Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
mana aure mu tafi." "A'a Obinna, ba zan iya abandoned din yarinya karama ba. Just nine years." Riko hannunta yayi yana me rarrashinta, da nuna mata fa'idar mai da Amanda familynta, tunda ta aure aka same ta. Kuma shi shaida ne, ba illegal child ba ce. Saka hannunshi yayi cikin nata, ya ce mata. "Idan har yana son yarki, ba zai wulakantatta ba, idan basu amshe ta ba. Zan dauke ta. " Kallonshi tayi sannan ta share hawayen da yake zuba mata, ta ce mishi. "Na amince, Obinna kasan bani da kowa bani da kome, idan zaka wulakantani. Tun wuri ka gaya min na rufwa kaina asiri na nime inda zan zauna." "Da zan wulakantaki ba zan tab'a nimanki ba Chioma, ina sonki sosai ba zan iya tozartaki ba." Kuka take itama, domin yadda ta wulakantashi akan wani banzan mutum da ya gama biyan buƙatar shi ya gudu ya barta da ajiyarshi. "Shirya ta mu zaga Enugu." Haka ta shirya ta, sannan ta saka mata mayafin da yake rufe fuskarta, suka fita yawo, yana tason yaga fuskar yarinyar, amma baki daya taki barin yaga fuskarta. Haka yayi musu sayayya musamman ita da zai a maida ita wurin danginta. Washi gari da sassafe, suka bar Enugu, domin baya son ya kara lokaci basu bar kasar bakiɗaya. Tafiya suka yi, me wuya da wahala. Domin sun bi dogon motar nan ne, kallon Chioma yayi ya ce mata. "Zamu kwana mu wuni. Kin rike address ɗinshi kuwa!" "Ba sai ta nime address din ba, nasan har kofar gidansu!" Kallon Amanda yayi yana son yayi magana, ta tari numfashinsa da cewa. "Ka kula min da Mamana!" Daga haka ta cigaba da zamanta, yana son magana amma ya kasa. Abinci da ibadar wasu musulmai yake tsayar da su, har suka shiga jos. Sauka suka yi aka ci abinci, suna zaune ya kalli Chioma ya ce mata. "Zan baki farincikin rayuwa. Yadda baki zata ba." "Wannan ai wajibi ne akanka, dole ka.kula min da Mamata." Kallonta yayi yana son magana amma ya kasa, cire mayafin tayi ya sauka akan kafadarta. "Jesus Christ!" Ya faɗa tare da rufe idanun shi gam. "Maza rufe kanki!" Mamarta ta gaya mata. "Kayi hakuri!" Ta juya tana kallon Obinna. "Taya kika haifi, devil." Rufe mishi baki tai da hannunta. "Ina sonta!" Ta faɗa, bayan ta mike tana me riko hannun Amanda, suka nufi motar da aka fara shiga. "Nne kada ki damu, yana da kirki sannan yana sonki, ba zai iya wulakanta ki ba, sai dai soyayyar da yaƙe miki bai kai wanda Papa yake miki ba, idan kika zauna da Papa zaki sha wahala, zaki takura. Amma Uncle Obinna zai baki abubuwa dayawa. Kada soyayyar Papa da dadin bakinshi yasa ki kara juyawa Uncle Obinna baya." "Waye ya gaya miki haka?" Juyawa tayi, sannna ta ce mata. "Angel of Guardians!" "Shiiiii!" Ta saka hannu a bakinta da tayi shiru. "Ok Nne!" Haka suka cigaba da tafiya, har suka iso Bauchi, da yamma. Tare taxi suka yi ya kalle Chioma ya ce mata. "Sunan unguwar!" "Unguwar barno jajja, daidai kofar gidan Malam Malami Jajja." Amanda ta faɗa da gangariyar hausa, ba zaka ce haihuwar kudu girman kudu ba ce. Dama Chioma tasha samunta da Hausawan da suke tura kura a kofar gidansu, suna hira da Hausa har tayi abokai tsoron kada a cutar da mata da yarinya ce yasa take hanata fita. Wani lokaci har fulatanci take yi, kuma lafiya lau, musamman idan ta samu abokan yinta sai kaji kamar a Yola aka haife ta. Haka idan ta juya Igbo zaka rantse bata iya wani yare sama da shi ba. "Tow yarinya! Ku bani dari biyar." "Ai dubu za a baka, domin kai ma ka kusan zama mai gidankanka a daina wulakantaka!" Ganin yadda take maganar yasa shi kallon Obinna da Chioma, ya bude baki zai magana ta ce. "Kai Malam sunusi, muje kawai zasu baka!" Jikinshi yaji kamar an zare mishi laka. "Taya kika san suna na!" Ya tambaye ta, yana me fitowa ya bude motar ya saka musu kayansu, wanda kusan kayan Amanda ne. "Ƙada ka damu." Ta faɗa mishi, sannan ta juya ta gayawa Chioma abin da zasu biya, babu musu suka shiga, ita da Mamarta a baya, shi kuma Obinna a gaban motar. Suna tafe ta fara jan driver da hira. "Garin Bauchi akwai kyau!" "Eh yana da kyau ba laifi, sai dai rashin cigaba da har yanzu bamu samu kamar da ba." "Amma kuma naga kamar akwai zaman lafiya!" "Eh sosai akwai zaman lafiya, amma shekarunki nawa?" "Shekaruna idan na gaya maka, motar kwacewa zata yi a hannunka. Kada ka tambaye ni shekaruna!" "Tow ranki shi dade! Amma kin tab'a zaman Bauchi ne?" "A'a baki daya rayuwata a Enugu nayi sh." "Shi ne kike hausa kamar girman arewa." "Eh saboda kakanina hausa fulani ne.... #Mai_Dambu [11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥 * EXQUISITELY BEAUTIFUL #Mai_Dambu 'Top-Notch Season 3 بسم الله الرحمن الرحيم Dan murmushi tayi tana kallon, roundabout din kofar fada. Ganin bata kuma magana ba, yasa shima yayi shiru har suka nufi titin unguwar, "Chioma gobe zamu koma ko?" Ya tambaye ta, saboda yana gudun kada su haɗu da Adamu Malami tace ta fasa bin shi. "Obinna ka yarda dani." Ta faɗa daidai lokacin da Amanda ta cewa drive din. "Ga gidan nan, me almajirai." parking yayi yana faɗin. "Taya kika san nan ne gidan?" Shiru tayi tana kokarin bude kofar motar, Uwar ta riko hannunta. "Ama ina zaki ne kike iri wannan saurin?" Nuna mata kofar gidan Malam tayi tana faɗin. "Grandfather na ne!" "Ama bana tunanin zan barki a wurin Musulmai, domin zasu mai da." "It is Fate!" "But fate is cruel for me and you! Ki rufa min asiri kada ki yarda da kowa. " "Nne! Ba zan iya binki ba, domin nan ne dole na, wurinki ba dole ba ne na zauna." "Keep quiet! Ina magana kina magana!" A hankali ta zame mayafin da ya rufe mata fuska suka haɗa idanu da Uwar. "Ya isa haka!" Inji Obinna, fitowa suka yi a tare, daidai malam yana tsakiyar almajirai ana karatu, wurin karfe hudu da wani abu na yamma. Kamar an ce mishi ya d'ago kai, ya hango yarinyar da Uwarta. Exactly mafarkin shi, Hadiye yawu yayi. Tare da mikewa yana kallon yadda Yarinyar take tafiya a iska, domin ba ta taka ƙasa. Kallon inuwayoyin da suke bin ta yayi, yaga daya cikinsu ya ja ya tsaya, bakar inuwar. Sai daya inuwar ne ya tsaya a tare da ita, fita yayi daga cikin almajiran ya nufe su. "Sannunku da zuwa!" "Baba Malam!" Ta kira sunanshi, murmushi yayi yana shafa kanta. "Na'am" Ya kalli Chioma da jikinta yayi sanyi, "Barka da zuwa Y'ata!" Sannan ya juya ya kalli Obinna, ya kira shi. Ba musu ya dauki kayansu, yana isa wurin almajirai suka amshi kayan, suka shiga da shi cikin gidan. A zauren gidan ya sauke su, sannan ya shiga cikin gidan da Amanda, yana faɗin. "Hajiya Sa'a! Zo ki taimaka min idan akwai sauran abincin, a bawa baki." Fitowa Innayo tayi tana kallonshi. "Wasu irin baki ne haka, da kake wani rawan jiki a kansu. " "Allah ne ya turo min su da baiwar Allah, gata nan." Fitowa Umma tayi, tana faɗin. "Kasan akwai wanda na saka aka yiwa Attahiru gashi nan, a basu sai Jamilah ta kuma min wani." Ita kan Amanda kallonsu tayi, tana murmushi da farinciki. Amsar abincin yayi zai juya ta ce mishi. "Baba malam, bani na dauka." "A'a ba zaki iya ba." "Zan iya mana!" Ta saka hannu ta amsa, yana biye da ita har zauren, ta ajiye ya fita ya kira almajirai Biyu ya basu dari biyar guda bakwai ya ce su tafi Bauchi club su sayo mishi namar kaza, sai kayan sanyi a shagon Mudan. "Tow Malam!" Sosai suka zauna suna kallon abincin, Amanda kuwa budewa tayi tana ci hankali kwance, tana faɗin. "Ku ba zai ji dadi ba idan baku ci ba" "Amaryata ke daya kike cin abincin?" Ya tambaye ta, "Eh Baba Malam." Shigowar almajirin da ya aika ya kawo ruwan sanyin, ya ajiye sannan ya fita. "Baba Malam!" Ta kira sunanshi a hankali. Kallonta yayi yaga tana kokarin bude coca cola, ya ce mata. "Amarya ba zaki iya budewa ba." Sai gani yayi ta buɗe murfin, ba tare da ta saka bakinta ba. A hankali ta sha sosai, sannan ta ajiye kwalbar cikin harshen Igbo ta cewa Uwar. "Nne! Kici abincin, uncle ba zai ci ba." "Amarya bari na baku wuri." Waje ya nufa ya sallame Almajirai, sannan ya bi ta daya kofar, ya shiga cikin gidan. Yana shiga ya samu su Innayo, Goma da Umma. Sai Jamilah da suke jiran karin bayani. "Malam bakin daga ina suke?" "Ban sani ba." Ya faɗa, yana me zama a bakin rijiya. "Ke dauko mishi kujeranshi." "Ita yarinyar da kuka shigo tare suke?" Kallon Innayo yayi sannan ya ce mata. "Yadda Attahiru da Amir suke kirana haka itama take kirana." "Nima nayi mamakin, yadda ta kira kamar tana cikin gidan nan!" "Jini na yake yawo a jikinta, baiwar Allah ce da babban al'amari." Ya faɗa a hankali, can wurin biyar almajirin ya dawo, ya kawo namar, ya ce a saka a tire a kai musu zauren. Haka kuwa Jamilah tayi, ta kai zauren. "Gwaggo Jami, ki cewa Baba Malam ya zo." Yadda tayi maganar babu wasa a cikinsa yasa Jamila ta amsa da cewa "Tow!" Bayan ta shiga ta gayawa Malam sakon shi, sannan ta kalli su Innayo ta ce musu. "Arna ne fa, ba musulmai ba." "Can musu!" Inji Innayo, sannan ta juya dakinta. Malam yana fita, Attahiru yana shigowa zauren, gaida su yayi yana rike da wayar Motorola. Gaisawa yayi yana faɗin. "Baki kayi ne?" "Eh Attahiru!" Ya gaishe su cikin harshen Ingilishi ya saka kai zai wuce, Amanda ta ce mishi. "Da ka dawo ka zauna, ayi maganar da kai domin su basu jin hausa. Malam baya jin turanci. " Wani irin abu yaji ya dira a kanshi ya dawo yana kallon yadda take cin nama. "Eh kuma haka ne, zauna ayi da kai." Zama yayi yana faɗin "tow!" Shiru zauren ya dauka, kafin Obinna ya fara magana da harshen turanci, ya ce musu. "Wannan sunanta Chioma ita ce ta haifi wannan Yarinyar, Amanda." Yayi shiru kafin ya ci-gaba da cewa. "Wato Adamu Malami Jajja, shi ya haifi wannan yarinyar nan." Wani irin shiru Attahiru yayi yana kallon yarinyar da take cin kasarta hankali kwance. Ganin yadda Attahiru yake zufa, malam ya dafa shi yana faɗin. "me ya faru?" "Wai sun ce yarinyar nan yar Baba Adamu ce." Murmushi Malam yayi, ya ce masa. "Ka tambaye su, da aure aka haife ta?" Sai lokacin Amanda ta ta d'ago kai tana kallon Malam. Yadda Tahir yayi tambayar yasa Chioma gyada kai tana faɗin. "Da aure aka haife ta. Shi sir Adam ya san kome." Tahir ya gayawa Malam, murmushi yayi sannan ya ce mata. "Ba zata hakura ta zauna da shi, ko akwai wasu rabon. Ni ta dauke ni a matsayin uba, ba zan taba barin wani abu ya same ta ba." In Sha Allah Yadda Tahir ya faɗa, sai da Obinna ya kaɗu, sannan ya kalli Chioma kamar zai kuka ya ce mata. "Kin ga abin da nake gudu ba." "Baba Malam." Ta kira sunanshi a hankali. Kafin ta ce mishi, "ka barta tana da nata Rayuwar." Shiru suka yi da Tahir kafin ya kuma magana, ta ce mishi. "Ya zaka yi da Innayo?" Sai da yayi shiru kafin ya bude baki zai magana ta ce mishi. "Mu ba mazauna ba ne, tafiya zamu yi ita yarinyar itace taku, Uwarta ku barta tana da rayuwarta. Kasan ƙaddarar da tasa muka kawo su nan? Hmmm Alhaji Sani Malami Jajja, zamu tafi amma lokaci zuwa lokaci zamu na kewayowa. Amma kafin nan ina son ka sani ita yar din jikar kace, ba iya mu ɗaya muke tare da ita ba, sai dai zuwan ta nan yasa muka bayyana daga gare ta. Mahaifiyarta zata tafi, dole ka saka idanu akan rayuwarta. Mun barka cikin amincin Allah." Daga haka, kwanta a wurin tana nishi. Nufar kanta Chioma tayi tare da riko hannunta. Yanzu take magana amma kuma yanzu jikinta ya kuma rikicewar kamar kwanakin baya a can Enugu. "Tahir ka kai wannan mutumin gidan baki, ita zamu shiga da Ita!" Haka kuwa aka yi, Malam da Chioma suka shiga cikin gida da Amanda, bai yarda ya kaisu wani wurin ba, dakin Hajiya umma ya kai su, har lokacin Ama birgima take tana kuka. Uwar ma kuka take domin ta gaji da ciwon Ama. Amma ba zata iya barin a wannan yanayin ba. Ta zata ta warke ne, sai dai me suna zuwa ciwo yana dawowa. Kiran sallah magariba, yarinya ta fara suma, tana ihu da gurnani. Tsaki Innayo tayi ta ce. "Saboda saka kai wahala ya dauko mana, arna zai musu magani." "Baki ga yarinyar taki yarda a ga fuskarta ba." Inji Hajiya Goma da munafunci yake cin ranta. "Can ta matse musu." Suka wuce dakinsu. Dakyar Umma tayi sallah, tana addu'a Ama ta fara ihu. Sai da ta shafa sannan ta kalli Chioma da bata jin Hausa itama kuma bata jin turanci. Shigowar Malam da wasu manyan dalibansa, suka shiga falon, anan aka shiga mata addu'a tare da fara karatu malam yana can gefe yana rubutu, ana bata tana sha da karfin tsiya. Ba karamin wahala suka sha ba, har zuwa lokacin da ta fara barci. Babu wanda ya huta domin tana fara barci zata fasa ihu ta fara shure-shure. Har wurin karfe daya na dare kafin suka samu ta yi barci, a lokacin kowa ya watse, sai dai me? Lokacin da suka nufi hanyar gidan kwanansu, anan suka hadu da wani abin al'ajabi. Domin kuwa wani katon bunsuru ne da gemunshi yake jan kasa, Idanunshi jajjur, ya kasa su da mugun gudu. Har suka shiga cikin gidansu dakyar. Tahir kuwa yana shiga dakinshi, a gajiye yayi addu'a ya kwanta. Babu abin da ya faru da shi sai mafarkin da yayi. Wai ya fito cikin dare. Ya ga wata yarinya a gindin rijiya, farin gashin kanta ya lullube ta baki daya. Tana diban ruwa daga rijiyar tana watsa shi a ƙasa ya nufi wurinta zai mata magana. Ta fasa wani irin ihu me bala'in ƙara, da ya tilasta mishi tashi a firgice. Yana kallon kofar dakinshi da yake wangale. Abin ya bashi mamaki dole ya mike tare da rufe kofar. Malam ma an kai mishi ziyara, sai dai basu kwashe da dadi ba, domin yana Sallar dare, aka zo mishi, basu yi nasara ba. Sai dai cikin daren akayi ta watsi da kayan aikin gidan, sai dai kaji an buga kofi da kasa, tare ihu me ƙarfi. Sai asuba aka daina motsi da kayan gidan. ★★ Gimbi Tunda Saif ya kirata, ya gaya mata zai wuce Azare kafin ya iso Bauchi, domin ta Kano zasu sauka, haushi ya cika ta. Bata kuma ɗaukar kiran shi, ya turo mata sako ya kai bila'adadin. Kamar tayi hauka, ita ɗayarta sai wani irin huci take tana jijjiga kafarta. Ita Saif zaima wulakanci?........ [11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥* EXQUISITELY BEAUTIFUL #Mai_Dambu 'Top-Notch Season 3 بسم الله الرحمن الرحيم Murmushi irin na manya Malam yayi, yana kallon Alhaji Adamu, sannan ya kalli Chioma da take kara k'ank'ame Yarta. Kallonshi tayi hawaye na zuba mata, ta zube akan gwiwarta, ko nauyin yar bata ji ba. "Me yasa ka tafi? Me yasa baka kuma waiwaya ta ba? Na cancanci haka daga gare ka? Ni fa marainiya ce? Ban san Uwata ba, mahaifin da nake jingine da shi ban san dadin shi ba, wancan kawai nasan dadinshi. Me yasa ka raba ni da shi? Ko tausayina baka ji ba, kasa ina tsaka da karatu aka kore ni, kasa kowa ya guje ni. Kasa duniya ta juya min baya, kasa duk inda na shiga, kowa farmaki yake kawo min. Kasan zaka tafi ka bar ni me yasa ka aure ni? Ban san ciwon kaina ba, just 16yrs yarinya karama da ni kayi abandoned dina ka tafi abinka." Bai damu da idanun kowa da yake kanshi ba, haka ya nufi inda take durkushe. "Wallahi ban gudu ba, ƙaddara ce ta same mu?" Tasss ta wanke shi da mari. Babu wanda yayi yunkurin dakatar da haka, "bukatarka ta biya, na haifa maka Y'a har office din hukumar bautar ƙasa naje na tura maka sako, ka bibiye ni?" "Jiddah!" "Don't!" Ta daka mishi tsawa, "na zata Allahnku yana jin rokon kune, ashe yaudara ce kawai. Na zata idan nayi sallah nayi.azumi kace zai amsa min bukatata. Karya kake? Kasan yadda na sha wahala? Na Barka na bar addininka, dama Amanda na kawo, amma i decided na juya da ita, ba zan iya barinta a hannunka ka lalata min rayuwarta ba." Kamar karamin Yaro, kuka yake da dukkan zuciyarshi. Wannan itace ranar da yake gudun zuwanta, "Jiddah!" "Idan ka kuma kirana da useless name din nan, sai na kashe ka." "Tahir! Ka bata hakuri, ka gaya min me tace." Inji Malam, A hankali ya shiga bawa Malam labarin abin da ta ce. "Kace mata, Allah yana jin rokon bawansa koda bazata yi imani da shi ba, tayi hakuri a matsayin mahaifin shi na bata hakuri." Ya cire rawaninsa, ya fara kokarin sauka akan kujeran, tayi maza ta rike gwiwarshi. Tana girgiza kai, ta cewa Tahir da yake gaya mata abin da Malam ya faɗa. "A'a idan ka durkusa min, zan mutu ina danasanin kimarka da na tab'a." A hankali ta sauke Amanda da take nishi sama sama. Ya zubawa fuskarta idanu da babu mayafi. "Kunga ikon Allah ko? Yarinyar nan jinin, Babawuro ne kuga kamar da take kwance bisa fuskarta." Sannan ya kalli Alhaji Adamu wanda yake kuka kamar me. "Ko ban ce maka Allah zai saka mata ba, kai kanka kasan tabbas sakayyar Allah sai ta bika. Na sha tambayarka me yasa kake cewa mu yafe maka, sai kace babu kome da ace tun wannan lokacin ka gaya mana abin da yake faruwa da mun magance maka shi, sai da kome ya lalace." Kan shi a kasa hawaye na zuba miishi kamar karamin Yaro, sai girgiza kai yake yana hawaye. "Malam ban gane ba, kun saka min Yaro a gaba kai da arniya sai cin mutuncin shi kuke me ya faru?" Inji Innayo, wacce take cika tana batsewa bata so haka ya faru a gaban Umma ba, taya zata facing kishiyoyinta da zancen da bata fahimta ba. Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya fara basu labariin, bai kai ga karshe ba Innayo tayi tsalle ta dira zani a hannu, ta ce mishi. "Wallahi idan na yarda Allah ya tsine min albarka. Wannan ai munafunci ne, taya Adamu zai auri mace a bayan idanun mu. Har ya haihu da ita bamu sani ba. Karya ce ba yar Adamu ba ce ta kwaso shegiya ce don ta bata mishi suna." Ta fada tana haki. "Indoh kin san dai nan babu me Miki karya, sannan ga Babawuro nan, tambaye shi da kunnenki." Ya nuna mata Alhaji Adamu, wanda ya kara diriricewa, ba zaka ce yana da mata da Yara ba. Domin ya rikice kamar Yaro karami. "Adamu wai yarinyar nan Yarka ce?" Kamar saukar aradu, haka yaji tambayar, a hankali ya d'ago kai, ilahirin jikinshi kerma yake kamar kasa ta bude ya nutse tsabar kunya, baki daya wurin kannen shi ne. Babu wanda yasan lokacin da ta iso wurinshi tana huci. "Gaya min Yarka ce?" D'ago kai yayi a karo na biyu, kafin ya san me take shiri ta kifa mishi mari, ta ce mishi. "Yarka ce?" Hawaye ne yake zuba miishi ya gyad'a mata kai. Bata san lokacin da ta rufe shi da duka ba. "Ni zaka kunya ta, da girmanka ka ajiye karuwa a waje har da yar dakar kuka. Wallahi ba zaka ja min abin kunya ba. Wallahi tun wuri ka san yadda zaka yi da su, ka kore su domin ba zaka ajiye min abin kunya ba." Yadda take magana da ihu, zai tabbatar al'amarin ya girgiza kwakwalarta da zuciyarta. Cikin wani irin heavy breathing ta fashe da wani irin kuka. Ta zauna a wurin tana kuka. "Ka cuce ni Adamu, duk Yarana a rasa wanda zai janyo min abin kunya sai kai da girman ka, tow wallahi na rantse da Allah da rayuwata da mutuwata take hannunshi, ba zan tab'a kaunar yarinyar nan ba, domin da ita gara na ga mala'ikan mutuwa. Ka je yadda ka sani kuka." "Keeeee! Aisha ina zaki kai rabon wannan yarinyar? Baiwar Allah da babu ruwanta, kada ki sake ki mishi baki, ƙaddara ce babu wanda ya tsammaci daga haka, kowa yasan yadda ƙaddara da rabo yake." Ita kan Chioma tsoron Innayo yasa ta kara rungume yarta. Mikewa Innayo tayi tana binsu da mugun kallo kafin ta ce mata. "Ban karbi yarki a matsayin jini na ba, don haka ta tattara ta su bar gidan nan kafin na bude idanuna." Duk da bata san me Innayo take fada ba, amma jikinta ya bata magana take gaya mata, don haka ta mike zata bar taron. Amanda ta farka, tana kallon Uwar murmushi tayi ta ce mata. "Nne ai na gaya miki ba zan bi ki ba." Rikota tayi, amma ta zame a jikinta ta koma gefen Alhaji Adamu, ta kwantar da kanta a jikinshi, "Papa ka gaya mata cewa, duk sakon da ta tura ya same ka, na ka ne bai same taba. Ka daina kuka. Zaka samu abin da kake ta son samu yau shugaban kasa zai saka maka hannu." Kuka yake amma haka ya rungume ta. "Malam Aishatu Nazneen Y'ata ce." Ya faɗa yana kuka, ya cigaba da cewa. " Duk sakonta yana isowa ta hannun hukumar bautar ƙasa, kuma nima nawa nasan ya isa can Anambra, ban san ya aka yi haka ya faru ba." "Matar Babanta da Babanta suke rike duk abinda kake turo mata." Hannu ta kai xata d'ago yarta, "Nne kije ba zan bi ki ba." Ta faɗa tana kara shigewa jikin Babanta, baki daya gidan tausayin Alhaji Adamu da Chioma suka koma ji, domin itama kuka take ya bata yarta ta fasa bashi yar, ta fasa auren kowa zata zauna domin yarta. Ita kuwa Yarinya ta ce bata zuwa ko ina taga ubanta. Abin tausayi haka Obinna ya rikota tana kwacewa ta ce mishi. "ka kyale Ni ba zan bika ba, yarinya ta tana hannunsa." "Chioma kizo muje, ba zasu baki yarki ba sannan ki yi godiya tunda gashi ya amshe ta ." "A'a bar ni na amshi Y'ata " "Idan kina son Yarki, sai dai idan zaki zauna da ni." Wani uban tsalle tayi ta koma bayan Obinna, jikinta yana rawa. "God forbid na dawo rayuwarka a karo na biyu, bayan ina gani Mahaifiyarka, bata amshi Amanda ba." Ƙasa magana yayi, yana riko yarshi, domin kuwa ba zai iya bata hakuri ba, baki daya yan uwanshi sororo suka yi domin babu wanda ya fahimci yadda za a kawo karshen rikicin nan. Wasa wasa

Chapter 6 of 12