Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yi ta kasa tashi daga gaban malamin nata tsabar damuwa, domin ta san wannan sharrin Alhaji Usman ne, in ban da sharri ita da karatunta dabam me ya hada ta dawani IT ofishin security? Rokon malamin nata ta shiga yi kan ya taimake ta ya canza mata musamma da ta bude takardar ta tabba tar ofishin uban su Amlah aka kai ta, kamar yadda take yi masa inkiya. Cikin kasala ta bar masa ofis din nashi saboda damuwa. Tana fita kai tsaye mashin ta hau ta ce da shi ya kai ta ofishin su Abban Amlah, a ganinta tana bukatar sanin dalilin da ya sa aka kawo ta gurinshi kuma a bakinshi take son ji, a ganinta Litinin ta yi nisa da har za ta jita ta fara zuwa kamar yadda ta gani a jikin takardar. Ai ko tana zuwa gare shi da rashin kunyarta a nan ta yi karon battar karfe da shi inda ya ba ta aikin da ya sanya ta a cikin garari, bai ba ta fuskar da har za ta iya mayar masa da raddi ba ya kore ta. To fa ga Amrah ga Babanta da sannanu za mu ji dalilin da ya sa ya kai ta wannan ofishi. *** Karfe daya daidai am karar alarm ya buga. Amra ta yi salati tare da mikewa duk da ba wani bacci ne mai yawa ta yi ba don ta kai sha biyu na daren ba ta yi bacci ba tana bincike kan takardun aikin da aka ba ta. Tana cikin binciken ne a nan bacci barawo ya dauke ta kwance akan takardun. Bandaki ta shiga ta dauro alwala sannan ta gaba tar da sallah raka'a hudu, hannunta ya kai minti ashirin a sama tana rokon Allah gafara ga mahaifanta tare da sauran bukatunta na rayuwa, ba ta sallame addu'a ba har sai da ta roki Allah nasarar aikin da za ta 18 AKWAI KURA fara tare da kariyarsa cikin hatsarin aikin. Idar da sallarta ke da wuya ta jawo wayarta kirar infinix ta hau bude sakonnin da aka turo mata na whatssap, wani tsaki ta yi sannan ta yi murmushi, agogo ta kuma dubawa; karfe biyu na dare amma ga online din yadda ta zama kamar rana don abokai ne da yawa maza da mata wadanda ba sa baccin dare sai daren ya raba sabod chating. Mts! Ta kuma jan tsaki, "Shegun friends Allah ma dai ya sa suna sallar nafila duka akan lokaci waya ba ta dauke hankulan nasu ba. Group nasu na makaranta ta shiga tana danna voice. "Ni kun cika min kunne kowa ya ware ya yi bacci." Ai ko tuni aka yi mata ca da korafi. Zahra Kasheem kawai ke kare ta, "E gaskiya ne, tun da dare ne ya dace yanzu kam kowa ya kwanta." Amra ta ce, "Rabu da su kawata ai makulli zan nema in rufe gidan in ga wani shegen da zai kuma budewa, kun ga ba ni da lokacin surutu goos night," ta sauka tare da danna wayar don ta kashe ta. Gabadaya takardun gabanta ta kuma jawowa tana nazari. *** Saleem sunanshi mai matakin mataimakin Konturola Janaral (Assistant Controller General) a Custom. Saleem haifaffen Kano ce mahaifinsa dan cikin unguwar Tarauni ne ya yin da mahaifiyarsa ta kasance Baturiya 'yar kasar Cairo. Mahaifinsa shahararren dan kasuwa ne wanda ake ji da shi a Nigeria; Alhaji Hamza; in za a lissafo masu gidan rana wato kudi tabbas za a sanya shi matsayin na uku ko na huďu a cikin masu 19 AKWAI KURA kudinmu na nan Arewa, matarshi daya tak! Mahaifiyar Saleem Hanna daga ita bai sake aure ba, yaransu uku akwai yayar Saleem Mera sai Saleem kafin auta Zara. Tun fil'azal Hanna Musulma ce mai Addini cikin Turawa shi ya sa Alhaji Hamza ya yarda da auren ta don tabba tarwa ita din macen kwarai ce. A Cairo suka fara zama don a can suka haifi duka yaransu, sai bayan wasu shekaru ne suka tarkata ya nasu ya nasu suka dawo Nigeria. Alhaji Hamza na da zumunci, mutum ne mai kyautatawa iyalansa har ma da duk wanda yake bukatar taimako daga family nasu har da makwabta. Ko da suka dawo Nigeria Kanon suka fara zama cikin GRA daga baya ne Hanna ta kawo ziyara Kaduna a nan ta yi sha'awar garin. Alhaji Hamza duk state din nan na Nigeria babu inda ba shi da gida, ganin matarsa ta nuna sha'awar Kaduna ya sa ya dawo da zaman nan, kasuwanci kuwa sai kara gaba yake yi (duk dukiyar da aka cire hakkin Allah ai gaba take yi kullum). Mera ta yi aure yanzu hakan yaranta biyu tana Lagos da mijinta. Saleem bai dawo Nigeria ba sai da ya kammala karatunsa a Cairo a matakin karatu ya gama PHD kafin ya dawo Nigeria. Dawowarsa babu jimawa ya fara aiki da hukumar custom, mahaifinshi ya so ya yi kasuwanci amma sam ya ki don ya fi sha'awar aikin custom tun da kuruciyanshi. Fara aikinsa ke da wuya ya samu ci gaba sosai saboda gaskiya da rikon amana, shekaranshi bakwai ya samu ci gaban da wanda ya shekara sha biyar cikin aikin bai samu ba. Da yawa mutane suna ha'inci ne akan aikinsu don cin hanci shi ko kudi gidansu an tara, in zai yi zamansa babu aiki akwai dukiyar da za ta ishe shi rayuwa, yana aiki ne saboda sha'awa. Saleem fari ne tas! Kamar mahaifiyarsa Hanna ya yin da Mera baka ce kamar mahaifinsu, haka Zara ita ma baka ce sak! Mera sai dai sunada kyawunsu na bugawa a jarida amma Saleem bai baro komai ga Hanna magaifiyarsu ba, da yawa mutane ba su 20 AKWAI KURA daukar shi matsayin Bahaushe saboda kamarshi da Turawa, sau da yawa in mutane sun ji ya yi Hausa sukan sha Mamaki, zatonsu ya ya aka yi Bature ya iya Hausa, ga Saleem ya fi kaunar harshensa na Hausa fiye da English ga shi kuma kasancewar bai tashi ckin Hausawan ba in yana maka Hausan za ku ci dariya amma a hakan yake yin abinsa in hakan ta kama. Mahir da Ahmad abokan Saleem ne na aiki a nan gidan custom suka hadu suka kulla abota amma in ka gan su a tare yasda suka shaku sai ka dauka abokai ne tun yarinta. Mahir da ne ga wani Basarake a nan cikin Kaduna suna da rufin asiri, haka Ahmad shi ma da ne ga wani atta jirin mutum. A takaice kowa na da rufin asiri daidai gwargwado, sai dai Saleem ya dare su nesa ba kusa ba, ko a ofis shi din nesa yake da su in don matsayi ne da ba su yi abota ba cikin wadannan abokai kowa gwani ne wajen kyau ga ji da kai da da wasa da naira. Abban su Amlah da saninshi ya je har makarantar su Amrah ya roki alfarmar a turo ta IT gurinsu domin burinshi ya ba da Amrah wannan bincike kamar yadda ya yi imanin binciken mace kadai za ta iya domin sun tura maza biyu daga cikin ma'aikatansu amma har yau babu labarinsu, wannan yake tabba tar musu cewa ma'aikatan nasu sun mutu wajen aikin. A zahiri aikin akwai hadari amma alkhairi ne ga duk wanda ya samo amsoshin case din, don gwamnatin tarayya ta yi alkawari tare da hukumar DSS cewa akwai kyauta mai tsoka gami da kujera mai girma da za a bai wa wanda ya yi wannan aikin. Lokacin da suka yi taro da manyansa kan aikin, Amrah kadai ta fado masa a rai, haka kawai ya ji a jikinshi jaruntar yarinyar za ta iya ya yi imanin mace ce mai kamar maza shi ya sa ba tare da Amrah ta sani ba ya je har gida ya sanar da Iya tare da Zainabu suka je don ita ya fara sanarwa. Da fari Iya tsoro ya hana ta yarda gani take yi kada Amrah ta rasa ranta kuma ita kadai ce take gani ta ji dadi tun da babu mahaifinta amma da Abban su Amlah ya yi mata bayani hadi da roko ba 21 AKWAI KURA don Iya ta so ba ta amince, daga karshe ya roki alfarmar kada ma ta nunawa 'yar rigiman nashi ta sani, a nan Zainab ta ba da shwarar sanya fuskar Bos ga diyar tata don kada ta tsinka shi gaban yara a ofis kuma ta hakan ne zai yi mata kowane umarni ta bi don ta yi imanin Amrah zuma ce shanta sai da wuta. *** Ta ja gwauron numfashi bayan ta gama karanta historyn Saleem da mukarrabansa, a karo na biyu ta kuma. daukar wayarta ta kunna datar ta bude ta yi log in a facebook, abu daya ya zo zuciyarta shi ne; duba assitant controller ko yana facebook, full name dinsa ta yi searching kamar yadda ta gani a jikin takardun Saleem Hamza jarumi. Ba a fi dakika hamsin ba ta yi nasarar samo shi, bincike ta fara yi a cikin profile nashi tuni ta shiga hotuna. Masha'Allah,' ta fada a ranta don ganin baiwar halitta da Allah ya yi masa daya bayan daya take kallon hotunan, wani cikin kayan aiki ya yi kyau sosai shi da family nashi a kasan hoton an rubuta my everything tabbas ko tambaya babu ganin kyakkyawar mace rungume da hannun Saleem a kirjinta shi ya tabba tar mata wannan ita ce mahaifiyarshi, a gefe kuwa ga kanwarsa da Daddynsu cikin farin ciki da katon cake a gabanshi an yi ado da fulawa da kyandir alamun daya cikinsu ke birthday. Da hanzari ta ci gaba da duba sauran rubutun kasan inda aka yi rubutu da manyan haruffa da kai haka JARUMI is +1 da alama hoton bai jima da yin birthday din ba. Da sauri-sauri don sanin yaushe ne ya yi wannan postin, ai kuwa ta yi sa'ar ganin date din; 30 first watan Oktoba, duk da bai da misalin karfe hudu na yamma hakan yana nufin an haife 22 AKWAI KURA shi ranar 31 ga watan October ke nan. Ta daga kai sama, "Yes haka ne." comments na mutane ta ci gaba da gani daya bayan daya, mutane sun kai dubu uku likes kuwa sun fi hakan, ba su gajiya ba suna yi masa wishes birthday, age wt Grace sir sir sir ita ce kalmar da ta fi yawa a cikin comments din, a maimakon ya bi daya bayan daya wajen reply a'a is rightita ce kalmar da ya rubuta a kasan ya yin da mutanen suka kuma yin ca wajen yabawa da nuna kauna a gare shi. Amra ta ja tsaki, "Kai kwadayi ya yi yawa a duniya kun wani damu kanku wajen nuna masa kauna shi ko ba shi da lokacin amsarku kai wannan da gani dan zafin kai ne girman kan banza kawai." Friends nashi ta so shiga ko za ta samu evidence a nan amma ina ya kulle friends na shi babu halin gani ba ta gajiya ba ta ci gaba da duba sauran hotunan da ya sa tana duba comments na mutane a kasan. A wani hoto ne da ya sa yana sanye da kayan Hausawa farar kaftan da malum-malum ya yi rubutu a kasan kamar haka; Kanawan Dabo ko da me ka zo an fi ka. Ya yi kyau kamar sabon ango. Amra ta ci gaba da kallon hoton, ya yi kyau sosai, a ranta ta ce; "Shi ko wannane cikin kaya kyau yake?" Ta turo baki kamar yana kallon ta, "To ni ina ruwana da wani kyansa kyan dan maciji mugu kawai ni din nan zan yi sanadin da za a yi ram da kai. Comments na hoton ta bi shi ma don duba kowa irin na shi yabawar ga Sir din, shi ko wannan karan ko darajar dubawa ba su samu ba. A wani comment ne da ta ga an yi magana ya yi reply, ai kuwa da sauri ta duba wanene mai sa'ar nan da ya ba shi amsa sai ta ga ashe mace ce. Comment din dariya ta yi hahaha sai rubutun da ya biyo baya Young millonia Baturen Kanawa lolz..... U luk like gorgeous my bro. A ya yin da shi 23 AKWAI KURA kuma rubuta mata Autan Mommy bulala biyar tukuicinki. Ba ta yi wani rubutu ba illa sanya fuskar kuka da ta yi shi ko bai kuma magana ba. Amra shiga profile nata ta yi, Zahra Hamza ta gani rubuce wannan kanwarshi ce zuciyarta ya ce to amma ga Mamakinta me ya sa ita babu kalmar jarumi jikin sunanta, ko dai sunan kanwarshi gare ta shi ya sa ta ce broda, adding nata Amra ta yi sannan ta kashe data. Bacci ne cike a idonta a wajen ta kuma kwanciya tuni baccin ya dauke ta. Asuba ta gari Miss Amra. *** "Granny na fito Zainabu kin shirya sai kuma ki yi." "Ina fada miki ba ni son sunan nan in ba za ki kira ni Amra ta ba to ki ce Zainab. Haba Granny ke kullum ba ki wayewa yanzu in da a gaban kawayena ne da kin kwabsa min ba ki ji ba ke ina kiran ki da sunan 'yan gayu Granny." Iya ta ci gaba da tauna goronta,"Yo ai ni gara ki kira ni Hafsatuna da wani gurani wa ya sani ma ko sunan takalmi kika ba ni." "Hahahaha," Amra ta sheke da dariya har tana tsugunawa, "ni kin ga tafiyata Granny kar kisa in makara." "To Allah ya tsare hanya a gaida min Zainabin da angwayena da kishi ya. Kasancewar yau Asabar weekend ne tun daren jiya ta daura aniyar zuwa har gida ta cimma shi ta san tabbas yana gida in ma ba ta same shi a gidan ba ta daura niyyar bin shi har gidan dayan matar tasa. A hankali take tafiya cikin shigarta mai kamala abaya ta sanya ta yi rollin da maya fin Amra ma'abociyar doguwar riga ce domin ta fi kaunarta fiye da 24 AKWAI KURA sauran kaya, bugu da kari abayar ba karamin kyau take yi mata ba kasancewarta fara tas kuma.doguwa sau da yawa in ta sanya abaya ita kanta ta fi samun nutsuwa in tana tafiya a kafa. Ta yi tattaki har ta kai ga Neco junction inda ake hawa mota. Motar na tsaye kwandastoci suna neman fasinja a bayan motar 'yammatane guda biyu suke zaune suna hirarsu kafin motar ta cika a kaisu inda za su je, kujerar baya kwandastan ya dagawa Amra, "Hajiya shiga ku cika uku/" A bayan bayan ta yi matsuguni wa kanta 'yan yi matan biyu ta yi wa sallama amma babu wanda ya amsa mata hakan ya yi mata ciwo amma sai ta danne, su ko 'yan yi matan kallo daya suka mata tuni hassada ta cika ransu na ganin kyawu da tsantsar kamala da Allah ya ba ta. Zaman Amra kusa da su sai suka gan su so local a gurin haskenta da kwarjininta ya cika masu ido wannan ya sa suka kasa boye bakin cikinsu ta hanyar kin amsa sallamar da ta yi musu. Ita ma wayarta ta ciro ta ci gaba da danne-dannenta, a haka har motar ta cika aka dauki hanya. A zahiri danna waya take amma a badini hankalinta na kan 'yan yi matan nan biyu don sauraron hirarsu da suke yi. Bakar mai nuna ta fi dayar jin kai ita ce ke maganar, "Ni fa Yasira in zan mutu wajen nemo hanyar mallakar Saleem billahil azeem ba zan gajiya ba ko da zan tafi tsirara sai na same shi na ga alamar Umma tana sanya to ni kam na kusa in fara neman mafita da kaina." Wadda aka kira da Yasira ta ce, "Mina na sha fada miki ki kwantar da hankalinki dan uwanki ne fa, hasalima ai mahaifinshi shi ne madaurin aurenki dan kanin babanki ne ai taki ta zo gidan sauki ko Saleem ya so ko ya ki ke ce matarsa. Yasira ta daga hannu ta dunkule, "Allah ya ja zamanin uwargidan jarumi." Amra da ke gefe tuni ta ramfo zancen, wai da ma maganar Saleem jarumi ake yi? Wato ba hukumar fasakwauri kadai ke 25 AKWAI KURA neman sa ba har da 'yan yi mata ana fafatawa da shi tuni tsanar shi ya dira a zuciyarta, ita ba ta son mai neman mata ko kadan wannan dalilin ya sa duk nacin samarin dake bin ta ba ta kula kowa, burinta karatunta don t acikawa mahaifinta dake kabari burinsa, har yau har gobe ba ta ba wa wani saurayi fuskar da zai shige mata ba, Granny ta yi mitar ta yi nacin amma sau dubu in saurayi zai ai ko ta zo a waje to korar dan aike take yi, karshe Granny gajiya ta yi ta sanya mata ido a cewarta in ta yi bandaro za ta kai hotonta masallaci. "mitsw!" Amra ta ja tsaki, "babu kunya babu tsoron Allah mota ta haya ba ta ubanku ba kuna hirar jahilci." "Kan uba!" 'yan yi matan biyu suka hada baki wajen furtawa, "Yau sai mun ci uwarki a motar nan shegiya mai farin bilicin." "Oh! Da ma hassadar farin nawa kuke yi ke nan shi ya sa da na yi muku sallama ba ku amsa ba to ko makaho ya shafa ya ji ya san ni din fentin Allah ce.':." Kokawa ce ta so ta kaure tsakaninsu, fasinja dake motar tuni hankalinsu ya kai kansu, hakuri suka shiga ba su amma 'yan yi matan nan sun ki bari, a cewarsu sai sun ci uwar Amra. Daya mai jin kan ta jawo wuyar rigar Amra, "Sai na ci..." Tas! Amra ta kwada mata mari, "Sake ni uwata ta fi karfin ki ci ta sai dai ki ci taki uwar." Kokawa ce ta kaure sosai a motar haya. Da sauri direban motar ya tsaya, "A'a ku rufa min asiri kada ku jawo min hatsari a hanya maza Danladi ba wa kowa kudinta ta kama gabanta ba zan iya da fadan tika-tikan 'yan yi mata ba." "A'a direba su dai wadannan masu rashin arzikin su fita ita kuma wannan ai ba ta da laifi dama tun shigowata motar nan hankalina na kansu ina jin hirar rashin arzikin da suke yi, 26 AKWAI KURA hakurinta suka kure kuma ta yi min daidai da ta more 'yan banza," wata 'yar dattijuwa dake kujeran ta fada. Daya daga cikin 'yan yi matan ta murguda baki, "Mu dai ba 'yan banza ba ne da iyayenmu ehe!" Ungo naki," dattijuwar ta fada tare da mata dunkulo. Daya daga cikin fasinjan ne ya ce; "Direba ka yi hakuri ai dukkanmu mun kusa isowa inda za mu je, daure ka sauke mu in ya so kowa ya kama gabansa," ya juyo gare su, "yan yi mata duka ku yi hakuri ba girmanku ba ne fada a titi. Ke 'yar fara dawo nan ki zauna ni bari in koma mazauninki direba mu je don Allah, sauri nake," ya mike tare da ba wa Amrah mazauninsa. 'Yan yi matan daya daga ciki ta funciko jaka za ta sauka dayar ta jawo kunnaeta tare da rada mata su bari a je inda za a sauke su in ya so su kama shegiya su lakkada mata na jaki. Ai ko tuni ta gamsu da hujjar kawar tata, ba don ta so ba ta nemi guri ta zauna. wayar ta ce ta yi kara ta kanga a kunnenta. "Hello!" cikin harshen turanci take magana, "Nasir... Е wallahi na iso mota ce ta lalace a hanya... E direba na ya je gyara... mts ta ja tsaki,"motar haya na hau sai wari ke damu na, ka san in ba a motar haya ba yaushe diyan talakawa za su samu ganin ka a araha bare har su maka rashin kunya... a'a ba sai ka zo ba kawai ka bari after sallar La'asar sai ka same ni a cikin GRA gida mai lamba 12... gidan ai ba boyayye ba ne, in ka ce gidan.... Ok ashe ka gane ma, no problem in ka iso sai ka yi min waya zan fito," cikin gadara ta kashe wayar a dole ita 'yar GRA се. *** 27 AKWAI KURA Cikin gadara ya fito daga cikin motar sanye yake cikin kayan aikinshi na custom fuskarsa toshe da bakin gilashi wanda ake kira da no respect ga dukkan alamu fuskanshi ta nuna babu respect din abin Mamaki mutane na tsaye maimakon su ji haushi illa yaba kwarjinin matashin jami'in custom din suke yi. Cikin wannan hali boss nasu ya iso gurin, gaba daya fasinjan dake cikin motar suka mai da hankali akan wanda ke tsaye convoy jere da shi don ba wa idonsu abinci tare da ganin mai zai aiwatar a wannan guri. A gefen hanya almajirai ne jere reras suna bara maza da mata. Direct gare su ya karasa kamar ba shi ba ya saki fuskarshi, murmushi mai kayatarwa ya baiyana daya bayan daya ya dinga sanya hannu a aljihu yana debo kudin da shi kanshi bai san adadinsu ba yana bai wa almajiran sadaka abin ya burge mutanen dake tsaye matafiya cikinsu har da gaba daya 'yan motar hayar, ita ma kanta Amra abin ya burge ta sai dai a kasan zuciyarta tunani take ta ya ya za a yi wannan matashi ya zamo mugu, bugu da kari aikinshi aiki ne na masu kau da fasakwauri ta ya ya zai kasance daya daga cikinsu? Tsayuwar minti biyar ya gama da almajiran sannan ya juya don komawa mota. Da sauri daya daga cikin 'yan yi matan nan ta bude motar cikin gudu kamar ba budurwa ba ta karasa gare shi "Yaya jarumi." Cak! Ya tsaya shi bai tafi ba shi bai juyo ba. Da sauri ta karaso gabanshi, "Motarmu ta lalace a hanya in gida za ka je ka yi min lift." Ko kallon ta bai kuma ba ya yi wa convoy nashi alamun su tafi. budurwar na jin hakan ta yi saurin bin bayansu amma sai ya yi mata alamun kada ta fara. Hannu ya sanya cikin aljihu ya ciro bandir na kudi bai saurare ta ba ya jefa mata akan fuskarta ya yi tafiyarsa, ya yin da convoy nashi suka rufa masa baya. Cikin minti daya tak bat! Suka bace a kan titin. Dariya sosai mata 28 AKWAI KURA san dake kan titin suka fashe da ita ganin ya tafi ya bar 'yar budurwar a tsaye, kunya tare da jin kamar kasa ta tsage ta buya a ciki su ne suka hana ta komawa motar hayar. Cikin borin kunya ta tsai da Keke napep da sauri kawar tata ta fito daga bus din ta fada a Keke napep din tuni suka bar gurin. Faruwar wannan abin shi ne ya raba fadan Amra da wadannan 'yan yi mata. *** A bakin gate suka hadu, tun daga nesa ya hango ta cikin gilashin mota, hakan ya sa ya umurci direbanshi ya yi parking. Mamaki yake karfin halin yarinyar, yarinya karama wai tana kishin ubanta, a hakan ma mutuwa ce ta raba, yo in mutuwar aure ne hala sai ta Allah. A wani bangare kuwa addu'a ya yi mata a cikin zuciyarsa, Allah ya sa ta yi dacen samun miji ita daya kwallin kwal! Don ya yi imanin wannan ta auri mai mata hm! Sai Allah. Ta karaso jikin motar, murfin baya ba ta tsaya Alhaji Usman ya ja gilashin ido cikin ido suka kalli juna, ganin ba ta da niyyar gai da shi ya sa ya sha mur yadda ta yi tsaye kamar sa'anta. Ya sha mur. "Madam Amra ya ya dai?" Ta cuno baki, "Barka Abban su Amla. Ya sha mur, "Zai fi kyau ki canza min suna ko ban samu darajar Abban ba, yanzu matsayin oganki nake." Ta kuma cuno baki tana kunkuni, "Sir bindigata na zo karba" ta ci gaba, "kun ba ni aiki mai hatsari sannan kun bar ni hannu Rabbana, wato ni ma a kashe ni kamar yadda aka kashe min uba ko?" 29 AKWAI KURA Baki Alhaji Usman ya saki sai da ya dara kadan sannan ya ce; "Bindiga kamar yaki? Ko an fada miki bindigar abar wasa ce? Ko da yake a zafin kanki hala kin dauka rana daya ake fara harbi ba tare da an horar da mutane ba?" Amra ta kuma shan mur, "Yo in har su 'yan uwan aikin nawa da aka ba wa suna rike da ita ai ni ma ya zamo dole a ba ni, matakan aiki ciki har da bindiga sannan ina son in san halinshi dan fasakwaurin saboda in san ta ina zan fara dakatar da shi." Ya daga mata hannu, "Halinshi ni ma ba ni da masaniya akai, a gurinki muke son mu sani. Abin da ya kamata a ce kin san shi a garemu duk na cikin fayil da aka ba ki sannan bindiga babu bukatar hakan a gare ki, hankali da tunani da rashin tsoro sune makaman aikin naki oya wuce ki ba ni guri zan turo miki da sako ta account naki." Direban motar, Danladi baki ya saki yana kallon Alhaji da 'yar rigimarsa inda sabo ya saba ganin rikicinsu, tun yana jin haushi har ya daina sai dai ido amma rigimar tasu ta yau ya ji dadin yadda Alhajin ya fara takawa yarinyar burki. haka kawai don kana auren uwar yarinya sai yarinya karama ta rainaka? Yarinyar da ka haifi wadanda suka kere sa'anninta. "Mu je Danladi," ya yi umurni wa direbanshi. 'Yan uku dake wasa a harabar gidan suka karaso da gudu, "Oyoyo! Aunty oyoyo Aunty." Ta rungume Ahmad, "Babana yau babu Islamiyya ne na gan ku a gida?" Yaran suka hada baki wajen cewa, "Malaminmu ne ya rasu aka ba mu hutun kwana biyu." "Ok Ummi na nan?" יי" E tana sama." 30 AKWAI KURA "Mu je," ta rike hannunsu. Da ihu yaran suka riga ta isa falon suna kwala kira. "Mommy Mommy ga Auntynmu Zainab wadda ta zamo babbar mace tuni ta rikide ta dawo." Hajiya Zainab ta sauko daga sama hannunta rike da carbi, ta idar da sallar walaha, "A'a Amratu yau ke ce tafe? Ashe yau za a yi ruwa har da kankara." Cikin jin nauyi tare da sinna kai na rashin gaskiya ita kanta Amra ba za ta iya kiyasta rabonta da gidan mahaifiyar tata ba, duk da kauna da nacin da 'yan uku suke yi mata tare da son kasancewa da ita koyaushe. Ta zauna kan chanis kafet don huta gajiya. "Ummi karatu ne ya yi mana yawa tare da nutsuwa kin san an ce aski in ya zo gaban goshi ya fi zafi." Uwar ta harare ta, "Ka ji yarinya in haifi 'ya a cikina ta ce za ta yi min wayo. Ni dai ina fatan

Chapter 2 of 12