Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya zo fa amma bana mutuwa na aure dan aradun Allah wannan gaye ya tafi da ni." Amrah ta fizgo wayar a hannun besty tare da fadin, "Mu ga wane mai sa'a ne ya sace zuciyar bestyna?" Karaf! Idonta ya sauka a kanshi, gayen ya hadu, sanye yake da bakin wandon jins tare da farar riga mai dogon hannu yana tsaye rike da 56 AKWAI KURA makullin mota, murmushi dauke a fuskarshi. 'Tabbas na san wannan fuskar,' Amrah ta fada a zuciyarta. Zahra ta ce; "Ya dai bestyna ko bai miki ba ne? Kin san duk kaunar da nake yi mishi in bai yi miki ba ai dole in kora shi gaba." Amrah ta kirkiro murmushi tare da rungume bestyn tata sosai, "Ya yi min bestyna ga shi kyakkywa kai congrat bestyna, mu ma Allah ya mai da mu madadinku." Zahra ta 6ata rai, "Ai ke kam kin riga ni samu besty, ko kin manta da Ya Anas?" Amrah ta ce; "Haba bestyna wai irin kunyar nan." Zahra ta daka mata duka, "yau kuma ina ganin sabon salo." Wayar ta kuma karba, Ba ni in kare ma angonmu kallo sosai." Zahra ta mika mata wayar, "Ai na tura miki hotonshi a facebook da whatssap tun da na ga ba ki hauba shi ya sa na je gida amma na taras baki nan besty ai kin san ba zan yi saurayi ba tare da na sanar da ke ba." "Ayya sory bestyna dan wani uzuri ne ya fitar da ni kin san na fara IT." "Wow! very fantastic ki ce saura kadan besty ta yi bankwana da school, kai congrat ki ce Yaya Anas ya fara shirin aure, Besty ina suka tura ki attachment?" shiru ta yi don ba ta da amsar ba ta a nan din. Kir! Wayar Zahra ta yi Kara. Hamdala Amrah ta yi a ranta. Zahra cikin zakuwa ta dauki wayar, "Bebyna albishir," a daya bangaren ya ba ta amsa, "Goro fari kal!" "Ga bestyna ta zo." "Kai ina gai da bestynmu babyna I miss you," ya ce da Zahra yayin da Zahra ta shagala tana hira da babyn nata. Amrah ta ciro wayarta dake jaka, data ta ta bude tuni sakonni suka fara shigowa ciki. Ba ta tsaya bude na kowa ba sai na bestyn nata, hotonshi ne ya bayyana kala wajen shida. Tuni Amrah ta dago inda ta san shi; 'Maheer' shi ne Amrah ta fada a ranta, ta yaya hakan zai faru, mugu azzalumi, shiine ne bestyna ta haukace akan son shi? No ina ga kama ce ta yi yawa ba shi ba ne.' Zahra dake kwance kan kafet tana wayarta tuni ta shagala da soyyaya, idonta kulle tana amsar sawon soyayyarshi ta waya. Amrah ta kalle ta, "Lallai bestyna ta yi nisa domin in ba ta yi karya ba iyakar rayuwarsu 57 AKWAI KURA ba za ta ce ga kanar da wani saurayi ya dauke hankalinta irin wannan ba, da alama bestyn ta manta akwai aminiyar tata a dakin saboda soyayya. Ai kuwa juyowar da Zahra za ta yi suka yi ido hudu da Amrah, ta daga mata hannu biyu alaman ban hakuri. Ita ko Amrah ta daga mata kai alamar babu damuwa. "Besty ga wayar ku gaisa," Zahra ta fada tare da sanya wayar a kunnrn Amrah. Karamar ajiyar zuciya Amrah ta sauwe tare da yi masa sallama cikin muryarta mai dadin sauraro. Cikin wasa ya ce da ita, "Bestynmu yau dai sai da muryar bestyn matata saura inga bestyn matata da ido." Kamar yana kallon ta ta daga gira, "Haka ne gaskiya ni ma sai da na ji dadin jin taka muryar angonmu. Ina fatan za ka rike bestyna hannu bibbiyu, daga kanmu babu kari ka san muna da kishi ni da bestyna." Ya yi dariya, "Daga kanku kallo ya kare, ni dai ina so a kula da ni ehe!" Amrah ta katse masa hirar don ta ga alamar shi ma dan caftan ne, ta ce da shi, "Sunana Amrah Ammat what of you?" "Maheer Jabir Saraki," ya ba ta amsa. Tabbas hasashenta ya tabbata dama ta yi hakan ne don tabbatar da shi din ne, kuma ya sanar da ita hakan da kanshi, "Nice to meet you,'," ta ce da shi tare da zare wayar a kunnanta ta mikawa bestynta. Zahra ta karba, "Babyna mu yi waya an jima zan ji da bestyna kada ta yi fushi." Maheer ba don ya so ba, "Ok babyna Kadunaa ki manta in ta tafi call me back, you know I miss you always," "Yes my love me too," sannan ta kashe wayar, bandaki ta shiga don ragewa kanta ruwa, bayan ta sanar da Amrah. Tafiyar Zahra ke da wuya Amrah a karo na biyu ta kuma bude datar wayarta don ya rage mata kadaici kafin Zahra ta dawo, data ta bude tuni sakonni suka fara shigowa daga wahtssap wasu daga messenger, don duba sawon friends a nan ta ga an yi accept na friend request nata da ta tura, sai ta ga an yi mata offline message da account na Zahra Hamza sai ita ma ta ba ta amsa tare da rubuta mata thanks so much my sis for accept me as friend Daya bayan daya take bin sakonnin tana ba su amsa, wasu kuma ta sa alamun dariya ko 58 AKWAI KURA kuka. Besty Zahra ta katse mata danna wayar tata, "Gayen ya yi miki? Don ban hango farin ciki a fuskarki ba kamar yadda na saba gani in har abu ya yi miki dadi I know you bestyna more than u think." Amrah ta rike baki, "Wacce mace ce za ta samu wannan gayen ta ce bai yi ba? Ai ko hassada za ka yi ka san gayen ya yi, yes ya yi min bestyna." "To in ya yi miki me ya sa kika zama so silen?" Tuni ta yarda da amsan da bestyn ta ba ta fa, "Wallahi gajiya na debo, kuma fa haka ne gaskiya ne don na ga alama tun da jikin neman ruwa na tarar da ke. Zahra ta kara matsowa kuwa da bestyn tata tana fada mata yadda aka yi ta san gayen wato sun hadu ne a Super market sun je shopping da Mama amma saboda ta burge shi ta tafi da imanin shi a gaban Mama ya zo ya kwashi gaisuwa sannan ya roki Mama alfarmar magana da ita. Mama ta amince, "Ke bestyna wallahi gayen ya iya soyayya, ai Mama tana matsawa ya ce da ni ya ga matar aure, shi tun da yake bai taßa ganin matar da ya ji lokaci daya ya kamu da son ta ba irina. hm besty kin san tun da muka shiga shagon na yi arba da gayen sai da ya burge ni sai da na ce ina ma ya ce yana so na, sai ga shi Allah ya dora ni a kanshi da kansa ya ce na yi mishi. "Tun da ya yi miki ni ma ya yi min bestyna Allah ya sa rabon ki ne mu sha biki ranar zan debo shoki." suka tafa tare da ihun jin dadi. Sun jima suna hirar Maheer tare da soyayyar da Zahra take sha a gun shi. Sai bayan sallar La'asar kafin Amrah ta yi sallama da besty ta rako ta har gate sai da ta ga tashin mai keke napep sannan ta shigo gida suna dagawa juna hannu. *** Tun daga ranar da suka samu matsala da Saleem.ba ta sake ganinshi ba hakan bai sa ta bar shirya masa dukkan kalolin abincin da yake so ba, ita dai ba ta da tabbacin Saleem din ke cin abincin ko zubarwa ake yi, aikinta dai ba ta fasa ba kamar yadda Mommy ta yi mata umurni ta ci gaba kama daga abincin safiyar har na rana da yamma duk tana yin su. A cikin wannan 59 AKWAI KURA lokacin ne Mera ta zo gidan ita da yaranta Affan da Afnan, Mera tana da.kirki sosai don ranar farko da ta zo har side na Kanin nata ta zo. Amrah na kicin tana girkin rana sai gani ta yi mace ta yi mata sallama cikin girmamawa. Amrah ta gaishe ta ita ma, a cikin sakin fuska ta amsa gaisuwar Amrah, "Bari in duba bro," ta ce da Amrah. "A fito lafiya Aunty," Amrah ta ba ta amsa. Affan ne ya hau mikawa Amrah hannu alamar yana so ta dauke shi. Yaro ne dabai wuce shekara daya da rabi ba. Mera ta rike baki, "Ikon Allah kin ga fa ba ya yarda da kowa daga ni sai Afnan sai Abbanshi ko Nanny tashi ba ya zuwa gun ta sai ta yi lullubi. Amrah ta mika hannu, "Kawo shi Aunty." "A'a kina aiki rabu da fitinar Affan," "Aunty kawo shi don Allah," Amrah ta fada. Mera ta mika mata shi, "to ni bara in je in ga bro in ya ki sai ki miko min shi ko." "To aunty," ta ba ta amsa. Wasa ta fara yi wa Affan tana tsilla shi sama, Affan sai kyalkyala dariya yake yi kamar ya san ta tun fil azal .Amrah da Kaunar yaron ya shiga ranta tuni ta ware tana yi masa wasa, dariya take yi ita ma.kamar yadda yaron yake yi tana yi tana aikinta. Can Affan ya fara lumshe ido alamar yana son bacci, "To fa," Amrah ta fada, "ni dai ba zan iya zuwa dakin wancan mara mutuncin ba. Dankwalinta dake daure a kanta samanshi hula ne na aiki shi ta cire, tuni tulin gashin kanta ya watsu a gadon bayanta, hular ta dauka ta mayar saman gashin kanta, duk da haka bai rufe gashin ba, suna zube a gadon bayanta, Affan ta sanya a bayanta ta dauki dankwalin ta goya shi da shi sannan ta ci gaba da aikinta. Affan kuwa sai don ya samu balance ya ci gaba da baccinshi, aikinta take yi tana wakar kuch kuch hota hai cikin muryarta mai zaki kamar ita ta yi wa kanta. A haka tare suka sauko daga sama ita da Saleem, suna tafe suna kyalkyalar dariya, da alama hirar ta yi musu dadi. Mera kamshin girki ne ya cika mata hanci tuni yawunta ya tsinke, "Bro mu hade dakin Mommyn ni bara in karbi Affan a kicin." "Mitsw," ya ja tsaki, "mata ba ku da hankali yaron naki za ki bai wa mai aiki a kicin? Ba ki gudun ta kona miki shi?" 60 AKWAI KURA Mera ta ce; "Kai Bro Allah zai tsare wallahi shi ne daga ganin mai aikinka ya fara rikici shi ya sa na ba ta shi." "Oho miki," ya yi hanyar fita. Mera ta kama hanyar kicin. Turus! Ta yi tana kallon gashi dake zube a kafadar Amrah kamar 'yar India. Mamaki ta kuma yi ganin Affan goye a bayanta yana baccі hanka linshi kwance, a gefe kamshin girkin ke kuma tafiya da imanin ta. Maman Affan Mera ta fada, "A'a Aunty kin fito? Sannu da dawowa ki yi hakuri wallahi ban ji zuwanki ba, ba komai amma me ake girkawa bro ne? Ni ma fa yau zan yi masa kwadayi. Amrah ta jawo fulas guda biyu a gefe, "Ga shi Aunty da ma na zuba wa yarona Affan na san zai iya ci." Mera ta shigo kicin din, ai ko har da Mommynsa wannan za mu ci ya ishe mu, kai na yi godiya sosai." "Maman Affan ba komai." Aunty Maman Affan ta ce; "Wannan suma sai ka ce daga Hindu kike," Amrah ta rufe fuska, "Wace ni Aunty? Hanyar Hindu ma ban san ta ba, in tambaye ki Maman Affan." Mera ta ce; "E tambaye ni." "Aunty mene ne yarenki?" Amrah ta yi far da ido fullo-fullo shuwa-shuwa." No wonder," Mera ta ce, יי" Ki ce daga tsatson kyau kike masha'Allah Allah ya yi halitta.' Amrah ta kuma rufe ido, "Aunty ni kunya nake ji." "A'a gaskiya ce dole in fada," ta katse ta. "Aunty mu je in kai miki Affan side din Mommy kada kaya su yi miki yawa ga abinci." "To na yi godiya sosai Maman Affan." Amrah ta ce" "Aunty kina sa ni jin kunya kamarki ki ce min hakan Aunty, ki ce Amrah don Allah," 'ta fada tana langwaße kai. Mera ta kuma washe baki, "Sunan naki mai kyau ne na ji dadin haduwa da ke Maman Affan, kuma ni ba zan ce Amrah ba daga yau sunanki a guna Maman Affan." Fulas din duka biyu ta dauka tana gaba Amrah na biye da ita da goyon Affan. A hakan suka shiga babban falon Mommy. Ba kowa a falon sai Mommy dake kwance tana kallon tashar Saudi Arabia. Da sallama suka shigo. Mommy ta mike, "Sannu da aiki Amratu ga aiki ga goyo." "Ba komai Mommy." Mera ta ce; "Mommy kin san boy" na ganin ta ya mika mata hannu da na ki ba da shi saboda na 61 AKWAI KURA ga tana aiki shi ne ta dage sai da na ba ta." Mommy ta ce; "Ayya ai Amratu akwai hankali ina jin dadin aikinta sosai." Ita dai Amrah ba ta ce komai ba durwusawa ta yi har kasa ta gai da Mommy tare da sunce goyon Affan ta shinfida shi a kan kujera. Sosai Mommy ta yi mamakin ganin tulin gashin dake bayan Amrah har sai da ta kasa hakuri ta ce; "Amratu zo nan ina yaba hankalinki, me ya hada ki da gashin doki?" Amrah ta yi narai-narai da ido kamar za ta yi kuka, "Mommy ban sa gashin doki ba," ta cire hular kanta tuni sauran wadanda suka boye a hular suka zubo, "Kalli Mommy ban yi kari ba." Daga Mommy har Mera kallon mamaki suke yi wa gashin Amrah don ko Mommyn da take Baturiya gashin Amrah ya fi nata tsawo ga cika. "Mommy ina son ta wallahi don Allah ki ba ni ita in tafi da ita Lagos." "A'a ba zan ba ki ba tana tare da ni mutu-ka-raba takalmin kaza,” in ji Mommy. Dariya suka yi dukkansu kafin Amrah ta yi musu sallama ta koma bakin aikinta. *** Meena 'ya ce a gun Alhaji Hamza domin Mamanta kanwa ce a gunshi, uwarsu daya ubansu daya, akwai dafari akwai shakuwa sosai tsakanin Saleem da Meena kasancewarta abokiyar wasanshi ta musamma. Za su yi waya suna tsokanar juna duk irin na abokan wasa amma daga baya sai Meena ta nuna ma iyayensu soyayya suke da Saleem. Meena ta kamu da Kaunar Saleem mai yawa a zuciyarta, shi ko Saleem kallo ba ta ishe shi ba, tun da ya fahinci inda ta dosa shikenan ya fita harkarta wasan ma ya daina da ita sai da 'yan uwanta maza, tuni ya goge lambar tata a wayarshi in za ta kira sau dubu ba zai dauka ba, daga karshe ma sai sanya number tata a black list. Meena yarinya ce maras kunya mai girman kai na gaske saboda kawunta na da kudi wato Daddyn Saleem kuma yana sake musu sosai, ita da uwarta don har mota ya sayawa Meena mai kyau ita ma kanwar tashi ya sai mata mota mai kyau, duk wasu 62 AKWAI KURA bukatunsu in har sun fada zai dauki nauyin su. A girme Meena za ta girmewa Amrah nesa ba kusa ba don ita din ba yarinya ba ce, ta yi karatu har zuwa masters, a halin yanzu tana aiki a gidan Radio Glop Fm Kano. Sau da yawa weekend takan zo Kaduna gidan unkul din nata tare da kissa da kisisina don ta dauke hankalin Saleem, sai dai ga Saleem kallo ba ta ishe shi ba ban da gaisuwa ba ya yarda wani abu ya hada su. Ummanta ta yi alkawarin ko Saleem ba ya son 'yarta amma koda boka da Malam sai Meena ta auri Saleem. Da fari Umman Meena Yayan nata ta yi wa maganar hada yaransu aure sai ya ce da ita, in har yaran suna kaunar junansu zai fí kowa murna, sai ta ce da shi Meena ta amince shi ma ya sa Saleem ya amince. Alhaji Hamza ya yi dariya "Kada ki yi mata dole don an daina wannan shirmen auren dolen, zan yi magana da Saleem in ya amince." Ba don ta so ba ta ce, "To." Da Alhaj Hamza ya kira dan nashi ya yi masa maganar auren Meena a take Saleem ya ce bai amince ba shi ma Alhaji Hamza ya sanar da kanwar tashi a bar maganar, Saleem ya ce bai amince ba. Haba! Nan kanwar tashi ta hau sama tana masifa daga karshe baram-baram suka rabu da yayan nata don ya ce shi ba zai yi wa dansa namiji auren dole ba tun da shi ma iyayenshi ba su yi masa auren dole ba. Hakan bai sa Meena ta rabu da Saleem ba kullum tana hanyar boka da malaman tsubbu ita da uwarta akan Saleem, abin da ba ta sani ba Saleem tsaye yake kan addu'a, sam ba ya wasa da iba da duk shagalarshi bai da wasa da hakkin Allah haka iyayenshi suna yi masa addu'a sosai saboda hatsarin dake cikin aikinshi wnnan ya sa koyaushe da zarar sun yi sihirinsu baya tasiri akan Saleem da izinin Allah. *** Sosai shakuwa ta shiga tsakanin Affan da Amrah, da zarar ta zo aiki in har ta je gaida Mommy to fa Affan zai dafewa 63 AKWAI KURA Amrah har sai ta dauke shi kuma ka'ida ne a gun Amrah in har ta zo to fa sai ta fara gaida Mommy kafin ta je bangaren Saleem, don fara aikinta a nan Affan zai dafe mata dole take dauko shi su taho sashen Saleem. Tana aiki suna wasansu da Affan, kun san an ce mai da wawa ne, tuni soyayyar Amrah ta shiga zuciyar Mera, saboda kaunar danta da da take yi. Amrah ta iya abinci sosai wannan dalilin ya sa kullum Mera ba ta cin abincin kowa sai wanda Amrah ke shiryawa Saleem yayin da Saleem.sau dubu za a yi girkin sam ba ya ci, falon Mommy yake zuwa ya ci na Mommy. Abin da Saleem bai sani ba abincin da Amrah ke yi shi Mommyn take sanya mai aikinta zuwa ta jera akan dinning don ba za ta iya barin wannan abinci mai dadi a yi asarar shi ba, ita kanta Mommyn ta san dadin abincin sosai, hatta Daddy ya yi na'am da dadin girkin, sau da yawa Saleem in ya ci girkin yakan yabawa Mommynshi kan kokarinta na girki kasancewar ita ke yi wa mahaifinshi girki ba ya cin na 'yan aiki, abin da ba su sani ba tun ranar da Mommy ta ci girkin Amrah ta ji dadinshi tun ranar ta kudira a ranta duk lokacin da ba ta jin aiki to fa Amrah za ta sa ta yi musu, sai gashi Saleem ya ce ba zai sake cin girkin Amrah ba, a ranar ta sanya mai aikinta ta canzawa Amrah timetable, na Saleem ta ajiye nasu na gida tare da umurtar Amrah kan cewa a kara girkin. Sarai ta san Saleem din, karshe ma ita zai dorawa nauyin girkin nashi, ai ko sai ga shi yana cewa, zuwa cin girkin nata ba tare da ya san wanda yake yin shi yake ci ba. Zahra kanwar Saleem wato autan Mommy ta zo weekend sau biyu bayan fara aikin Amrah a gidan sai dai ba su taba haduwa da Amrah ba har sai zuwan Aunty Mera a nan da fari da ta ga Amrah ta ji tana kaunar ta amma da ta ga inda Mommynta take son Amrah hakan Aunty Mera ke son Amrah, tuni ta fara jin haushin Amran wannan dalilin ya sa koyaushe suka hadu to fa zagi ne da cin mutumci Zahra ke yi wa Amrah, ita ko Amrah kallo bai ishe ta ba domin ta gano in ta ce fada za ta yi to fa aikin da ya kawo ta gidan ba za ta aiwatar ba, shi ya sa ta aro 64 AKWAI KURA hakurin da ba ta da ta shi ta sanyawa zuciyarta kafin adadinta ya cika ta rantse daya bayan daya sai ta ci uban Zahra da duk wanda ya ci mutumcinta wannan bashi ne sai ta biya. *** Ran shi a bace tamkar an yi masa albishir da mutuwar tsohuwarshi, huci yake yi yana masifa kamar wanda yake wa masifar ya haife su, shegiya naira mai mai da tsoho yaro mai mai da yaro babba, cikin karaji ya fara magana da murya sai ka ce Bos, ba za ka ce matashin saurayin nan ba ne mai ji da naira da izza ba, uwa uba ga kyau, "Hukuma ta yi kadan billahil azim ba ta isa ba sun yi kadan su toshe mana hanyar cin abinci. Wato ba su samu sa'a wancan karon ba da wadancan ma'aikatan nasu ba, bai ankarar da su hatsarina ba shi ne suka kuma turo wata. A wannan karon gunduwa-gunduwa zan yi da dan aikensu sannan in tura musu gawar." Ya kalli matashin dake gabansa a kalla matashin zai ba shi shekara uku ya ci gaba da magana, "Duna yaushe ka fara sanya wasa a cikin aikinka? Yaushe akayi hakan? Wato son mata ba zai bari ka yi min aiki da kyau ba ko? Ta ya ya mace za ta gagare ka? To wallahi na tabbatar da hadin bakinka kai ma ba zan bar ka ba sai na yi daga-daga da kai," ya fada yana zare ido. "Alhajin Allah ba za ka fadi ba sai a gadon baccinka ka jima ka yi karko, ka ci dubu sai ceto, murucin kan dutse ba ka fito ba sai da ka shirya babu wanda ya isa ya karya dokada ka ya kwana lafiya, wallahi ta shammace ni ne, yarinyar da alamar ita ma mace ce mai kamar maza ta bace mana bat! A kan kwalta, maigida ka yi hakuri in kere na yawo zabo na yawo za a hadu ne ai, Allah ya huci zuciyar Alhajin Allah, Allah ya huci zuciyar maigida." "Dakata," ya daga masa hannu yana huci, "sati daya tak na ba ka ka kawo min yarinyar nan a raye ko a mace ba zan lamunci hakarsu ta cinma ruwaba mazan ma ya suka kare balle mata lallai lallai ne a kawo min 65 AKWAI KURA ita cikin sati guda." "Cau! Alhajin Allah an wuce gurin ka sa a ranka ni Duna dan duniya na kawo maka yarinyar nan an gama na rantse da sarkin dake busa numfashina sai na kawo ta gabanka a mace ko a raye." Jin wannan magana ya sa maigidan nasu ya dan saki fuska tare da murmushi, tuni kyansa ya bayyana tare da kwarjininsa. "Duna na san za ka iya, ka sani ranar da hakan ta faru akwai tukwici mai tsoka sai da ranka ka tabbatar an yi abin cikin sirri, sannan ka ankare kada a samu matsala ban yarda da matsala ba, matsala ba ta san ni ba ni ban san ta ba." "An gama Maigida," ya kuma fada tare da kada kada hannu alamun jinjina masa. *** Da wuri ta gama aiki Karfe biyar daidai na yamma ta gama shirin tafiya gida. Da sassarfa ta fara hawa saman benen Mommy don yi mata bankwana saboda tana son ta biya Saloon ta wanke gashinta, karo ta ji ta yi da wani abu har tana shirin fadowa daga step na benen. Da sauri ta kama jikin karfen benen, imagine kamshin shi ne ya ziyarci hancinta, ko ba a fada mata ba ta san shi ne. Da sauri ta shiga nutsuwarta don ganin da wa ta yi karo, "Am sorry," ta ce da shi. Yau 'yan mutumcin suna kusa kala bai ce mata ba ya raba gefenta ya wuce. 'Yau na sha da kyar,' ta fada a ranta tare da girgiza kafada, ta haura sauran step din don shiga babban falon Mommy. Zahra ke zaune jikin computer tana browsing. Da sallama ta shigo dakin amma kamar da iska take magana. Mommy dake cikin dakinta tana hutawa ta ji muryar Amrah na kira, "Mommy zan wuce." Ta fito daga dakin "Maman Affan wato saboda Affan sun je Kano kwana biyu shi ne aka daina yi mana doguwar hira ko? To ai yau suna hanya, dan naki zai kawo min ke hira har dakina." Amrah ta washe baki, "Ai ban sani ba Mommy da na yi wa yarona shiri na musamman, ina kewanshi Mommy ban da ina son zuwa wanke kaina da na jira na tarbi dan gidana." Mommy ta yi dariya, "Ai ko shi ma yana 66 AKWAI KURA kewar ki don jiya da muka yi video call yana ta kiriniya yana kiran Maman Affan." Amrah ta yi dariya don tuno sunan da shi Affan din yake gaya mata; Maman Affan shi ma yake fada kamar yadda ya ji Mommyn da Aunty ke fada, shi ya sa shi ma a cikin gwalantinsa na yara har ya iya fadar Maman Affan. Mommy ta katse mata tunanin “Ayya ga shi cikin satin nan suke son wucewa Lagos, lallai Affan zai yi kewar Mamansa." Amrah ta kada kai alamar jimami, "Mommy ni ma zan yi kewar yarona." Zahra dake jin hirarsu a gefe ta ja dogon tsaki, "Kalan dangi kawai mutum babu dangin iya babu na Baba amma yana shigewa uwata saboda kwadayin abin duniya." Kallo duka suka bi ta da shi. Mommy ta ce; “Ai Amrahtu 'yar uwata ce tun da musulumci ya hada mu kuma ni na dauki Amratu kamar 'yar da na haifa a cikina." "Kai Mommy," Zahra ta hau buga kafa, "Allah ya sauwake ki haifo wannan a cikinki Mommy me za a yi da talaka? Ai tsakaninmu da talaka sai dai a taimake shi kamar yadda ita ma taimakon ne ya hada mu. Mommy ta sha mur, " Fatima zan saba miki wacce irin magana ce ta marasa hankali eye? Yaushe kika dawo hakan ko universty ce ta mai da dabi'arki hakan? To ki kiyaye ni zan saba miki sosai, in ban da rashin hankali da mai kudi da talaka ai duk daya suke a gurin Allah, wanda ya fi tsoron Allah shi ne sama da wani, ki shiga hankalinki zan sa son ya tattaka min ke, kin san shi sarai." Zahra ta

Chapter 5 of 12