Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tana yi masa tambayar gabas. Murmushi ya yi tare da nuna mata gabas hadi da mikamata jallabiya dake kan gado. Ba ta ce komai ba ta karba ta rufe kanta ta ta da sallah Magriba da Isha i duka ta yi. Tana sallamewa ko addu'a bai ba ta damar yi ba ya kwashe da dariya ya kyalkyale kamar ya zare. Amrah ta bi shi da ido tana mamakin me ya sa shi dariya, fizgo ta ya yi tare da kama gashin kanta ya murde, Amrah ta yi ihun azaba tana neman dauki. Ya bata rai kamar bai taba dariya ba "Wace ce ke? Wa kike yi wa aiki?" Amrah ta yi wiki-wiki da ido tana.shakar numfashi tare da cije azabar zafin da take ji a kanta na rike mata gashin kai. Cikin tsawa yake maganar, "mace ta yi kadan ta yaudare ni, tabbas ke din mai kyau ce da za ki dauki hankalin duk wani tantiri amma ban da ni, ko da na bar ki kika yi ibada saboda ni ma musulmi ne, kuma ki sani Ahmad ni murucin kan dutse ne ban fito ba sai da na shirya," ya nuna kansa, "zan iya fasa kanki da bindiga yanzu in har ba ki sanar da ni wa ya turo ki ba," ya sanya hannu cikin aljihunsa tare da ciro bindiga ya sanya a kanta goshinta tare da saita kunamar bindigar, kiris yake jira ya tashi. *** Cikin second daya kwakwalwatta ta ba ta amsar da ta ba shi tare da cire tsoro, ido cikin ido ta kalle shi ta yi murmushi, "Za ka samu amsarka matukar ka ninka min farashi fiye da nashi wannan kana iya fasa kannawa don na san wanda ya turo ni in ya gama da Saleem kai ma ba zai bar ka ba." ta yi dariya mai sauti, "mutuncinka aljihunka, ni ba ni da mutumci akan kudi duk wanda ya ninka farashina shi ne maigidana." 137 AKWAI KURA Kamar soko haka ya sauke bindigar daga kanta yana murmushi tare da matsowa daf da ita har suna gogar juna, "Nawa ya biya ki?" Amrah ta kalle shi tare da kara matsowa kamar za ta shiga jikinsa. Hannu ta dora a kan fuskarsa tana shafawa, cikin muryarta mai dadi ta ce; "Miliyan biyar." A zahirin gaskiya ita kanta bakinta ya yi mata zugal wajen fadin kudin amma sai ta gimtse tana ci gaba da shafa fuskarshi. Tuni ya fara daukar layi saboda jin dadin shafar da take yi masa. Cikin sauri ya jawo ta jikinsa tare da kai fuskarshi daidai tata yana shirin hada bakinsu. Amrah ta yi fari da ido tare da daga masa hannu, "maganar farashi kuke ba na harka ba, ka nutsu ni bana cikin Kananan karuwai, mai kwana da ni sai wanda ya kai." Cikin bacin rai ya jawo ta da karfi ta fadi kasa tare da taka kafarta daya yana murdawa, "Ni ba karamin mutum ba ne, miliyan biyar din banza, na kara miki miliyan biyar.""Waye shi?" Amrah ta kalleshi tana nazari, tuni ta ramfo gidan zancen. Ba za ta taba mantawa ba lokacin da Abban Amlah ke fadin an kama Alhaji da hodar iblis, daga karshe ya ce; "Saleem ne maigidansu, hasalima shi ke shigo musu da hodar iblis din kasancewarshi ma'aikaci a hukumar yaki da fasa-kwauri saboda wannan dalilin hukumar DSS take zargin sa bisa ga zargin aka wakilta bincike, Idonta a kanshi sai dai a zahiri tariyo abin da ya faru take yi ita da Abban Amlah. Amrah har ta juya za ta fita office din ta dawo, "Abban Amlah waye shi?" ya kalle ta da alamun tambaya, "Wa ke nan?" "Alhajin," ta fada tana kallon sa. "Ba ki bukatar sanin sunanshi." "A wanne dalili?" ta fada tana yi masa kallon raini. Bai ce mata kala ba ganin ya raina mata hankali ya sanya cikin fushi ta kama hanyar barin office din, kamar daga sama ta tsinci muryarsa na fadin, "Alhaji Musa Dancanji." Amrah ta 138 AKWAI KURA yi dariya bayan ta gama tariyo abin da ya faru ita da mijn Ummi.. a hankali tamatso kusa da shi bakinta ya kai daidai kunnensa ta furta, "Pay me my money first before I offer you what you want from me." *** Ta kira wayarta ya fi sau sha uku ba ta dauka ba, daga karshe ma sai aka kashe wayar. Da fari hankalinta bai tashi ba ta yi zaton ko sun wuce gidan su Zahra ne amma bayan an yi sallar Isha'i sai ga shi Zahran ta kira ta a waya Kan cewa ta bai wa Bestyn nata wayar saboda ta kira bestyn wayar ba ta shiga, Ummi tsaye take saura kadan ta fadi saboda jin maganar da Zahra ta fada a waya, salati ta saka tana sallamewa Zahra ta ce; "Ummi lafiya me ya faru?" "Na shiga uku," ita ce kalmar da Ummin ta fada, "Zahra Amrah ba ta dawo gidan nan ba a ina kuka rabu?" cikin tashin hankali Zahra ta fashe da kuka a waya, "Ummi wallahi kin ji abin da ya faru tiryan-tiryan ta sanar da Ummin yadda suka yi a Super market. Ummi ta dan ja ajiyar zuciya, "Ina kyautata zato ko ta wuce gidansu bari in kira Iyan in ji," ta fada tare da kashe wayar tata, lambar Iya ta nema cikin sauri ta fara kira sai dai kash! An fada mata wayar Iyan na kashe. Kuka Ummi ta fashe da shi tana fyace majina. "Amrah ina kika shiga, Amat ban rike amanar gudan jininka ba yau in Amrah ta rasa ranta tabbas sakacina ne," ta fada tana kuka sosai. Da sauri 'yan uku da ke falonsuna kallo suka taso, "Ummi wa ya saka ki kuka? Abba ne ya dake ki? Yi shiru Mammynmu za mu rama miki in mun girma." Ummi ta jawo su jikinta ta kuma fashewa da kuka mai kara, su ma 'yan ukun kwamciya suka yi a jikinta suna kuka, cikinsu babu mai lallashin wani. Wayar tata ta kuma dauka ta kira Abban su Amlah da ya dauka ta fashe da kuka mai tsuma rai, "Zan je gidan Iya," Abban su Amlah ya ce; "Lafiya?" Ummi ta ci gaba da kuka ta kasa magana. "Ummin 'yan uku kada ki fita ko ina 139 AKWAI KURA ban yarda ki yi tuki ba, gani nan zuwa gidan nan ba da jimawa ba," ya fada tare da kashe wayar ... "Me ya faru?" uwargidansa ta fada tana kallon sa a tsorace don ta ji dukkan wayar da suka yi da Ummin, 'Yan uku danna handsfree suka yi kasancewar akwai kyakkyawar alaka tsakaninsa da matan nashi. Alhaji Usman ya ce, "Ban sani ba Hajiya, don Allah ki yi min..." ta daga masa hannu, "Ba ka bukatar tambaya ta izini don sai da komai maza tashi na yafe maka, daren yau in ka je ka kwana sannan kada ka manta ko me ye ya faru don Allah ka sanar da ni ko ta hanyar sako don in samu nutsuwa in yi bacci." Alhaji Usman ya shafa kan matarsa, "Allah ya yi miki albarka." "Amin!" ta fada tana kokarin mika masa key na mota. Jallabiya ya sanya ya bar gidan zuciyarsa cike da damuwa ta rashin sanin me ke damun Ummin.'yan uku. Tafiyar minti ashirin da bakwai ta kawo shi gidan kasancewar akwai 'yar rata sosai tsakaninsu. Maigadi ya wangale masa gate ya wuce cikin sauri ya rufe motar ko sauraron gaisuwar maigadi bai yi ba ya sanya kansa cikin gidan. Maigadi kansa ya yi mamakin ganin maigidan nasa don yana hankalc e yau ba kwanan amarya ba ne. "Allah ya sa lafiya," ya fada tare da rufe gate. Ummi ta janye 'yan ukun da suka yi bacci a jikinta a hankali, ta daga su tare da kiran mai aikinsu ta kai kowa gurin kwanciyarsa. Daga ita har 'yan ukun babu wanda ya samu damar cin abincin daren da ta dafa, ta ji karar motar Abban Amlah. Da gudu ta fito bakin kofa daga nesa ya gan ta, cikin sauri ta karasa gare shi tare da fadawa jikinsa. Kuka ta kuma fashewa da shi mai cin rai, "Abban Amlah in har Amrah ta rasa ranta kan aikin nan ba zan taba yafewa kaina ba tabbas da 140 AKWAI KURA sanina gudan jinina ta salwance wallahi ko tantama ba ni yi mata nan nan za su iya sace min yarinya koyaushe.' Abban;yan uku ya rungume ta yana bubbuga bayanta alamar lallashi, rungume a jikinsa har suka karasa dakinsu na bacci. "Me ya faru? Wa ya fada miki Amrahn ta bata?' Cikin kuka ta zayyana masa abin da ya faru. Shi kansa Alhaji Usman hankalinsa ya tashi tuni ya fara jin zazzabi na son rufe shi, "Yo ai in har hasashen Ummin 'yan uku ya kasance to babu wanda zai kai shi shiga damuwa don shi ne silar komai. Cikin dauriya da jarumta ya 6oye damuwarsa, "Haba Ummin 'yan uku Amrah ba ta bata ba na san tana gidansu, in kin lura ai ma ta yi kokari, yaushe Amrah ta taba zuwar miki kwana? Amma zuwanta kusan sati guda fa ta yi miki please ki yi hakuri da safe za mu je gidan Iya na san dota tana can," ya fada tare da kara sassauta murya alamar rarrashi. Ummi ta kwanta a jikinsa tana sauke ajiyar zuciya alamar ta ci kuka. Can ta ji ta samu nutsuwa da kanta ta shiga bandaki ta yi wanka tare da dauro alwala ta zo ta yi sallahr nafila kafin ta dawo gadon ta kwanta jikin mijinta. Ya yi murmushi yana mata kallon kauna, "Ba ni two minute in turawa yayarki sako." Ummi ta boye fuska don kunyar kwacen kwana da ta yi wa yayar tata. Bayan ya tura ne ya rungumo matar tasa suka kwanta tuni bacci ya dauke su zuciyar kowa cike da tunani. *** Tare suke da Mommy a falo suna hira wayar shi ce ta yi kara ya kara a kunnensa. "What?" ya fada tare da mikewa, "ga ni nan zuwa," ya fada tare da kashe wayar. Mommy ta kalle shi, "Son lafiya?" Saleem ya kama hanyar fita, "Mommy bari in dawo za mu yi magana." Mommy ta sha gabansa tare da sakawa kofar falon key, "Wallahi son babu in da za ka je har sai ka sanar da ni me ke faruwa." Saleem ya kalle ta yana shafa gemu, "Mom lafiya 141 AKWAI KURA fa, please," ya fada cikin sanyin murya. "Son yadda na ga hankalinka a tashe ba hauka nake ba da zan bar ka ka fita kuma a cikin dare, ka duba fa karfe tara na dare, Daddy Daddy! Ta kwala kira. Daddyn nasu dake sama da sauri ya sauk,o jin kiran matar tashi. Hannunta rike da na Saleem ta tare kofa ba zai fita ba. "Lafiya jarumin Daddy?" mahaifin nashi ya fada tare da kama hannun dan nashi. Mommy ta fashe da kuka tare da fadawa Daddy abin da ya faru. Saleem ya sanya hannu yana share hawayen Mommy. Kuka Mommyn Saleem ta saka. "A’a ni ba zan iya jure ganin hawayen sweettheart ba mu je in zauna tun da fita ce ba ki so in yi." Mommy ta gyada kai tare da kamo dan nata, "Zauna son, tsorona Allah tsorona mutane musamma da yanzu suka sa min kai a gaba ba ka ci musu ba ba ka sha musu ba. Saleem ya ce, "Addu'arku ita nake bukata, Mommy zamana ba shi zai hana makiya bi na ba sai dai ita addu'a tana canza kaddara musamma ta iyaye." *** "Dad waya Dakta ya yi min wai yaran nan an same su a mace." "What?" Daddy ya fada tare da mikewa, "ba dai wadanda aka kama masu son kashe min kai ba.""Su mana." Dad ya ce "Subhanallah!" Mommy ta kuma fashewa da kuka, "Ka gani ko. Daddy wato masu farautar ran son ba su daddara ba, har yau suna kan bakansu tun da ga shi sun bi wanda ake bincike sun kashe, wayyo ni Allahna," ta fada tana shesshekar kuka. Saleem ya kwanta a jikinta cikin shagwaba yana rarrashin ta, "Is okey is so right ba mai kashe miki ni sai kwana na ya kare insha'Allah ba zan mutu ba sai kin ga matar son dinki tare da 'yan dugui-dugui dina." Ya matso kusa da kunnen Daddy ya yi masa rada. Dariya suka fashe da ita dukkansu har da Mommyn. Saleem ya shagwabe fuska, "Bari in je in kwanta tun da katoto da ni an hana ni fita no problem Mommyn Saleem, gobe na je in bibiyi case din." "E je ka kwanta goben 142 AKWAI KURA ido na ganin ido sai ka je.." Saleem ya fita yana jin dadin kaunar da family nashi suke yi masa. *** Account no ya fada yana kokarin ciro wayarsa daga aljihu. Amrah ta yi fari da ido, "Wayata," ta fada. "Don tabbtr da alert ba ki bukatar waya a nan." "Ina bukata,"ta fada, ya zamo dole in ga alert, ganin sa kadai ne amfanin wayar a gare ni." Bai ce mata komai ba ya kara waya a kunne, "Ku zo mata da wayarta," ya fada, bai saurari amsar ba ya kashe wayarsa. Daya daga cikin yaran nashi ya shigo falon a buge kamar zai fadi tare da mika masa wayar. Da ido ya nuna masa alamar ya ba ta. Hannu ta sa ta karfa tare da kunna wayar. "Tell me your account no." ya fada yana kare mata kallo tare da lashe baki, Ta kada kafada alamat babu tsoro. "Account nawa sun fi goma saboda tsaro, bari in duba wanda ya dace," ta fada tana danna wayar. Message ta shiga a hankali ta fara karanta masa account no nata wanda yake haddace a kanta yayin da cikin dabara ta hau kan sunansa ta yi masa rubutu An samu matsala but Ummina kada su sani don't reply aika masa ta yi tare da gogewa yayin da ta kai karshen fada masa account no da account bank da account name. Tana gama fada masa ta mika masa wayar kamar ba ta yi komai ba, sako ne ya shigo wayar, da sauri Amrah ta mika hannu za ta karbi wayar amma sai ya daka.mata tsawa tare da bude sakon. Cikin sauri ya tunkaro ta gadan-gadan. Amrah da ta tsure tuni ta fara ja da baya idonta zare tana jiran me zai faru da ita. 143 AKWAI KURA Masha'Allah na godewa Allh da Ya bani ikon gama littafi na daya, a nan na kawo karshen labari na daya. Ku saurare ni cikin littafi na biyu nan ba da jimawa ba don cigaban labarin. Tabbas 'Akwai Kura'yanzu aka fara. Taku har kullum. Sayyada Taheer. 08100044786 Ba zan rufe littafin nan ba, har sai na yi miki fatan alkhairi uwa mafí uba ko da uban sarki ne; Hajiya Khadija Musa Bukur. Allah Ya ja kwana Hajiyata, Allah Ya ba ki aljanna ba tare da hisabi ba, Amin. Ina Kaunar ki Mamata. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 12 of 12