Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
11 / 12
wani ciwon". Ya yi shiru yana tunani, sannan ya ce "Eh, to hakan ma kinyi dai-dai to amma kin san me ya kawo ni?" Ta ce "A'a". Ya ce "Zuwa nayi in maida ke dakinki". Ji tayi kamar ta rungume shi don murna, ta ce "To shikenan na gode, Allah ya Kara kauna". Ya ce "Amin". Sannan ya kalleta yayi murmushi "Yanzu me kike da bukata?" Ta yi murmushi ta sunkuyar da kanta ta ce "Ka ga Yalwa ba lafiya, tabin hankali ne ya same ta ga tsufa babu mai kula da ita". Ya ce "Yanzu tana ina?" Ta ce "Ta na can gidan mai magni". Ya ce "Ai wannan shirme ne can, da wannan ai Gwauron Dutse za a kaita, amma kun kaita can gidan bokaye? Yanzu dai ki fara komawar tukunna, in yaso ma san abinda za a yi". Ta ce "То, yanzu in na tafi waye zai kula da Baba, gidan babu kowa?" Ya ce "Ina Lawan?" Ta ce "Ai Lawan shi ne ya mutu". Ya ce "Au ina Auwalu?" Ta ce "Ya fice shi da baya son zama a gida?" Ya ce "To shi kenan, na ji yanzu dai zan barki nan zuwa sati in an sami wanda zai zauna shi kenan..." Sallamar Auwalu ya jiyo, ya ce "Au to ga ma Auwalu nan, bara ya zo sai mu ji in zai zauna". Auwalu na shigowa ya yi kiransa ya amsa ya zo ya 132 Kwadayı barıjana!- Amina Abdullahı Sharada gaishe shi, bayan sun gama gaisuwa ne sai Alhaji ya ce "Dama ina son ganinka, wai shin Auwal sai yaushe zaka nutsu ka yi hankali ne? Ka ga fa iyayen nan naka sai ka yi biyayya gare su zaka sami rahamar Allah, yanzu abin da nake so da kai shi ne ka zauna a wurin Baba ka daina yawon kana kula dashi, in don abin da zaku ci ne, zan dinga kawo muku". Ya ce "To shi kenan Alhaji, mun gide, ya cе "Yauwa, kuma in har Baba ta sami lafiya zan daukeka zuwa can aksuwar mu ka dinga tayani ciniki". Cikin murna ya ce "To Alhaji na gode Allah ya saka da alheri". Ya ce "Amin". Ita ma Halima ta yi ta godiya. Bayan Halima ta koma gidanta da kamar sati aka kai Yalwa asibitin mahaukata, cikin ikon Allah tana samun magani da kulawa har aka samu ta saitu, wato ta koma cikin hankalinta. Cikin ikon Allah kuma aka sallamo su suka komo gida ta warke ras, ta tambayi wa ya biya aka kaita asibiti, aka sanar mata, nan da nan sai hawaye, ta ce "A gaskiya komai ma ya sameni ni na jawa kaina, yaran nan tun farko ni ce ban basu cikakkiyar tarbiya ta gari ba, shi yasa suka kasance fandararu, daga yanzu ina rokon duk wata UWA da ta tsaya ta kula da tarbiyar yaranta, don gudun fadawa halin da nawa suka fada, domin ance ka so naka duniya ta ki shi, ka ki shi duniya ta so shi, to wai kin ba ana nufin ka nuna masa kiyayya ba ne, a'a ana nufin kar ka so shi tsananin son da zai 133 Kwadayibari jana'- Anuna Abdullahı Sharada hanaka ka tarbiyantar da shi, ka dinga biye masa yana tabargazar da yaga dama, shi yaro rakumi ne sai da akala, sannan kuma ka bi da shi ta hanya madaidaiciya in ka kama akalar bayan nan kuma mu iyaye don Allah a rage KWADAYI da son abin duniya, ga shi tun farko shegen KWADAYINA ne ya janyo min har na fada cikin wannan mummunan halin. Sai dai ina rokon Allah ya yafe min abinda na yi tsakanina da shi, amma tsakanina da yarana sai dai kash na makaro da har suka mutu ban roke su gafara ba, domin ni ce silar su ta shiga wannan mummunar hanya, amma ina mai tubarwa Allah mahaliccin kowa da komai ya yafe min, ke ma Halima ki yafe min". Halima cikin kuka ta ce "Ba komai Yalwa na yafe miki". Та се "Тo, Malam kaima ka yafe min". Ya ce "Ba komai Yalwa mu yafi juna, kuma Allah ya yafe mana". Sannan ta cewa Halima "Tashi ki koma dakin mijinki, ki yi zamanki kar ki saba masa, ki kasance mai biyayya da hakuri". Alhaji ya ce "Ai Halima macen aure ce domin tana da duk abinda kika zano". Ta çe "Yauwa Allah ya yi miki albarka, kai kuma Auwal ka sami sana'ar yi domin zama babu sana'a ita ke janyo lalacewar tarbiyya". Alhaji ya ce "Ai tare zamu dinga zuwa kasuwa yana tayani ciniki". Ai nan da nan sai murna ta yi ta sa masa albarka, sannan ta ce "To ni yanzu zan dinga kula da Malam don haka kar kiyi komai ni 134 Kwadayı bariLana'. Amina Abdullahı Sharada ma ina bukatar samun lada, don in dan ciccika na da da ba a tsaya an samu ba". Suka yi dariya baki dayansu, sannan kowa ya watse. Yanzu dai gida ya yi dadi, hankalin kowa a kwance, Halima ana gidanta tana zamanta lafiya, babu wani tsangwama ko kyara, domin babu ruwanta da Hajiya Jamila, ko ta yi mata ma bata kulawa, sai ta dauke kai domin ta ji fadan mijinta da İyayenta. *** Tana zaune a falonta ita da Hajiya Jamila sai ga yaro ya shigo ya ce "Halima wai ki zo inji Jamil". Nan da nan gabanta ya fadi, hankalinta ya tashi, ta ce "Yau na shiga uku, wai me yasa Jamil yake min irin wannan ne? Bari inje in gayawa Alhaji kawai". Ta mike ta nufi dakin Alhaji. Hajiya Jamila ta kalleta ta tabe baki, ta ce "Kya san ta dai da shegen munafurci sai ta je ta gama masha'arta sannan ki dawo kina mazurai, in ya biyo ki gida ki rude, ai da can ma sirinki zai toni wato kin je kin yiwa Alhaji asiri ya komo da ke, zaki koma kan harkar ki?" Duk wannan maganganun a zuci ta ke yinsu, don haka Halima bata san da su ba. "Alhaji ka ji wai Jamil ne ya komo yana kirana, ni dai na shiga uku Alhaji ya zan yi?" Sai hawaye shar a fuskarta. Alhaji ya ce "Yana ina?" Tа се "Yana can waje". Ya ce "Yi zamanki kyaleshi na 135 Kwadayı barıjana'- Amına Abdullahı Sharada karbi rigimar a hannuna, bara in fita". Nan da nan ranta ya yi mata sanyi dama tsoro ta ke kar ya sake korarta. Yana fita falo Hajiya Jamila ta ce "Yanzu Alhaji fita zaka yi, bayan ta gama iskancewarta, sannan zaka fita ka yo me? Ai a daukeka kaima marar mutuncin?" "Kin ga babu abinda ya shafe ki da wannan maganar, ni ba na son shisshigi kin ji ko?" Nan fa ranta ya 6aci, ta fara maganganu amma ko kallonta bai yi ba, ya ficce. Zuwa ya yi ya tsaya a wajen Jamilu ya cẽ masa "Ina son muyi maganar fahimta da kai, ka ga wannan maganar bata yara ba ce, ka je ka turo mahaifinka, da shi za a yi wannan maganar ka ji ko? Domin ni bana so ka dinga zuwa kana sallama da matata, in baka turo shi ba, to ni zanje". Ya ce "Zan turo shi, amma wallahi koma me za a yi sai an bani 'ya ta". Ya ce "Eh, na ji amma ka turo shin. "Wawan banza a ina 'yar taka ta ke za a baka, wa ya san inda ta ke? Kai in banda ma sha-sha-sha har ka zo ka ce wani kana son 'yarka to a wurin wa? Kar in kara ganinka daga yau, maza ka bace min daga nan, in ba haka ba wallahi zan sa a kama min kai". Ya ce "Na ji zan bar maka kofar gidanka, to amma wallahi sai Halima ta fito min da 'ya ta". Ya ce "Oho dai". Ya juya ya koma gida yana fada. Shi ko Jamil yana komawa gida, sai kawai ya 136 Kwadayi ban jana!- Amuna Abdullahı Sharadа tafi gidansu wajen mahaifinsa Alhaji Ali, yana kuka, wallahi shi fa sai an bashi 'yar sa, ran Alhaji Ali ya yi mummunan baci, ya ce "Wai kai Jamilu ko ka fara shaye-shaye ne? In ba ka fara shaye-shaye ba to me ya kawo haka?" Ya ce "Ai Alhaji Usaini ma ya ce ka je". Ya ce "Kar ka kara sa ni a cikin zancen banza marar tushe ka ji ko? Ko ni ma irin ka ne mutumin banza? Ba inda zan je duk abinda za su yi maka su yi maka". Nan ma ran Jamil ya kara baci, ya ce "Daddy wallahi ni na san ba zan taba samun haihuwa ba, domin ina da matsala babba, don haka nake son a samo inda ta kai yarinyar da ta haifa, ko Allah zai sa in samu". Alhaji Ali ya ce "Ta ya ya za'a iya samun yarinyar da aka 'yar sama da shekara sha takwas? Ai kai ma ka san ba za a samu ba, to amma akwai wani abu guda da nake tunani, hanya daya za a bi in an bita to kila a dace, hanyar dayar nan ko ita ce a tambayi ita Halima a ji a ina ta yar da yarinyar in ta fada sai aje gidan renon yara kafin nan za a yi kokarin jin mecece shaidar ita Halima, a lokacin da ta yar da jaririyar, in ta fada inda rabo sai ka ga an samu". Cikin tsananin murna ya ce "To ai kuma mijin Haliman ba zai amince inyi magana da ita ba, sai dai ku kuje". Ya ce "Na ji zan je wurin shi Alhajin inji". Ya ce "Yauwa Dad, to yaushe za ka?" Ya ce "A'a tunda na ce zanje ai zanje, yau zan ji bakin naci, ga 137 Kwadayı ban jang'- Amına Abdullahı Sharada shi nan duk ka bi ka rame ka kanjame tamkar wani mai wata cutar daban, haka kawai ka sanya kanka cikin tashin hankali, haihuwa ba ta Allah ba ce?" Yà ce "A gaskiya ni Dad sai sun bani 'ya ta". Ya ce "Shikenan sai ka yi ta yi, amma ina ji maka tsoron wannan iskancin da ka ke yi, duk ranar da aka се babu raina babu mai raga maka, domin a yanzu in kayi ana ganin idona, kuma ka ga kai kadai na haifa". Cikin kunan rai ya mike, bai ma tsaya ya saurari fadan da ake masa ba, ya fice abinsa, uban yana ganin ya tashi a fusace sai kawai ya mike ya nufi hanyar fita shima. Yana zuwa dai-dai lokacin da ya dauki motarsa sai ya dakatar da shi, ya ce masa bayan ya tsaya "Ка jira ni in fito sai muje". Nan da nan, cikin murna ya tsaya ya jira uban har ya gama shiryawa, sannan suka rankaya sai gidan Alhaji Usaini. Suna zuwa suka sa ayi sallama da shi, jim kadan ya fito yana fitowa ya yi arba da Alhaji Ali, cikin mamaki ya karaso gami da cewa "Alhaji yau kai ne a gidan namu?" Ya ce shi ma cikin mamaki "Dama gidanka ne nan?" Ya ce "Gidana ne Alhaji ku shigo mana". Suka bi bayansa ya jagabance su har kayataccen falon saukar baki, suka zauna yayin da ya umarci akawo musu dan abin motsa baki, nan da nan aka wadata su da kayan marmari mai kyau. Bayan sun kammala Alhaji Ali ya dubi Alhaji Usaini ya ce "Alhaji wannan rigimammen dan naka 138 6 Kwadayı barıjana'- Amina Abdullahı Sharada ne ya jajibo ni, wai akan wata maganar banza tasa marar tushe bare asali, dama abin da ya kawo ni duk da ban san cewa gidanka ne ba ma, to in mun zo in gaya maka cewa ka yi mana wata alfarma mai dakinka ta fada maka inda ta yar da jaririyar sai mu je can gidan renon yara mu sanar musu, da ranar da kwanan watan in ma akwai wata shaida sai mu tambaya ka ga shi kenan in su suka tsinta sai su bamu, in ma babu sai ya hakura, in ma ta mutu shi kenan, ka ga kowa ya huta, amma wannan alalafa ta Jamilu ta ishe ni kamar wani karamin yaro". Alhaji Usaini ya ce "Ai ba komai, bara ma inyi kiranta ta fada muku da bakinta". Ya mike ya shiga ciki. Yana shiga Alhaji Ali ya dubi Jamil ya сe "Amma Jamil ka ji kunya yau, domin Alhaji Usaini mutum ne duk da cewa na girme masa, muna mutunci abokin harkar kasuwanci na ne, don haka ban so abinda ya faru ya zamo a gidan sa ba ne....". Yana rufe baki sai ga Halima da Alhaji Usaini sun fito, Halima na janye da hannun 'yar ta Zainab, tana zuwa ta durkusa ta gaida Alhaji Ali, sannan Alhaji Usaini ya bata umarnin ta fadi inda ta ajiye yar da kuma in akwai wata shaida ta fada. Nan take Halima ta fara zayyana musu yadda ta haihu a wurin, sannan kuma ta nade jaririya da bakin mayafınta da ma wurin da ta haihun duk ta shaida musu, bata rage komai ba, sai dai ta mance kwanan R0 Kwadayı bari jana'- Amuna Abdullahu Sharada watan amma bata mance raanr ba. Cikin tsananin mamaki Alhaji Usaini ya mike tsaye ya ce "Alhaji ai yarinyar ma tana hannunmu, ai mu muka tsinci yarinyar!" Ba Halima ba, hatta Jamilu da Alhaji Ali sai da suka razana, cikin tsananin mamaki suka ce "Kamar ya ya Alhaji?" Ya ce "Bari in yi kiran Hajiya Jamila, za ku tabbatar da wannan maganar". Yana rufe baki sai ya shiga cikin gida da sauri. Jim kadan sai ga su da Hajiya jamila, bayan ta zauna suka gaisa sannan Alhaji Usaini ya ce mata "Ko mayafin nan baki da muka taba tsintar yarinya da shi, yana nan?" Ta ce "Yana nan a kasan akwatina". Ya ce "To maza dauko shi". Та се "То". Ta tashi cikin sauri ta dauko mayafin, a kulle cikin bakar leda, ta mikawa Alhaji Usaini. Ya karbi mayafin ya nunawa Halima, ya ce "Halima ko kin gane wannan mayafin ne?" Cikin rawar jiki ta mike la ce "Wannan ai mayafina ne wanda na rufo jaririyar da shi". Suna jin haka, suka yi kabbara baki daya, cikin mamaki Alhaji ya ce "lallai komai nufin Allah ne, Halima Maryam 'yar ki ce". Ta ce "Wacce Maryam din?" Ya ce "Maryam tawa ta Jamus'. nan da nan cikin firgita ta dafe kirji ta ce "Ya ta Alhaji?" Ya ce "Kwarai kuwa 'yar ki ce, domin kuwa ita na tsinta a cikin wannan bakin mayafin ranar sha biyu ga watan uku 12/3/1991". 1440 C Cikin doki Jamil ya ce "yanzu ina yarinyar?" Alhaji Usaini ya ce "Tana can gidan mijinta a Jamus har ma ta haihu". Alhaji Ali ya ce "To yanzu ya zamu yi kenan?" Alhaji Usaini ya ce "Waya zamu yi musu lallai su zo domin wannan lamari abu ne ba karami ba, tunda ita yarinyar har yau bata san cewa ba mu muka haifeta ba, ka ga kuma kafin mu saitata ta gane komai sai anyi da gaske". Ya ce "Haka ne yanzu dai zamu kyale komai sai in sun zo din ayi mana magana". Ya ce "Shi kenan ba komai". Har sun tashi Jamilu ya ce "Ko akwai hoto yarinyar a hannunku?" Ya ce "Hotuna kai, har ma da wadanda ta ke 'yar karama, har ma da wanda ta ke jaririya duk akwai". Suka ce "To idan da hali a ba mu wasu daga ciki". Nan da nan Alhaji Usaini ya umarci Hajiya Jamila ta kawo. Ita ko Halima mamaki ne ya hanata magana, sai tunani take kala-kala, har kowa ya fashe bata tashi ba, ita ma ta koma ciki ta samu Alhaji a falonsa yana zaune yana tunanin wannan lamari, ta sami wuri ta zauna ta ce "Alhaji dama ashe yarinyar nan Maryam 'ya ta ce?" Ya ce "Yar ki ce mana". Ta ce "To yanzu ya za ayi ta amince cewar ni ce mahaifiyarta?" Ya ce "A to nima yanzu abinda nake tunani kenan, amma ina ganin kamar zata amince sai dai yadda zamu tunkareta da maganar ne abin tunani". Ta ce "Ba ka ce zaka yi musu waya ba?" Ya ce "Waya yanzu ko zan buga musu". Ta ce "To ai in 141 sun zo sai ayi maganar a gaban kowa". Ya ce "Dama abinda nake so kenan,yanzu kira min Hajiya jamila" Ta сe "Тo". Ta tashi ta nufi dakin ta. Ta sameta ta hada kai da gwiwa tana ta faman kuka, karam ranta zai fita, cikin sanyin jiki ta nufi inda ta ke ta ce "Hajiya ki yi hakuri dama wannan abu dole sai an yi hakuri, wai ki zo inji Alhaji". Ва magana ta mike ta bi bayanta, suna zuwa ya dubi fuskar Hajiya Jamila ya san cewa kuka take sai ya fara bata hakuri, gami da nasiha, sannan ya zauna ya warware mata abinda ya faru har Maryam ta kasance 'yar Jamilu da Halima, sannan ya dora da cewa "Wannan abu kaddara ne don haka ki kwantar da hankalinki, insha Allahu komai zai zama kamar bai taba faruwa ba". Anan Halima ta yi ma Hajiya Jamila alkawarin Zainab in har aka gama wannan rikita-rikitar, zata bata ita har auranta, nan da nan Hjiya Jamila ta dan saki ranta, dama sun saba a tafiyar da Halima ta yi ta barta. Yau dai gidan Alhaji Usaini cike yake kaf da baki, wato su Alhaji Gambo da Alhaji Hassan, can kuma gefe daya Alhaji Ali ne da Jamil, nan kuma Baba ne da Yalwa da Baba Abu, can kuma Bashir ne da Faruk, sai kuma su Hajiya Jamila da Maryam da Halima suna zaune, domin tattaunawa akan abinda yake faruwa wwanda ya janyo kiran wannan mitin na gaggawa, domin a san yadda za a 6ullowa lamarin. 142 C Kwadayı harijana Amuna Ahdullabu Sharada Alhaji Usaini ne ya fara jawabi kamar haka: "Jama'a 'yan uwa da abokan arziki, assalamu alaikum". Bayan sun amsa sallamar ya ci gaba da cewa "Walo abinda ya tara mu baki daya anan, shi ne akan wata 'yar matsala da ta taso, matsalar kuwa ita ce, shi wancan yaron Jamil shi ya dinga zuwa nan aeman 'yarsa a hannun Halima wanda zuwansa na farko sai da ya yı sanadin na dan bata hutu ta je gida, saboda, bacin ran abında ta yi min, to bayan na huce na komo da ita sai ya kuma ci gaba da zuwa har dai na aike shi ya turo min mahaifinsa domin wannan maganar sai da manya Bayan ya zo ne na ga ma ashe na san shi, muna matukar mutunci da shi, to a wannan zuwan da suka da shi ne muka gano cewa ai Maryam 'yar Jamılu ce, domin mun gane a inda muka tsince ta anan uwarta la haifeta ta barta, wato Halima, kuma har shaidar mayafinta duk ga su don haka na tara ku anan domin mu warware wannan lamari cıkin maslaha ba atre ad zuciya ta sosu ba". Har ya gama bayaninsa, Maryam bata san inda aka dosa ba, domina zatonta ba ita Maryam din ake nufi ba, don haka ta zunguri laruk cikin rada ta ce masa "Faruk mu me ye namu a ciki aka kira mu?" Ya ce "Ke dai ki kasa kunne ki ji komai". Ta ce "To". Kamar Alhaji Usaini ya san abinda ake nufi, don haka sai ya ce "Maryam ina so ki tuna cewa imanin mutum baya cika sai ya yarda da abubuwa guda shidda, su ne a turance a ke kira Sid Aticle of path, cikinsu kuwa har da imanı da kaddara mai kyau da marar kyau, don haka in har ka yi imani da wannan to ka zamo mai 143 Kwadayı bari jana'-Amına Ahdullahı Sharada cikakken imani, abında nake so da ke kuma nake so ki fahimta shi ne, ina so in sanar da ke abinda baki sani ba. ban san yadda zakı dauki abin in kin ji ba, to amma in kinyi hakuri kuma in kinyi imani da kaddara mai kyau da marar kyau, to abin zai zamo miki mai sauki". Tuni Maryam ta gano abinda ya ke nufi, tun bai karasa bayaninsa ba, ta ce "Abba na riga na fahimci abinda ka ke so ka ſaďa min, kana nufin ni ba 'yarka ba ce kenan ko?". Ya yi murmushin karfin hali, domin bai san ma abinda zai ce mata ba, ai abinda nauyi ya ce mata eh, ta ce "Ko ba a bani anısa ba ni na gaen domin ina da hankalina, ni yanzu so nake a nuna min waye mahaifin nawa kuma ta wacce hanya aka same ni?" Cikin sanyin jiki Alhaji Usaini ya nuna Jamil, ya ce "Ga mahaifinki nan Maryam, kuma ko ma ta wacce hanya aka same ki, ni ba zan iya fada miki da bakina ba, shi ya fada miki". Ba wanda bai zubawa Jamil ido ba, kuma nan take suka fahimci lallai shi ne mahaifin Maryam, domin suna kama, kuma ga zahii babu abinda ya raba su da dan Maryam din, wato Saddik. Jamil cikin sanyin jiki ya ke maganar kamar haka "Maryam ki yi hakuri kamar yadda Alhaji ya fada miki, komai mukaddari ne, ba sai na fayyace miki komai ba, za ki gane don haka ki yi hakuri ni ne mahaifinki, kuma bani da kowa sai ke kadai na mallaka, don haka ki yi min afuwa Maryam, a lokacin da haka ta faru babu mai wadataccen hankali a cikinmu, saboda haka ki yi hakuri". Hankalin Maryam ya yi mummunan tashi, fuskarta ta yi duhu, ranta ya baci, ta yi wata iri nan da nan sai hawaye ya fara zubo mata. 144 Kwadayi barijana!- Amuna Abdullalu Sharada Cikin kuka ta ce "Abba ba komai ne ya dame ni ba illa yanzu na san makiyina, kowa ma ya sani, to amma ya Faruk zai dauke ni domin na san abinda ya sa Alhajin su Bashir ya ki aure na da Bashir kenan, amma a wancan lokacin ban gane ba, to amma a yanzu ya ya batun aurena da Faruk zai ci gaba da zama da ni a wannan halin ko kuwa shi ma zai guje ni ne? Abinda ya sa na yi wannan tambayar na san wannan shi ne mahaifina, ma'ana na amince, to amma ai ba a wurinsa zan zauna ba tunda na yi aure, ina wurin mijina. To amma ban sani ba ko shi mijin nawa zai amince ya zauna da ni bisa wannan hali na kasancewata ba 'yar halak ba?" Tana gama wannan magana Faruk ya cafe da cewa "Maryam ai tun kina aririyarki na jima da sanin matsayinki, dukkanmu habu wanda bai san matsayinki ba, tun ma kina ( jaririya don haka kar ma ki kuma sako wannan maganar ta wuce har abada, domin ni da ke mai raba mu sai dai mutuwa, sai dai in ke kika ki ni?" Nan da nan wuri ya dauki kabbara, sannan Maryam ta ce "Shi kenan na gamsu kuma na san Faruk kai masoyina ne". Alhaji Usaini ya ce "To ni yanzu jamil magana ta gaskiya ba zan iya baka Maryam a yanzu ba domin irin shakuwar ad na yi da yarinyar nan, Allah ya sani". Hajiya jamila ma ta ce "Ka ji Alhaji in ab don ni ba ya za ai yarinyar ta zo wurinka? Ka manta artabun da muka yi kafin ka amince a dauko ta?" Nan da nan ta shiga basu labari aka yi 145 Kwadayı barı jana Anuna dullahn Sharnda ta dariya, sannan ta ce "Kuma kowa ya san ni na rike Maryam ma'ana na rene ta nima kuma ba zan iya rabuwa da ita ba har sai mai rabawa ta raba". Jamil ya ce "Duk na ji wannan batu naku, tunda dai kowa ya shaida Maryam 'ya ta ce kuma ga ta hanyar da aka same ta, Maryam bata da gadona, to amma na raba duk abinda na mallaka biyu na bata don haka da shirina na zo, ga takardu nan zan sa hannu, duk shedar sa hannu ga iyayenmu a zaune". Nan ya fito da takarda, aka dinga rattaba hannu, duk sai da ya raba dukiyarsa kaso biyu ya baiwa Maryam sannan ya ce ta je ta ci gaba da zamanta a gidan mijinta, sannan in ta zo nan sai a dinga tura mishi ita yana ganinta, ya kara da cewa "Kuma a bani adireshin gidan su na Jamus domin ni ma ina zuwa can, sai in dinga ziyartarta in naje. Bayan haka kuma Maryam uwa-uwa ce Halima ita ce mahaifiyarki, wanda na yi imanin ba don an tilasta mata rabuwa da ke ba, da babu yadda za a yi ta kyale ki. Maryam ki yafe mana jefa ki wannan hali da muka yi, domin da munyi aure sannan aka sameki da duk haka bata faru ba, ni yanzu na fi kowa bakin cikin wannan abu, domin a yanzu bani da da sai ke, kuma ke din ga yadda ta kasance, hakan ya jefa ni a cikin dunbin nadama domin da ace ban bi wannan hanyar ta yaudara har aka same ki ba, da yanzu ke ma halatacciyar 'ya ce, to amma ina kira ga sauran mutaen masu hali irin nawa da su daina domin 146 Kwadayı barıjana', Amuna Abdullahı Sharada gudun afkawa hali irin nawa. Na san Allah ya jarabce ni da son da domin na samu kuma na wulakanta, don haka jama'a ayi hattara a gujewa shiga hanyar halaka, a gujewa shiga haramtacciyar hanya". Yalwa ta mike cikin kuka ta cc "Jamilu ba kai kadai zaka yi wannan gargadin ba, har nima domin duk abinda ya faru NI CE SILA, don ni na janyo muku shiga wannan halin. Saboda son abin duniya irin nawa, inda ace tun farko na tsawatar ai da haka bai samu ba, to ina anin ana cika min baki da kudi, sai ga shi na saki duk wata hanya ta tarbiyantar da yarana KWADAYI YA JA NI! A sakamakon haka ya ana biyu na rasa ta hanyar da bata adce ba, kunga ko ince mai tsawatarwa maceya kamata inyi wa nasihar su daina, domin gudun fadaya halin da ni na tsinci kaina". Alhaji Ali ya ce da Maryam "Maryam ni Kakanki ne wanda ya haifi Mahaifinki, saboda haka ina so ki yi hakuri da abinda ya faru, ni ma tawa nasihar kenan". Malam Usman ma ya gabatar da kansa ga Maryam, sannan ya ce ta bi mijinta sau da kafa, kar ta yarda ta saba masa, domin mai kaunarta ne, tun da bai aureta ba sai da ya san halin da take ciki, kuma bai taba nuna mata ba, in ba yau da ta ji ba. Nan dai taro ya watse kowa na mamakin wannan abu. Malam Usamn ya koma gida shi da Yalwa suma su Alhaji 147 Kwadayı han jana- Amuna Abdillaln Sharada Ali suka koma shi da Jamil, Alhaji Gambo da Faruk suka koma na su kasar. Maryam ce zaune tana kallon yaronta Saddik duk jikinta a sanyaye ta ce a ranta "Hakika Saddik yana kama da mahaifina". Tana cikin wannan tunanin ne Faruk ya shigo, ta dube shi ta ce "Faruk ina

Chapter 11 of 12