Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 12
Ya ce "Mama wallahi na koma gidan ne sai na ji gidan babu dadi ni kadai shi ne na zo na tafi da ita" Suka kwashe da dariya sannan Hajıya Jamila ta ce "Sam ba inda za ta sai da dare kwa tafi". Ashe Alhaji Usaini ya na nan ya na jin abinda ake cewa sai ko ya fito ya ce da Bashir "Kai dauki matarka ku tafi, ma za wai ku Hajiya me ya sa ku ke irin wannan ne sai kace wasu yara? Tunda ya ce zai tafi da matarsa ai ba kwa haan ba, ina laifi da ya akwo ta ma? Ai kuna so nan gaba ya kara kawo ta tazo, ni ba an son rashin hankalı" Nan dai Bashir ya ja matarsa suka kama hanya. Hajiya Jamila ta cewa Halima "Ai dama na san in Alhaji ya na nan sai ya yi magaan kina gani ke mai mai ya hana Maryam zuwa garin nan duk haihuwar nan biyu da kika yi ta bai bari ta zo ba, wai ba ya so su sami sabani da mijinta". Halima ta ce "Aiko haka ya fi ma da ace kullum ana hanya kamar wasu bitalman ai zaman gidan mijinka ya fi maka komai a rayuwa". Nan dai suka yi ta hira har wani lokaci. 82 Kwadayı barıjana'- Amina Abdullahu Sharada *** Z ama ya yi matukar dadi tsakanin Maryam da laruk domin a yanzu soyayya ta ginu mai karfin gaske, a kullum sai zubawa juna so suke kara yi, ga cikin Maryam yaznu ya kara tsufa sai faman shagwaba ta ke zuba masa, shi kuma ya na ta faman aikin rarrashinta a kullum suna manne da juna a yanzu haka ma ba sa son ko fitowa falon Mum sabanin da da а kullum sai ta koresu, malana in Maryam ce ta zo sai ta yi faam da ita akan ta je ta kula da mijinta, sai dakyar ta ke -zuwa, to amma a yanzu sai kusan goma ake saukowa a gaida ita, don Daddy ma ba ya samun gaisuwar tunda shi da wuri ya ke fita. Yau ma suna manne da juna har kusan goma na safe basu ma fito ba bare su sauko a gaisa, ta na zaune a gefen gado yayinda shi kuma Faruk ya ke ta sharar bacci. Ta juya ta kara juyawa jikinta cikin rashin jin dadi, sai kawai ta mike domin ta je ta yi wanka, ta shiga bathroom din da ke falon ta yo wanka ta fito, ciwo ya sarketa a wurin, ciwon ma kuwa mai karfi, ai nan da nan ta durkushe ta na matagugu ta ma ka sa magana saboda zafin ciwo, ta fara kiran "Wayyo Allah Faruk! Wayyo zan mutu! Faruk ka taimake ni! Ka tashi zan mutu!" Cikin bacci ya ji kamar ana kiran sunansa, ya bude ido ya kasa kunne ai ko ya ji tabbas Maryam ce ke kiransa, ya ko diro daga gadon a rude ya na neman inda ta ke, ashe ma ta na gaban wardrop dinshi. Ta na murkususu, 83 t 1 C C S Kwadayıhan jana - Anuna Abdullahı Sharaри cikin saurı ya karasa ında ta ke ya na tambayar me ya sameta? Da kyar ta ce "Faruk ina jin haihuwa ce". Ya yi sauri ya kıra Mum, sannan ya koma Mum ta biyo bayansa ita ma suka taitayeta sai hospital nan da nan aka karbcta. bai fi minti ashirin da zuwansu ba sai ga wata nurse ta fito cikin fara'a baki daya suka mike suna tambayarta ya ya? Ta ce "Ai ta haihu lafiya danta namiji". Ai nan da nan suka fara murna, suna mika godiyarsu ga Allah, to dama shi Daddy ya an can office dinsa da ya ke asibitinsu aka kaita, nan da nan Mum ta tafi fada masa, shi kuma Faruk ya shige dakin da aka kai Maryam domin ta huta, ya sameta kwance da jaririnta a gabanta, dama sai da aka hada musu komai na haihuwa sannan aka shiga da ita. Sai gashi nan da nan sun gama gyarata kun san abu namu wato mahaifinsa shi ne babba a asibitin kowa ya riga ya san su don haak ba jira. Idonta a rufe ya sameta cikin dokin ganinta ya kira sunanta, ta bude a hankali ya ce "Ya jikin?" Ta ce "Ai na warke". Ya ce "To Allah ya karo sauki". Sannan ya dauki Babby ya na kallo, ya dubeta ya ce "Maryam tashi ki gani yaron nan da wa suka yi kama?" Ta ce "Da ni". Ya yi murmushi ya ce "Wallahi kuwa da ke yake kama domin kamar taku ma har ta yi yawa, kamar an tsaga kara". Ta yi murmushi ta ce "Amma dai ni ma ai kyakkyawa ce?" Ya ce "Sosai ma, ai wallahi Maryam duk gidanku babu mai kyan ki, inda kika san ba 'yar gidan ba don babu wanda kuka yi kama a gidan sai ka се Balarabiya, kin fi kama da Larabawa". Ta yi murmushi kawai, ta ce "Wannan kyau nawa ai baiwa ce daga Allah, ni ma sau da yawa ina wannan tunanin, na kan ce ni 84 Kwadayı barıjana!- Amına Abdullahı Sharada kadai Allah ya zabe ya yi min kyakkyawar sura a gidan". Ya yi murmushi ya ce "Ai ni Allah ya yiwa gata domin, ya yi ki ne don ni". Ta yi dariya marar fitar da sauti ta ce "Son kai kuma ya tashi ke nan?" Ya ce "Ai gaskiya ne...." Suna cikin wannan hirar ne su Mum suka shigo, suna ganinsu Faruk ya mike ya na cewa "Dad zo ka ga yaron kyakkyawa dashi kamar uwarsa". Mum ta ce "To marar kunya, ka kyale mu mu fada mana sai kai?" Ya sunkuyar da kanshi ya na sosa keya, daga nan sai ga su Zainab da Ibrahim sun shigho, suma suka karbi yaron su na yaba kyawunshi, nan dai aka yi ta hira har wani lokaci, sannan Alhaji Gambo ya ce su tafi gida baki daya, har mai jegon domin tunda lafiyaria kalau ba ta zauna ba, dama sun sanar amsa cewa za ta haihu da ba sai sunzo ba, sai ya tura musu likitocin har gida su karbi haihuwar acan gidan. Nan suka hada komatsansu sai gida, suna zuwa kuwa suka yi ta buga waya suna fadar haihuwar, tunda ga kan 'yan uwansu Mum har 'yan uwan Alhaji Gambon babu wanda basu sanarwa a ranar ba. Sameera na fama da laulayin ciki aka sanar mata haihuwar Maryam, ta dinga murna don za ta je suna, Bashir na dawowa ta sanar masa, ya ce ba zai yiwu ta je ba, ai nan da nan sai hawaye, don ta na son ta ga Mamanta, da 'yan uwanta amma ya ce wai ba zaat je ba, sai kawai ya ficce abinsa. Hakan shi ya sa ta shiga cikin tsananin 6acin rai, bai ma dawo gidan ba sai can dare don kar ta sake yi masa maganar, ya dawo ya lallabа уа kwanta ba ta sani ba, sai da safe sannan ta ganshi ya na shirin Kara fita. Ta tashi cikin sauri ta ce masa "Yaya Bashir ina 85 1 1 1 1 1 Kwadayı barijana Amina Abdullahı Staradа zaka kuma" Ya daure ma ta fuska ta ce "To ina da magana da kaı, amma ka jita ni inyı sallah tukunnan" Ya ce "Jeki ina jirankı" Ta je ta yı sallah ta idar sannan la komo ta sameshı a falon Bayan ta gaishe shi ne ta samu wun ta zauna ta dubeshı ido cikin ido ta ce masa "Y aya Bashir amma dai ina tunanın har yanzu baka hakura da Maryam ba?" Ya ce "Saboda me ki ke min wannan tambayar?" Та се "Ai wasu lokacin ne ta ke takenka suna nuna min hakan" Ya yi murmushi kawai, bai ce komai ba, ranta ya kara baci ta dubeshi ta ce masa "Yaya bashır ina so ka fada min gaskiyar abinda ke zuciyarka in har ka na kaunar maryam ka fada min, wallahi in har ka san baka so na Maryam ak ke so to ni na yi maka alkawani zan hakura domin bai kamata in dinga zama da abinda ba ya kaunata ba!" Cikin mamakin jin wannan magana mai kaam da saukar bindiga ya dago kai ya kalleta ido cikin ido ya ce "Samecra wai wacce irin magana ki ke fada min ne" Ta ce "Ai ga ra in san matsayina a wurinka, in ina da shi, in babu in san abinda na kama domin ba zan zauna ina shukar dusa ba". Ya ce cikin wani sabon mamakın "Waı Sameera shakkar kaunar da nake yi miki ki ke yi ne har yau?" Ta ce "Ai ba wai shakka ba ce, gani na yi in ba haka me zai sa ka ki barnina inje sunan Maryam?" Ya yi murmushi ya ce "Ashe wai dama duk wadannan maganganun saboda ban amince ki je suna Maryam ba ne?" Ta ce "Saboda haka ne". ya ce "To ki kwantar da hankalinki wallahi ba don komai na hanaki ba sai don ganin baki da lafiya, kuma wurin nan ba ma kasar nan ba ne shi ya sa". Ta ce "To in dai haak ne ai can inda zanin ma gida ne". Y ace "To in haka ne na ji ki 86 Kwadayı bar jana Amuna Abdullahu Sharada je ai ban san irın zargın da kıke yi min ba, ashe gani kı ke har yau ina son Maryam To ai ni tunda Allah ya dasa min sonki a rai na daina ko tunanin Maryam ma". Ta yi murmushin jin dadin maganarshi ta ce "Ai wallahi da ni na saka tsanar Maryam a rai na saboda kai amma yanzu na zare". Ya ce "Ai gara ki cire domin a yanzu ba wata a gabana sai ke Sameera!" Gidan Alhaji Usaini ana ta faman shirye-shiryen zuwa suna, haka ma gidan Alhaji hassan tuni Hajiya Rukayya ta kammala na ta shirin musamman Alhaji Gambo ya turo musu kudi ta account din Alhaji Usainı cewa su rage kudin jirgi. Bayan ya karbo ya ce "Ai wannan ya fi karfin ragewa sai dai a biya baki faya". Nan dai ya kaşa ya kaiwa Alhaji Hassan na shi kason, sannan suka shirya abinda zasu saya su tafi musu da shi domin tsaraba. Hajiya Jamila na zaune shirim a falo, sai ga Halima 'ta shigo ita ma ta zauna. Hajiya Jamila ta kalletą ta ce "Wai ke Dubu da 'ya'yan zaki tafi baki daya ne?" Tа се "To Aunty wa zan barwa? In har za'a dani ai ya zama dole in tafi da yarana". Ta ce "Lallai kam, wa ya ga yuya?" Ta ce "Ai ni ban ga yawansu ba ma, yaran uku en fa kacal?" ta ce "ai sai ki yi ta zuwa da su!" Ta mike ta shige cikin daki abinta ta bar lHalima nan zaune, to dama Halima ta saba da irin wannan halaye na Hajiya Jamila don haka ba ta damu ba, ya ci ace sun daidita a junansu, amma duk yawan shekarun nan har yau ba sa wani jituwa shi kansa Alhajin ya yi ya gaji kuma laifin na Hajiya Jamila ne ko kadan ba ta kaunar Halima da yaranta don dai kawai Alhajin ya na tsaye a gidansa en shi ya sa ake samun saukin lamarin. 87 Kwadayı han jana'- Amina Abdullahu Sharada Yau sauran kwana biyu ayi tafiyar Alhaji na dakinsa a zaune, wato Alhaji Usaini, lajiya Jamila n gefensa ta kawo masa abincin dare da ya ke ita ta y girkin, ya na ci ta na zaune suna hira, a hankali ta takul maganar tafiya domin ta haan ayi da Halima, ta dubi Alhaji ta ce "Alhaji Halima ba ta jin shawara". Ya се "Kamar ta me fa?" Ta ce "Wai dazu ne na ce ma ta dama ta hakura da tafiyar nan tunda babu inda za ta kai yaran nan shi ne ta ke ta faman gaigaya min maganganu har da su gore-goren haihuwa". Alhaji ya ce "To ke don em za ki ce ta hakura bayan ta na doki ta je?" ta ce "To ai gani nayi yanzu ba wai fata ake ba, wannan tafiyar Allah ya kiyaye a samu wani hadari akan hanya ka ga duk 'ya'yan aka kwashe aka tafi dasu ba a rage ko daya ba, ya kamata in za'a dinga tafiya in yaran mutum biyar ne ya debi biyu ya bar uku, to amma tunda ita babu inda za ta kai su ai sai ta hakura in yaso in mun dawo taje tunda zuwan ya zame ma ta dole!" Ya ce "Eh to maganarki kam akwai kamshin gaskiya kin san ita Halima ta faye taurin kai ina ta ke, kira min ita yanzu ma". Ta ce "To". Ta mike cikin doki ta nufi dakin Halima, ta na zuwa ta sameta ita da 'yan yaranta har sun kwanta ta ce "Ki zo inji Alhaji". "To". Ta се ma ta, ta taso yayinda ita kuma ta juya. Ta na shiga ta durkusa ta ce "Ga ni Alhaji". ya ce "Yauwa dama kiranki na yi in gaya miki wannan tafiya an fasata da ke, ki yi zamanki ki kula da yaranki tunda kin taba zuwa". Ta na jin abinda ya ce, ta yi sak, don ta san ba makircin kowa ba ne sai Hajiya Jamila, ba tare da ko musu ba ta ce "Shikenan Alhaji ai ka san ba na ketare umarninka, duk abinda ka ce inyi dai-dai ne". Ya ce 88 Awadyr bartjana!- Auna Abdullahı Sharada "Yauwa na gode mi ki Allah ya yi miki albarka". "Amin". Ta ce mishi, ta mike, ta ficce daga dakin, ta koma kan gado ta na ta faman tunanin abinda Hajiyа jamila ta ke ma ta, inda sabo ma ya ci ace ta saba. Tunda safe suke shiri domin tafiya suka gama shirinsu suna haramar tafiya, Auwal ya makalewa Alhaji Usaini, wai sai ya bi su, shi ko ya ce da Halima hado masa kayansa ma za mu tafi". nan da nan ta tashi cikin murna, ta san ko ba komai dole ran Haljiya Jamila ya sosu, ta ahdo masa kayansa a 'yar jakarsa ta mika wa Alhaji Usaini, ya karba ya ce musu "Ku muje". Tunda aka ce za'a tafi da Auwal Hajiya Jamila ta yi dif da ita, babu walwala har suka fila. Halima na musu adawo lafiya, Alhaji ne kawai mai amsawa, ya an yiwa Zainab wasa ya an cewa "Ko ke ma zaki ne?" Halima ta ce "Haba Alhaji ai sai su yi muku yawa". Murmushi ya yi ya ce da direba ya ja motar su je gidan Alhaji Hassan sannan su tafi tare. Can kuma bangaren masu jego ana ta shiryeshiryen suna da tarbar baki ko da ya ke sunan can ba irin na nan bane domin lamari ne na jajayen fata, to amma tunda lamarine na musulunci to an sami banbanci a wajen taron da wanda suka saba yi domin iyayen musulmai ne, suka rada sunan da ranar sunan ta zo, aka radawa yaro suna Abubakar Saddik, kowa sai sa masa albarka ya ke yi, nan aka yi ta shagali har dare. Kwanan su Hajiya Jamila biyar suka komo gida, aka bar Maryam da kyakkyawon jaririnta Saddik, suka rabu akan in ta yi arba'in zata zo ta ga gida. maryam ta yi ta murna domin rabonta da gida yau ku san shekararta guda da rabi kenan. Ita kuwa Sameera ba ta komo a 89 Kwadayı bari jana'- Amina Abdullahı Shara da wannan lokaci ba, don su Alhaji cewa suka yi ta zauna sai ta kara ganin gida ta koma, ran Bashir bai so ba, to amma haka ya hakura don jin kunyar iyayensa da har ya fara murna Alhaji Gambo ya ce ba za ta zauna ba, to sai kuma murna ta koma ciki, don Alhaji Hassan da Alhaji Usaini sun dage akan ya kyaleta sai ta gaam gaisawa da 'yan uwanta. Haka ya hakura ya kyaleta akan dole, don gani ya ke kamar ba a kular masa da ita ba, saboda cikin da ke jikinta har Hajiya Rukayya ya samu a gefe daya ya ce ma ta "Mama don Allah ki sa baki a bani Sameera mu tafi, kinga ba ta da lafiya, ciki gare ta a kullum sai faman amai ta ke yi". Hajiya Rukayya ta ce "Au sannu gwani, wato nan ba za'a iya kula da ita ba kenan ko? Sai kai wato uwarta ma da ta raine ta har ta girma har ka samu ka aura ka fi ta iya kula da ita ko?" Cikin jin kunya ya zame ya tsere ya na sosa keya. Tunda suka komo gida Bashir ya zamo tamkar wani maraya, don gidan sai ya yi masa fadi, hakika yanzu kam ya na bala'in kaunar Sameera don shi a yanzu ba ya ko son ya ga Maryam ko don yanzu muharramarsa ce? Oho! Da suka je suna ma ya yi mamakin abinda ta yi masa a da ya dauka zata kulashi kamar da, sai kawai ya ga ta wani dauke masa kai kamar ab ta san ma daga inda ya ke ba, Allah Sarki bai san irin yakin da Faruk ya sha ba kafin ya shawo kanta ta so shi ba, wannan zuwan ma sai da ya ji fargabar kar ta ganshi ta kara rikice masa, sai gashi abin mamaki duk abin da yake zato babu wanda ya samu sai ma wani tsana-tsana da take d'an nunawa Bashir din, to sun dai tafi kuma ya na zaune lafiya da matarsa da dansa Saddik tsakanin Sameera da Maryam kuwa sai wasa da dariya in sun haďu suna hira sai su kai sha biyun 90 Kwadayı barı jana!- Amına Abdullahı Sharada dare, Maryam ta na tambayarta game da gida, da ya ke bata samu damar zama sunyi hira da su Hajiya ba, har suka koma gida, amma ta ce ta na yin arba'in zata je ganin gida. Faruk ne zaune ya dauki jaririnta Saddik ya na masa wasa kamar wani mai wayo. Ita kuma Maryam na can gefe daya ta an kishingide ta nai masa hira, wata ya amsa, wata kuma ba ya ji, hankalinsa na wajen Saddik har dai Maryam ta gaji ta ce "Ni ko Faruk ina tsoron ranar da zanyi magana ka ki dauka Saddik ya yi ka karba". Ya juyo ya kalleta ya ce "Kamar ya ya?" Та се "To gani na yi ko hira na ke ma ka baka saurarona in azaton dai wala rana ma sai na yi kamun kafa da Saddik sannan zan tambayi abu a wurinka". Ya yi dariya "Ke kuma kina kishin haka ko?" Та сс "A'a ba kishi na ke ba". Ya ce "Kishi ne mana, lallai ma Maryam to kina kishin dan ki ina ga kuma in karo aure?" Ta yi saurin mikewa zaune "Aure Faruk?" Ya ce "A'a to haramun ne?" ta ce "A'a, ba zancen wasa ba da gaske aure zaka yo?" Ya ce "In Allah ya kaddara ai sai inyin...." "Kaikai-kai don Allah daina fada kar 'yan amin su amsa, wallahi ka fadar min da gaba, a gaskiya yau ban san irin baccin da zanyi ba". Ya ce "Bare kuma ace yau ga shi na yo ta ba?" Ta ce "to ka yo mana har da wani nanatawa, wallahi ta na shigowa ni kuma ina barin gidan". Ya се cikin dariya "Ina zaki je?" Ta ce "In koma inda na fito mana". Ya yi murmushi "Ina ne inda kika fito?" "Oho!" Ta ce mishi cikin nuna alamar fushi, ya kuwa kwashe da dariya ya ce "Kinga hakan da kika yi har kin tuna min wani wasa da na gani a can nigeria na su dan ibro wai sai abokin tafiyar tasa suna cikin tafiya su biyu 91 ya ce Kwadayı han jana'- Amına Abdullahı Sharada "yanzu dai muna cikin tafiyar nan mu tsinci kudi". Sai ibro ya ce "Da sai mu raba". Dayan ya ce "Ai anwa sai ya fi naak yawa". sai kuwa Ibro ya ce "Don me naka zai fi nawa ba tare muka tsinta ba?" Ya ce "Aiko ba za'a raba dai-dai ba." Nan fa fada ya sarke har da kwabe riga aka fara dakuwa tun kafin a tsinci kudin, to yau sai kike gwada min". Maryam ta yi ta dariya ta ce "Ai su su Ibro nasu mai sauki ne ni fa kishiya ka ce? Tabdijan Allah ya tsare ni da ita". Ya ce "To wai saboda me ba kya son ayo miki kishiya ne?" ta ce "Saboda na fi son in mallakeka ni kadai ba na son mu dinga musayarka da wata". yayi dariya "To ni kuma in na gano wata ina so fa?" Ta cе "yanzu saboda Allah duk kyautata ma kan da nake yi har sha'awar aure ka ke yi?" Ya ce "No wannan daban, kin san sunna ce kuma wata rana zan zamo mai sha'awar yin hakan don haka na ke so ki saba da zancen tun kafin lokacin ya zo". Ta ce "lallai faruk ni dai to ba na son zancen". Ya ce "To an daina shikenan?" Ta yi murmushi ya ce "Wai ni Faruk na ga tasku a da lallai so so wani abu ne, duk irin kayar nan da ki ka dinga yi min ba na gani". Ta ce "to me kuma ya akwo wannan zancen?" Ya ce "Tuna baya!" Ta ce "Ka fara ba? Ni ka ga ma baccina zanyi". ya ce "ai wallahi ba ki isa ba, sai kin tashi mun yi hirar". ta ce "To wai ba ka rama ba? To kuma me ka ke so ayi?" Ya ce "Bai ramu ba". Ta ce "Kamar ya ya bai ramu ba?" Ya ce "Wancan karon kin sa mun samu Saddik ba ta hanyar nutsuwa ba, to wannan karon zamu samu kaninsa ta cikin nutsuwa". Ta na jin ya fadi haka ta yi saurin mikewa tsaye ta na cewa "Faruk yau fa kwanana talatin da biyu, amma ka ke min wannan batu?" Ya janyo 92 Kwadayı ban jana!- Amına Abdullahı Sharada hannunta ya ce "Ina zaki je?" Ta ce "Ni dai cikani?" Ya ce "to ai a dakinki muke, ina kuma za ki?" Tа се "Ка cika ni mana ka ga inda za ni?" ya ce "Na ki, wayon ki gudu ne". ya janyo ta jikinsa ta na kokarin kwacewa ya maida bakinsa a nata, shikenan sai jikin ya mutu ab ta san lokacin ad shaukin so da kauna ya sa ta mai da masa martani ba. Sameera kam sai da ta samu cikakkun wata biyu sannan ta koma, shi ma din Bashir ne ya daemsu da waya gashi dai ba zai iya cewa ya na so ta komo ba, to amma fa sai faman kiransu ya ke a waya yau in ya kira wannan, gobe sai ya kira wancan har dai Dad ya gaji ya če da Mum "Wannan yaron Bashir na san fa abinda ya ke yiwa yawan waya, so ya ek matarsa ta koma, saboda haka a wannan satin za ta tafi". Mum ta ce "Ni ma ina da niyyar gaya maka haka, ai gara ta koma gidan ai ta zaunu". Ya ce "Yauwa ai gara ta koma yanzu me za'a shirya mata na komawa?" ta ce "Ba abinda zata tafi da shi sai dai a tura musu kudi a banki kawai". Ya ce "to shikenan". Kwana uku da wannan maganar sai kawai suka fara hadawa sameera kayan ta, don kashe gari za ta wuce, haka ko aka yi da ranar ta zo, suka sa ta a jirgi sai nigeria Bashir na gida a zaune bai fita ko ina ba, ya ji sallamar Sameera cikin mamaki ya ce "Yaushe kika zo?" Ta ce "Saukar kenan". ya ce "Wa ye ya dauko ki daga airport?" Ta ce "Motar haya na hawo". Ya ce "To me ya sa ba ki yo min waya ba?" Ta ce "To ai ban san uzurin da ke gabanka ba shi yasa ya ce karka kara yin irin wannan". "Ai ko ni baki yo min ba sai kijewa su Abba dasu Abban gidan su Maryam". Ta ce "To ni dai wallahi 93 win ha LAAitalu Sharnf ban kira kowa" Ya ce "To ya su Mum da Uncle?" Ta "Suna nan lafiya, ka san kuwa Dad ne ya ce lallai in t bo Ya ce "Aı ya kyauta kına can kin barni da kewarki Ta ce "Dama ai sarda na ayyana". Ya ce "Yanzu ke da basu ce ki taho ba, ba zaki taho ba kenan ko?" Tа y murmushi "Haba Bashir mahaifa fa aka ce ma?" Ya ce "A'a lallai, ai ko baki fada ba na sani" Tayi murmushi "Ashe na mance na bar dan tasi da kaya a mota, zo muje ka taya ni daukowa". Ya ce "A ina mai gadi, baya nan ne?" Ta ce "Ban ganshi ba". Ya ce "To muje Haruna mai wanki na san shi ya na nan don yanzun nan ya gama guga". Nan dai duk ta yi wa su Hajiya Jamila waya a komo da su Hajiya Rukayya, wato mahaifiyar Bashir kenan, sannan shi kuma ya sanarwa su Abbansu, nan dai suka yi ta bugowa sunai mata sannu da zuwa, kuma ta yi wa can gidan nasu waya cewa ta sauka lafiya, ta samu kowa lafiya Bayan kamar wata guda da dawowar Sameсrа Maryam ta yo waya cewa ita ma ga ta nan zuwa, nan aka yı ta shurin taryar ta, cikin doki da murna. Kwana biyu kuwa da yin wannan maganar sai ga shi ta yo waya cewa ta iso, ta kuma bukaci Abba ya aika a dauko ta, dai-dai misalin hudu na yamma Abba ya amsa mata da to. Lokacin na cika da kansa ya tafi daukota ya ko yi sa'a saukarsu ke nan taan hango shi ta rugo da gudu tana murnar ganinsa, ya amshi jinjirin ya rungume ya na faman murna har dai wani lokaci sannan ya dauki kayan nasu ya sanya a boot suka taho gida suna ta faman murna da farin ciki. 94 Kwadayı barı jana!- Amına Abdullahı Sharada hannunta ya ce "Ina zaki je?" Ta ce "Ni dai cikani?" Ya ce "to ai a dakinki muke, ina kuma za ki?" Ta се "Ка cika ni mana ka ga inda za ni?" ya ce "Na ki, wayon ki gudu ne". ya janyo ta jikinsa ta na kokarin kwacewa ya maida bakinsa a nata, shikenan sai jikin ya mutu ab ta san lokacin ad shaukin so da kauna ya sa ta mai da masa martani ba. Sameera kam sai da ta samu cikakkun wata biyu sannan ta koma, shi ma din Bashir ne ya daemsu da waya gashi dai ba zai iya cewa ya na so ta komo ba, to amma fa sai

Chapter 7 of 12