Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ba ku amma ku bar min yarona, lafiya ba ta ishe shi ba," ta fada tana shesshekar kuka. Daddy dake kwance duk addu'ar da ta zo ranshi yake karantawa. *** Gudun ceton rai take yi kamar za ta tashi sama, ban da bambancin halitta ta mace da na namiji ba za ka taba cewa wannan mace ce ke zuba uban gudu akan mashin ba. Sai da ta yi tafiya mai nisa inda ta tabbatar ta yi musu nisa kafin ta dan rage gudu. Anas ta kira yana dauka ta ce masa, "Kana ina?" ya ce; "Ga ni hanyar gida," "Yawwa ka same ni yanzu a gida, yanzu fa!" ta ce cikin karaji. "Beb I hope babu matsala?" "Ka zo din please," ta kashe wayar har ta kama hanyar gida ta sake tunani wayar ta kuma cirewa ta kira shi, "Mu hadu a Gamji gate," "Ok," ya kuma fada. Amrah ta canza akalar mashin din ta dauki hanyar Gamji gate a kusan tare suka iso ita da Anas domin tana tsayuwa ta hango motarshi. Da sauri ta sauka daga kan mashin din ta fada gaban motarshi. Nikabin ta cire ta ajiye tare da hijabin ta hau sauke numfashin gajiya. Anas ya bi ta da kallo yana murmushi, "Beb, Beb, ba ki gajiya fa yau kuma me ya faru?" "Ruwa!" ta ce mishi. Anas ya miko.mata sauran ruwan da ya sha a gora. Amrah ta karba ta shanye tas! sannan ta yi ajiyar zuciya. "Dear mashin din nan yau ya gama aikinsa a san yadda za a yi da shi." Anas ya kalle ta fuskarshi 90 AKWAI KURA cike da son jin dalili ta ci gaba da magana, "na san an dauki mumber na mashin din a kowanne lokaci jami'an tsaro za su iya neman shi. Anas ya shafa gemunsa, "Yau ita ce karo na farko da na ga tsoro a fuskarki Beb, me kika aikata?" Amrah ta hada girar sama da ta kasa, "Ka san dai ba zan yi kisan kai ba ko?" Ya yi dariya, "Ni ma ban ce ba kawai ina son sanin me kika yi ne don in san ta yadda zan bullowa al'amarin." Amrah ta sanya hannu cikin aljihunta ta mika masa bindiga, "Na gode sosai da ba ni taimako cikin kowanne hali," Anas ya yi tsai da ido a kanta, "Beb me ya sa har yau in na yi miki tambaya sai ki canza tambayar da wata? Hm! Ka ba ni lokaci ni da kaina zan sanar da kai komai, bayan na gama cinma nufina." "Ok mu je in sauke ki a gida, mashin din ki bar shi a nan duk wanda ya dauke shi rayuwarshi na cike da tambayan 'yan sanda, mu je kawai bar shi gurin tun da ya gama aiki, neman kai ake da shi yanzu." Amrah ta yi dariya "Dadina da kai akwai saurin gano mafita, mu je ka sauke ni gida ina son canza kaya in koma gun aikina." "Kuma?" Anas ya kuma fada, "lallai zan auri jaruma ba irin matan zamani ba masu son jiki ko girki ba su iya ba. *** Tun da ta dawo gidan ta fahimci ba su dawo ba, hankalinta ya kwanta, kicin ta wuce kamar daga asibiti take ta fara aikin abincin dare. Ta kai minti ashirin da fara aikin kafin ta fara jin hayaniya. Duk hayaniyar dake faruwa a gidan tana jin su ita dai tana kicin tana ci gaba da aikinta ko alama ba ta nuna ta san wani abu na faruwa a gidan ba. Grace ce ta shigo kicin din cikin damuwa ta sanar da Amrah abin da yake faruwa da oga a hanyar dawowa gida daga asibiti. Amrah ta zare ido ita ma cikin damuwa tare da addu'ar Allah ya tsare na gaba. "Maman Affan, Maman Affan," Mommy ta kwala mata kira daga side 91 AKWAI KURA na Saleem. Da sauri ta rage gas din don kada abincinta ya kone ta haura saman Saleem din. Har kasa ta tsuguna ta gai da Mommy tare da yi mata Allah ya kyauta akan abin da ta samu labarin ya faru yanzu. Mommy ta shafa kanta "Ashe ke kin riga kin dawo gida, Mera ta fada min Alhamdulillahi Allah ya tsare ki,ba rabon za ki ga tashin hankali." Amrah ta yi dan murmushi ta mai da hankalinta kan Saleem din dake zaune kasan kafet yana shan lipton karamin cup cike da girmamawa cikin muryarta mai zaki ta ce da shi, "Oga jarumi, Allah ya kiyaye na gaba Allah ya kuma tona asirin mugu a duk inda yake." Ba ga Saleem kadai ba hatta Maheer sai da ya juyo daga kujerar da yake kwance ya kalle ta tare da amsawa, "Amin amin Thanks," Saleem ya furta a hankali. Amrah ta dube shi da mamaki a kan fuskarta da ma akwai abin da zai sassauto da zuciyar wannan mugun? Ta yi murmushi a ranta lafiya uwar jiki wato ciwo ya fara dawowa da shi saiti. Mommy ta katse mata tunani, "Ki kara abinci kin ga gidan namu yau akwai baki kuma ki dan yi wa Saleem pepesup na kaza mai dan yaji ki soya masa arish yanzu please." "No Mommy dambun kaza nake sha'awar ci irin wanda kike yi mana shi nake bukata." Mommy ta rike haßa, "Son wannan bakin da muke yi 'yan Allah kyauta ina ni ina wani shiga kicin?" "Mommy ba komai bara in yi masa, na iya." Amrah ta fada. "Yauwa 'yar albarka je ki ki yi masa kada ki makara ki yi magana wa Mera na falona ta dan taya ki wani abin kada aikinki ya kai ki dare." "Ba komai Mommy zan iya," ta kuma fada. "Shikenan agogo sarkin aiki je ki kada ki makara." Amrah ta mike don barin falon. Ga mamakinta Saleem bai ce a'a ba kamar yadda ya saba ba ya cin abincinta Maza an ji jiki ta fada a ranta kafin ta bar musu falon. Mommy ta mike ita ma, "Bari in je in dan samu ruwan zafi in watsa ko zai rage min gajiya." Maheer ya hau tsokanar ta, "Mommynmu ki kwanta 92 AKWAI KURA ki yi baccin gajiya ki rabu da wannan tuzurun yanzu kam ai muna gida babu abin da zai taba miki shi," Mommy ta yi dariya, "Ai tuzuruan dukkanku ne, ni dai Allah ya nuna min ranar aurenku." Saleem ya ce; "Amin! Mommy na gode miki ai shi ma matsayinmu daya." Fitar Mommy ke da wuya Maheer ya sauko kasa, "Abokina alamu sun nuna ita ce ko?" Saleem ya rike gashin kanshi, "wa ke nan?" "Mai mulkin ranka ita ce yau ma ta kuma taimakon mu." "Yes she is." "Ba muguwa ba ce," Maheer ya fada. Saleem ya kada kai, "ban san ta a cikin layinsu ba tun last time bare dis time da ta zamo ita ce silar kauce kaddararmu," ya tsai da idonshi kan Maheer, "abokina ina zan gan ta? Lallai ina son in san wace ce ita." Maheer ya dafa kafadar Saleem, cooldown za mu nemo ta duk inda take a fadin kasar nan jikina na bani kuna tare always," Saleem ya kada ido alamun tambaya. Maheer ya gyada kai, "I mean ita ma kana cikin rayuwarta akwai lokaci abokina kawai mu ci gaba da addu'a." Maheer ya canza maganar, "wannan wadda ta fita wacece ita?" "Oh! 'Yar aikina ce." "Very beautiful gaskiya ta yi ba karya ba don akwai Babyna ba da na zago ta nan." Saleem ya yamutsa fuska, "Kun cika son mata, ai sai ka je in ba ka da M." Maheer ya yi dariya, "Mata ai abin so ne in ban so mata ba maza zan so?" Saleem ya kauda kai tare da lumshe ido alamun bacci, "lets sleep." *** Gaba dayansu suka mike daga kwancen da suke, dukkansu suka rungume Saleem suna kuka don jin dadin arzikin da ya auna a karo na biyu. A daidai lokacin ne jami'an tsaro suka iso gurin Saleem ya daga musu hannu, "Ku je kawai ba mu bukatar taimakonku," ya fada cikin fada, "ku je ba ma so yanzu ku me za ku yi mana? Ashe da ma hakan kuke aiki a banza kuke karbar salary ba ku san kan aikinku ba?" Gaba dayansu hakuri suka shiga ba wa Saleem don sun san in har bai huce ba to fa kowa zai shafi aikinsa. Bai saurare su ba illa 93 AKWAI KURA waya da yake amsawa daya hannunsa rike da bindiga da suka Kwace a hannun farayin. Jiniya ce ta motar asibiti ta karaso gurin tare da rundunar motocin custom da na soja suka iso gurin cikin kamewa daya bayan daya suke sarawa Saleem, Ku kai su asibiti ina bukatar su samu lafiya, wannan ba aikin ku ba ne aikina ne da kaina in gano wa ya turo su, lallai zan gano shi ko ma wane ne ko da yana cin kasa ne lallai ni Saleem Jarumi ni zan gama da shi da hannuna," ya yi murmushin gefen baki. Maheer ya yi umurni a sanya su a mota, Daddy na rike da hannun danshi gani yake kamar wani abu zai kuma samun shi ji yake kamar ya maida Saleem ciki saboda kulawa. Mommy da su Mera su dai kuka suke ta yi tare da godiya ga Allah da ya tsare su duka. A motar Maheer Daddy ya ja su Mommy da Aunty Mera su ko Saleem a motar su ta wajen aiki suka karaso gida, su Maheer da Ahmad tare da rundunar tashi dake take musu baya. Ahmad ya fi kowa cikinsu damuwa kan abin da ya faru, "Abokina wa ke son kashe ka? Mun shiga uku wa muka tarewa gaba yake son gamawa da mu?" Maheer ya kalle shi, "Ai ba mu ake son gamawa ba jarumi ake son kashewa, abokina ya ya kake magana kamar ba jami"in tsaro ba, ni da kai wa ya taba mu? Ai duk alamu a fili suke ya nuna JARUMI ake son kashewa. "Shi dai Saleem kala bai ce da su ba illa numfashin 6acin rai dake cirewa tare da kudura niyyar ko ma waye tabbas ya taro match. *** A bakin gate na farkon shiga gidan nasu ya sallami duka matakan tsaron Saleem ya juyo kan abokan nashi, Ku ma ku je ku samu hutu." Ahmad ya ce; "Maheer mu je ka sauke ni gida." Maheer ya ce; "Ka wuce da motar mi ina tare da abokina mu je ai motar na ciki da ita Daddy ya dawo." Ahmad 94 も AKWAI KURA da hankalinshi ba ya jikinshi sai wutsil-wutsil yake da ido alamun damuwa. Saleem na hankalnce da shi ya sassauta murya, "Abokina ai mun saba karon-battar karfe da abokan gaba wannan ba komai ba ne ka je gida kawai." Ahmad ya yi murmushin yake, "Mu je in dauki motar." Da kafarsu suka taka cikin sauran gate din har suka kawo gate na karshe da zai sada su da cikin gidan, a farfajiyar gidan Daddy da Mommy da kowa na cikin gidan suka tarbe shi haka ma'aikatan gida har masu gadi ko ina sai Allah ya kyauta suke yi masa. Shi dai Saleem, "Na gode, na gode," ya ke ce da kowa. Sannan ya wuce side nashi. Maheer na take masa baya tare da sauran 'yan uwansa. *** Karfe biyar da rabi na yamma ta kammala dukan girkin nata har da dambun naman kadan ta gama, bayan ta kammala ne ta raba gida biyu ta raba ta nemi tangaran mai kyau manyamanya ta zuba. Amrah da yawa ta dan yi shi saboda ta yi har da Mommy da Aunty Mera. Daya daga cikin naman ta dauka da kanta ta yi sallama falon Saleem. Ga mamakinta Saleeem na kwance na bacci, Maheer kaďai ke zaune yana kallo a katuwar talabijin dake manne jikin bangon falon. Sallama ta shiga dakin, sannu da hutawa ta yi masa kafin ta ajiye dambun ta juya za ta fita, Maheer da ya kura mata ido ta baya yana yaba kyan halittarta ya sanya baki, "Yanmata ya ya sunanki?" Amrah ta tsaya ba tare da ta juyo ba ta dan yi jim kadan sannan ta ce; "Zainab." Maheer ya ce; "Kai Zainabu Abu, tsohuwa ce ashe to mun gode da delicious." kasancewar sunan kakar shi ce wadda ta haifi mamanshi, Zainabu. Amrah ta fita daga dakin tana murmushi tare da yaba saukin kanshi duk da bai san ta ba amma ya yi mata wasa, a ranta ta ce; 'Alhmdulillah da ba su taba haduwa a gun besty ba da yanzu asirinta ya tonu duk da bestyn ta kai mata shi sau biyu gidansu amma ko rana daya ba su taba samun ta a gida ba 95 AKWAI KURA sai dai su gai da Granny. Amrah ta koma kicin da kanta ta dauki daya tangaran din ta yi side din Mommy don kai mata nata yayin da Grace ta fara kai abinci side na Mommy kamar yadda yanzu take yi. Ba ta tsaya hira ba yau kasancewar a gajiye take, ita kanta tana bukatar hutawa. Bayan ta gai da Mommy ta tsuguna ta ajiye mata tangaran din. Mommy ta washe baki tana yi mata sannu tare da yi mata godiya, "Maman Affan ai da kin mika masa." Amrah ta ce; "Mommy wannan naki ne na kai wa Oga nashi." Mommy ta rike baki tare da jawo tangaran din ta bude. Kamshi ne ya cika falon. Da sauri Mommy ta damki dambun ta kai bakinta tana kada kai alamar gamsuwa tare da jinjinawa Amrah wajen kwarewa akan wani irin girki, dambun ya yi dadi sosai har ya fi natan da take yi musu dadi, a ranta ta ce, 'In ma son bai ci ba ai gaba ta kai ni sai in hada duka in ci dadina.' Godiya Mommy ta shiga yi mata tare da sanya mata albarka kamar kyauta ta kawo mata Amrah ta sunkuyar da kai tana murmushi tare da jin dadin addu'ar da Mommy ke yi mata, "Amin," ta ce tare da yi mata sallama ta fice daga dakin, har ta fita sai ta dawo ta ba Mommy sako a gaida Maman Affan in ta tashi daga baccin firgici tare da yaronta Affan. *** Amrah tana fita Maheer ya tashi da kanshi ya shiga karamin kicin dake side na Saleem wanda yake dauke da 'yan abubuwan amfani kamar cokali da dan fulet na dai bukata in ta kama ba sai ka fita falo ba ya dauko karamin sosa na gilas tare da karamin cokali na shan shayi five alive yadauko mai sanyi a firjin kicin din sannan ya dawo falon. Dambun ya bude tuni kamshin dambun ya karade falon, Maheer ya fara hadiyar miyau, kut! Kut! Cikin zakuwa ya dibi dambun da dan dama ya zuba a filet din sannan ya matsa da sauran gefe, kasa ya sauko ya zauna a kan kafet ya fara cin dambun, 'Wai wai, dadi ke nan,' ya fada a ranshi tare da ci gaba da cin dambun kamar AKWAI KURA mayunwaci yanaci yana gyada kai alaman dadi ya tafi da shi. Sai da ya cinye tas! Kafin ya dauki lemon ya sha. Tangaran din dambun ya kuma ja ya bude ya kara a filet din, wannann karon a hankali yake ci yana jin dadin shi. Saleem ya bude ido ya sauke shi kan Maheer. Murmushi suka yi wa juna duka. Saleem ya kalli filet din gaban Maheer, tuni ya tuno da mafarkin da ya gama yi yanzu nata akan ta kawo masa dambun kaza. Abin ne yaba shi mamaki ganin da gaske dambun kaza ne a gaban Maheer. Cikin dakiku kadan ya fara tariyo mafarkin nashi. Yau ma kamar kullum sanye take cikin riga da wando fuskarta rufe da nikabi tare da babban hijabi ya rufe mata jiki har kasa sai dai ko kadan shigar tata ba ta 6oyewa baiwar kyan jikin nata ba kirar coca-cola shape. A hankali budurwar ta tako ta zo har gabanshi ta tsaya. Fuskarta kunshe da nikabi, Saleem ya yi murmushi alamar jin dadin ganin ta. Hijabinta ta bude ta zo gabanshi ta ajiye masa kwanon dambun nama cikin muryarta mai dadi ta ce masa, "Jarumina tashi ka ci abinci ba ni son zamanka da yunwa ka ga wannan dambun kazar da hannuna na yi maka na ga kana kaunar shi." Saleem ya riko hannnunta yana murmushi "Thanks jarumata matar jaruma to a dan bude min fuskar mana in gani, in ga kyakkyawar fuskar matata ko?" ya daga mata gira tare da murza zara-zaran yatsun hannunta masu kyau farare tas. Cikin dariyarta mai sauti ta daga nikabin za ta bude fuskar tata ke nan sai karar talabijin da Mahir ya kara ta tashi Saleem daga mafarkinshi mai dadi ba tare da ya ga fuskar tata ba. "Mitsw," ya ja tsaki yana hararar Maheer, "dan iska ka raba ni da abar kaunata ban ga kyakkyawar fuskarta ba." Maheer ya hau yi masa dariyar shakiyanci, "Sorry abokina ban sani ba da na bar ka kun sha soyayya." A kasalance Saleem ya mike ya shiga bayi, wanka yake yi zuciyarshi cike da nishadi tare da sauri-yana cikin dokin son cin dambun kazar. Bayan ya gama wankan, alwala 97 AKWAI KURA ya dauro don lokacin Magriba ya gabato cikin shirinsa mai kyau na hap jamfa blue mai aikin ruwan zuma ya fito daga ciki hannunsa rike da kum yana taje gashin kanshi. Cikin nutsuwa fuskarsa cike da nishadi ya jawo tangaran din dambun naman kazar, yatsunsa uku ya sanya ya fara kai wa bakinsa. Ido ya lumshe alamun dadin naman na ratsa kwanyarshi Maheer dake zaune shi ma ya sauko ya sa hannunshi suna ci suna shakiyancinsu tare da yaba dadin dambun kazar. *** Karfe tara daidai ya faka matorsa a harabar asibitin cikin kasaita da izza yake taka kasa kamar ba zai tafi ba hannunsa daya still daure da bandeji, waya ya ciro ya kanga a kunnensa, maganar minti biyu ya kashe wayar. Da sauri doctor din ya karaso gurinsa, "Ranka ya dade barka da dare kai ne haka yanzu? Ya ya jikin?" ya fada cikin tausaya. Saleem ya amsa, "Da sauki mu je ko?" Likitan ya ce; "Bismillah ranka ya dade." Ya shige gaba Saleem na biye da shi a baya. Daki mai lamba 16 likitan ya nufa. Jimawa Saleem ya ce da shi. Likitan ya dawo baya da sauri yana sunkuyar da kai alamar girmamawa, "Je ka ka yi aikinka in na fito zan neme ka," "То ranka ya dade," ya kuma fada tare da barin gurin. Saleem ya yi jim na second daya sannan ya sanya kafarshi hanyar dakin. A daidai kofar shiga security ne uku ke gadin dakin. Da sauri suka kame alamar girmamawa ga Saleem tare da mika masa gaisuwa, kamar ba zai amsa ba ya amsa gaisuwa tare da dosat shiga sakin da sauri. Daya daga cikinsu ya bude masa kofa ya shiga dakin. Gado ne guda biyu a dakin mai dauke da katuwar talabijin manne a bango sai toilet shi ma guda biyu kowa da nashi haka firji guda biyu ne a kusa da kowanne gado tare da katuwar loka ta sanya abin ajiya cikinsu,da alama dakin na musamma ne, gefen kowanne gado security ne daya rike da bindiga. Shigowar Saleem gabadayansu suka kame tare da kai 98 AKWAI KURA gaisuwa. Saleem ya kalle su, "Ku jira ni a waje ina fitowa." "Ok Sir." Tsayuwar minti biyu bai ce da kowa kala ba a cikinsu, kallon su yake yi cike da nazarin su haka su ma suka tsura masa ido cike da rashin tsoro. Saleem ya karasa jikin gadon, daya daga cikinsu kafarsa daya ya dora a kan gadon yana yi masa kallo cike da izza, "Jarumi za ku kashe ko? Tabbas jarumi zai mutu amma in kwanansa ya kare amma ba a hannun kananan ‘yan iska irinku ba, wa ya turo ku?" ya furta tambayar cikin karaji. "Oga ba wanda ya turo mu,"1," wanda ke daya gadon ya fada. Saleem ya kai masa mari mai cike da kara, "Don ubanka kai na tambaya na ce kai na tambaya dan ubanka?" ya shako wuyan rigarshi, "kai karamin dan iska ne tun da har yanzu ka da kashin wani kake 'yan uku naira goma Becareful," ya fada tare da cakumo wuyan wanda ya fara tambaya, "kada ka bata min lokaci answer me, wa ya turo ku?" "Oga mu muka turo kanmu," ya fada cikin nuna rashin tsoro. Saleem ya shako wuyansa ya kai masa 6arin makauniya, "wane ne kai da ka yi yunkurin kashe ni? Wane ne kai, ko ubanka? Kai duk zuri'arku sun yi kadan a biya fansar raina da ku, za ku sanar da ni wa ya aiko ku ko sai na sanya bindiga na tarwatsa daya kafar taku?" ya fada cike da murya mai karfi."Ko kashe mu za ka yi oga ba za mu fada ba, kowa ya tuba don wuya babu lada ai akwai amana." Saleem ya yi murmushin gefen baki, "Za ku fada daga karshe kuma in kashe ku sai dai bakin naku na rashin kunya shi zai fada," ya sanya hannunsa a aljihu ya ciro bindiga yana kada ta, bai ce kala da su ba ya juya zai fita. Sai da ya kai bakin kofar ya kuma juyowa, tas! Tas! Tas! ya sakarwa kowa bindiga a daya kafar, dakin ne ya dauki kara tare da karae shegun biyu na azaba, "Za mu fada, za mu fada. Saleem ya sanya kanshi ya bar dakin yana huci. 99 AKWAI KURA Sintiri yake ta yi a dakin ya kasa samun nutsuwa, hankalinsa in ya yi dubu ya tashi bai taba jin tsoro muraran irin na yau ba yadda ya ga safiya haka ya ga dare bai runtsa ba. Mafita kawai yake nema, ya daga kai ya kalli agogon dake manne a dakin nashi, karfe uku daidai na dare. Ko alamu babu na bacci a cikin idon nashi sai damuwa. "Saleem kai wanne irin shaidani ne, komai na sanya a gaba sai ka yi kokarin ka lalata shi? Ba zan bar ka ba Saleem ba zan bar ka ba. raina fansa ne a kanka ba zan taba barin ka ba har sai na ga bayanka, yadda kake son ka ga bayana ni ne nan sai na ga bayanka dan shegiya," ya fada da karfi kamar Saleem din yana jin shi. Matarshi ce ta shigo falon da gudu da alamar daga bacci ta farka, maganar Alhaji da karfi ita ta ta da ta daga bacci, "Alhaji lafiya me ya faru?" ta karaso ta rike hannunsa, "Raina fansa ne a kan shi," ya kuma fada yana kallon ta. "Wane ne shi? Ba dai Saleem ba?" "Akwai wani bayan shi ne wannan karon ba zan taва asarar kayana ba ya kuma rike kayana saboda dazu na samu labarin hakan ina bacci aka tashe ni aka sanar da ni." ya fesar da iska mai zafi daga bakinshi wannan karon na daura niyyar sai na kai shi kasa ba zan bar Saleem ba, Matar tashi tahau shafa kanshi, "Wannan an yi dan tsinanniya yo in ba a shigo da irin wadannan kayan ba yaushe za mu samu kuzi a cikin kasar nan Nigeria? Ai rayuwar yanzu sai da hakan shuwagannin sun zame cinye duka daga su sai 'ya'yansu, in ban da ta hanyar shigo da hodar iblis ba za su taba ba mu kudinsu ba, yo na ga ba sata kake yi ba sana'a ce kuma ai in har gaskiyar ce me ya sa ba za a kama har da masu shan ta ba sai kai da kasuwancinka kake yi?" mitsw ta ja babban tsaki tana shafa kanshi cikin sigar lallashi. Ya yi lum a jikinta ya samu dan san yin zuciya. "Na rantse ni da Saleem sai dai mu yi mutuwar kasko." *** 100 AKWAI KURA Mommy da Daddy ke saukowa daga dakin Daddy a tare, hannun Mommy rike da jakar Daddy suna hira, da alama fita zai yi. Kai tsaye dinning table suka wuce don yin break fast wayam babu komai. Mommy ta kwalawa 'yar aikinta kira, "Hajara Hajara." Hajara ta fito da sauri tare da durkusawa har kasa ta gaida Mommy sannan ta gai da Daddy. Mommy ta kalle ta, "Yau lafiya ban ga break fast ba? Grace ba ta zo ba ne?" "Ta zo Hajiya." "Ok kira min ita." A tare suka shigo da Grace din ita ma Grace har kasa ta duka ta gai da Mommy da Daddy. "Grace lafiya yau har muka sauko ba a jera break fast ba? Maza ki yi sauri ki jera, Daddy zai fita yau da wuri." Grace ta kuma dukawa cikin ladabi, "Mai girki yau ba ta zo ba." Mommy ta kalli Grace da sauri, "Ba ta zo ba? Subhanallah lallai Amrahtu babu lafiya don ba ta taßa kin zuwa aiki ba ku je kawai zan neme ku, Daddy yarinyar nan ba lafiya jikina ya bani hakan don akwai ta da hazaka." Daddy ya ce; "Ah to in hakane sai a bincika a ji lafiyar tata, ina ce dai akwai wanda ya san gidansu cikin yaran?" Mommy ta gyada kai alamar babu, "Zauna Daddy bari in nema maka abin da za ka ci da sauri kada ka makara." Daddy ya jawota jikinsa "Mommyn yara na yafe miki yau kam na yi miki uzuri." Mommy ta kuma kwanciya a kirjin mijin nata, "Bari in dauko maka sauran dambun kaza sai in hada maka da 'yar juice mai sanyi ka yi manage da shi." Murmushi Daddy ya yi, "Na gode abar kaunata." Suka yi dariya duka. Mommy da kanta ta shiga kicin ta hada break fast tare da taimakon mai aikinta sai da ta kammala komai kafin ta ji motsin Affan da Mamansa suna saukowa. Mera ta karasa saukowa tare da gai da Mommy. "Lafiya lau," Mommy ta amsa, "yauwa tun da kin sauko bari in shiga wanka ki karasa shirya komai." "Mommy yau ina Maman Affan?" Mommy ta yi jim, "Wallahi ba ta zo ba ko lafiya? Allah Masani." Mera ta 101 AKWAI KURA zaro ido, "Ai kuwa ba lafiya ba Mommy don Maman Affan ba ta da wasa kan aikinta amma bari a kira ta a waya a ji lafiya." Mera ta kwalawa Zahra kira "Autan Mommy." Zahra ta amsa tana saukowa daga dakinta, "koma ki dauko min wayata a kan gado, don Allah ki yi sauri." Zahra ta juya dakin, ba ta jima ba ta dawo da wayar rike a hannunta. Mera ta dubo number Amrah ta danna kira har ta gama ringing ba a dauka ba, ba ta daddara ba ta kuma danna kira still yanzu

Chapter 8 of 12