Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
har aka yi sallah magariba da isha, ana magana daya, Chioma bata fasa rokon ya bata yarta ba amma ina yaki, tunda tace ba zata yi Muslunci ba, kuma ba zata zauna da shi ba, haka yasa aka barwa Malam al'amarin yafi kowa sanin abin da ya dace. Amma a daren aka kai Innayo asibiti, saboda yanda ta yanki jiki ta fadi, a can suka kwana. Washegari aka tashi da magana, Malam ya kira Chioma da Obinna, ya tambaye shi alaƙarsu, nan yake gaya mishi ai suna son juna, kuma kafin zuwa Alhaji Adamu suke soyayya, zuwan shi ya lalata soyayyarsu. Ya tambayi Chioma tana son Obinna kuwa? Ta gyada mishi kai, yaso ta bawa Adamu damar ya aureta a karo na biyu, amma haka ya roke ta da ta bar mishi Aishatu Nazneen. Ƙasa magana tayi tana kuka, don Allah ya gani tana tsoron kada su kashe mata yarta. "Ki yi hakuri ba zan tab'a barin wani abu ya sami Nazneen ba!" Inji Alhaji Adamu, wani harara ta watsa mishi, tana jiran Abinda Malam zai ce, wani abin mamaki rokonta Malam yayi tare da neman alfarmar ta bashi yar zai riketa. cikin sanyi murya tana share hawaye ta ce mishi. "Idan kai zaka rike ta, na amince amma ina tsoron a bashi ita." Tahir ya faɗawa Malam, Alhaji Adamu yana kallonta, yayi laifi amma hukuncin yayi mishi tsauri.. "Chioma nayi laifi amma, hukuncin yayi min tsauri,ki bari a bani yarinya ta zan bata farinciki." Murmushin takaici tayi tana faɗin. "Lokacin da ya dace ka riketa me yasa baka zo ba? Sai yanzu da na kawo ta zaka ishe ni da munafurcin kana son yarka, ba zan baka ita ba, ni dai kada a bashi Y'ata." Sunkuyar da kai yayi, ya rasa me zai ce mata har ga Allah akwai shiga hakki. Amma haka ya hakura domin yau da yaje asibiti Innayo koran kare tayi mishi, don dole ya dawo, sauran kannenshi kuwa dauke kai suka yi suna jin haushinsa. Dakyar Chioma ta amince ya dauke ta, amma don Allah idan za a cutar da ita. Ya dawo da ita wurin Malam don tasan shine kawai zai rike mata Yarinya, shima kuma abinda yasa ya amince da ya tafi da ita don yadda Innayo ta d'aga hankalinta akan yarinyar ne. A ranar suka bar Bauchi, bayan malam ya mata shatara na arziki, domin yace ba zai biya ta abin da tayi mishi na rikon yar ba, yasan ta sha wahala. Da wannan suka bar gidan, shima kuma a ranar yaso ya wuce amma yasan dole ya jira a sallami Innayo yaji me zata yanke akanshi da yarshi, wacce take kwance ciwon ya dawo sabo. Duk wahalar da ake sha, wurin danneta shi daya yaƙe riketa. Idan tana irin wannan abin wani lokaci hawaye yake da murmushi, har malam yake yawan tambayar shi meyasa yake murmushi akan ciwonta. "Malam ciwon gadarshi tai, haka nayi fama da mahaifiyarta." "Amma kuma ka tafi ka barta da wannan laluran?" Malam ya tambaye shi. "Malam tsoron yadda zaku amsheta. Amma wallahi na rantse da Allah, ina sonta." "Allah ya sa haka ne mafi alkhairi!" Hawaye ne ya zubo mishi. Haka yanayin ya kasance har ranar Monday, aka sallami Innayo, tana shiga cikin gidan, ta hango NAZNEEN da take bakin famfo anyi sa'a yau an tashi jikin da sauki, tana shigowa ta hango yarinyar tana wasa da ruwan, dake ta tsani yarinyar shiga kitchen tayi ta dauko itacen marke ta nufi yarinyar ta shiga labta mata, amma Yarinyar ko gizau. D'ago kai tayi tana kallon Innayo, murmushi tayi tana faɗin. "Ai bani kike duka ba, ga wanda kike duka nan." Ta nuna mata gabanta wanda yake tare dukan, kallonshi tayi tana kyalkyale mishi dariya, "Guardians da zafi?" Fisge itacen aka yi, tare da watsar da Innayo da itacen. Ta kyalkyale da wani mugun dariya. Ihun Innayo yasa kowa ya fito, Sakamakon d'aga itaccen da aka yi za a buga mata bata ga kowa ba. "Kyaleta!" NAZNEEN ta faɗa tana tsalle da murna tana tafa hannunta. Cikin farincikin da sauri Alhaji Adamu ya rungume yar shi, yana kallon Innayo da Goma ta d'agota tana mata sannu. "Su goma uwar munafunci, murna kike a ranki." Inji Nazneen, ★★ Lagos...... [11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥 * EXQUISITELY BEAUTIFUL #Mai_Dambu 'Top-Notch Season 3 بسم الله الرحمن الرحيم Kiran wayar ya kuma, idanunta kur akan wayar amma taki dauka. Kiran ya katse ya sake kiranta bata dauka ba, a takaice dai sai da ya mata kira talatin da biyar a na shida ya kira Mamanta. Tana ɗauka ya kwantar da kanshi ya fara bata hakuri. "Mama ki bata hakuri, kiran gaggawa aka min, shi yasa ban samu zuwa ba. Sannan ga wurin aikina dakyar suka bani pass." "Tun wancan sati kace zaka zo, amma baka zo ba. Yanzu kuma sai kace ba zaka zo ba, sai ka tafi Azare. Tow me zan maka?" Shiru yayi kafin ya ce mata. "Ki kara bata hakuri, kakata ce bata da lafiya, ina son naga jikin ne kafin nazo. Don Allah tayi hakuri zan zo." Haka yayi ta basu hakuri suna mishi tijara kala-kala, babu yadda ya iya ne amma tabbas yana jin babu dad'i haka suka gama rashin mutuncinsu, sannan suka kashe wayar tare da mishi zagin kare dangi da shi da zuri'arshi. A can Azare kuwa dama maganar aurenshi da Khalwat ne haka yasa baki ɗaya hankalinsa ya rabu gida biyu, domin ya rasa yadda zai yi. Yana shiga Azare ya nufi zaweeya, tunda ya shiga cikin gidan yake daure fuska kamar an zage shi. Don ma kada Hajja Marih ta mishi zancen Khalwat yasa shi sauka a dakin Mama Hajja,duk yadda yaso kada a yi zancen Khalwat, sai da aka dauko zancen. Cikin hucky voice dinshi me dan karen sanyi ya ce mata."Mama Hajja dole ne sai na zauna da mata biyu? Naga dai rayuwata ce, kuma iya matata ta wadace ni." "Alhaji Malam, mace daya bata wadatar ba, muna bukatarka shi yasa muka barka da ita yarinyar da ka aura. Alhaji Malam a wannan karon kayi mana biyayya ka auri yar gida kamar yadda muka bukaci haka, kayi biyayya yau shekara bakwai muna son ganin gudan jininka kai ma!" Cikin wani irin damuwa ya kalli Mama. Daidai lekowar Hajja Marih. "Mama Hajja idan yace baya bukatarta, ai ba laifi ba ne" Shiru yayi domin yasan tunda ya ji Kakarshi ta faɗi haka, definitely tana jin haushinsa. Kuma yasan kawaici irin nata, ko iyayenshi ba zata yiwa magana ba, don haka ya ce. "Shi kenan Allah yasa haka shine mafi alkhairi, na amince." Dake ita Hajja Marih bata tsaya ba, tunda tayi maganar ta wuce abinta. Addu'ar da Mama Hajja take, sai da yaji jikinshi yayi sanyi. Kafin ya kalli agogon hannunshi ya ce mata. "Zan wuce Bauchi!" "Ba zaka kai gobe ba?" "A'a akwai taron da za ayi a gidan, Shehi na Majalisar kolin malamai." "Allah ya taimaka." "Amin Ya Allah." A hankali ya ciro kudi ya ajiye mata, sannan ya fita, zuwa dakin Hajja Marih. Yadda ta dauke kai daga gare shi, yake kara tunzura shi, amma sai ya share kamar bai ji zafi ba, ya ce mata. "Zan wuce Bauchi." "Allah ya tsare!" Ya ajiye mata, kudi ya fita, sannan ya leka falon Hajja Kubrah, ya gaida ta, tayi mishi nasiha sosai, yayi mata godiya, ya bar falon bayan ya ajiye mata itama kudin, yana fita ya samu drivern shi da yazo tun kwana biyu da suka wuce. ya shiga motar, suka bar zaweeya. Wayarshi ce tayi kara, cirowa yayi ya duba, Hero ya gani a rubuce. "Assalamu alaikum, Abba!" Ya kira sunan a hankali. "Naji zaka wuce Bauchi ko? Kayi kokarin duba Khalwat makarantarsu, sannan Mama Hajja ta kira ni ta ce min ka amince?" Lumshe idanu yayi yana jin wani irin d'aci, kafin ya ce masa. "Eh na amince." "Allah ya maka albarka." "Amin Ya Allah, na gode sosai Abba!" kashe wayar Abban shi yayi, zuciyarshi tana wani irin tiriri. Ba zasu gane halin da yake ciki ba shi yasa suke kokarin kwakumamishi auren wata yarinya. A rayuwarshi ya tsani abin da zai batawa Gimbin shi rai, balle yasan darajar ta. Dake motar sabuwa ce, sosai drivern yake falfala gudu. ★★ Gidan Malam. Tun bayan sallar asuba Malam bai koma cikin gidan ba, har zuwa karfe sha daya na rana, Almajiran da suka taya shi aiki suke bada labarin abin da ya faru. Attahiru da yake gefen Malam yayi gyaran murya, ya gayawa Malam abin da ya faru. Shiru yayi kafin ya ce masa. "Ka gayawa iyayen jibi asabar ina son ganinsu?" "Eh Baba Malam!" Ya mike yana fadin. "Bari na shiga cikin gidan." "Tow shi kenan" dake Alhamis aka wayi garin ranar . A hankali ya dubi magidanta da suke zuwa karatun safe. Tunda suka tafi yake zaune a zauren. Abin da yasa shi zama a wurin bakin duhun da ya gani a kan Amanda yake aikin kafe shi, amma wani abin da ya bashi mamaki yadda bakin duhun yaki tafiya. Fitowar Tahir yake gaya miishi, "Baba Malam kazo fa." Tashi yayi ya nufi cikin gidan, ai kuwa bakin duhun ya bishi har cikin gidan, kafin su isa dakin ya rigasu ta isa. Suna shiga dakin, yarinyar tayi wani irin lankwasa da yasa hannayenta suka juya suma. Yadda take juya kasussuwan jikinta zai tabbatar maka, babu dan adam da ya isa yin haka. Dariya ta fashe da shi, lokacin da ta juya kirjinta yana kallon kasa, bayanta ta juya shi sama, kamar wata dabba. Fararen gashin kanta suka rufe mata, fuska rub tayi wani irin tafiya kamar gizo-gizo, ta shiga bin bangon dakin. Wani irin kara Chioma ta saka tare da ambatar "jesus Christ" ta zube akan gwiwarta. "Amanda!" Ta kira sunanta da mugun ƙarfi, tana me fashewa da kuka. Kura mata idanu Malam yayi sannan ya cewa Tahir. "K shiga dakina, ka dauko min ruwan zam-zam." "Tow!" Zai fita Malam ya riko hannunshi, "ka tabbatar ka shiga da addu'a, domin shadanin ya wuce tunaninka." Gyada kai yayi, sannan ya wuce, zama Malam yayi yana fara karanto ayoyin ruki'a, wani irin ihu tayi tare da fadowa daga bangon "dumm". Ta nufi wurin Uwarta da gudu."Nne take me away from then!" Sai lokacin Tahir ya shigo dakin da Zam-zam da wasu kayan rubutu, ya ajiye. "Ka dibo min gaushi." Da sauri ya fita, ya amso gaushin ya kawo, suka shiga addu'a Malam yana tofa addu'a. Yana yi suna hayakin habbatu saudata da aka hadashi da wasu maganin, ihu ta shiga yi, tana kuka a tafi da ita, su bar gidan kawai, su bar gidan kada Maman ta ajiyeta, watsa mata ruwan Addu'a yayi, ta zube a wurin bayan ta saka wani irin ƙara da yasa gidan amsawa suma da suke dakin sai da suka toshe kunnensu. Kafin ta samu barci. Ajiyar zuciya Malam ya sauke yana faɗin, "ya fita, amma ba dukka ba domin ya jima da ita, kuma zai yi wuya ya barta baki daya. " "Alhamdulillahi, Jibi insha Allah kowa zai iso!" "Allah ya kai mu" "Amin Ya Allah!" ★★ *7:45 pm* Ya iso Bauchi, kai tsaye gidansu Gimbi ya wuce. Ya samu tarba da bakaken magana kuwa. Amma dake yana son matarshi, sakata yayi a gaba suka bar gidan. Zaranda hotel suka nufa, inda ya kama daki. Tunda suka shiga ta lura yana dan sussuce mata, yasa ta dauke miishi wuta da wani uban jan aji. "Ni fa na gaji da halin!" Rungumeta yayi, suka wuce ban daki. Bai kyaleta ba, sai da suka yi wanka suka fito, ya samu biyan buƙatar shi ya riko hannunta. "Kiyi hakuri, nasan ban kyauta miki ba, amma babu yadda zan iya ne, amma kiyi hakuri!" Wani kallon banza ta miishi, sannan ta ce mishi. "Ina aure aka ce kayi?" Hadiye yawu yayi yana kara sumbatar goshinta. "Eh my heart!" "Ba wani heart, bayan gashi nan iyayenka zasu saka ka aure, ni dake bamu da arziki." "Kin ga ni ba haka nake nufi ba, ki fahimce ni." Kuka ta saka mishi, a daren ba karamar rigima ya sha ba, ya mike zai shiga yayi wanka ta saka kuka ta ce mishi. "Tun baka yi auren ba, ka fara guduna." "Ba haka ba ne" yafada yana me rungumeta, suna hira barci ya dauke shi. Har dare ya raba, bai samu damar yin wanka ya tsarkake jikinshi ba, wurin karfe daya Uwarta tazo daukarta, anan suka zare kurwanshi. Ta kalli Uwar cikin matuƙar tsorata "Me zaki yi da shi?" "Babu kame miki shi za ayi, yadda ba zai miki gardama ba, sannan ba zai tab'a zarginki ba, zai rufe idanunshi akan duk abin da yake faruwa koda kuwa karya ce ke zai bawa gaskiya." Haka kuwa aka yi, suka tafi da kurwarshi, ta lashe shi tas, sannan aka yi yar tsatsuba,.suka dawo gidan. Bayan shugabansu ta bata damar ta amince da yayi auren, babu wanda ya isa ya tab'a zarginta, babu macen da ta isa zama da Saif ba tare da ta mutu ba. Wannan abin ya mata dad'i, ba karamin gargadi aka mata ba, domin an gaya mata, ban da kishi ta hakura tayi biyayya, idan ta sake ta fara kishi zai kwace kuma zai kore domin asirinta zai tonu. Da wannan ta amince da sharuddan shugabansu. Suka dawo ta yi wanka, ta kwanta wurin asuba shima ya tashi da wani irin kaunarta, yayi wanka ya gabatar da sallar nafila, tana kallonshi sai dariya take a ranta. Bayan ya idar da sallah, yana zaune sai da garin ya waye sannan ya tawo wurinta. Ya kwanta, rungumeta yayi yana faɗin. "Tashi kiyi sallah." Kallonshi tayi ido cike da barci ta ce mishi. "Baby na amince kayi auren, tunda kaga har yau Allah bai bani haihuwa ba, gara ka yi auren ko za a dace." Ware idanu yayi yana faɗin."are you sure?" Gyada kai tayi tana shafa fuskarshi. Ba karamin dadi ya ji ba, anan ya kara turmusata kamar ba gobe, sannan suka shiga wanka, ya fito ya musu odar abinci, ana kawowa yaci ya tafi taron majalisar kolin malamai, lokacin da ya isa, anyi taron a open air theatre ne. Taron zai dauki kwanaki uku, domin karkashin kungiyar mabanbanta akidu ne, yan darika, yan izala, da yan shi'a, mai girma gwamnan jahar Bauchi, Hamza Abdullahi rauta, ya shirya domin samun hadin kai tsakanin al'umma. Sai la'asar aka tashi taron ranar farko, washi gari Juma'a, anan ya wuni. Koda aka tashi sallar juma'a, a babban masallacin juma'a na gwallaga suka yi sallah. Ana tashi ya nufi makarantar su Khalwat, ya zauna har ta fito, ba laifi yar doguwa da ita, tana da kyau ga nutsuwa. Tunda ta ganshi ta dan shiga nutsuwarta. Gefen motar ta shiga, dake tana gidan Kanwar Babanta da take aure a tambari housing estate ne. Tunda ta shiga motar yake wani cin magani, yayi ta kafa mata kashedi. "Kada ki ce zaki rena min matata, bana son rashin kunya." Magana dai marasa dad'i, yayi ta mata, kanta a sunkuye. Abin tausayi tana da wanda take so, hajja Marih tasa Babanta da Mamarta suka sallame shi. Idanunta cike da kwalla, haka suka isa gidan ya sauke ta bayan ya daura mata kudi a saman cinyarta. Muryanta na rawa ta ce masa. "Na gode!" Ta ajiye miishi kuɗinshi ta fita motar. "Ke!" Ya daka mata tsawa, "Maza dauke kafin na mare ki." Dauka tayi tana kuka, ya kuma ce mata. "Maza hadiye kukan!" Haka ta Hadiye kukan, sannan ta juya ta nufi gidan Kanwar Babanta. Shima ya juya ya koma hotel din, Saif har ga Allah don dai Gimbi tace yayi auren ne, amma baya son abin da zai bata mata, ranar Saturday suka gama taron, ya wuce da Gimbi Lagos, ta mota domin ya rarrasheta. ★★ Tun ranar juma'a, gidan Malam Malami ake ta saukar baki, tare da dafe dafe, washi gari yaran gidan suka halarci taron, Alhaji Adamu Malami da sauran waɗanda suke kusa duk sun zo, wurin la'asar aka bude taron da addu'a. Domin a tsakar gidan ake taron, Yara da jikokin Malam suke zaune. Shiru Malam yayi kafin ya cewa Umma. "Sa'a fito min da bakin nan, kai kuma Tahir ka je ka tawo min da bakon nan!" "Tow, Malam." Suka fada lokaci guda, Umma ta shiga tasami su Chioma, ta ce su fito. Tana rungume da Amanda. Ta fito daidai lokacin da Tahir ya shigo da Obinna, mikewa Alhaji Adamu yayi yana me rike kanshi..... [11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥* EXQUISITELY BEAUTIFUL #Mai_Dambu 'Top-Notch Season 3 بسم الله الرحمن الرحيم Chapter 13 Lagos. A hankali yake takawa, hannunshi rike da wasu litattafan aikinshi, gefen damarshi sab'e yake da jakar laptop ɗinshi. Juya hannunshi yayi ya kalli agogon hannunshi yaga karfe biyar da arba'in. Kallon hanyar yayi sosai, ya nufi wurin motarshi, tun kafin ya karasa kusa ya danna remote control car din, ya bude motar, yana isa ya bude bayan motar, ya zuba su. D'ago kai yayi da niyyar rufe motar, sukayi kicibis da Nassef. "Amma dai baka da mutunci." Ya faɗa fuskarshi a daure domin tunda ya zane Gimbi yake fushi da shi. "Ih haka kowa yake faɗa, musamman waɗanda naci uban matansu." Tsaki Saifullahi-Khalid yayi ya shiga motarshi. Komawa gefen mai zaman banza Nassif yayi yana faɗin. "Banza a banza kare ya taka leda, tow sai me don ka min tsaki? Baya fitowa a jiki balle ya nuna tabon shi." "Fita min a mota!" Kwantar da sit din Nassif yayi yana faɗin. "Ai banza, idan da ace bani da hanyar sayan mota ne zaka gaya min haka, ba zan fita ba idan kaso kayi waje da ni." Ya faɗa yana lumshe idanunshi, kwafa Saifullahi-Khalid yayi yana faɗin. "Allah sai na kai kar'arka wurin Jadda." Tabe baki Nassif yayi yana faɗin. "Idan ka kai, ka gaya mata nayiwa wancan dorinar ruwan duka ne." Ya cigaba da abinda yake yana wasa da wayarshi. A hankali tafiyar ta fara nisa ya cewa Saifullahi-Khalid. "Naji an saka aurenka nan da sati Uku." Saura kiris kan motar ta kwace mishi. Ya juya a hankali ya ce mishi. "Wani irin an saka auren sati Uku?" Cigaba yayi da game ɗin da yake wayarshi ya ce masa. "Lokacin da ka amince, hala giya kasha ko? Tow aure daram nazo ne akan batun kayan aure, tunda dan Uban mutum ya zama ɗan gata. Aure ma su zasu biya maka sadaki." "Nassif me yasa baka da mutunci ne? " Murmushin takaici Nassif yayi sannan ya ce mishi. "Gado nayi daga wurinka. Aure babu fashi shegen gora, mata biyu ni ko daya ban ajiye ba. Maza turawa Aunty Mariya kudin kayan auren." Yasan matuƙar ba sallamar Nassif yayi ba, ba zai tab'a barinshi ba, don haka ya sauka a gefen hanya ya tura mata kudin, sannan ya mikawa Nassif wayar ya gani, sannan ya ce mishi. "Miliyan uku? Yayi kyau, mun tura namu gudummawar." Daga haka suka bar gefen titin, Saif ya je ya ajiye shi a gidansa sannan ya tsaya kafin ya fita ya ce masa. "Na san kai mutum ne mai yawan ibada, ka saka idanu akan kanka, da matarka sannan na san matarka tayi luff ne, idan tayi wani abu na hauka. Wallahi sai ta kare rayuwarta a jail." "Me yasa ka tsani gimbiya ne?" Murmushi Nassif yayi, sannan ya fita daga motar, ya nufi cikin gidanshi, shima ya kad'a kan motarshi ya bar unguwar. Gimbi. A dakinta, da ta hana Saif shiga, zaune take gaban madubi, tana kallon Saif da Nassif ta tsani Nassif kamar ta kashe shi. Tana jin yadda yake fadar magana akanta, murmushi tayi, tana jin a ranta dole ta haɗa wani abin da zai gama da rayuwarshi. Ganin Saif ya juyo da motarshi gida, ta shiga yan abin da zata yi, tana gamawa ta fito, ta nufi kitchen ta fara hada abincin, wanda aka zuba duk wani bala'i da masifa, sannan ta haɗa abinda zata hada, jollof din taliya ce, da aka zuba kazanta a cikinshi, sai kunun zak'in da shima kazantar ya samu a cikinshi. Tayi alƙawarin ba zata tab"a barin shi ya samu nutsuwa ba, tunda suka saka kafar sai ya mata kishiya. Tana aikin taji dirin motarshi, dake yana son pepper chicken, yanka hannunta tayi ta d'aga jinin da wani bakin gari, ta shiga juya namar, tunda ta auri Saifullahi-Khalid ta saka ya kore mutumin da ya bata kayanshi, tare da mishi barazanar sai ta kashe shi idan ya tona mata asiri. Rage karfin wutar gas din tayi, sannan ta juya ta fita. Daidai yana shigowa. "Barka da dawowa." Murmushi yayi mata, yana faɗin. "Baby na gaji." Wucewa kitchen tayi ta kawo mishi kunun zak'i, ta bashi ya sha da sanyi. "Princess! Kunun nan, yayi dad'i." "A karo maka kenan!" "Eh kai!"ya faɗa da muryanshi me sanyi, "Jeka yi wanka ka huta" "duk yadda kika ce!" Haka ya nufi dakinshi, ya zube a bakin gadon yayi shiru, can sai gata ta shigo. "Dama nasan baka shiga wankar ba " haka ta nufi ban dakin ta zuba abunda zata zuba a cikin ruwan wanka, ta zo ta taimaka mishi, ya cire kaya sannan ta raka shi ya shiga, ta fito ta dauko, wata bakar leda a bakin zaninta, bude ledar tayi ta ciro babyn wasan yara, da aka caccaka mishi ƙusa. Ta d'aga katifar shi, ta bude rigar katifar ta saka a ciki. Ta rufe ta maida ta cigaba da gyara gadon. Katon gwangwanin madara ta ciro a cikin drower dinsa, ta cusa a kasar gadonshi, sannan ta mike tare da barin dakin bayan ta hada turaren wuta, shima wasu bala'in ne, ta zuba ta saka a falon kafin ta kawo dakin. Ta fita. Wanka ta shiga, bayan ta gama domin wannan aikin an fiso tayi yana gidan, kungiyarsu ta mayyu suka hada mata. Domin tayi alkawarin kawo musu mata masu ciki har biyu. Shi yasa yau ta shirya kyam. Sai da tayi wanka sosai sannan ta fito ta same shi, ya fito ya ɗan kwanta yana kallon silin, "kasa kaya, kazo kaci abinci." Juyawa yayi ya kalle ta, sannan ya ce mata. "Tow!" Haka ya mike yana saka kaya, ta tako har gabanshi, tare da kai hannunta kan bulalarshi. "Yau ina son kayi fucking dina crazy!" Shafa kumatunta yayi suka fito, ta saka mishi abinci, yana ci ita kuma ta koma gefe, tana cin farfesun ganda. "Ba zaki ci abincin ba?" "No need!" Ta fada tana cigaba da cin abincin, tana gama ci, shima haka ta kwashe kayan abincin ta kai kitchen. Tana fitowa, ta nufe shi, tunda ya ga yadda take, fitinar shi. Ya biye mata domin yana daga cikin matsalarta, shine bata son ya cika damunta, sai suyi fada yanzu. Yadda ta kunna shi, haka ya zame mata masifa, suka shiga abun arziki. Sosai ya dakata kamar ba gobe, kafin yayi nisa ta fara

Chapter 7 of 12