Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
fashe da kuka tare da dannawa Amrah harara, "Mayya ki fita a zuciyar Mommyna, Mommyna ba ta taba yi min masifa ba sai a kanki, wannann dalilin ya sa na tsane ki," fu! Ta bar falon tana kuka. Amrah da ranta ya yi bala'in 6aci ji take yi ina ma a waje suke ta nunawa Zahra ita ma fa ba tayar baya ba ce, ta hadiyi wani yawu mai daci tare da hadiye fushinta, kafadarta Mommy ta dafa, "Ki yi hakuri Maman Affan, yarinta da rashin hankali ke damun ta, wate rana na yi imanin da kanta za ta ba ki hakuri bayan ta gane kurenta." Amrah ta yi murmushi dan kwantarwa Mommy da hankali. Tabbas Allah shi ke cire rayayye a cikin mamaci 67 AKWAI KURA kamar yadda yake cire matacce a cikin mai rai akwai kauna mai zafi na Amrah dake ratsa zuciyar Mommy, haka ita ma Amrah take son Mommy da a halinta saboda karamci da take nuna mata. Agogo ta kuma.kalla, "Zan wuce Mommy ina da uziri kada dare ya yi." Mommy ta shafa kanta, "A gai da gida Amrahtu ki gai da goggon taki." *** Bayan sallar Asuba kamar yadda ya saba kullum cikin shirinsa na training ya fito, jugging na gudu yau ta gabas ya mike sabanin arewa da ya ke bi kullum. Hakan kawai ya tsinci kanshi da son mikewa gabas. Hanyar ta GRA shafe take babu mutane kasancewar anguwa ce da ake rayuwar shiru ba sosai za ka ga mutane suna hayaniya ba kamar cikin gari. Saleem ya ci gaba da sassarfa hanyar da ya bi shiru ba ka jin komai sai kukan tsuntsaye sai kalilan jefi-jefin mutane da yake shigewa a kan titi. Sanye yake da riga ja mai gajeren hannu irin ta 'yan kwallo wato Arsenal sai wandonta ita ma kamfanin Arsenal sai facing cap mahadin rigar wanda ya kara masa kyau kasancewar su kalar ja. Da ka gan shi ka ga kakkarfan namiji mai cikar zati da siffar jarumta, ga wanda bai san shi ba zai dauka irin Turawan nan ne ko Larabawa don kowanne ka sanya shi cikinsu tuni zai saje da shi. Cikin gudunshi mai dauke da sassarfa yake jiyo kamar karar bindiga, hannunsa ya shafa cikin aljihunshi amma sai ya ji wayam babu bindiga, tuni ya tuno ashe ya bar ta cikin aljihun kayan da ya cire jiya na training, cike da karfin guiwa ya ci gaba da bin hanyar da yake jin harbin, a lokacin ne ya kara jin karar harbin sosai, yana dukan kunnuwanshi. Gudun nashi ya karawa kaimi don son iske inda yake jin harbin, babu tsoro ko kadan a zuciyarshi ya yi imanin in har hukuma ce shikenan sai ya yi tafiyarshi haka in barayi ne ya kudura a ranshi yau fa sai dai shi ko su. Mafi rinjayen zuciyarshi ta ba shi farayi ne don a hanyar gurin sam babu office na hukuma ko gurin training na hukuma a gurin 68 AKWAI KURA bare ya ce su ke koyar da yaransu harbi. Daga nesa ya hangosu kowa rike da bindiga, mace da namiji, ya gane macen ce ta siffan halittar ta dake da bambanci da na namijin, cikin su biyun kowa fuskarshi rufe take ta mask sanye suke da riga da wando iri daya mai tambarin arsenal jajaye kamar na jikinshi. Saleem jarumi cikin sanda ya fara lallabawa don cafke daya daga cikinsu, burinshi ya rike bindigar daya, ya san tabbas ya gama da su. Daga inda ya boye yake hango su, namijin ya rike hannun macen da alama ita yake koyawa harbi. Tas! Tas! Tas! Kake ji, ta saki harsashin bindigar sama sannan ya saki hannunta tare da umurtar ta ita ma ta yi, inda ya yi cikin kuskure da rashin kwarewa ta saita bindigar sama maimakon ta harba sama sai ta harbi gefen da Saleem.yake. "Wash Allah na!" ya fada cikin muryarshi mai sanyi, take karfi ya shige shi, da gudu ya fito a maboyarshi ya tunkari inda mace da namijin suke hannunsa daya rike da inda ta harbe shi tuni jini ya fara bulbula a hannunshi, namijin ne ya fara ankarewa da saurayin da ya dumfaro su, ai da gudu ya fauce daya bindigar dake hannun macen ya ari na kare. Sam ita ba ta kula da abin da yake faruwa ba, zatonta don ta yi mistake ne ya kwace. Cikin murya mai karfi ya kwala mata kira, "Beb ki gudu mu je Beb Beb yi sauri yi sauri mu gudu." Ina! Kafin ta ankare tuni saurayin ya cim mata, rike ta ya yi sosai tana kokarin fusgewa, ai tuni ta hada dukkan karfinta ga karfin tsoro ta danna ma hannunshi inda ta harba cizo, karamar kara ya yi, bai san lokacin da ya sake ta ba ta gudu, sai mask nata da ya samu damar cirewa. Da gudu ta ari na kare yayin da gashin kanta da farin bayanta ya bayyana, ko kadan ba ta yi tunanin juyowa ba don kada ya gane fuskarta, don ita tun ganin farko da ta yi masa har ta yi yunkurin guduwa tuni ta gane shi. Da gudu sosai ta cimma saurayin ya tada mashin hawa ta yi tuni ya ja mashin din a guje suka bar wajen, sai da suka tabbatar sun yi masa zarra kafin ya nemi gefen titi ya tsaya. "Beb ba mu da lokacin magana ki tafi gida za mu yi waya kawai," "Ok," ta fada cikin 69 AKWAI KURA sauke numfashin cin nasara. Jakarta ya ciro a jikin gaban mashin din, "Karbi kada a yi ram da mu, kin ga gari ya fara wayewa sosai." Ta kalli agogon hannunta karfe shida saura minti daya. Saurayin ya ja mashin ya tafi. Tafiyarsa bai fi minti guda ba mashin ya tsaya a gabanta, da alamun da ma ita ya zo dauka. Cikin sauri ta haye mashin din, "Yi sauri kada in makara." cikin sauri ya ta da mashin tare da sanya masa giya mai karfi ya dauki hanya don kada su makara. *** Jini ne sosai ke zuba a hannunshi, tuni jiri ya fara dibar shi saboda zubar da jinin da ya yi duhu-duhu ya fara gani, amma haka ya daure ya ci gaba da tafiya domin ya yi imanin in har ya fadi a wannan gurin sai dai gawarshi don wannan jeji shi kanshi da yake cikin anguwar bai taba sanin da shi ba sai yau da tsautsayi ya kawo shi, ya jika labba cikin jarunta ya kuma mikewa yana tafiya, burinshi daya shi ne ya fito inda zai samu mutane domin neman taimakonsu ya yi tafiya mai nisa yayin da jinin yake ci gaba da zuba a hannunshi. Dabara ce ta fado ranshi na ya cire rigarshi ya daure hannun, saboda kada jininshi ya kare a kasa. Numfashin wahala ya ja tare da sanya gwiwarsa duka a kasa yana kokarin cire rigarshi da daya hannun da babu ciwo. Wayarsa ya ji alama wanda dimuwa ya sanya ya manta da ita tuni ya ji sanyi a ranshi, cikin dauriya ya ciro wayar number Daddy nashi ya fara kira amma bai dauka ba. 4 missed call ya yi masa still ba a dauka ba. Momminshi ya kira, wayar Mommy a kashe hankalinsa ya ji ya kuma tashi jijiyar hannunsa na masa tsa nanin ciwo saboda a nan harbin ya same shi. Saleem ya ciza baki shi kansa ya san matsala ta jijiya yana bukatar emergency. Tuno da hakan ya sa shi kuma tashi ko Allah zai sa ya fito inda zai cimma mutane domin ya yi imani komai zai iya faruwa da shi, a karo na uku cikin sauri ya lalubo number Auntynshi, bugu daya ta dauka. "Ka ga jarumin jarimai yau an yi mafarkina ne?" cikin nishin wahala ya ce da 70 AKWAI KURA ita, "Zan mutu zan mutu," a firgice ta mike daga kan gadon, "Kana ina Bro?" "Wallahi ba ni gida ina tare da Abban Affan...wash!" ya katse mata maganar, "Mommy. Mommy nake son ji." Dif! Wayar ta katse, tuni ta bi layin da kira ta yi.masa 6 missed call amma ba ta dauka ba hakan ya sa ita ma ta kira Daddy amma bai dauka ba ta kuma kiran wayar Mommyn a kashe, tuni ta fashe da kuka. Abban Affan dake wanka da gudu ya fito daure da towel ya rike ta yana tambayarta lafiya amma sai kuka take, "Bro bro!" "Me ya samu da shi?" da kyar ta sanar da shi me ke faruwa. Cikin sauri ya dauki jallabiya ya sanya, "mu je gidan." A hanya suna tafiya tana kuka, tuno da Amrah da ta yi ya sa ta dauki wayarta ta hau kiran Amrah don ta san in har Amrah na lafiya to fa ta zo aikinta gidansu, ai ko cikin sa'a Amrah na gaban Mommy suna gaisawa cikin sauri ta ce, "Maman Affan kai wa Mommy wayar." "Ina gabanta Aunty ga ta nan," Amrah ta mikawa Mommy wayar Mommy ta karba da kuka Mera ta sanar da Mommy abin da ya faru Mommy cikin sauri ta kashe wayar maimakon ta dauko nata dake kashe tuni ta fara sanya number Saleem a cikin wayar Amrah ringin biyu ba a dauka ba, Saleem dake cikin wani hali saboda azaba duk jarumtarshi yau kam ta kare ya gama sadaukarwa yau kam tashi ta kare. Yana ganin wayar tashi na kara number babu suna amma ba shi da ikon dauka saboda azaba, da kyar ya samu ya daga wayar, nishi kawai yake saukewa. muryar Mommy da ya ji ya sanya ya fashe da wata wahalalliyar kuka, "Mommyna zan mutu, please ki yafe ni." Mommy a rude take fadin, "Kana ina son?" amma ya kasa ba ta amsa, "please son yi kokari daure ka tabbatar min da sunanka da Daddynku yake fada 'JARUMI' daure ka yi min wannan alfarmae." Idonsa ya sauke akan gidan ruwan cikin duru-duru da idonsa yake masa ya samu damar hada haruffan, "Gidan ruwan FAISAL Eksal Table water." Dif! Numfashinsa ya dauke. 71 AKWAI KURA A rude Mommy ta yi dakin Daddy. Tsabar rudewa Amrah na tambayar ta lafiya lafiya, ina, ta yi gaba a rude ta shiga tashin Daddy dake bacci tana kuka, "Daddy son son," A firgice ya tashi a mafarkin da ya ke yi na Saleem din yana neman taimako babu wanda ya taimake shi. "Me ya samu son?" ya fada yana rike ta. "Mu je Daddy mu je," take fada. Da sauri ya biyo ta zuwa kasa. Amrah da Zahra dake tsaye suna rude Mommy ta karbi hijabin jikin Amrah, "Mu je Daddy." "Muje ina?" "Son yana gidan ruwan Faisal eksal table water."Cikin rudewa Daddy ya ce, "Mu je kada dana ya rasa ranshi, mu je, na gan shi a mafarki cikin jini." Tare suka fito dukkansu har da Amrah cikin damuwa ba ka jin komai sai kukan Mommy da na Zahra, ita kanta Amrah sai da ta zubar da hawayen tausayin wannan family. Daddy da kanshi ya shiga direbin side. Mommy da ta fada ciki suka fice a rude kamar za su taka masu gadin a first gate, a guje suka fita. Agate na karshe ne suka cimma motar su Mera. Mera ta fito tana magana, ina, Daddy ya cinna hancin motar kan titi, ita ma Mera da mijinta da sauri suka rufawa Daddy baya. Bai sha wuyar gano inda gidan ruwan yake ba kasancewar Daddy ya san unguwar sosai tuni ya gane gidan ruwan da ake nufi. Cikin minti bakwai ya kawo su wajen gidan ruwan amma wayam babu Saleem. Cikin gidan ruwan suka shiga nan ma babu Saleem sai ma'aikatan gidan ruwan; mutum biyu dake shirin aiki da alamar yanzu su ma suka zo. Cikin damuwa Daddy ya tambayesu ko sun ga Saleem amma suka ce ba su ga kowa ba. Da sauri suka fito daga gidan ruwan. "La! Mommy kalli can kamar mutum ne kwance." Da sauri Daddy ya ta da kafa don cumma gurin da Mera ta nuna, ai ko a rude ya rike shi, "Son son wa ya yi maka wannan aikin? Inna lillahi wa'inna ilaihir rajiun!" yake maimaitawa. Mommy da Mera sai kuka suke yi Daddy tsabar ya rude ya rasa yadda zai yi da Saleem dake kwance illa fadi yake, "Son wa ya yi 72 AKWAI KURA maka hakan?" tuni hawaye suka fara sauka daga fuskarshi na tausayin dan nashi. Abban Affan ne ya ankarar da shi da, "Daddy mu je Asibiti." Daddy ya manta da maganar asibiti. Da sauri suka ciccibi Saleem suka sanya shi a motar Daddy. Abban Affan ne ya ja motar don kai Saleem asibiti, domin ba zai bar Daddy ya yi dirabin cikin wannan halin ba. Mera ba ta motar mijinta suka rufa musu baya zuwa asibiti, "Ibrahim mu je 44 hospital," Daddy ya ce da Abban Affan. *** Hankalinta ya tashi sam ba da niyya ta harbe shi ba ita da take bincike a kanshi ta ya ya za ta kai masa hari. "No," ta furta a fili.hasali ma ba ta san yana wajen ba, ita kanta ba karamin mamaki ta yi lokacin da idonta ya sauka a kanshi. Ta razana sosai lokacin da ta ankare shi ne tsautsayin mistake nata ya hau kanshi. Amrah ta dan muskuta a katifarta ta kalli hannunta da harbin ya kwace ta yi dan murmushi, "My hand wato akan makiyinka ka fara kwarewa a koyon harbi!" Amrah ta tsayar a ranta da za a ba ta bindiga karo na biyu don koyo tabbas za ta harba cikin kwarewa. Don yau fitarsu ta dauki haske sosai musamma da ta yi mistake a nan ta gane harbin sosai. Mommy ce ta fado mata a rai tare da Maman Affan ganin irin tashin hankalin da suka shiga saboda Saleem. Tuni tausayinsu ya cika mata zuciya musamma da ta tuno yadda Mommy take kuka faruwar abin sam ranta bai yi mata dadi ba ganin masu nuna mata kauna suna cikin damuwa kuma duk ita ce sila, wayarta dake kara ita ce ta katse mata tunaninta cikin kasala ta danna kore, “Anas ina ka shiga? Kira nawa ba ka dauka ba?" Anas ya ce; "Yi hakuri Beb wallahi ba na nutse ne saboda abin da muka aikata don tsoron kada a ce wanda kika harba ya gane mu, tsorona daya aikina da abin da zan taras na hukunci. Beb da ma na fada miki aikin fa akwai hatsari. Ina son ki da yawa Beb ta inda bana hango matsalar da za ki sanya ni a ciki." Amrah ta karba, "Haba Anas sai ka ce 73 AKWAI KURA kai din ba hukuma ba? Waye zai ga bindiga a hannunka ya tuhume ka? Ai ko ni da nake mace ban karaya irin taka ba, please ka kwantar da hankalinka kada ka karya min zuciya daga ni har kai babu abin da muke yin shi cikin son zuciya aiki ya zo mana da hakan." Anas bai sare da rashin tsoron Amrah ba sai yau, mace mai kamar maza ya fada a zuciyarshi. Wani abin mamaki Amrah ta ki sanar da shi dalilanta na son ya koya mata harbi, abu daya ta sanar da shi shi ne in lokacin ya yi za ta sanar da shi dalilinta. "Hello kana ji na?" muryarta ta dawo da shi cikin hankalinshi. Beb amma kin san wanda. kika harba kuwa?" ya jefo mata wannan tambaya. " A'a ban sani ba kai ka san shi ne?" ta fada don son jin amsar da zai ba ta. "Assitant controller na custom ne," ya fada cike da sanyin murya. "To sai me?" Amrah ta fada, "ka ga Anas ni kada ka ka sa in karaya abin da ya wuce ya wuce matukar muka ce za mu dinga tuna abin da yawuce na barna ko bakin ciki lallai hakarmu ba za ta cimma ruwa ba." "Ok," ya fada cike da karfin gwiwa. Kiran da ya yi mata ya yi mata ne cike da damuwa amma abin mamaki tuni Amrah ta sanya shi ya manta da damuwar illa karfin gwiwa da nishadi da yake ji sai don dadin muryarta. Ba su ajiye wayar ba har sai da suka canza location na fitar Asubahin gobe, gare su babu abin da za a fasa tsakanin mutuwa da hisabi. *** A sume suka iso da shi asibitin, Saleem bai san wanda yake kanshi ba. Da sauri Nurse suka tura shi kan gadon marasa lafiya. A rude Daddyn nashi ya fito yana hawayen kada ya rasa danshi, tuni ya manta da shi din waye a gari. Tuni Doctors sun rufu a kan Saleem don ceton ranshi, kasancewar tuni sun farga da waye mara lafiyar, matsayinsa bugu da kari Daddynsa shi ma babban mutum.ne a Nigeria. Gaba daya Daddy da Mommy sai sintiri suke sun kasa zama. Haka Mera sai kuka take yi mijinta na rarrashin ta. Daddy da Mommy kowa na 74 AKWAI KURA cikin damuwa babu mai rarrashin wani a cikinsu. Bayan share tsawon awa daya da rabi likitocin suka fara fitowa da sauri. Daddy ya fara tambayar su lafiyar danshi. "Mu hadu a office," daya daga cikin doctors din ya ce, da alamar shi ne babban cikinsu dukkansu Daddy da mommy suka rufawa likita baya, Mera kadai aka bari a tsaye ita da mijinta. "Bismillah," Doctor ya nunawa Mommy da Daddy kujeru biyu dake office din. "Doctor I hope dana zai tashi?" Doctor ya share gumi, "Ка kwantar da hankalinka insha'Allahu he gonna br alright, jini ne ya zuba sosai a jikinshi kasancewar harbin kan jijiya aka yi masa, Alhamdulillah Allah mai yadda ya so yau kwana biyu ke nan Saleem din ya zo nan asibitin aka dibi jininshi kamar yadda ya saba ba da kyauta time to time a baiwa mabukata, kun ga Allah cikin ikonshi ba mu yi amfani da jinin ba da rabon wannann karon tanadin jinin ya yi wa kanshi." Daddy ya share hawayen da ya zubo masa sai don dadin abin da dan nashi yake yi na alkairi ba tare da ya sani ba. "Masha Allah," dukkansu suka fada shi da Mommy, alkhairi danko ne ga shi Allah ya nuna mana ishara akan son! Allah ya karawa Annabi daraja Sallallahu alaihi wasallama,” "Amin," suka hada baki wajen fada. Doctor ya ci gaba da yi musu bayani, " mun yi nasarar cire masa harsashin, Allah ya tsare ma an kawoshi asibiti cikin lokaci don gurin bai kame ba lallai an auna arziki, harbi a irin wannan gurin shi ne yake sanyawa hannun mutum ya nakasa, kuma in ya zo da karar kwana ma tuni ake rasa rai saboda hanyar nan jini yake gudana, nan da nan jinin yake tsiyayewa.” “Alhmdulillahi mun godewa Allah," Mommy ta fada. Daddy ya ce; "Doctor yanzu babu damuwa ko?" "Babu damuwa Alhaji duk wani taimako an gama yi masa insha'Allah farkawarsa zai tashi da sauki sai mu ci gaba da addu'ar hakan." "Muna iya ganin shi?" Daddy ya сe; "E mu je ba matsala." A tare suka fito, Doctor ya yi musu jagora har dakin da aka kwantar da Saleem. Daki ne na musamma da ake warewa manya, Saleem na kwance yana baccin wahala, a hakan 75 AKWAI KURA dukkansu suka shigo dakin cikinsu har da Mera da mijinta. Daddy ya karasa jikin gadon na kwance yana bacci hannunsa daya sanye da jini ana yi masa karin jini. Daddy ya rike daya hannunsa da babu komai. "Allah sarki son, yau daya fuskarshi ta yi fayau alamar babu wadataccen jini a jikinshi, da gani ka san yana shan wuya." Daddy addu'a ya shiga tofawa dan nashi. Mommy ma yadda Daddy ya yi ita ma hakan ta yi ta tsaya kusa da kanshi tana shafawa tana tofa masa addu'a tana tsiyayar hawayen tausayin dan nata. "Allah sarki son Allah ya saka maka ko waye ya yi maka wannan abin," .Mera kuwa kuka take yi wanda babu kara saboda kada ta ta da kanin nata a bacci. Ranar dai babu wanda ya yi yunkurin barin asibiti, burin kowa Saleem ya farka su ga ya ya lafiyarshi, haka 'yan gida ma suna ta waya kan suna son zuwa amma Daddy ya hana ya ce su bari ya farka sai karfe goman dare kafin Mommy da Mera suka dawo gida yayin da suka bar Daddy da Affan Affan a asibitin duk da ba a bukatar mai jinya kasancewar babban asibiti ne na kudi komai suna da mai yi musu amma haka Daddy ya ce babu inda zai je har sai ya ga tashin dansa. *** Washegari tuni labari ya baza cikin zuriya har ma da garin Kaduna duk inda ka zaga maganar daya ce take rushing an harbi Assistan controlla tuni jita-jita ta baza ko ina wasu su ce makiya ne suka harbe shi wasu su ce Gwamnati ke son kashe shi saboda an ga ya fara sanya ci gaban al'umma an ga yana da gaskiya. Maganganu kowa da albarkacin bakinshi. Shi ko Saleem tun da ya farka daga suman wahala bai ce kala ga kowa ba ta kanshi yake duk da tarin tambayoyin da yake sha daga Dad nashi Mommynshi kai har ma da hukumar'yan sanda dana Custom wanda tun samun labarin faruwar abin suka yi wa Asibitin 44 kawanya, su ma hukumar sojoji ba a bar su a baya ba kasancewart asibitin na 44 asibiti ne private na sojojin Land 76 AKWAI KURA Army. Tuni suka ba da gudummawarsu ga Assistan controlla na security ko ina ka bi a cikin asibitin jami'an sojoji ne dana custom, hatta bakin kofar na Saleem security kyakkyawan matakann tsaro aka sa. Babban shugabansu na custom ya sanya tsaron lafiyarshi tare da alwawarin ko waye ya yi wannan aika-aikar ga yaronshi zai dauki mataki mai tsauri akai. Ganin hukumar tasu ta dauki mataki da kanta ya sanya Daddy ya bar nashi daukar matakin sai dai sosai ya kara burin taimakon al'umma don ya ga ribar taimako akan gudan jininsa Saleem. *** A halin yanzu ta gama kwarewa kan harbi ta sanya a ranta in za a fita filin daga na yaki da ita tabbas za ta iya fafatawa da arna a fagen yaki in har da bindiga ne wannan ya sa ta zuba makudan kudi ta mallaki bindiga tata ta kanta ta hanyar Anas. Shi kan shi Anas lamarin na Amrah ya daina ba shi tsoro da mamaki sai burgewa gare shi, ko a tarihi ko a films bai taba cin karo da labarin mace kamar Amra ba. Kusan koyaushe suna tare wajen koyon harbi hakan ya kara musu kusanci sosai ita da Anas, a baya ba ta jin burbushin soyayyar Anas a ranta. amma saboda kusancinsu na yanzu da yadda yake ta sadaukar da ranshi kan faranta mata rai, wadannan dalilan ya sa ta fara jin soyayyar Anas na huda jijiyoyin jikinta, Abu kamar wasa har ta fara baiyana masa hakan a fili. Tirkashi! Ga Anas nan da nan ya fahimci ya fara samun fada a gun Amrah, ba karamin farin ciki ya yi ba na samun sauyi gun Amrah imfact ma har ya fara jin shi kam wannan aiki da ya hada su gaba ta kai shi wai gobarar Titi a Jos. Kiriniya irin ta Amrah tare da saurin kwarewarta kan abin da ta sanya ranta tuni ta koyi mashin gun Anas. Ranar da ta fara maganr koyon mashin Anas ke tuka su ita kuma tana bayanshi za su dawo inda yake sauke ta kullum daga gurin koyon harbi ta ce da shi ya ba ta ta kai su gida. Kamar da wasa Anas ya ce; "Ai ba ki iya ba." 77 AKWAI KURA Amrah ta ce; "Ai ina kallon yadda kake control hands naka don haka na fara ramfo zancen." Anas ya yi dariya "Ko ni dake ba amfani da mashin nake yi ba mota ya sakalta ni yanzu da kika sanya ni amfani da mashin ranar farko da na hau sai da na yi kamar zan fadi." Cikin shagwaba ta ce; "Ni dai ka ba ni." "Ni a su wa in hana matata mashin? Bara in faka gefen titi." Ya faka, "zo ki hau Beb," ya sauka ya ba ta gurin zamansa. Ga mamakin Anas sai gani ya yi Amrah ta fara jan su, sai dai rashin kwarewa. "Beb tsaya gobe in mun fita zan koya miki sosai sai dai lokacin namu babu yawa kin ga minti talatin garemu 5am 25 muke fitowa mu tashi shida saura 5 minute lokacin ya yi mana kadan gaskiya, ko za mu bari mu gama da daya?" "A'a duka za mu yi shi." Anas ya ce; "To Beb sai abin da kika ce, ni kin san bawanki ne kawai umurni za ki yi min ki ga aiki da cikawa." Amrah ta harareshi, "Kai bawan Allah ne, ehe ba nawa ba, amma me zai hana mu fara fitowa 5 am da minti 20 tun da karfe 5: am da minti 15 ake sallar Asuba ka ga sai mu raba lokacin biyu ma mashin da harbi tun da yanzu ai na kware ba ni da matsala, kawai muna fita ne don kara basira ko?" "An gama Beb hakan za a yi. Washegari tana idar da sallar Asuba ta tsuke cikin kayanta na training kamar yadda ta saba in za ta fita. Anas ya zo da ma shi ya dauke ta. Granny dake dakinta wanda ba ta taba sanin wainar da ake toyawa ba zatonta Amrah na fita wajen aiki ne kamar yadda ta sanar da ita fara aikinta gidansu Saleem kan son bincikenta da Abban Amlah ya ba ta, sau da yawa tun da ta fara fita biyar da rabi na Asuba ta dauka sauri ne yake hana Amrah yi mata sallama bare ta karya kumallo, yau kam asirinta ya tonu ta gama shirinta ta dame ke nan tana shirin fita fuskarta 6oye da mask wanda farayi ke sanyawa tana kokarin daura nikab ta kuma 6oyewa fuskar Granny ta dumfari dakin don tashin Amrah ta yi sallah kasancewar ita Grannyn ta makara zatonta Amrah ba ta tashi ba. Kicifis! Ta yi arba da 78 AKWAI KURA idon Amrah dake cikin mask, da sauri ta koma baya cikin tsoro a zatonta barayi ne suka shigo, ko da wasa ba ta dauka Amrah ba ce. Ita ko Amrah da

Chapter 6 of 12