa sani"/ Ya ce
"Mum wallahi ni ban san abinda na yiwa Maryam ba,
kuma ina onta, ba zan iya rabuwa da ita ba....."
47
Amon
Kwadayr harra A Arhillahı haraня
"Kai tafi can marar mutuncı, yanzu da ka ganni ba?
Ai wallahı ka banı mamaki, ban taba zaton zaka kunyata
mu ba, kai fa ka ce ka na son yarınyar nan, amma daga baya ka zo ka ke wulakantata, wallahı muddın ba ka sake hali ba sai dai ka saketa don ba zaka zo ka kunyatamu ba abin zumunci".
Shiru kawai ya yi ya na sauraronta, don ya rasa ta cewa, hankalinsa aa tashe, tuni ta ficce ta na ta faman fada
shi ma sai ya tashi tsam ya nufi dakin Maryam, ya
sameta zaune bisa gefen gado, shi ma ya shiga ta na ganinsa kawai ta mike da sauri cikin razana ta dauka ırın
abinda ya saba yi mata ne ya kawo shi, wato ya bukaceta bisa dole.
y1 Maryam bai kamata in ba kya sona ba ki dunga
min sharri ba, don Annabi (S.A.W) Ya ce in zaka yi so ka yi shi domin Allahi, in zaka yi ki ma ka yi shi don
Allah, to ke babu abinda ki ke yi don Allah, wai shin ke ba ki koyi da wannan hadisin? Ni na san ce wa bakya kaunata, to wai me ya sa zaki dinga hadani da iyayena? wai ke ba kya tsoron Allah ne?"
Ya ci gaba da "Maryam ina so ki sani wannan wata daam ce kike da ita game da ni ina jiye miki kar ki yi sake damar ta wuce ki, shi wanda kike so din ya yi aure, kuma su na zamansu lafiya da matarsa, tuni ya ma manta ki amma ke kina nan ki na kwasar zunubi saboda shi, kuma wani abin haushin ma ko da ace mun rabu da ke
aure ya haramta tsakaninku domin na ri ga ya na aureki shi kuma kin san dai auren kanwata ya ke, kina ganin wannan kwadon zai yiwu? Saboda haka ya kamata ki san
nasihata
me kike yi, ki bar bugun taki ga jaki, wannan shi ne ta karshe daga cikin dumbin nasihohin da nake
48
Kwadayı bari jana!-Amina Abdullahi Sharada
yawan yi miki".
Ya na gama wannan bayanin ya tashi ya ficce ya barta. Shiru kawai ta yi ta na tunani, jikinta a sanyaye ta
ce "Lallai na yarda da maganarsa gaskiya ce, don ga shi
tunda aka yi bikin Sameera da Bashir shiru zamansu, su
na can su na shan shagalin amarcinsu, kai jama'a lallai na yarda namiji bashi da alkawari!"
Faruk kam tunda ya yiwa Maryam wannan nasiha bai sake sauraranta ba, don shi mutum in ya dauki
nasihar da akai masa ai ankance za'a gani, to babu abinda
ya sauya shi ya sa ya ce har yau Allah bai kawo iyakar
wahalar ba. Maryma ma ba lafiyar ce da ita ba, yau fari
gobe tsumma, kuma ta Ki ta je asibiti in Mum ta ce ta zo akai ta sai ta ce ta warke, haka Mum za ta hakura ta kyale ta.
Yau ma jikin ya tashi ta na falo kwance ta na
lissafin yau kwanan Faruk biyu bai fito daga daki ba, ko
dai ba ya nan ne? Don duk inda zashi ba ya fada ma ta.
Ta na fito ya na nan ta na wannan tunani, Faruk ya
hada hanya, duk ya rame ya kode. Ya na zuwa dai-dai
inda ta ke amai ya kamashi, ina? Kafin ya yi wani
yunkuri sai ya fito gami da tari, nan da nan ya fadi
bakinsa a bude ya na kiran Maryam da kyar, ko kallon
inda ya ke bata yi ba bare ta san halin da ya ke ciki, a
maimakon haka ma sai ta mike za ta koma daki, ta daka
masa harara, ai ko hararar da ta daka masa sai ta koma
kallon abin mamaki, domin aman da ya ke yi aman jini
ne.
Cikin rudani ta yi saurin zuwa inda ya ke, shi kam
a halin yanzu bai san inda ya ke ba, ta yi saurin juyo shi,
ai ko bakin idanun nasa ya juye ya koma fari, ganin haka
49
Kwadayı bar jana!- Amina Abdullalu Sharai
ba
mai
Karamin
razanarwa,
tsorata ta ya yi ba, sai kuwa ta kwala kara su Mum su na falo dasu Ibrahım da Z.ainab da Abbansu ana ta hira suka ji karar Maryam.
Mum ta ce "To Alhaji gashi can zai kashe musu
yarinya, ma za je ka". Baki dayansu suka runtuma da
gudu su na rige-rige, ai ko suna isa suka yi turus suka
tsaya kallon ikon Allah don ganinsa suka yi kwance cikin jini kamar ba rai.
Ibrahim ne ya ce "Me ki ka caka ma sa haka?
Cikin kuka ta ce "Ba komai, amai ya ke yi na jini". Mum
ta ce "Alhaji ai sai ayi gaggawar kai shi asibiti."
Shi dai Alhaji saboda rudewa sai ya ce "Yo me za'a
kai asibiti bayan ya mutu?" Ibrahim ya ce "Daddy bai
mutu ba, suma ya yi". Zainab kam sai kuka ta ke yi ta ka
sa zaune ta kasa tsaye, nan dai Alhaji da Ibrahim suka
taitaye shi zuwa mota, jikinsu duk ya baci da jinin aman
da ya yi, Alhaji ya ja motar sai asibiti.
Da zuwansu, nana da nan aka karbe su, aka sanya
masa wannan robar a hanci don jan numfashi aka yi
dakin da ya dace ayi treat dinshi, su kuma su Mum sun
yi tsaye su na faman saſa da marwa, su na jimamin
abinda ya faru, kuma ya haddasa ma sa wannan lamari
wanda in ba ayi hankali ba zai iya sanadin ransa cikin
lokaci kalilan, jim kadan sai ga shi su Daddy sun fito da
shi sun tura shi zuwa wani daki, bayan sun bashi gado ne
sai da ya karaso inda suke "In baku manta ba shi Daddy
fa babban likita ne, abinda ya sa aka kawo shi asibitin ma
don ya fi fahimtar me ya ke damunsa, kuma asibitin da
ya ke aiki nan aka kawo shi
Daddy ya zare safar da ke hannunshi ya dubi Mum
wacce a halin yanzu duk jikinta ya yi sanyi, ya ce "Ilusna
50
Kwadayı barı jana'- Amına Abdullahı Sharaрв
wai me ya ke damun yaron nan ne?" Ta ce "Ai kai zan tambaya domin ku ne likitoci". Ya ce "No ba wannan
ba, ina nufin wane tension na rayuwa ya shiga haka har
ya samu wannan ciwon?" Cikin damuwa ta ce "Alhaji
wane irin ciwo ne ya same shi?" Ya yi tsaki "Wallahi ya kamu da ciwon zuciya ne".
Ba ma ita ba hatta su Ibrahim sai da suka razana, ita
kuwa Mum rawar sanyi ta kama yi a wurin don fargaba,
ya ci gaba "Yanzu dai munyi kokarin gano abinda ke damunshi sauran kuma mu bashi maganin da zai samu lafiya insha Allahu, amma akwai magana sai mun koma gidi. Ya kamata a san me ke faruwa tsakaninsa da
Matarsa, la gaya mana gaskiyar lamari kar ta boye mana
domin ya zama dole a san me ye ke damunsa har ya
samu wannan ciwo haka".
Nan dai suka yanke shawarar ita Zainab ta zauna a
wurinsa domin ba'a san abinda ke damunsa ba, game da
zamansu da matarsa ba a sa ta yi jinyarsa ba, nan dai
suka dan zauna a wurinsu, su Mum suka wuce gida don dauko abinda za su bukata.
Tunda Faruk ya samu rashin lafiyar nan aka kai shi
asibiti har yau din nan kwana biyu Maryam ba ta je ba, ta
na gida, yanzu ma a kwance ta ke ta na ta faman tunani
hankalinta a tashe, tayi shiru ta na ayyana abinda ta yi
kam 'Lallai ba ta kyauta ba, wai to me ma ya ke janyo
hakan? Anya kuwa abinda ta kewa faruk kiyayya се?
Emana ita ce mana, in ko ita ce lallai ya ci ace ta saurara
masa haka, ko fa dubashi bata je ba, yanzu ko ba za ta ji
nauyin kowa ba. ai ta ji na iyayensa wadanda suke
matukar nuna ma ta so.
Lallai kan ya kamata ta je ta duba shi don ta wanke
51
Kwadayı barijana'- Amına Abdullalu Sharada
kanta wurin iyayensa". Nan da nan ta fara shiri ta na ta
faman kokarin tafiya sai dai kash! Ba ta san asibitin ba,
wai ina ne ma? Wa ya kamata ta tambaya? Ta dauko
mayafinta ta sauko falon kasa don ko za ta samu wanda
zai ma ta kwatancen wurin.
Ta kuwa yi sa'ar samun Ibrahim, ta na ganinsa ta ce
ma sa "Yauwa Ibrahim don Allah ko zaka kai ni can
asibitin da Yaya ya ke a kwance?" Ya ce "Ba zan samu
dama ba". Ta ce "Kai Ibrahim don Allah ka taimaka". Ya
ce "Na gaya miki ni ba zanje yanzu ba, ki bari sai na
samu lokaci na je". Ta yi turus sannan bayan ya tafi ta
bishi ta na cewa "To don Allah yi min kwatance sai inje"
Ya ce "Da cần me ya hana ki binsu sanda za'a je? Ni ma
ban sani ba". Cikin tsabar kidima ta ce "Haba Ibrahim ka
daure ka fada min mana, na san za ku yi fushi, to amma
ku yi hakuri". Ya ce "Oo ni meye nawa a ciki? Kinga in
kin san wuri ki tafi kawai, amma ni ba zan kai ki ba".
Ta ce "to ya jikin na sa?" Ya ce "Yana nan sai
abinda hali ya yi, don in ance ya mutu ma babu mamaki".
Ba ta san sa'in da ta rike masa hannu ba ta na girgizawa
"Ibrahim me ya ke damunsa?" Ya ce "Ciwon zuciya ne"
Ta ce "Na shiga uku".
Ta cika masa hannun ta dafe kanta cikin tsananin
fargaba ta koma sama ta shiga dakinsa, kamar me neman
wani abu da ya ke tunda aka kawo ta bata taba shiga
dakin ba sai yau, shi yasa ya zame ma ta bako, tsayawa
ta yi a tsakiyar dakin ta na dube-dube, kamar wacce za ta
ganshi, ya ci ace tsaruwar dakin da haduwarsa ya
burgeta, to amma da ya ke hankalinta ba ya jikinta ba ta
lura da wannan ba, ita kanta ba ta san me ya kawo ta
dakin ba.
52
Kwadayı barı jana!- Amına Abdullahi Sharada
Wani zazzafan hawaye ne ya zubo ma ta daga ido
ta alka bisa gadonsa ta fara kukan da ba ta san dalilin
yinsa ba "Wayyo Allah Faruk kar ka mutu! Ka dawo
Faruk na saba maka, Faruk ya zanyi da dumbin hakkinka
in na rasa ka?"
Wani tafkeken hotonsa ne lamination, a jikin
bangon dakin ya ke kallonta, ya na murmushi, can kusa
dashi kuma na ta hoton ne da Mama ta bashi, wato
Hajiya Jamila, ta dauka da wata doguwar riga mai kyau
kalar blue ta sanya hijabi shima bulun, ta sa hannayenta
biyu ta kwantar da kanta bisa hannun ta na murmushi, ta
yi bala'in kyau, kallo daya ta yiwa hoton ta dauke ido ta
mai dashi ga kallon hoton Faruk wanda duk da haduwar
nata, to na Faruk ya fi nata, a hoto kenan ma, amma a
zahiri Faruk ya fi haka ahďuwa don ita kanta ta san ya
yagawa Bashir nesa ba kusa ba a komai da komai, to
amma why da ta tsane shi? Har ta ke son kashe wannan
santalelen yaro haka?
Ba amsa sai kawai ta mike ta dauko horon ta nufi
hanyar fita, sai da ta kai karshen kofa sannan ta juyo ta
kalli dakin wanda kamshin dakin da kamshin jikin Faruk
iri daya ne, wato kamshi ne mai dadin shaka. Hoton ta
rike a kirjinta ta komo ta janyo kofar ta na rufewa, sai ga
Ibrahim ya shiga, ta ce cikin sauri "Ibrahim in zo ka
kaini?" Ya ce "A'a ni da abinda zan dauka in fita".
Ya shige dakin, ita kuma ta koma dakinta, ta sa
hoton gaba ta na ta kallo, zuciyarta a yanzu ta yi tankade
da rauraya duk bakin ilahirin son da takewa Bashir in ma
da kari to ya koma kan laruk don in banda tunanin irin
abinda ya faru a baya ba abinda take yi, anan ta fahimci
ce wa lallai Faruk ya na matsanancin sonta, to amma me
53
Kwadayı barава Аnиа Abdullalu Sharnda
ya dace ta yi in Allah ya abshi lafiya? Banda ma haka
so ta kamar da kuwa? Bare ya na ganin ga abinda
faru? To wannan amsar dai sai in Allah ya bashi laliyw tukunna ma gani.
Ya na kwance bisa gadon asibiti ya yi tagumi ya n
tunani, can ya daga kai ya dubi Mum da ke zaune gel
daya ta na jan carbi bayan ta idar ad sallar la'asar, gash
dai Mum da ba asalin musulma ba ce kirista ce,Alhaj
Gambo ya musuluntar da ita ya aureta sai gashi a yanzu
haka har ta fi wanda aka haifa cikin musuluncin riko da
addini a koda yaushe za a same ta tana faman lazımi ko
kuma yawan azumi, kamar an ranar litinin da alhamis.
Gashi ta san abubuwa da dama fiye da wani wandy
ya girma a musuluncin don ta na koya kuma ta na
bayarwa a sayo mata littattafan addini na turanci, gashi ta
na yawan sauraran laccar manyan Malamai irin su Shaik
Ahmad Didat da sauransu, shi yasa a kullum za ka ganta
cikin nutsuwa ga yawan ibada haka ma yaranta mazan da
matan suke.
"Mum!" laruk ya kirayi sunanta, ta amsa gami da
dago kai "laruk me ka ke so?" Ya ce "Ba komai Mum,
wai har yanzu Maryam ba ta zo asibitin nan ba?"
Mum ta ce "Ta zo kana bacci shi ne ta ce kar a
tashe ka". Ya girgiza kai "Ki yi hakuri Mum kar ki ce na
Karyata ki, amma na san Maryam ba zata zo wurina ba
ko da ace zan mutu, na san maryam ba ta so na Mum".
Ta yi murmushi "Ta na sonka mana ka san Maryam
yarinya ce mai tsananin kunya shi yasa ka ga bata nuna
maka a fili ba".
Shiru kawai ya yi don zuciyarsa ba ta taba amince
wa wai maryam ta na kaunarsa ba, "Mum bani ruwa mai
54
Kwadayı bar jana'- Amına Abdullahı Sharada
sanyi insha". Та се "To". Ta mika masa cup daya ya
shanye, sannan ta ce "Ga abincin in dan zubo maka maan
ka ci ko ya ya ne?" Ya ce "Na koshi Mum". Ta ce "Me
ka ci, za ka koshi? Ai gara ka ci ko ya ya ne?" Ba ta jira
ya sake magana ba ta bude kular abincin ta fara zuba
masa a plate sannan ta sanya cokali ta mika masa.
Ci kawai ya ke amma bakin babu dadi, ya dubi
Mum ya ce "Na koshi". Ta ce "Haba Faruk me ka ci
kenan cokali biyu fa ka yi? A'a ya kamata ka kara". Ya
ce "Ba na ci ba?" ta ce "To shikenan ajiye ai an samu da
da baka ci kuma fa?" Ya ajiye ya dauki ruwan ya kara,
sannan ya sha magani ya kwanta ya na tunanin abinda ke
faruwa, ya ga dai ana nuña masa kulawa ina ma ace
yadda ya ke samun kulawar nan haka zai samu kulawar
Maryam? Ai shi da ya zama dan gata a rayuwarshi, shi
kam yanzu ya gama sadakar cewa ba za ta taba sonsa ba,
to amma ya zuba ma ta ido sai abinda ta yi.
Maryam na zaune kallo daya zaka yi ma ta
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 4 Chapter of 12