Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 12
faman kiransu ya ke a waya yau in ya kira wannan, gobe sai ya kira wancan har dai Dad ya gaji ya ce da Mum "Wannan yaron Bashir na san fa abinda ya ke yiwa yawan waya, so ya ek matarsa ta koma, saboda haka a wannan satin za ta tafi". Mum ta ce "Ni ma ina da niyyar gaya maka haka, ai gara ta koma gidan ai ta zaunu". Ya ce "Yauwa ai gara ta koma yanzu me za'a shirya mata na komawa?" ta ce "Ba abinda zata tafi da shi sai dai a tura musu kudi a banki kawai". Ya ce "to shikenan". Kwana uku da wannan maganar sai kawai suka fara hadawa sameera kayan ta, don kashe gari za ta wuce, haka ko aka yi da ranar ta zo, suka sa ta a jirgi sai nigeria. Bashir na gida a zaune bai fita ko ina ba, ya ji sallamar Sameera cikin mamaki ya ce "Yaushe kika zo?" Ta ce "Saukar kenan". ya ce "Wa ye ya dauko ki daga airport?" Ta ce "Motar haya na hawo". Ya ce "To me ya sa ba ki yo min waya ba?" Ta ce "To ai ban san uzurin da ke gabanka ba shi yasa ya ce karka kara yin irin wannan". "Ai ko ni baki yo min ba sai kijewa su Abba dasu Abban gidan su Maryam". Ta ce "To ni dai wallahi 93 Kwadayı barijana'- Amina Abdalalu Sharada ban kıra kowa". Ya ce "To ya su Mum da Uncle?" T се "Suna nan lafiya, ka san kuwa Dad ne ya ce lallai in ta ho". Ya ce "Ai ya kyauta kına can kin barni da kewarkı" Ta ce "Dama ai saida na ayyana" Ya ce "Yanzu ke da basu ce ki taho ba, ba zaki taho ba kenan ko?" Ta y murmushi "Haba Bashir mahaifa fa aka ce ma?" Ya ce "A'a lallai, ai ko baki fađa ba na sani". Tayi murmushi "Ashe na mance na bar dan tasi da kaya a mota, zo muje ka taya ni daukowa". Ya ce "Au ina mai gadi, baya nan ne?" Ta ce "Ban ganshi ba". Ya ce "To muje Haruna mai wanki na san shi ya na nan don yanzun nan ya gama guga". Nan dai duk ta yi wa su Hajiya Jamila waya ta komo da su Hajiya Rukayya, wato mahaifiyar Bashir kenan, sannan shi kuma ya sanarwa su Abbansu, nan dai suka yi ta bugowa sunai mata sannu da zuwa, kuma ta yie wa can gidan nasu waya cewa ta sauka lafiya, ta samu kowa lafiya. Bayan kamar wata guda da dawowar Sameera Maryam ta yo waya cewa ita ma ga ta nan zuwa, nan aka yi ta shirin taryar ta, cikin doki da murna. Kwana biyu kuwa da yin wannan naganar sai ga shi ta yo waya cewa ta iso, ta kuma bukaci Abba ya aika a dauko ta, dai-dai misalin hudu na yamma Abba yа amsa mata da to. Lokacin na cika da kansa ya tafi daukota ya ko yi sa'a saukarsu ke nan taan hango shi ta rugo da gudu tana murnar ganinsa, ya amshi jinjirin ya rungume ya na faman murna har dai wani lokaci sannan ya dauki kayan nasu ya sanya a boot suka taho gida suna ta faman murna da farin ciki. 94 C Kwadayı bari jana'- Amina Abdullahu Sharada Suna zuwa gidan fa su Hajıya Jamila da su Halima aka dinga murna, Halıma ta ce "Miko min yaron in ganshı, kin san ni banje suna ba". Ta mika mata shi, karbar shi ke da wuya sai gaban Halıma ya yanke ya fadi, ta ko zubawa yaron nan ido kirr ta na tunanin gano da wa suka yi kama, ta dai san mai irin fuskar nan amma ta manta, sai can ta tuno lallai wannan jinjiri suna mata kama da tsohon saurayinta Jamil wanda ya yi mata cikı ya kore ta ya barta da kajaga, ta ce a ranta "Allah mai iko, ji bi dan nan sai kace sun hada iri da Jamil, ko da yake uwar ma tana kaam da Jamil din, to amrna kamannin sun fi bayyana ga yaron, wannan abin mamaki da yawa yake, lallai in kana dã rai babu abin da ba zaka gani ba, dubi dai yadda yaron nan ya debo kamanin wani banza can bare". Tana cikin wannan tunanin ne Hajiya Jamila ta kalleta ta ce mata "Ba dai ya auren da ke kika zuba masa ido, kinga sirmin saurayi, to kin yi masa tsufa". Cikin wasan ita ma ta ce "Nima bana so a kaiwa Hajiya Rukayya, ko Hajiya Husna su ne suka fi dacefwa da shisabuwar fata, mu kam mun tsufa". Maryam ta ce "O har yanzu dai kuna nan da abin nan naku?" Halima ta yi dariya ta ce "Maryam ke nan, ai kin san ni da Auntyn tawa kamar abokan wasa". "Au Aunty ina 'yan kannena da aka haifa bana nan?" Halima ta ce "Wallahi dazun nan Bashir ya zo ya kwashe su baki daya suka tafi gidansa wai su taya Sameera wuni". "Ke ni ko ina Baba Abu din nan?" Ta ce "Tana nan ai kafin ki koma ya kamata ki je ki gaishe su". Ta се "Zani wallahi, har can gidan kuma na yi niyyar zuwa". 95 Kwadayı barijana!- Amuna Abdullalı Sharada Ta ce "Aiko da kin kyauta, dama ko kanwata Asabe tana gıdan ba lafiya sai mu tafi tare ki dubata". Ta ce "To muje in an kwana biyu". Ta ce "To shi kenan, Allah ya kaımu". Tuni Hajiya Jamila ta shige daki ta barsu, don haka sai Halima ta ce "Ki shiga mana ku gaam gaisawar inyaso kya zo mu ci abinci". Ta ce "To". Ta shiga dakin Hajiya Jamila. Tana shiga Hajiya Jamila ta ce "Lallai Maryam na yarda mai hali baya fasawa, wato har yau kina nan da halin nan naki, to maye na tsayawa a wurin wannan banzar har ma wani kina cewa zaki je gidansu wata Abu can, to sai kin dawo sha-sha-sha, marar hankali". Nan da nan Maryam ta zumburi baki "To in naje gidan laifi na yi? Wai ni Mama me yasa kuke haka ne? Ni dai gaskiya bana son ku dinga irin wannan......" "Kinga rufa min baki kinji ko? Bana son wani surutu". Halima ko na can tana ta al'ajabin abinda ta gani dangane da kamannin wannan yaro har dai wani lokaci, sannan ta táshi ta kawai Maryam abinci ta ci ta koshi, sannan Maryam ta fito falo suka zauna suna hira har wani lokaci. Nan Alhaji ya dawo ya same su shima ya zauna ana ta faman hira da shi har sallar magruba, bayan sun gama cin abincin dare ne Maryam ta koma inda aka tanadar mata don ta sauka, wato dakinta na tun tana budurwa, nan ta yi kwanciyarta da yaronta Saddik kusan sha dayan dare agogon nan Nigeria, Faruk ya bugowa Maryam waya, ta dauka bayan sun gaisa ya ce "Ina Saddik?" Ta ce "Ga shi nan har ya yi bacci". Ya ce "Ai na san yanzu dare ne". Ta ce "Wallahi kuwa ka ga ma shirin kwanciya muke yi". Ya ce "Ni ko kinga shirin fita 96 Kwadayı barıjana'- Amına Abdullahu Sharada ma ne ke y1, shi ne na ce bara in kira kı". Ta yi murmushi ta ce "Wai dazun nan da na kira ka bayan na sauka kana ina ne?" Ya ce "Ina can office din Dad akan maganar fara aikina". Ta ce "lallai to Allah ya taimaka". Ya ce "Amin, zan kira ki can bayan karfe biyu". Ta ce "To shi kenan Allah ya kaimu, sai anjiman". Ya kashe wayar sannan ta kwanta ta na mai godewa Allah da ya bata miji mai tsananin sonta da gaskiya. Kwanan Maryam uku ta fara zaga 'yan uwa da abokan arziki kamar su gidan Alhaji Hassan gidan Bashir, gidan su Hajiya Jamila ma anan gidan lyayen Hajiya Jamila, gidan su Baba Abu, har gidan su Yalwa ta je, sannan ta komo gida, tana mai mamakin ganin gidansu Yalwa da yadda gidan ya lalace ba don komai ba sai don rashin tarbiya, wato baki dayan gidan ya zama tamkar gidan taron garken dabbobi kowa da tambelen da yake yi, da niyyar kwana ta je, amma a daddafe ta yi awa daya a gidan ta komo gida. Bayan ta dawo ne Halima ta yi ta fargaba don karta fadawa Hajiya Jamila abinda ta gano a gidan ta bar mata abin giri, hakika Maryam ta cika 'ya mai hankali domin kuwa ko a fuska bata nunawa Hajiya Jamila ba, dama ta tambaye ta komai yasa bata kwanan ba sai ta ce "Yaron n yake mata rigima shi ne ta fasa kwana don kar ya hana su bacci, ita ko Halima da Maryam ta shiga dakinta sai ta се mata "Maryam kin ga gidan namu ko?" Ta ce "Na gani Aunty, wannan gida naku ai ya rikice". Ta ce "Wallahi shi yasa tun da na ganki na ce akwai dalili na san ba zaki iya zama ba". Ta ce "Ina zan iya wannan tashin hankali wai wanna Lawan din kaninki shi ne suke ta fada da abokinsa sai ya sari abokin nasa ko a ka ne, shi ne ya 97 jang Ma Naunali Sarada debo masa 'yan sanda, yanzu zancen da ake yı ya gudu wai kuma sai suka kama dayan wato Auwalu wai shi ma dama nemansa ake, ya yi wani laifi, ita kuma Asabe na daki a kwance ba lafiya duk ta rame ta yi baki sosai, Yalwa sai kuka take yi, wai an tsanar mata 'ya'ya an sa su a gaba sai an ga bayansu". Halima ta ce "Ai Yalwa ba zata taba barin halin ta ba, ni ko naga sanda Yalwa zata gane wallahi yaron nan zaman su a gaban Yalwa matsala ne, dama dai kawai can aka kai su gidan horo aka bar su a can in sun nutsu a komo da su". Maryam ta ce "Wai har tabar wiwi Auwal yake sayarwa". Halima ta ce "Ai ya jima yana wannan cnikin, sau nawa ana kama shi akan haka?" Maryam ta ce "Wai yanzu babu wani abu da za a yi a kai ne?" Halima ta ce "Me za a yi musu a kai wanda za su nutsu bayan sun riga sun gama fandarewa? Dama-dama ma Auwalu amma shi Lawan ai abin nasa ya yi nisa domin ya zama sai kace wani gagarumin dan fashi in kin gan shi ma baki son kara dubanshi". Maryam ta ce "Shi Auwalun da zai sami wata sana'a ya dunga yi aiai da ya fi". Ta ce "Da da abin bai yi girma haka ba, yana zuwa bakin titi wani yana taimaka masa yana dan taya shi gyaran mashi yana biyansa, to shi ma yanzu ya daina ya biyewa Lawan". Maryam ta kawar da kai gefe ta ce "Ai ina ga shi yanzu in aka janyo shi aka bashi jari zai nutsu?" Ta ce "To kila in anyi sa'a zai zauna, to amma wa kike gani zai iya bashi jarin?" Ta ce "Ga Abbana ki gaya masa mana". Ta ce "A'a ni ba zan fadawa Abbanki wannan magana ba domin kuwa ba irin taimakon da ba ya yi mana in na gaya masa zai zama kamar rashin godiyar Allah ne" Maryam ta ce "Shi kenan sai yadda ta yiyu kawai, amma 98 Kwadavi harmal Kwadayı bar jana'- Anuna Abdullahı Sharada ya kamata ayi wani abu akan lamarin nan" Yau satin Maryam uku da zuwa yaronta ya kara wayo sosai domin ya shiga wata na uku kenan, kamannin kam da Jamil sai kara fitowa suke yi, Ilalima tana mamakin wannan abu, to amma bata nuna ba sai ta boye abin a ranta domin bata son kowa ya san halin da take ciki, ita ko maganar Jamilun ma bata sonta, sau da yawa dai ti kan tunano 'yar da ta haifa ta tafi ta barta, wani lokacin ta kan yi tunanin ko 'yar na nan da rai? Wani lokaci kuma sai ta tunano ko ta mutu oho, amma dai ita sai a yanzu take ganin ta yi farar dabara da ta bar 'yar domin da suna tare Alhaji Usaini ba zai aure ta ba da yanzu suna gidan Yalwa suna cin bakin ciki tare ga shi yanzu asirinta a rufe, ga yaranta mijinta yaan kaunar ta, ga shi suna zaune abinsu da shi lafiya lau ba ya son laifinta yana taimakawa 'yan uwanta da iyayenta, yana kaunar yaranta kamar ya hadiye su, duk wani makircin Hajiya Jamila in ta kulla shi ba ya tasiri a kan sa, to yanzu wanda ya ke cikin wannan zaman lafiyar da kwanciyar hankali me zai dame shi? Gara kawai ta kara kwantar da hankalinta ta yi zamanta cikin rufin asiri, dama irin fadan da Baba Abu take mata ke nan a ko da yaushe domin ta zauna lafiya a gidan mijinta, shi yasa ma duk abinda Hajiya Jamila zaat yi mata bata kulata domin bata son batawa mijinta rai suna zamansu lafiya. Watan Maryam guda da 'yan kwanaki sai Alhaji ya ce ta shirya domin ta koma gida, ai tama jima haka ta shırya aka hada mata sha tara na arziki, ta koma gidan mijinta wato can Jamus. A lokacin shi kuma Faruk ya fara aiki a wani asibiti mai zaman kansa da aka bude. Tana komawa gida ya nuna matukar farin cikinsa daam 99 Kwadayı barıjana'- Amina Abdullahu Sharada ya damu da rashin dawowarta, kunya ce ta sa shi kasa magana kun san Faruk akwai kunya kamar ba dan turawa ba, ko da yake ruwa biyu ne shi yasa. Kwanci tashi cikin Sameera na kara girma har ya kai wata tara kowa na murna da wannan ciki domin shi ma bashir zai sami dan kansa su maman Bashir da su Hajiya Jamila sai faman shirye-shiryen taryar haihuwa ake yi, kowa sai faman dokin zuwan ranar ake yi, domin a wannan lokaci ne aka sa shi ma Ibrahim ya fidda matar da zai aura domin sun ce ba zai auri jar fata ba, gara ya dawo nan ya yi auransa har ma Alhaji Usaini da Alhaji Hassan sun gama karfi wuri guda sun kera masa wani kyakkyawan gida, shi Alhaji Hassan ya ce akwai wata 'yar amininsa mai suna Alhaji Ashiru zai bashi ita, domin yarinyar ta na da hankali. Tun da ya ga yarinyar ya ji yaan ma Ibrahim sha'awarta, to Ibrahim din ma ya yi na'am domin an kai musu dankareren hoton ta sun gani, saura gani da ido kuma. Sameera na kwance a falo kusan sha daya na dare da tsohon cikinta tana jiran dawowar Bashir, shiru tun da Alhaji ya ce ya zo sa tafi unguwa shiru ba su komo ba, can sai ta mike don ta koma cikin daki, ai ko ikewar nan da zata yi kamar an tsira mata ciwo, nan ta cije baki ta fara murkususu, tana kiran Allah har wani lokaci, cikin hukuncin Allah bashir na jeho kafa falon ta dan ma na fitowa. Da gudu ya karaso gami da tallafeta ya nai mata sannu akan tsananin mamaki domin shi dai lafiya ya barta ba ko alamar ciwo ba don yanayi da za a iya gani na nuna alamun an sah wuya ba, za a iya cewa kamar a sadaka ta sami dan, to fuskarta ce zata nuna alamar wuyar da ta sha kafin dan ya zo duniya. 100 Kwadayı harijana'- Amuna \bdullahı Sharada Waya Bashir ya dauko ya fara kıran su lajiya Rukayya cewa Sameera ta haihu, sannan ya sake bugawa su lajiya Jamila ya kuma buga can Jamus wato gidan iyayen Sameera, ai nan da nan sai murna, cikin daren nan kowa ya dinga murna kamar anan aka yi haihuwar a cikin daren su Ilajiya suka isa suka gyara jaririn sannan suka gyara mata gidan ta tsaf, sannan kuma ita kanta bayan sun gama komai suka bar su da jaririnsu suka tafi gida. Kashe gari kuwa jama'a aka cika gidan tamkar ranar ake suna, da yake abinka da 'yan dangi ga shi kuma auren zumunci ne, kuma wasu ma domin su zo su ga irin haduwar da za ayi a sunan suka zo, haka dai aka dai aka yi ta zowa, tare da burin zuwan ranar sunan. *** M asu karatu kar fa ku manta da labarin Jamilu wanda ya yiwa Ha;lima ciki tun shekarun baya da suka wuce akalla za a sami kimanin shekaru goma sha takwas da 'yan foriyar watanni. Jamilu ne zaune ya hada kai da gwiwa cikin dumbin takaicin abinda ke damunsa, ba ko wani abu bane ya dame shi ba, sai matsalar rashin haihuwa, akallah ya yi auren mata dai-dai har biyar amma duk ya sake su saboda sun ki zama babu yarinyar da zata yarda ta zauna babu da, idan ma ta amince da an fan samu shckara biyu ko uku sai ta bijire ta ce ya saketa ita ba zata zauna da shi ba, domin in sunje likita ya auna su sai ace matsalar daga gare shi ne, ga dai dukiyar Allah ya bashi, abin ba a magana, amma abu daay 101 ya rage masa Kwadayı han jana Anuna Abdullam Sharada an dadi, ahın nan kuwa shi ne rashın magaji domin shi ma yana so ya ga 'yan dugwai-dugwai a gabansa, to amma babu hali. Na san zaku ce ai ko Jamilu na haihuwa, domin ai shtya yiwa Halima cíi, to hakika a wannan lokacin yaan haihuwa abinda ya faru shi ne. Tun ranar da Yalwa ta kai karar Jamilu gidansu wurin mahaifinsa Alhaji Ali in baku manta ba shi Alhaji Alın ya tura shi waje domin ci gaba da karatunsa zuwa mataki na biyu, ma'ana digirinsa na biyu, kuma zai yi ne a bangaren harkar kasuwanci domin shi ya zaba, kuma ya ke so ya yi Alhaji Ali ya shirya masa komai don ganin ya tafi kuma ya shaida masa cewa ba zali dawo yanzu ba sai bayan wasu 'yan shekaru, kafin lokacin kowa ya gama rurumar zancen ya yi wa wata 'ya ciki, abin ya wuce don haka sati daya da yin wannan hatsaniya tsakanin Yalwa da Alhaji Ali sai ya tura shi can kasar Amurka ya ce kuma kar ma ya sake ya komo musu sai bayan wasu lokutta ko ince shekaru, haka ko aka yi domın tun da ya tafi bai komo a sai dai ya buďe kan iskanci a kasar kasancewar an sakar masa kudi sosai wai don ya ji dadin zama, sai ya zama shi ne shugaban 'yan iska a can, saboda gidan sa ma ya koma tamkar dandalin karuwa, kuma wani abu da yake yi basa kula yarinyar da la riga ta fandare sai dai wacce take da mutunci ko а yaudare ta da kudi ko kuma kyau, domin na gaya muku Jamilu kyakkyawa ne sosai domin yanayin kyansa yana yin kyan jarumin līlm din indiya shi yasa 'yan mata da dama suke rudewa akansa, to haka ya bude babin iskanci shi da masu hallaya irin tashi suka gama kai. To matsalar da yake samu, sai ya kasance duk yarinyar da ya kusanta sai ta sami ciki, ayi ta kai ruwa Kwadayı barıjana'- Amuna Abdullahu Sharada rana, wasu da dama sun salwanta sakamakon cıkın da suke samu ta hanyarsa haka ne ya sa shi sauya dabara, saı yaje ya sa aka yi masa allurar da take kashe masa kwaikawaycn haihuwarsa baki daya domin a wannan lokacı duniya na rudinsa gani yake shi haihuwar ma bata da wani amfani a tare da shi. Ya jima yana faman tafka shadancinsa kafin daga bisani abin ya komo kunnen Alhaji Ali, kun san daam ance zancen duniya baya buya, don haka nan da nan sai ga shi da kansa ya zo ya tusa dansa a gaab ya koma da shi gida domin ya ma bincika ba wani karatu da yake yi sai tsiya da yake tsulawa kala-kala, don haka sai Alhaji Ali ya ce lallai ne in sun koma gida ya sami mace a yi masa aure, shi ne zai fi zaman lafiya, haka ko aka yi yana komawa gida sai ga shi Alhajin yana ta kawo masa 'yan mata daga bangaren abokansa, amma yana ki sai can dai ya amsa daya, wato wata 'yar abokin Alhajin mai suna Zahra ya ce yana so, domin yarinyar ta hadu, kuma aka yi sa'a tana sonsa, to shi ne ma har aka yi auren bayan uban ya kera masa gida suka zauna a ciki, aka yi biki cikin jin dadi aka watse, zama ya mike har kusan shekara biyu sannan suka fara tunanin samun haihuwa, wato ita ce ta ma damu shi ba ruwansa da ya samu da, ganin ta damu ainun sai ya je ya sanar da mahaifinsa, shi kuma ya ce to aje asibiti domin a tantance waye ba ya haihuwar, shi dai mahaifin nasa ya san cewa dansa ba shi da wata matsala don haka sai kawai ya ce suje a duba su aga waye mai matsalar, shi kuma bai san zai ce haka ba don haka bashi da zabi sai ya bi umarnin mahaitinsa haka ya dauketa suka je aka bincike su, nan da nan aka gano cewar Jamil ne baya haihuwa sakamakon mutuwar 103 KwadayıIiri jana' Amna Abdullahı Sturasdа kwayayen hathuwarsa baki daya, an Zahra taan jin abinda aka ce ta ce ba zata zauna da shi ba, Iallai ya sake ta, ganin zata tona masa asiri a wurin mahaifinsa sai kawai ya sauwake mata. Mahailinsa na jin ya saketa sai ya rufe shi da fada, shi ko ya ce ni likita ne yace bata haihuwa, shi ne shi kuma ya saketa,ya ce "Ai baka saketa ba sai ka auro wata ka hada su". Ya ce "Ai rashin kunya zata yi masa shi ne yaga ya dace ya hakura da ita, nan dai mahaılinsa ya yi ta yi masa fada har wani lokaci. ba har Tun da ya saki Zahra bai kara maganar aure sai da mahaifinsa ya matsa masa domin ya dawo da shashancinsa sabo dal, nan dai ya takura masa har ya sake yiń wani auren, nan ma suka sake samun kusan shekaru biyu sai nan ma rashin haihuwar ya dami yarinyar mai suna Aisha, ta yi iya kokarinta akan ya je asıbitı ya ki, har dai ta haji ita taje likita ya tabbatar mata da lafiyarta lau bata da wata matsala game da haihuwa, nan ma abin ya dame shi da ya ji bayanin da ta zo da shi, ga shi kuma yana kaunar Aisha fiye da Zahra, haka ya ci gaba da lallabata ya nai mata nasihar Allah ne bai basu ba har suka kai kimanin shekaru hudu, sannan dai Aisha tura ta kai bango son da ya fi a aranta, sai kawai ta ce ita ya sauwake mata ta je ta yi aurenta a wani wurin ko zata haihu, nan dai babu yadda zai yi sai ya saketa, uban fa ya same shi ya yi ta fada akan abinda yake yi, har ya ce "Ba ka gado ni ba, domin ni tunda na ke ban taba kara aure ba bare saki, gara ma kawai in daina shiga maganar aurenka don ni zaka dinga baiwa kunya". Nan ya yi ta baiwa uban hakuri har dai ya hakura amma da sharadin kar ya sake aure, ya saki matar, to fa nan ya ga babu sarki sai Allah domin ya zama lallai ya 104 Kwadayı barjana'- Amına Abdullahı Sharada sanar da shi cewa matsalar nan fa tare da shi ne, ba wai gamatan ba, to nan ne ya dan samı rangwame, to amma fa uban bai san cewa shi ya saiwa kansa wannan matsalar ba. A takaice matansa hudu suna fita, sai a ta biyar dince har yanzu dai ba a ji kansu ba, domin a yanzu haka shekararsu ta daya kenan, da yin wannan sabon auren, da haka zamu leka gidan nasu muga wacce wainar ake toyawa? Jamil ne zaune a katafaren falonsa ya kishingida bisa wata kujera doguwa ta alfarma, yayin da idon sa yake a lumshe daga shi sai babbar riga da gajeran wando, babbar rigar ta wata rantsatsiyar shadda ce, ruwan madara ta sha aiki, ga wani shegen agogo a hannunsa mai tsadar gaske, kallo daya zaka yi masa ka gaen shi domin har yanzu kamanninsa yana nan da farar fatar da komai, sai dai kiba da ya dan yi, sabanin lokacin da yake saurayi siriri dogo, to yanzu ya yi dan jiki kuma ya aje dogon saje da gashin baki siriri wanda ya kara masa kyau sosai, yana nan a kwance sai ga Sakina ta fito wato matarsa, sanye da doguwar riga kanta babu dankwali ita ma dai doguwar ce, to amma ba can ba kuma irin wankan tarwadan nan ce, ta zauna akujerar da ke kusa da shi ta ce "Wai ya maganar zuwana gidan namu ne, ka san fa matar Yayana ta haihu zanje ganin jaririya?" Ya ce bayan ya bude idonsa ya kalleta "Kin faye son fita wallahi, ba shekaran jiya kika je gidan ba ne?" Ta ce "to ai na gaya maka haihuwa ta yi jiya". Tsaki ya yi gami da juyawa ya fuskanci bangon kujerar ta mike ta shige cikin daki ta dauko hijabi da jaka ta fito, ta suri makullin mota ta dube shi "Sai na dawo". Ya ce "Ki gaishe su". Та се 105 Awaulayı baıjana Amuna Abdullahı Sharada "to sa ji" Ta fice abınta yayın da ya juya ya zuba mata ido har ta fice, ya tashı ya je ya kunna tıbi ya kamo da remote a hannunsa yana canza tashoshin tauraron dan adam, ko zai sami wacce ta dace da ganınsa. Can saı ya gama danna-dannansa ya kamo M.B.C Action domin ganın film din da suke yi, zai yi kyau, ya ko yi dacen ganın wasu 'ya'yan turawa na wasan kwallo a waat koriyar ciyawa su uku, can gefe kuma iyayen su ne ke kallo su nai musu alkalancin wasan, sai abin ya burge shi ya ce a ransa "Ina ma nima ina da 'ya'ya wallahi da zan zamo mai saukin kai a cikin iyalina domin ina sha'awar magidanci zaune cikin iyalinshi ana barkwanci". Yau shi kadai ne tafe a motarsa yana Kokarin komowa gida daga kasuwa, yayin da danja ta tsaida shi. sai ko ga wani mai mota kirar jeep irin tasa sak! Ya yi birki kusa da shi bayan motar wasu yara ne su biyu mace daya suna ta faman hangen na waje, akwai dan duhu a motar, amma zaka iya shaida na cikin motar. Jamilu ya zuba musu ido har aka bada hannu, bai ankara ba, zuciyarsa cike da shaukin son yara ya ce a

Chapter 8 of 12