Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 12
kasan cewa ta yi bala'in ramewa sosai kamar wacce bata cin abinci koma bata cin oho, don ta shiga wani hali na damuwa da nadama gami da dana sani marar amfani na abinda ta yiwa Faruk. A wani bangaren kuma son 'shi da kaunarshi sun zama tamkar abincinta don kuwa a kullum cikin begensa ta ke, wannan abu ba karamin damunta ya ke ba, kuma ya na daya daga cikin abinda ya haddasa ma ta ramar. Yau kimanin satin Faruk biyu kenan, amma ba ta je asibitin ba, don kowa ta ce ya kaita sai ya ki, sai ta sauya dabara ta je da safe bayan ta gaida Daddy ta ce masa "IDad in zaka je asibiti ni ma zanje". Ya ce "To ki shirya in anjima zan je". Ta ce "to". 55 Kwadayı barijana'- Amına Abdullalu Sharada Ta shirya tsaf, ta dafawa laruk farfesun kaji mai dan romo-romo mai dadi, sai kamshi ke tashi, sannan ta nemo kula mai kyau da plates masu kyau ta hada masa lemo mai sanyt sosai, ta dura a wani katon jug ta nemi glass-cups masu kyau ta dora a mota ta fito suka tafi. Allah-Allah ta ke yi ta ga halin da Faruk ya ke ciki, da ma irin yarda zai karbe ta in ya ga alamar ta na Kaunarsa, ai ta san yau murna a wurin shi abin ba dama, don ta san irin kaunar da yake ma ta, ha kadan ab ce zai yi matukar farin cikin jin cewa a yanzu ta na sonshi, ta na cikin wannan tunanin ne suka shiga harabar asibitin, amma me? Sai gabanta ya ke faduwa in ta tuna yadda ta yi masa, da yadda bata je duba shi ba, wanda kamata ya yi ace ita ce ke jinyarsa maimakon kanwarsa da mahaifiyarsa, to ma banda wannan me za ta ce da Mum, don dai ko ba komai ma sai Mum ta zargi wani abu saboda ku san sati biyu ba ta je ba. Mutumin da aka dauka a gabanta rai a hannun Allah aka kai asibiti, ai ka biyo baya ka duba shi, nan ta ke karaya ta zo ma ta, da kunya mai tsanani wanda a da ba ta yi tunanin haka ba don babu son a ranta. Daddy ne a gaba ita a baya, yayinda suke hawa benan asibitin, daki biyu suka wuce suka zo nasu mai lamba 9. Daddy ne a gaba har yanzun ma ita kuma rike da kayan da ta kawo musu, ya murda kofar ya fara shiga, yayinda ta bi bayansa zuciyarta cike da kunya da dakin fargaba. Sallamarsa ta yi dai-dai da dago kan su na cikin ganinsu baki dayansu suka zuba musu ido kamar ba su taba Mum ba, har Daddy sai ya zamo abin kallo a wajensu. ce mai karfin halin cewa "Shigo mana nan ga 56 wuri" Kwadayı barijana'- Amına Abdullali Sharada Maryam anan gwiwarta ta dan yi kwari don a da jikinta ya sabule-subul, ta zauna kusa da Mum ta gaisheta, ta amsa sannan ta dubi Zainab ta ce "Z.ainab ba magana?" Zainab ta ce "Ai na ga kuna gaisawa da Mum ne kinga ba na yi miki magaan ba?" Ta ce "Haka ne". Sannan suka gaisa, ta tambayi Mum jikin nasa, ta ce "Da sauki". Daddy ya matsa kusa da shi ya ce "Ya jikin naka?" Ya ce "Da sauki". Ya ce "Ka gama shan wannan maganin da na baka jiya?" Ya ce "Eh, na gama Dad". Ya ce "Shikenan Allah ya kara sauki, yanzu zan shiga, zan turo maka da wani". Ya ce "to". Sannan ya kalli Mum alamar ta dan basu wuri. Mum ta kalli Zainab ita ma ta tashi suka ficce. Faruk na ganin sun fita ya maida kansa ya kwanta, cikin sanyin jiki Maryam ta mike ta karasa bakin gadon ta ce masa "Yaya ya jikin naka?" Shiru ya yi, sai can ya ce "Da sauki". A ciki ya amsa maganar, gabanta ya fadi, shiru ta yi ta na tsaye ta kasa magana, ba ta san abin cewa ba, sai can ta tuna da abinda ta kawo masa, ta koma ta zubo mishi farfesun a plate ta sanya cokali ta tsiyayi lemon ta kawo masa, ta zauna a gefensa ta ce "Yaya tashi ga abinci na zo maka dashi". Ya na daga kwancen kamshin farfesun ya buge shi, amma sai ya kawar da kai ya ce "Na koshi". Ta ce "Ko in aje maka sai anjima?" ya ce "Duk yadda kika yi". Amsar ba ta yi mata dadi ba, to amma ita hakuri ya kama dole ta yi shiru ta zuba ma sa ido kawai, da ya ga ta na nan zaune a gefen gadon sai ya fara tunanin tashi ya bar mata dakin ma, ya na cikin wannan tunanin ne ya ji ta sa hannu ta dan dafa kirjinsa wai ko akwai zazzabi har 57 a a a 11 yanzu? Ya daure fuska ya sa hannu ya cire nata liannun, ya mike zaune ya fara kokarin barin dakin, hakıka ranta ya yi bala'ın baci, to amma shi mai tarko ba ya tada kara. Shi ya sa ta ahkura kawai don ta ci riba ta san dai hakurin da ya yı ya fi wanda za ta yi anan gaba. Komawa gefe ta yi ta zauna ta ce "Koma ka zauna na tashi". Ko waiwayenta bai yi ba ya ficce. Can kuma wurin su Mum ta na zaune a office din Alhaji suna hira, shi ne ta ke fada masa cewa "Anya kuwa ba ciki ne da yarinyar nan ba Alhaji?" Ya ce "Me kika gani?" Ta ce "Gani na yi ta yi wani irin dushewa duk ta kode, gashi sai tayi wani rangwam da ita". Ya сe "Ba mamaki tunda ai kwanaki kince ta sha rashin lafiya ko?" Ta ce "Eh, ai har yanzun am ba ta gaam warwarewa ba". Ya ce "To babu mamaki ciki gareta, in shi ne Allah ya ingata". Ta ce "Amin". Komawar Faruk cikin dakin ya yi dai-dai da tafiyar Maryam toilet da gudu domin yin amai, ya na jin yadda ta ke ta sheka amai kamar za ta amayar da hanjin cikinta har ta gama ta fito ta d'an kwanta don ta huta. Ya fara satar kallonta ya na tunanin me ye dalilin aman na ta? Ko ta ci wani abinda ranta bai kwanta ba? Ta na gama aman ta koma ta zauna ta na tunani "Wai me ya ke damuna ne? A kullum da safe sai na yi amai, kai ni dai ban san abinda ya ke damuna ba!" Duk wannan tunani da take yi kuma Faruk ya sami damar kare ma ta kallo ya na tunanin abinda ya sa ta rama haka, da kuma kodewa da ta yi. Har kusan yamma ba ta tafi ba, sai can dab da magruba lbrahim ya zo Mum ta ce ya maida ita gida, 58 Kwadayı barıjana!- Amına Abdullahı Sharada haka ta dauki mayafinta akan dole ta tafi, ta kuma bar kayan in sun gama ci gobe a kawo, har za ta fita ta dawo ta ce "Mum sai gobe zan dawo". Faruk ya yi farat ya dubi Mum ya ce "Mum ta yi zamanta kawai ba sai ta komo ba". Mum ta ce "To Maryam ki yi ma zamanki kawai ba sai kin dawo ba". Cikin karaya ta ce "To Mum na tafi". Та се "Shikenan ki gada gida". Suna tafe bisa hanya ta na tunanin irin kallon da Mum ta ke ma ta kamar wacce ta ke kokarin gani wani abu, sannan kuma ta dinga tunanin yadda Faruk ya rufe ido akan ta kamar bai santa ba, ta yi mamaki ta ce a ranta "Kīla don dai ba ta je da wuri ba ne shi ne ya ji haushi, kuma banda abinsa ai ba ya ce kar in kara zuwa ba a gaskiya ni kam yanzu ni zan shiga tasku domin na san Faruk sai ya rama abinda na yi masa, sai dai inyi addu'a kar ramuwar ta yi yawa ko ta yi tsayi". *** C an kuma Nigeria, gidan Bashir ya zama tamkar gidan kurame don duk irin biyayyar da Sameera ta ke yi ma sa ba ya gani, hasalima ba ya ko kallonta, rai da rai ta na zaune da shi babu i bare a'a, rannan ta na zaune ya shigo, ta mike bayan ta yi masa sannu da zuwa ta ce "Zani gidansu Mama in gaishe su?" Ba abinda ya fito bakinshi sai cewa ya yi "Duk inda ki ke son zuwa ki je, ki ma wuce gaba da gidansu Mama in kina so sai kin dawo". Abin ya daure ma ta kai, cikin mamaki ta ce "Wacce irin magaan ce wannan in wuce gaba da gidansu Mama ma in ina so, ai wannan zai 59 1 S Π S Kwadayı barijana'- Amına Abdullalu Sharada janyo ka kashe aurenka in kana irn wannan wata rana!" Bai ko kalleta ha, ya yi gaba abinsa, ya shige dakı. Nan da nan ta ji ranta ya ki ma ta dadi, hawaye ya zubo ma ta, ta koma daki ta dauko mayafi, ta ko yi sa'a ya daga ta ce "Inje ko kar inje?" "Allah ya kiyaye hanya, a gaishe su". Nan da nan ta ji ran ta ya yi ma ta sanyi, ta yi murmushi gami da goge dan guntun hawayen da da ya yi ma ta fitar dole, ta shirya ta kulle ko ina ta nufo dakinsa ta kwankwasa, ya amsa ma ta da "Ina zuwa". Ta koma gefe ta na tunani. Sannu ba ta haan zuwa yanzu ga shi har ina samun ana amsa min magana ko ba dadi, wanda a da ba na samun ko amsar ma, ai abu ya yi." Fitowarsa ce ta sa ta saurin ja da baya gami da katse tunaninta ta ce "Dama zuwa na yi in sanar ma ka na shirya". Ya ce "To me zan miki?" Ta ce "Ai ba zan gane gidan ba, ka san tunda aka kawo ni har yanzu ban je gidan ba". Ya ce "Sai ki yi tambaya". Ta ce "To kuma in 6ata fa Yaya?" Ya ce "Shikenan" na Ta yi murmushi "Kai amma dai wannan ba amsa ba ce". Ya ce "Ita na ga damar bayarwa". Ta sake murmushi ta ce "Shikenan tunda ba ni da wanda zai rakani na hakura". Ta na gama fadar haka ta koma daki, ta zauna, to fa ashe ba ya son ta je gidan don kar ta fada musu halin da suke ciki, bai tuna cewa in ita bata je ba su zasu zo kuma in ta yi niya za ta fada musu, to amma ita abinda ta ayyana a ranta shi ne ba za ta taba fadawa iyayenta ko na sa wannan lamari ba, don in ta fada fada za su ce zasu yi masa, kuma wannan zai iya sake tunzura shi ya yi abinda ya fi da, shi yasa ta yi hakuri ta barshi ta na faman addu'a 60 Kwadayı harijana Anuna Abdullahu Sharada don samun nutsuwarsa zuwa gareta Wayar ta ce ta yi ringing, ta dauka don ganın ko waye? Abin mamaki ta ga lambar Bashır cikin doki ta daga wayar don ta ji abinda zai ce, ta ji ya ce "Iito mu tafi". Cikin sauri ta fito ta na ta faman murna yau za ta fita, rabonta da fita yau wata biyar kenan tunda aka kawo ta. Gidan baya ta shiga don babu fuskar shiga gaban, suna tafe babu i bare a'a sai kidan zamani da ya ke tashi a sannu har suka kusa kaiwa kwanar su. manyan gidajen ma'aikata za iya kiran unguwar da Kundila sai dai kuma masu hannu da shuni sun tsandara gidaje a wurin sannu bisa hankali motar ta karya kwanar wani katon get da masu gadi buzaye ne zaune su uku suna ganinsa daya daga cikinsu ya bude masa get ya shiga, ya samu wuri ya yi parkingi din motar, ya fito sannan ya ce ta fito. Ta fita ta na mamakin me ya sa ya kawo ta nan, bayan gidan Alhajinsu Maryam ta ce? Babu damar tambayar don haka ta ja bakinta gam. Ta na biye dashi, bai sake magana ba har suka shiga ciki, ya danna kararrawa wasu kyawawan yara su biyu mace da namiji da dan shekara biyar da dan shekara huďu ko uku da rabi, suka rugo suka bude suna ganin Bashir suka rungume shi suna kiran " Uncle oyoyo-oyoyo". Ai kuwa sai ga uwarsu da sauri ta fito "Au har kun iso?" Ya ce "Mun zo". Ta cе "Sannunku da zuwa". Ya ce "Yauwa". Suka samu wuri suka zauna, suna hira, can ta dubi Sameera ta ce "Amare kenan?" Samira ta durkusa ta gaishe ta sannan ta kuma yin shiru, su kuma suka ci gaba da hirarsu ta zumunci, yayinda Fatima ta umarci mai aikinta ta kawo musu dan abin motsa baki, 61 Kwadayı barijana'- Anmna Abdullalu Sharada sannan ta dubi Samecra ta ce "Samera ba kya magana kamar kurma? Ki saki jikinki nan ma la gıdanku ne". Samecra ta yi murmushi kawai ta sunkuyar da kai ta се "Ina ga dai bakı sanni ba, ni ce fa Aunty latima Yayar Bashir". Sameera ta ce "IDama tunda na ga yaran nan suu dare Yaya su na murna sai da na ayyana haka". Ta dube shi "Au baka sanar ma ta nan zaku zo ba ne?" Ya ce "Na sanar ma ta mana, kin san ba ta san ko ina ba...." "A'a ba wani baka fada ma ta ba, da ba za ta ka sa agne ni ba". Ta dubi Samecra "Wai da gaske ya fada miki?" Ta ce "Ya fada min, ai na dauka nan gidan Yaya Faruk ne?" Ta ce "Oho, a'a ai ba añan unguwar Yaya Faruk ya ke ba, ya na can jamus, daga nan gidansu Abba Zamu je". Та се "Aі can ma zamu ce, ance matarsa ta haihu?" Ta ce "IEh, ta haihu yau kwana biyu". Ta ce "To zamu je nan din ma". Haka dai ya tafi ya bar ta akan zai komo ya dauke ta. Yanzu kam ta samu ya na kulata, amma dai har kawo wannan lokacin babu wanda ya taba shiga dakin wani, kuma kulawar ma sai baya-baya don ko kallonta baya yi, sai in ya ga dama in ko zai kula din am bai wuce wane ya zo nemana? Ko kuma in anzo ace na tafi wuri kaza, ta ce to shikenan, wannan fa kenan maganar don ko abincin ta har yanzu ba ya ci, to amma dai an samu sabanin da da ko maganar ma babu, kuma ta na zaune bıyayya ko har yau bata daina ba, kar ku ce wai ko Sameera ta na wani hali ne da zai tsane ta, to ko kadan ba haka ba ne. Sameera ta na da tsafta sosai, ga ta ma'abocıyar son kamshi, ta bangaren sanya sutura kuwa ba kalar da 62 Kwadayı hariha Anuna Abdullahı Sharnte bata sawa, kuma sai dai ba'a nunawa bature sanya kananan kaya a don mafi yawancin kayan Sameera Kananu ne, wa lokacın ma zaki sameta da wando irin three kuater din nan ta sanya Karamar riga ta na yawo a falonta ba, ba ta ko jin dar in ta agnshi domin al'adar su ce haka, duk da cewa ba ta fita ko ina ba, kuma in har anyi baki sa ta sanyo kaya. Hakika a yanzu Bashır ya mato akan Sameera ganin yadda ta ke kara cika, kyanta ya Kara bayyana, gashi kuma irin kayan da ta ke sakawa da turaruka ya kara zamo masa tamkar wani maganadiso na janyo kaunarsa gareta a kullum ya dubeta sai wani matsanancın kwadayinta ya dameshi to amma bashi da hanyar da zai dosheta, kuma ya rasa dalili ko kuwa kunya ce ta ke hanashi? Oho!, don shi ya san bai kyauta ba, saboda Allah kyautatawa babu irin wacce bata yi masa amma ko kadan ba ya gani, don haka ta zuba masa ido ba ta dai fasa ba ta ce duk lokacin da ya ga dama hankalinsa ya juyo. Yau Sameera ba ta da lafiya don haka ta na can cikin daki tun safe ba ta fito ba, ganin haka hankalin Bashir ya ka sa kwanciya, sai jewa ya ke a falon ya kai mari ya kai gwauro hankalinsa na wajenta, kuma ya kasa shiga dakin ya tambayeta abinda ya ke damunta domin dai ya san a kullum ba ta afshin gaishe shi, to yau gashi ba ta ma fito ba. Kitchen ya nufa don ya ga shaida za ta tabbatar masa cewa ba ta fito ba. Ya na shiga kuwa ya samu babu kowa kuma ko alamar girki babu, sai kawai ya koma dakinsa domin ya dauko wayarsa ya kirata, ya ji ko ba zata daga ba. Ya na shiga ita kuma ta na fitowa falon don ta 63 Kwadayı barıjana' Anana Abdullahu Sharada kwanta gudun karya ga shıru ba ta lito ba, bai san abinda ya ke damunta ba, ta na kwanciya ta ga wayarta na ringing la dauka cikin mamaki, ta yi saurin daga wayar domın sabuwar lamba ta gani, muryar Bashir ta ji ya na lambayarta "Wai lafiya har yanzu baki fito falo ba?" Lumshe ido ta y/cikin tsananin murna jikinta har rawa yake yi ta ce "Wallahi yau jikin nawa ne babu dadi" Ya na in abinda ta fada, bai sake maganaba ya kashe wayar kawai. Ita kuma ta na jin ya akshe sai ta yi tsammanin ko m ko maganar ta ce ta bata ma sa rai, ta runtse ido ta na faman tunani, alama ta ji cewa ana kallonta, don haka ta bude ido da sauri, ta na bude ido kuwa suka yi ido hudu a shi, cikin sauri ta mike zaune gami da sunkuyar da kai, don tun ahduwarsu sai yau ne ta ji ta na jin kunyarsa. Cikin sanyin rai ya ce ma ta "Me ke damunki?" Ta ce "Kaina ne ya ke yi min ciwo". Ya се "Kin sha magani?" Ta ce "A'a ban sha ba". Ya ce "biyo ni ki karbа". Та сс "To". Ta mike ta bi bayansa har dakinsa ta na mai mamakin wannan lamari na bazata. a Suna shiga dakin gefen katafaren gadonsa ya nuna ma ta ya ce ta zauna, ba musu ta zauna ya dauko ma ta magani sannan ya bude tridge ya debo ma ta ruwa cup ya miko ma ta, ta karba ta sha maganin, sannan ta atshi za ta fita, ya ce ma ta "Ina zaki je?" Ta ce bayan ta bude kofa "Daki zanje in kwanta". Ya girgiza kai ya na murmushi ba tare da ya yi magana ba, kuma bai dauke ido daga kallonta ba, sai can ya ce cikin kasa-kasa da murya "Ina son ki dawo ki zauna nan ma daki ne". Cikin sanyin jiki ta saki kofar ta koma ta rufe. Kusan azhar ta fito daga bathroom dinshi daure da zani daurin kirji, jikinta da ta rufo tawul ta na tsane 64 Kwadayt hartjana Anina Alutullalu kharnda rowa shi kuma ya na gefen gado daure de tawut din h ma, yayinda ta fito suka hada ido sm kunya ta kamata ta ss hannu ta kare fuskarta ta na murmushi, shi ma eikin murmushin ya matso gami da" Ilohe youf Yayinda ta yi wala NANNanyar ajiyar zuciya Ia ce "/ huhe you tut Romance kawai ya wakar ma ta, daga nan sni aka ји labule T un sa'in da F'aruk ya ce Maryam ta y zamanta ba la sake zuwa asibitin ba har yau, ta na kwance a falo ta na tunanin yadda lokacr dayn Kaunar l'aruk ta shige ma la zuciya sai kawar la ji ya yi sallama, ta amNA Kallamar gami da dago kanta sama, ta kalleshi ta yi masa murmushi, ta ce "Nannu ad zuwa Yaya". Yn amsa ma ta da "Yauwa". Ya wuce dakinsa Jim kadan ta shiga dakin, ta durkusa ta gaishe shi, ta tambaye shi ya jin nasа, ун се ун nami sauki annan ta fito Ta na fita ya lara zancen zucr, "Anya kuwa iya yin abında ya shiryawa Maryam? Don shr dai ha zar iya hade kwadayinta da ya ke ba" Hoton ta da ke dakınshu ya dauka ya zuba masa ido ya na mar shaukin kaunarta, sai dai abu daya shi n dole ya yr hakurı ya daure domn gudun kar ya yı saurın sakar ma ta ta komo da halayen da, don haka ya maida hoton bayan ya sumbacı horon ya komo ya zauna, sa kuwa ga ta da kayan abinci ta shigo ta ajtye gabansa la dube shi ta yi murmushı, "Yaya ga abinci nan, yanzun nan na gama shı" 65 Kwadayı barı jana'- Amına Abdullahı Sharada Ko kallonta bai yi ba, a maimakon ma ya dubetan sai ya mike ya fafa hathroom domin yın wanka ya barta nan zaune. Har ya gama ya fito ba ta tashi ba, tana ta sakar zuci, shi kuma ya na ganinta a zauen ya yi saurin sauya kaya ya ficce abinsa, ko kaďan bakinta bai iya furta komai ba har ya ficce sannan dai ta mike cikin sanyin jiki ita ma ta ficce, ta koma dakinta ta na cewa a ranta "lallai in haka ma'abota soyayya suke ji yayinda suke tsananin kaunar dayansu kuma ya juya musu baya to lallai suna kokari, domin ni dai ina ganin ba zan iya jure wannan lamarin ba, ashe ba karamin ga sa Faruk na yi ba? Lallai kam ya yi ciwon zuciya, to Allah ya kiyaye, ni ma kar ya janyo min ciwon zuciyar domin muddin ina cikin haka zan iya shiga kowane irin háli" Da wannan tunani bacci ya sace ta, ba ita ta farka ba sai can ku. san la'asar ta mike a firgice ta dauro alwalla ta zo ta yi sallah, sannan ta tashi ta nufi dakin Faruk wai ta gano ko ya ci abincin da ta kai mishi, ai ko ko bude shi bai yi ba, kuma ba ya ma fakin, ba ta damu ba ta fito ta nufi can falon kasa wurin Mum ta gani ko ya na can. Ai ko ta na zuwa ta sameshi Mum ta zuba masa abinci ya na ci, nan ta ke ta ji ranta bai ma ta dadi ba, amma bai kyauta ma ta ba, ai sai Mum ta ga kamar ba ta bashi abincin ba ne, ta shiga ta zauna ta kalleshi ta ce "yaya amma ga abincin can na kai maka fa na ga ka ke cin na Mum?" Ya ce "To me ye?.Ai duk daya ne" Mum ta ce "A'a ba ka dai kyauta ba, yanzu saboda Allah da ma ta gama abincin ka zo kana ci anan?" Ya ce "Haba Mum share ta kawai don na ci abinci anan to me ye?" T ace 66 Kwadayı barıjana!- Auna Abdullahu Sharada "Ai dai bábu dadi tunda matarka ta girka maka sai ka zauna ka ci ka san dai mu mata yadda muke da kishi in an ki cin abincin mu". Ya ce "To amma Mum ko za lai kishi ai ba zata yi da ke ba domin ke ba kishiyarta ba ce ba". Mum ta ce "Wai ai misali na ke akwo ma ka, ka san dai ba ka kyauta ba ka ke wani kewaye-kewaye". Mikewa ya yi ma ya ficce, daga Maryam din har Mum suka bishi da ido dama Maryam ba ta sa musu baki ba. Ya na zaune bisa kujera da mujalla a hannunsa ya na karatu, Maryam ta fito daga kitchen sanye ta ek da wasu riga da siket na wata rantsattsiyar shadda dark green sun yi ma ta kyau, ta murza dauri, banda kamshi babu abinda ke tashi a jikinta, ta dauko hadadden lemo da tayi da kanta ta sashi ya yi sanyi ta hafo masa da cake don motsa baki saboda tunda Mum ta yi ma sa fadan cin abincinta bai sake ki ba, sai dai babu fuska sam-sam. Ta na dire ma sa a gabansa gami da cewa "Gashi Yaya lemo ne da na dan hada maka ka dan sha ka ji dadin karatun". Ya dago kai ya dubeta kawai zuciyarsa cike da mamaki ya na cewa a ransa "Ai Maryam ciki gareta gashi har ya fara bayyana? lallai kam ciki ne!" laka ta dire ma sa ta koma ta barshi ya na faman zancen zuci, a daddafe ya sha lemon ya mike ya sauka zuwa dakin Mum ya sameta zaune ta na saka katin waya, sai da ya bari ta gaam sannan ya ce "Mum!" Ta dago ta kalleshi ba tare da ta yi magana ba, shi ma bai jira amsarta ba ya ci gaba da cewa "Ni ko Mum gani na yi kamar Maryam ciki garcta?" Ta yi saurin dago kai ta dube shi tsawon lokaci sannan ta ce "In ma cikin ne ai zai bayyana don dan duma ne yado yake yi". Ya ce 67 Kwadayı barıjana!- Amina Abdullalu Sharada "To ki grala mana ki tambayeta?" Ta ce "A wane dalili zan kirain tambayeta bayan kai da kuke lare ba ka sani ba sai ni an Tambayeta? in ka gaza hakuri to ka sameta ka ji komai, ko ince gaskiyar lamari". Shiru ya yi ba tare da ya yi magana ba, ya mike ya na tunanin abinda zai ce a ransa har ya koma cikin falonsu ya zauna a lokacin Maryam ita ma ta adwo falon ta kwanta. Ta na jin ba dadi don amai ne ya ke taso ma ta, nan da nan ko sai ta tashi da gdu ta nufi toilet ta fara kwara amai, cikin mamaki ya zauna ya na sauraron yadda ta ke fama da aman kaamr ya je to amma sai ya ka sa don bashi da niyyar ya saurare ta yanzu, to amma yanzu ya tabbatar masa ad cewa tana da ciki, sai dai bai san ko wata nawa ba ne, gashi kuma har ya turo, sake tashi ya yi ya koma wurin Mum ya sameta har ta dan fara bacci, ya tashe ta "Mum kinga amai take yi wallahi". Ta komawa ce "yanzu?" Ya ce "h, ina na samu ta na amai". Ta ce "IDama ai da ganin Maryam ga alamun taan da juna biyu...." "Gashi nan ma har ya fito!" Inji Faruk, ta ce "In ko har ya fito to ai ko ya girma ma domin cikin budurwa atata in har ka ganshi ya bayyana to ta kusa haihuwa". Ya ce "Amma ko ta gaya min?" Ta ce "To me ye? Kunya ta ke ji ka kyale ta, ni banga abin damuwa anan ba". Ya ce "Ai ni ma ba damuwar na yi ba". Ta се "A to

Chapter 5 of 12