Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 12
ba na son ka kuma janyo wani rikici a tsakaninku, ka ga zaman aure zaam ne na din-din din, ba wai yau azo gobe a koma ba, dama ina so in same ka in yi maka wannan nasihar na ga dukkanku babu wanda ya ke daukar abinda muhimmanci, na fuskanci akwai wani abu da ya ke faruwa a tsakaninku. 68 Kwadayı barıjana!- Amina Abdullalu Sharadn Faruk kai ne babba, kai ne mai hankali kar ka dakata tata ka biye ma ta ku zo kuna zaman doya da manja, kai ak kawo don haka kai hakuri ya kaam dole ne ka dinga hakuri da abinda zaka gani, don samun ci gabanka, ka ga yanzu nan gaba za ka fara samun yara in har kuna irin wannan a tsakanínku za ku dinga raba kawunnan yaranku, kuma in har kuna da mace a ciki ta na girma ta na ganin abinda ya ke faruwa, za ta dinga koya ita ma ta na yiwa mijinıta. Ka ga babu ci gaba kenan? Kuma babu tarbiya saboda haka ba don komai ake son zaman lafiya da kwanciyar hankali magıdanta ba sai don kar su barwa aransu abin gadon abin fada, domin muddin suna irin wannan to tarbiyar yaransu za ta yi fata-fata har mazan ma don shi da namiji abinda ya ga mahaifinsa na yiwa ta sa nmahaifiyar haka zai yiwa matarsa kamar yadda 'ya mace za ta kwaikwayi halayyar mahaifiyarta ta dinga yiwa na ta mijin. Ka ga ba ki dayansu tarbiyarsu ta lalace kenan?" Cikin sanyin jiki ya ce "Na ji abinda ki ka ce Mum, kuma na gamsu na gode Allah ya saka muku da gidan Aljanna Firdausi". Ta coe "Amin summa amin". Daga nan ya mike ya tafi can ya samu Maryam ta gama aman ta komo falo, ta na kwanc'e ta sa hannunta ta kare fuskarta idonta a lumshe, ya tsay a a gabanat cikin sanyin murya ya ce "Maryam me ya k damunki ne?" Ji ta yi maganar kamar a mafarki, ta yi saurin bude ido ta kalleshi ta ce "Ai ni babu abinda ya ke damuna". Ya ce "Amma na ga kina amai?" Ta na jin haka ta yi murm ushi kawai ta ce ma sa "Dama na saba ai kullum ne wan nan aman". Ya се "То me ya sa ba ki sanar min ba?" Tia ce "Yaya ga ni na yi 69 Kwadayı barı jana!- Amına Abdullahi Sharada kamar baka so in yi maka magana shi yasa ni kuma na ka sa gaya maka domin gani na ke in na gaya maka ba zaka dauki abinda muhimmanci ba". Ya ce "Saboda me? Ai ya zama dole a matsayina na mai gidanki in saurari uzurinki, kuma in jibanci lamarinki". Ta yi murmushi "Dama ba wani abu ne ya ke damuna ba wallahi sai....." Shiru ta yi ta ka sa fada, shi kuma ya na jin haka sai kawai ya yi shiru ya na kallonta, don ya san kunya ce ta dameta, a zuciyarsa ya na godewa Allah don a yanzu ya san cewa Maryam ta na kaunarsa kuma ta yi zurfi, kallonta ya yi bayan ya matso kusa da ita ya janyota jikinsa gami da runguma ya ce "Bara in duba ajiyata ko ita ce ta janyo wannan amaye-amayen?" Hannu ta sa ta rufe fuskarta cikin jin kunya ta na murmushi yayinda yanayin kamshin jikinsa ya kara am ta sonshi, hannu ya sa ya fara shafa cikinta, ya ji shi da dan tudu kamar ta kifa karamin koko, ya yi murmushi ya ce "Amma Maryam ba ki kyauta min ba". Ta yi saurin kallonsa a shagwabe ta ce "Me kuma na yi'?" Ya ce "Saboda me zaki samu ciki amma ba zaki sanar min ba? ki yi ta amn dakonsa ke kadai gashi har ya girma". Kanta ta boye a kirjinsa sannan ta ce "Kai yakamata ka fara bincikensa domin dai ka san da kunya in sanar ma ka". Ya ce "To me ye abin kunyar? Wallahi duk ke ki ka janyo mana gashi shi kansa cikin ba a cikin nutsuwa a ka sameshi ba, ni kaina ban zaci akwai shi ba". Та се "То ai yanzu komai ya yi dai-dai sai ayi min afuwa". Ya ce doki "Da gaske Maryam kina kaunata?" Ta lumshe manyan fararen idonta ta ce "Ina kaunarka Yaya, ai da ni na so in bar jaki in doki taki, a yanzu ne na san cewa na yi sa'ar miji, ga hakuri, ga kyau, ga... Kai ka 70 Kwadayı barnıjana!- Anına Abdullalu Sharada hada komai da komai ma wallahi!" Ya ce "Kai amma ba na tunanin na taba samun sa'ar da ta kai ta yau a rayuwata ba, lallai kam an godewa Allah Maryam ina kaunarki wallahi kaunarki ce ta kusa hallakani, to amma na godewa Allah da ya akwo mu lokacin da har ke ki ke furta min kalmar so da bakinki". Saukar numfashinta a dai-dai fuskarsa shi ya kara rudashi da kidimashi har ya fara kidima ya na sakin layi, ta na ganin haka ta fara bayyanar masa wasu abubuwa da zasu kara jan hankalinsa, ai ko nan da nan ta hargitsa shi, rude suka koma bedroom dinsa, daga nan suke rufe kofa, sauran bayanan kuma sirrine. a *** A l'amarin gidan Yalwa mahaifiyar Halima kuwa, yanzu abin sai dai ayi addu'a, gashi dai Yalwa ta saduda to amma ta rasa yadda zata bullowa yaranta su koma kan hanya, ga tsufa ya kamata har shi Malam Usman shi ma dai ya kara tsufa sosai, don har ta kai baya zuwa ko ina sai masallaci, amma abin Allah da bakinsa da idonsa da kuma kunnensa, kafa ce kawai ke bashi matsala domin baya iya tafiya mai nisa, haka ma Yalwa ta ke fama da kafa ita ma, amma ita tana tafiya ko ina nan mako ta da nan cikin unguwa duk tana zuwa. Kuma IHalima ta na iya kokarinta wajen taimaka musu don daga kan abinci har wajen abin sawa suna samu. Alhaji Usaini ya na taimaka musu domin ita Halima ba ta sana'ar komai kullum ta na gida, gashi yanzu haihuwarta uku a gidan wato Auwal sai 71 S Kwadayı barıjana'- Amuna Abdullahu Sharada Kamaluddin wanda suke kira da kamal sai kuma macen mai sunan Baba Abu wato Zainab ake kiranta da Shahida, shi yasa yanzu Halıma ta zama 'yar gaban goshin Alhaji Usaini, kuma game da Alhaji Hassan ya kama yaran nan ya rike sosai, ya na matukar son su domin 'ya'yan dan uwansa ne na hakika a kullum da abinda zai sayowa yaran nan koma ya dauki Auwal ya yi kwanaki a gidansa, tarkacen kayan wasansa da ya ke kawowa yaransa ma ga wasu dunkunan da yake musu na musamma. A takaice dai sun dawo tamkar da, shi da ma Maryam ce baya so don haka aka samu sabani, to a yanzu haka zumuncinsu ya fi na da ma domin suna matukar son junansu. Yau Alhaji ya komo daga kasuwa ya wuce kai tsaye dakin Halima don itace da girki, a lokacin su Auwal da Kamal sun tafi makaranta. Bashir ne mai dauko su kullum ko shi ko direba, to direban suna tare da Alhajin don haka sai shi zai dauko su, ya na shiga dakin ya sameta ta na ta faman kuka, yarinyarta Zainab na kwance kusa da ita. Ganin haka ya yi saurin shiga ya na tambayarta "Lafiya? Me ya same ki?" Ta yi shiru ba ta ce ma sa komai ba, ya zauna gefen gadon ya ce ma ta "Na fuskanci tun lokacin da ki ka je gidanku kika dawo ban sake ganin walwalarki ba, ina so ki sanar min me ya ke faruwa?" Shiru ba ta ce komai ba, ya sake tambayarta "Wai me ya ke faruwa ne?" Ta yi shiru don ita bata so ya sameta ta na kukan ba, ba ta so ya san halin da suke ciki, ba ta son zancen duniya baya buya ba, shi tuni ya san cewa an kaam su Auwalu babba, wato dan gidan Yalwa kaninta, da Lawan sun karyawa wani mai shago kofar kanti sun debar masa 72 Kwadayı barı jana Amına Abdullalu Sharada kaya za su gudu aka kaamsu, bayan dan karamın duka da suka ci aka kai su police-station sannan kwana bıyu aka mika su kotu aka yanke musu hukuncın dauri na wata bıyar da tara ta dubu ashirin Ya gyara zama bayan ya yi wannan tunanin ya ce "Halima ki fada min abında ya ke damunki, kin san bana son ganinki cikin wannan bakin cikin, kuma ma to in ba kı fada min me ya ke damunki ba wa za ki fadawa? kin san dai ba ki da wanda ya fi ni inba iyayenki ba ko?" Cikin kuka ta dago kai ta ce "Suma din ai basu fi ka ba, don kai muke tare yanzu". Ya ce "To wai me ya ke faruwa ne?" Ta ce "wallahi idan na tuna al'amarin gidanmu wato gidan Yalwa sai inji komai ya sauya min, wallahi na rasa jin addi. Alhaji duk 'yan uwa sun kewaye mana tsinke babu sauran mai Kaunarmu sai Baba Abu saboda halayyar yarannan gashi yanzu ma su na daure ga su Yalwa ba sa samun abinci sai dai wai yalwa ta yi bara in wasu sun ba ta wasu su hanata wannan abin ne ya ke ba ni haushi wallahi, ya ke sa ni bakin ciki da ace ni namiji ce da ba abinda za su yi zan dinga nemowa ina kai musu". Ya ce "Kar ki damu in don abinda za su ci ne, to ni zan yi kokari inga ina basu har ma da suturar da zasu daura don ina ga in har na dauke musu wannan abin zai komo da sauki ko?" Ta ce "A'a ai shikenan dama ni iya abinda ya ke damuna kenan, tunda ni ba wani kudi gare ni ba da zan dinga yi musu ba". Ya ce "Ki bar wannan zance ai ya wuce". To wannan shi ne abinda ya faru da Halima har ya zama Alhaji Usaini ya na taimakonsu don Halima ta zama wani bangare na jikinsa, 'ya'ya har uku wasa ne? maza biyu mace daya ai an zama daya ko? Kuma alakar 73 a 7 1 S Kwadayı barijana'- Amumn Abdullalu Sharadи yaran nan ta sa ya na matukar son Halima ita kanta Ilapya Jamila ta yi ta gaji ta kyale su, amma sam ba ta kaunar zaman Ifalima a gidan, Halima har cewa ta yi in ta yaye Zainab za ta bata ita ta rike tunda ita ta aurar da lata 'yar har yanzun ta ba ta san cewa Maryam ba 'yarta ba ce, kai wannan fa-shine hautsini, ku dai kar ku gaji ku biyo ni ku ji me zai faru akan Maryam nan gaba kadan? Asabe ce aka zo gida, amma wannan karon duk ta bi ta rame duk da man da ta ke faman shafawa na bleachingbai sa ta tayi hasken sosai ba, don duk ta yi baki sosai ta na shigowa da kayan akwatinta aka ta sami Yalwa a zaune ta na korar kaji ta shanya waken da lalima ta kawo ma ta, ta barshi ya an leda har ya fara kwari, ta na ganin Asabe ta mike cikin murna ta na cewa "Asabe daga ina?" Ta ce "Wallahi Yalwa daag Legos na ke, ai na dawo gida gaba daya". Cikin tsananin murna Yalwa ta ce "Kai amma na godewa Allah da ya kawo mu wannan lokaci da na ga nutsuwarki tun kafin in mutu yadda ki ka shiryu Allah ya sa 'yan uwan naki su ma su shiryu haka". Ta ce "Yauwa". Yalwa ta kai jakar daki sannan ta koma wurin Yalwan ta zauna ta dube ta "Yalwa aure zanyi!" Cikin doki ta kalleta "Haba dai 'yan nan, kin samu wanda za ki aura din ne?" Ta ce "A'a ban samu ba, amma dai na san zan samu insha Allahu, an zo da kudi da yawa ina so insa Malamai su kawo min mijin da zan aura ta hanyar rokon Allah ina son mutum mai hankali nutsattse". Ta се "То Allah ya kawo, je ki ki sanarwa Babanki ya na ciki". Ta ce "To". Ta shiga dakin Malam Usman ta sameshi kwance ta gaishe da shi, sannan ta ce ma sa "Baba na zo na sanar 74 Awadayı harijana Aına Ahdullalu Sharada maka na komo gıda bakı daya, aure zanyi". Ya ce "To madallah kai amma na ji dadin wannan lamari Allah ya kara shurya ku amın". Ita ma ta amsa, sannan ta tashi. Yau kusan watan Asabe biyu da komowa gida, don haak ta na ta faman zuwa wurin Malamai wai ta samu mijin aure, suna ta faman ba ta maganin farin jini da kwarjini a haka har ta dace mutane su na yi mata magana har ma wasu su na tambayarta ko ta na da bukatar yin aure, daga cikin masu zuwa wurinta akwai wani mutum magidanci ne mai suna Alhajı Rabi'u, matansa uku, 'ya'ya goma sha biyar har na goye ya an da hali dai-dai gwargwado domin ya na da gidan sa tafkeke da motarsa da kuma sana'arsa ta kasuwanci, shi ne ya ce ya na son ya auri Asabe, to kasan zancen duniya ba ya boyu don haka sai aka samu wasu munafukai suka je suka sanarwa Iyalinsa cewa zai auri wata cikakkiyar kasuwa wacce ba ta dade da komowa daag yawon banzan ta ba, gashi gidan su ba tarbiya Yayarta ma sai da ta haihu a gida ta yi aure, 'yan uwanta duk 6arayi ne gasu 'yan daba, mashaya, don haka su saurari daukar mataki akai, kar a shigo musu da masifa. Suna jin wannan magaanr hankalinsu ya yi matukar tashi suka rasa ya zasu bullowa zancen sai uwargidan ta oc musu "Yanzu abinda ya kamata muyi shi ne mu kyale shi sai in ya zo mana da maganar sannan mu san abinda zamu sanar masa, amma yanzu in munyi ma sa maganar zai iya dauka wani matakin akan mu, ko dai ya sanar da iyayenmu, ko kuma ya bullo da wani abin daban". Suka ce "Eh, haak ne ya yi wannan shawarar da ki ka yanke ta yi". Kwanci atshi magaanr aure ta mika tsakanin Alhaji 75 Kwadayı barı jana'- Amına Abdullalu Sharada Rabi'u da Asabe har ma ya kai komai, an sa rana, ana maganar daurin aure, ya tara iyalansa wato matansa ranar wata juma'a da dare ya ce musu "Ni fa aure na ek son yi". Suka ce "Kai amma muna yi ma ka murna a ina ne?" Ya kwatanta musu Asabe, suka tabbatar ita ce wacce aka kawo musu tseguminta, sai suka ce "Munji mun amince, to amma muna ba ka shawara a matsayinmu an wadanda suka zama daya kafin ka yi wannan auren ka fara zuwa a gwada jinku, don kar ka ce ita kadai ta je ta ha'ince ka, sai kuyi tare in an gwada ka ga sakamako mai kyau ne to shikenan sai ka komo ka yi binciken tarbiyya in ko ba a dace da sakamako mai kyau ba sai ka kyaleta ka samu wata mu ba ma bakin ciki da aurenka don Karuwa се babu wanda zai ce ba ya son karuwa", Inji Uwargidan don ita ta ke bayanin "Ka ga duk gidannan akan idona aka tarasu kuma ga su sun yadu munyi yawa, ina jin dadin zama da su ta wajen wannan ma ga shi har sun tara zuri'a a gidan mu ya kara yawa, to amma ka ga a loakcin da ka auro su zamani bai rikice kamar yanzu ba, amma in ka ga wannan shawarar ba ta yi ma ka ba zaka iya canzawa". Ya nisa ya ce "Kunyi gaskiya domin yanzu lokacin nan na yanzu sai da bincike kuma insha Allahu gobe zamu je a dauki jininmu da ita baki daya, kinga a san me ye abin yi in an same ta da wani abu in kuma ta na lafiyа shikenan sai ayi kawai". Ta ce "Yauwa Alhaji haka ya kamata ayin". Kashe gari tunda safe ya yiwa wani mutum Likita abokinsa waya cewa yau zai zo oflice dinsa ya na son ya dauki jininsu shi da Amaryar da zai aura, ya ce to shikenan ya na saurarensu. 76 Kwadayı barıjana!- Amina Abdullahi Sharada Gidansu Asabe ya wuce kai tsaye ya sameta ya ce ta shirya za su unguwa, ta ce "To". Ba wani musu, ta shirya tsaf ya dauke ta sai wannan asibiti. Bayan sun isa office din ne ya karbesu hannu bibiyu, dama shi aikinshi ke nan daukar jinin masu cutar kanjamau din. Bayan wani dan dogon bayani aka fahimtar da Asabe abinda ake son yi, ta kuma amince har aka gama gwajin. Suna zaune to fa ai wurin fidda sakamako nan aka sha banban domin shi Alhaji Rabi'u jinsa garau ya ke, ita ko Asabe an sameta da kwayar cutar har ma ta fi ta daga matsayin H.I.B ta koma S wato Aids, abin ba karamin razana Alhaji Rabi'u ya yi ba, ita ko ma Asabe ai sai kawai ta sulale kasa ta fadi, sai wani daddan farin ciki ya kama, ya ringa murna, don a ganinsa Uwargidansa ec ta janyo masa wannan lamari da yanzu ya janyo musu bala'i har wani doki ya ke ya je ya samesu ya sanar da su kudin mota ya baiwa likitan ya ce ya ajiyewa Asabe, in ta farka ya bata shi ya yi gaba. Ya cc "To ya za'ayi haka?" "Ka san dai ni yanzu ba abinda zai sa in aure ta, to me kuma zan jira inyi ma ta? Kai na tafi kawai, in ta farka ta ga bana nan ai ba sai na tsaya dogon bayani ba ta san na fasa". Kawai murmushi Likitan ya yi ya ce "To ai shikenan na ji". Ya na zuwa gida ya tara matansa baki daya ya sanar musu abinda ya faru, kuma ya gode wa Uwargidansa da ta zamo silar gano wannan abu, da yanzu ya zuba musu alakakai, da yanzu ya zamo saandin gano wannan abu. Ta сe "To Alhaji ai ka zama ni na zama kai in har wani abu zai faru yakamata mu bincika ko a boye ne kuma mu sanar ma ka ba tare da hankali ya tashi ba". Ya ce "Ai ke dai na gode Allah ya bar maan ke amin". 77 Kwadayı barıjana!- Amına Abdullahı Sharada Bayan Asabe ta farka ta fara zunduma ihu ta na kukan bakin ciki. Zuciyarta cike da tsananin tarin nadama mai yawan gaske ta mike ko sallama ba ta yiwa Likitan ba ta ficce ta samu dan acaba ta ſada masa inda zai kai ta, wato unguwarsu bai yi birki ba sai kofar gidan, ya na tsayawa ta sauka ta shiga gida ta karbo ma sa kudinsa ta bashi. Ku duba ku ga yadda Asabe ta ke bala'in son kudi wanda hakan ne ya kai ta ga halaka KWADAYI YA JA TA! Ta afka cikin gurbatacciyar rayuwa, gashi yanzu lokaci daya kudin sun fita daga ran ta sakamakon tiket din da ta ke ganin ta yanka na tafiya lahira wato aids, sai kawai ta barwa Likitan kudin da Alhaji Rabi'u ya bāta don ta hau mota, abin mamaki sai gashi ta shiga wurin Yalwa ta na kuka, ta na kiran "Yalwa kin cuce ni kin janyo min bala'i, yanzu ya zanyi da raina?" Yalwa ta ce "Me ya faru Asabe?" Та се "Kе сe kika turamu a wannan amsifar ba kince mu nemo miki kudi ko ta halin ya ya ba? Gashi nan yanzu na je na dauko cutar da za ta kai ni kushewa!" Cikin tsananin kidima Yalwa na kwance ta mike ta na cewa "Asabe me ya sameki?" Cikin jin dacin maganar ta yi shiru, can ta се "Ва 'zan fada din ba, ai ke ce ki ka janyo min duk halin da na shiga ciki wallahi fadanki bai amfana mana komai ba, sai wahala, yanzu ga shi kannanmu sun zama 'yan daba, duk don sakacinki ga tarbiyarsu, yanzu gashi na zaam abin tausayi, karshe zan mutu ba wan ba kanin, ni dai na shiga uku! Wallahi ban san yadda zan tubarwa ubangijina bisa wannan sabawa da na yi ma sa ba!" Ta kuma fashewa da kuka, tana cikin wannan maganganun 78 Kwadayı banjana!- Amına Abdullahı Sharada ne Babansu wato Malam Usman ya leko ya ce "%o nan Asabe". Ta ce "To Baba". Ta je ta zauna ta ce "Ga ni". Ya ce "Kar in kara jin kin gayawa Yalwa wannan maganar don mahaifiyarki ce, duk abinda ta yi don kanta amma in kina irin wannan zа ki kara dorawa kanki wani bala'in, saboda haka ki guji kona ma ta rai, kuam duk abinda ya samu bawa kaddara ce, laifinki daya da kika biyewa son zuciyarki KWADAYI YA JA KI ki ka botsarewa mahaliccinki, ai ko shaidan ma ana neman tsari da shi a wurin Allah ba re mutum don haak kar ki kara ga ya ma ta wata magana domin ke ma kina da laifi. `Kuma na ji kina cewa wai ya za.ki yi ki tuba, to babu maganar ya zaki yi don duk mutumin da ya ke da wani laifi babu wanda ya canenci ya dosa sai Allah, shi ne mai yafiya yanzu tunda kin gane gaskiya sai ki yi istigifari har Allah ya gafarta miki, kuma mai halayya irin taki ma ya ci ace sun tuba tunda wuri tun kafin Allah ya kama su, domin ko wannan masifar da kika daukarwa kanki ta ciwon nan ita ma kadai wani sakamakon abinda ki ka yiwa Allah ne, don ba ta inda ba ya kama bawansa, kinga ita 'yar uwarki Halima ta huta ta na gidan mijinta haihuwarta ta uku kenan, ta na zamanta lafiya, ga shi ko da yaushe sai sa ma ta albarka na ke yi". Ta ce "Ai ni ma sai ka sa mun albarkar Baba". Ya yi murmushi ya ce "Ai ya zama dole domin in hannunka ya rube babu yadda zaka yi ka yanke ka yar, saboda haka ke ma Allah ya sa miki albarka". Та се "Amin Baba, ai ni yanzu sai dai addu'a domin ni tawa kuma ta kare". Ya ce "Wai me ya same ki?" Ta ce "wani ciwo ne da ni wanda ake dauka ta hanyar yawon banza, 79 ku na Li za ya ku ba K ra ta la A g .. Kwadayı harijana'- Amina Abdullahu Sharada ko mijı ya daukowa matarsa ko mata ta daukowa mijinta shi ne na samu, to na san wannan ciwon ba warkewa zanyi ba shi yasa na ce tawa ta kare! Ka ga shima Alhaji Rabi'u da ya san ina da ciwon ai ya gudu ya fasa auran nawa". Ya ce "To aynzu ya za'ayi ke nan?" Ta ce "sai hakuri, sai kuma jiran lokaci". Ya ce "To Allah ya yi mana da kyau". Ta ce "Amin". Sannan ya ci gaba da yı ma ta fada akan maganar kar ta sake yiwa Yalwa rashin kunya domin mahaifiyarta ce, ya kamata ace ta dauki mahaifiyarta da muhimmanci, ta ce "Na ji Baba insha Allahu na amince". Ya ce "Shikenan na ji tashi ki je, Allah ya kyauta". Ta ce "Amin". d ti k C S *** A l'amarin Bashir da Sameera kuwa yanzu soyayya ta yi nisa, har ma sun zama tamkar dama can sun saba da junansu, yanzu dai Samecra an samu abinda ake so don kuwa Bashir ya gama mutuwa akanta, ko gida ya je su na magana ba shi da wata magana sai ta Sameera, ran iyayensu ya yi matukar dadi sosai. Yau ma Bashir ne ya dauki Sameera zuwa can gidan Alhaji Usaini ta gaishe shi, sannan ya kai ta can gidansu wurin Hajiya Rukayya, bayan sun isa ne aka tarbe su da murna Hajiya Jamila na cewa "A'a yau Amare ne a gidan namu?" Ta yi murmushi ta ce "Mama ya na ganki ke kadai? Ina Aunty Halima?" Ta ce "Ta na ciki yanzu za ta fito, ai Abban na ku ma yau ya na gida". Suka zauna bayan sun gaisa, ta ke cewa da su "Yaushe za ku koma gida ne?" Bashir ya ce "Anjima 80 Kwadayı bar jana'- Anuna Abdullaht Sharada kadan zamu tafi gidansu Mamata don ta gaishe su" Ilajiya Jamila ta ce "laba dai ka barta anan mana mu gama gaisawa wajen gobe kuma ta je can gidan na ku?" Ya yi murmushı sannan ya ce "Shikenan Mama ga ta nan da dare na zo in dauke ta, fita zanyi". Ta ce "Yauwa ko kai fa? Ai gara ka kyaleta ka ga sa gaisa ma da Abban ku sosai, ya ce "To shikenan, ni zan koma". Та ce "To sai ka komo". Ya mike zai fita, Sameera ta mike don ta raak shi wajen motarsa. Suna zuwa ya dubeta ya ce "An samu abinda ake so yawo ba?" Ta yi dariya "Ai ni dama cewa ka yi in kwana haka na ke so". Ya се "А haba dai kwana? Ni kuma fa?" Ta ce "Kayi kwanciyarka a gida ko tsoro ka ke ji?" Ya ce "Tsoro kai". Ta ce "То me zai sameka?" Ya ce "Ba abinda ba zai sameni ba, komai ma samuna zai yi" Ta yi murmushi "Ilaba dai yau dayan?" Ya ce "Ashe kin gane?" Ta yi murmushi sannan ya ce "Ni na tafi sai daren?" Tа се "То а dawo lafiya, Allah ya kiyaye min kai". Ya ce "Amin". Ya na mai jin dadin addu'ar da ta ke yi ma sa in dai zai fita. Ita kuma ta koma ciki. Hajiya Jamila ta ce "Ilar ya tafi?" ta ce "Eh ya tafi". Ta koma ta zauna jim kadan Halima da ke rike da Zainab a hannu da Alhaji Usaini suka fito, suna zuwa suka ga Sameera. Alhaji Usaini ya ce "Sameera saukar yaushe?" ta durkusa ta ce "Uncle yanzu muka zo". "Okey ina Bashir din?" T ace "Yanzu ya fita ya ce zai komo ya dauke ni zuwa dare". Ya ce "Allah Sarki ai kin jima ba ki zo maan ba". Та се "Wallahi ba ya barina inje ko ina Abba". Ya ce "Ai ya kyauta domin ni ma ba na son fitar, gara ya zama muturn ya na killace wuri daya sai ya li, kinga ai gashi kinzo mana a marmarcе". 81 Kwadayı barjana'- Anuna Abdullahu Sharada Ta yı dariya sannan suka gaisa, ta karbı Zainab gamı da tambayar ina su Auwal? Suka ce "Su Auwal suna can makaranta ba a taso su ba tukunna" Nan dai suka yi ta hira har wani lokaci, sannan Halima ta tashi don dora musu abincin rana, ta komo suka ci gaba da hıra Yamma na yı Bashır ya dawo, da mısalın karfe hudu, ya an shigowa su Hajiya Jamila suka ce "bashir har ka yi me?" Ya ce "Har na dawo mu tafi gıda" Ta се "Lallai Bashir ka zama dan kadafi wato kai baka amince ta kai daren ba kenan?"

Chapter 6 of 12