of health, yana nan a Bauchi a nan jajjan, da matanshi da Yaranshi shima.
*Fatimah Malami Jajja
Tana koyarwa a FGGC Bauchi, tana zaune a Ibrahim bako, tana da Yaranta. Kusan sun dauko halin uwarsu.
Hajiya Goma, kai jama'a Hajiya Goma Allah ya daura mata munafunci, idan kana niman munafuka ka samu Hajiya Goma, a shafa fatiha a rufe da addu'a kana a kara da salatin Annabi, domin yadda Al'amarin zai wuce. Duk da ta tsufa, amma munafika ce na bugawa a jarida, ga hada husuma ta koma gefe tayi shiru. Tana da Yara bakwai da a gidan, uku sun mutu saura huɗu.
*Habibu Malami Jajja
Shine babban dahta, shi ne sa'an Usman, yana kasuwancin shi, a central market. Yana zaune a dutsen tanshi da matanshi.
*Hadiza Malami Jajja
Tana koyarwa a primary school din sale manga, tana da Yaranta, anan jajja take da zama.
*Aminu malami Jajja.
Dan union ne a tashar mass, yana zaune a cikin jajjan gidan Malam sannan yana noma, masanin sirrin noma ne. Allah ya bashi wannan baiwar.
*Jamilah Malami Jajja.
Ance kamar kumbo kamar kure, tana nan Allah bai bata haihuwa ba, tana sayar da abinci a cikin gidansu, domin kuwa halinta da ta gada a wurin Uwarta shi ya hanata zama a gidan aurenta, har kotu sai da aka kaita saboda munafunci da hada husuma.
Hajiya Lami.
Tana da zafi da fada, da kuma faɗar gaskiya ko zaka mutum, sannan itama Malama ce, tana aikin wa'azi idan za ayi suna ko biki, walima da sauransu Yaranta ne kananu, kuma Amaryan Malam Malami Jajja, wacce tayi nasarar sace zuciyar dan dattijo. Tana da Yara uku,
*Jamal Malami Jajja
Yana karatun master a Atbu, kwanan nan yayi aure
*Aisha Malami Jajja
Tana aure a jama'are, tana aure a gidan Sarkin jama'are, tana kasuwanci na fitar hankali, domin mijinta yana da rufin asirinshi, don ma Mahaifiyarshi ta hana shi tafiya da A'ishan ne.
*Balkisu Malami Jajja
Autar malam, kenan ga kyau ga ilimi kaf gidan ita ce ta dauko Malam a kyau da tsawo. Tana aure a Abuja, kuma tana karantar medicine,
Malam yayi kokari da koda ya baka auren Yarshi, sai ya gaya maka yarshi zata yi karatu, a cikin Yaranshi. Jamilah ce taki boko kamar me, shi yasa ya duba inda Allah ya dafa mata, ya bata kudi ta fara sana'ar abinci.
Hajiya Innayo da Hajiya Goma tafiyarsu daya, Hajiya Umma da Hajiya Lami, tafiyarsu daya. Idan ka cire Hajiya Lami da Hajiya Umma, Goma da Innayo kamar su kashe kansu don kishi. Wani irin azzababen kishi ake kowa boye na shi laifin yake..
Duk da wannan nasarar da suka samu, Malami bai tab'a yarda a saya mishi kome a cikin gidan shi ba. Hatta namar miya yana da dabbobinshi a cikin ɗaya gidanshi da yake kiwo. Malami ya yarda da kanshi, shi yasa duk wata buƙatarshi yake miƙawa Allah tare da tsayawa akan kome.
Idan akwai mutumin da yasan darajar rayuwa da mutane, Malam Malami Jajja ne. Bafulatani ne daga kasar Kamaru, yawon almajiranci da kasuwanci ya kawo shi Bauchi shi da danginshi da suke Rijiyar Malam. Kyakkyawan mutum ne wanda har yau kana ganinshi ka ga wanda zamanin samartakarshi an buga kyau. Wani abun da yake kara ja mishi kima a idanun mutane, mutum ne mai yawan sadaka, duk ranar juma'a ana sadaka a gidanshi.
Kuma wani abin da ba a cika samu a wurin Malaman tsangaya ba shine, yana daga cikin wadanda suke bawa almajirai damar karatun boko da na addini. Tun da ya zo Jajja ya kafa unguwa aka mishi lakabi da malami Jajja. Wato unguwar Jajja samanta kadan akwai wani unguwa da ake kiranta Unguwar Borno, dayawan mutane da tarihi suna faɗan cewa mutanen borno sun zauna kafin suka bar wurin, amma a asalin labarin unguwa yana cikin unguwar da Aljanu suka zauna.
Izuwa yanzu babu wani wanda zai baka labarin unguwar, ta can yamma da unguwa katon gulbi ne da ruwa yake taruwa, haka yasa dole unguwar ta zama matattarar Aljanu da miyagu.
Zuwan Malami Jajja, ya fatattake su aka kafa makarantar allo ana koyarwar ba dare ba rana, Malami Jajja. Mutane dayawa suna cewa yana tarayya da aljanu, mutanen boye shi yasa wani lokaci yake yawan sadaka da yanka, bayan nan duk inda aka samu matsalar Aljanu wurinshi ake zuwa. Domin aikinshi ne.
Koda yake ba iya aikin Aljanu yake ba, hatta matsalar maita, asiri, da tsafi..yana bada taimakonshi daidai yadda Allah ya sanar da shi, shi yasa gidanshi baya rabuwa da masu zuwa amsar addu'a da Magani. Har kwanan gobe yana bada magani da addu'a, sanna sadakar da zaka bada ƙalilan.
Sannan Yaranshi idan mazan, suna bada taimako na fitar hankali. Wani abu da mai karatu zai sani, Yaran Malami suna da dabi'ar son mata, mazansu basu zina amma fa duk inda suka ga mace matukar suna da interest akanta, sai sun nime ta. Haka Malam Malami shima yana son aure aure, kafin ya cike mata hudu yayi aure aure, sai dai matan basu zama ne domin mutum ne me tsananin bukatar gaske.
Sannan Yaranshi ma haka suke, har kowa yasan cewa haka halinsu yake na shegen son mata, matukar zasu ganki magana ya ƙare.
Kaf zuri'ar Malami jajja babu wanda ya dauke shi a kyau, da tsawo da haske. Har girmanshi, yellow ne shi, domin tsananin haskenshi dayawan mutane cewa suke ya haɗa iri da larabawa, murmushi kawai yake domin shi yasan shi me kyau ne, ko a gidansu na Kamaru ana kiran gidansu da Gidan kyawawa.
Basu da arziki fa, amma kuma akwai ilimi kamar me, amma kuma babu arzikin da za a bude baki ace shahararrun masu kudi ne, sai da akwai na rufin asirin da biyan buƙatar rayuwa, noma da kiwo ya rike shi gam. Sannan yana kara saka Yaranshi a kan lallai su nime ilimi. Bayan haka ya kara musu wani irin kusanci da junansu, suna son juna suna tausayin junansu. Kishin iyayensu bai shafe su ba. Domin har yau da yake da shekaru Tamanin da biyu, yana tsaye ne a kan kafarshi. Don tsabar tsawonshi har sai da yayi doro.
Idan ka cire Dr Adamu Malami wanda ya dauko tsawonshi. Amma kyau da farar fatar Malami, sauran yaran fatar iyayensu mata ne.
_This article is a fictional story, it is not made to insult anyone or any other, it is not made to abuse a community or religion, it is written under the guidance of research and the author's guess, it is wrong to turn the story in any way without asking permission, not a writer, this is against the law of self-ownership, in the law section, it can face a severe punishment or the option of paying a fine._
#Alhamdulillah, gabatarwar mu, kenan acikin labarin nazneen ban san me gobe zata haifar ba..... Amma... Labari ne me tab'a zuciya. Labari ne me cike da alhini da ban tausayi. Soyayya da sadaukarwa, ƙaddara me cike da kalubalen rayuwa.
Kudai kubiyoni acikin rikitattacen labarin Domin ganin salon da ke dauke dashi🥰..... Ina fatar zakuzo ayi tafiyar nan tare da ku💃💃💃💃💃💃
Mai_Dambun
Marubuta🥰❤🔥
Message Mai_Dambu on WhatsApp. https://wa.me/2348130269641
[11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥*
EXQUISITELY BEAUTIFUL
Top-Notch
Season 3
Chapter-3
The little demon
بسم الله الرحمن الرحيم
Yawun tsoro ta hadiye, sannan ta riko hannunta. "Please stop it, am worry about you." Kallon idanun mamar tayi, da kwayar idanunta masu bala'in ban tsoro. "Am I starved you?" Rungume ta mamar tayi, hawaye na cika mata idanu. "No" ajiyar zuciya ta sauke, cikin wani irin murya mara dadi da harshen hausa ta ce mata. "Ki bashi!" A razane ta kalleta, zubewa tayi a gaban 'yar, tambayoyi ne a bakinta amma yanayin 'yar da abin da take yasa gaba daya tsoro ya cikata. "I said!" Rufe mata baki tayi tana girgiza kai. "don't shout for me!" Yadda mamar tayi maganar ya sa ta juya zuwa jikin bangon dakin, ta cigaba da tsayuwarta, tana wasu kananun magana. Da sauri ta fita daga cikin dakin, ta same shi tsaye. Ta mika mishi ledar. "Kaje ka dauki kuɗinka, ka dawo min da sauran." Ta juya daki da sauri. A hankali ya juya yana kallon wurin ba kowa, sannan ya bude ledar. Dollar ne, a razane ya juya tare da nufar kofar dakinta ya buga. "Chioma!" Ya kira sunanta. Kamar ta fashe da kuka ta ce mishi. "Yes!" Ta amsa tana fitowa, kallon juna suka. "A ina kika samu wannan kuɗin?" "Ka dauki naka ka bani sauran, kawai abin da nace kenan!" Ta tsinci kanta cikin wani irin juriya. "Na san baki fara sata ko fashi da makami ba." Ganin Amanda suka yi a tsakiyarsu, ta ce mishi. "Tunda an baka kudinka cire naka, ka dawo mana da sauran aka ce." Gyada kai yayi, yana kallon yadda gashin kanta, ya rufe mata fuska. Sai hancinta kawai yake iya hangowa. Hadiye yawu yayi cikin tsoro ya juya, tare da barin kofar. Rike hannunta tayi ta kwace tana faɗin. "Ki daina tsoron mutane." Suna shiga dakin, ta nufi inda kayan stuff ɗinsu yake ta cire musu garin kwaki. Zata jika ta ce mata. "Nnen me! Ba zan sha gari ba" "Amanda ya kike so nayi Tow?"
"Kudin can, da yake hannun mutumin nan, zai ishe mu!"
"Kina son a fara zargin muna sata nake ko kungiyar asiri na shiga? Kin san irin mutanen da muke raye a cikinsu."
"Me yasa ba zaki nemi mutumin da ya jefa ki cikin wannan Yanayin ba? Me yasa kike blaming kanki da abin da baki isa sauyawa ba, Nne?"
Hawaye ne ya zubo mata, ta rarrafo gaban yar, ta juyota. "Waye!" Ganin yadda idanunta yake juyawa kamar agogo, ta fahimci ba Ama dinta ba ce, fa baya ta ja.
"Please ku kyale min Y'ata! Na haɗaku da abinda kuka yi imanin dashi." Ta faɗa muryanta na mugun rawa, domin izuwa yanzu ta fahimci wani mugun al'amari ya tabbata akan Yarta. Wutar dakin ne ya fara daukewa da kawowa, abin da ta gani yasa ta komawa da baya, domin kuwa sai da ta kusan suma. Don numfashinta barazanar daukewa yayi, wutar dakin ne ya tsaya cak, takowa Amanda tayi ta zube a jikinta, hawaye ne ya zubo mata. A haka suka cigaba da zama har landlord na gidan ya dawo musu da sauran kudin. Zata fita mamar ta riketa. "Please Amanda!" Kallon mamar tayi, "let me talk to him!" Ta faɗa da wani kakkausar murya, kamar wacce aka daureta haka ta cigaba da zama,bata san lokacin da ta bar dakin ba, asalima wani tsoro ne ya kamata domin kamar Amanda tana tafiya da kafarta. Tana fita ta kalle shi, "wannan shi ne kudin da muka baka? Ka koma ka dawo da shi, ko kuma nan da minti biyar a fara kukan mutuwarka." Yadda take maganar tsoro ya cika mishi ciki domin bai tab'a ganin abin tsoro ido da ido irin yau ba, gaba daya gashin kanta sun mike tsaye, kwayar idanunta kamar agogo haka suke wani irin juyawa, kuma duk da duhu ne, wani irin haske suke kamar wuta. Wal-wal-wal,
Zubewa yayi a gabanta, "ku yafe min, zan dawo muku da kudinku!" Domin gaba daya ji yayi kamar an daure ƙafafuwanshi.
Yadda ya sunkuyar da kai, ba karamin tsoro ya cika shi ba. Ganin haka ta koma daki, shi kanshi bai san lokacin da ta koma dakin ba, sai dai d'ago kai da yayi yaga wayam ba kowa. Da sauri ya fita zuwa cikin gidan, can sai gashi rike da ledar kuɗin. Wannan karon bata fito ba Uwar ta fito ya zube a gabanta yana faɗin. "Chioma ki yafe min, naso cutarku gashi nan na dawo muku da kudinku, ni dai ki taimaka min ku bar gidan nan!"
Wani irin sanyi jikinta yayi tana son rokonshi ya barsu kafin ta samu wani wurin, amma bakinta yayi masifar nauyi. Haka ta juya tare da rufe kofar, ranar bata iya barci ba, da assussubar fari ta farka sakamakon nishin da Amanda take, zama tayi ta d'ago kanta, tana faɗin. "Ama meke damunki?"
Hawaye ne ya zubo mata, bakinkirin yana sauka a saman fuskantar. "Ama gaya min." "Nne mu bar unguwar nan, wadancan mutanen da suke ihu, yana saka min ciwon kai. Kaina kamar zai fashe bana son abin da suke yi!" Wani irin faduwar gaba ta ji, ta rike ta tana kara nazarin abin da take nufi. "Allahu Akbar!!!" Bata san lokacin da ta kamkame yar ba, "kiran sallah yana saka miki wani abu ne?" Gyad'a kai tayi hawayen na kara zuba mata. "Nne mu bar unguwar nan!"
Barcin da basu koma ba kenan, ita kuma Amanda ta cigaba da nishi da gurnani, har sai da aka fita Masallaci. Sannan wani wahalallen barci yayi gaba da ita. Ganin haka Chioma ta tashi, tayi duk abinda zasu bukata, sannan ta tafi shagon da take aikin saloon, ta gaida matar da take shagon.
"Chioma ya jikin Amanda?"
"Aunty da sauki, sai dai har yau bata barci. Da ta fara, zata farka wurin 4 :30 zuwa six ta koma!"
Shiru matar tayi sannan ta ce mata. "Ki amince sai mu kaita, wurin Baba ya dubata." Shiru tayi da cire tsammani da laluran Yarta ta ce mata. "Anya zamu dace kuwa?"
Ta faɗa tana taraddadi, kafin ta kalli matar, murmushi matar tayi tana faɗin. "Idan akwai wani abu zai gaya mana, idan kuma aikin ba na shi ba ne, shi ma zai gaya mana." Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce mata. "Bari na gama aiki, sai mu tafi"
"A'a muje ai sai da lafiya ake kome, idan ba lafiya baki isa kiyi ba."
Haka tabar aikin, suka nufi gidansu. A hanya take gaya mata landlord ya tashe su."tow ina zaku?" "Ban sani ba, sai dai muje wurin Baba muji,kafin nayi tunanin wurin da zamu koma"
Da wannan suka shiga cikin gidan, tare da gaida mutanen da suke tsakar gidan kowa yana harkar gabanshi. Dakinta suka nufa, ta bude har lokacin tana barci. Wani mayafi ta dauka, tare da lullube Amanda, wacce take barci kamar gawa. Ta goyata suka bar dakin, da gidan gaba daya suka.
Tafiya ce da ta dauke su tsawon mintuna arba'in da biyar, kafin suka iso wani karamin kauye, a wajen gari. Sai da suka shiga cikin kauyen wanda shima dogon tafiya ce, sannan suka isa wani gida me dauke da wasu dirka-dirkan bishiyoyin rimi. Kasancewar akwai mutane dayawa a kofar gidan, yasa suma suka nemi wuri suka zauna suna jiran layin yazo kansu.
A cikin gidan kuwa kukan, dabbobi ya haukata musu lissafi, sai gudu suke suna neman maboya, d'ago kai tsohon yayi ya kwala kira. "Emeka!" Da sauri wani saurayi me daure da jan kyalle ya leko. "Yes Papa!"
"Akwai baki da suka zo, ka ce su zo." "Ok!"
Fitowa yayi waje, ya ce cikin d'aga murya..
"Su waye suka zo yanzu?"
Mikewa matar tayi, tana faɗin. "Mune!"
"Ku shigo inji Baba!" Ya juya tare da nufar cikin gidan suka bishi a baya.
Suna shiga cikin gidan wani katon kare, yayo kansu, yana ihu. Kamar zai kai musu cizo. Tsayawa Chioma tayi, cikin tsannanin tsoro. Wani irin kuka karen ya fara tare sa birgima a kasa. "Ya isa haka!" Tsohon ya daka tsawa, tashi karen yayi da gudu ya bar wurin tare da shiga cikin wani keji, yana me buya.
"Sauke ta!"
Ya faɗa yana kallon Chioma. Sauke Amanda tayi, ya taka har gabanta. "Shawara daya zan baki, ba zaki iya rike ta ba, ki mai da ta cikin ahalinta sune zasu riketa, zasu yi ta baki wahala ne kina kashe kudin da kike samu. Ki mai da ita cikin danginta. Kina da rayuwa me kyau, ƙaddararta ce ta haɗa ku. Ba zaki iya riketa ba. Shi ubanta zai rike ta kamr yadda yake ririta rayuwarshi. Wannan ki saka mata a hannu, baku ne kuka ci bashi ba sannan ba ita ba ce aka ce ya tsayawa ba, amma ya tsaya akanta, laifi-laifi ne, amma laifin da aka yi shi ya haifar da tsayawa akanta, ba shi daya ba ne, akwai wasu. Ki maida ita wurin danginta, zaki yi farincikin rayuwa sama da tana nan, duk da ɗa da uwa. Soyayyar ba zata gushe ba. Kuma zata nime ki duk inda kike!"
Daga haka ya juya tare da komawa dakinshi, "na gaya miki, ki mai da ita tunda kuruciyarki." Jiki a mace ta kalli matar da ta kawo ta. "Haka zan mai da ita?"
"Muje!"
Juyawa tayi ta goyi, Amanda. Suka fito daga cikin gidan, fitowa dattijon yayi. Tunda yake aikinshi bai tab'a haduwa da mutanen da suka bashi tausayi ba. Sai dai dole ya gaya mata gaskiya, yarinyar ba zata iya da ita ba. Manyan evil spirits da suke kanta sunyi yawa.
A hankali ya koma dakinshi, ta jikin madubin dakin, yaga wani katon mutum. Rike da wani zabgeggen takobi. "Me yasa kace ta mai da ita wurin danginta!" "Ka tafi babu ruwana da kai, tunda suka ce zasu zo ka rigasu zuwa, bayan ka min kashedi. A matsayina na dan adam na basu shawara. Sauran kuma ra'ayinka ne."
Wani irin gurnani yayi madubin yayi kamar tsawa. "Akanta zan aikata kome."
Daga haka ya b'ace.
★
Bauchi State, Nigeria.
Kusan har dare Gimbi bata yanke abin da yake ranta ba. Domin bata son hanyar da Uwarta take. Kallon agogon dakin tayi sha daya, saura kwata. Komawa gadon tayi ta shiga kiran numbershi. Ringing daya yayi aka dauka, yadda aka sauke ajiyar zuciya yasa ta daure fuskarta tam.
"Kana nan akan bakanka ko ka janye?"
Cikin wani irin hucky voice ya ce mata. "Princesse! Ki duba ni!"
"Dalla ka min shiru, ina cewa aure aka ce kayi."
"Listen to me, Princess sunan aure ne, amma bani da wata mace bayan ke, ki yarda da ni."
"Kasan Allah kada ka kuma nima na, balle kayi tunanin zan dawo gidanka, har nice ake min gori naki haihuwa."
"Princesse ki fahimci wani ba, bana son muna haka dake please, ki dawo idan ma ba zaki dawo ba, zan zo na dauke ki."
"Ni dai kada kazo, ku ishe mutane da wa'azin Allah ya ce Annabi ya ce, nan kuwa ku a gidajenku ba haka ba ne!" Sauke numfashi yayi yana jin babu dad'i, kafin ya ce mata.
"Kiyi hakuri, ki duba na tura miki sako babu yawa, zan zo jibi idan aka sauko juma'a."
"Dan turowa kayi babu yawa?, bayan kasan ka hanani aiki balle kasuwanci? Saifullahi-Khalidu, na gaji da zaman gidanka, ka sawwake min kawai na gaji. Yan uwanka su bani wahala, kai ka bani wahala, kowa gani yake na hanaka aure kawai ka sake ni ka auri wacce zata maka abinda bana maka." Kamar yayi kuka haka yaƙe ji, Gimbi tasan ita ɗaya ce, shi yasa take haka, da yana da wata macen ba zai iya daukar halinta ba, amma shi gaba daya baya jin sha'awar auren wata mace kawai rashin fahimta ce irin nata, da kuma dabi'a irinta mata, cikin nutsuwa da kwantar da murya ya ce mata.
"Please" ya faɗa cikin rarrashi, yana murmushi. "Shi kenan, amma ka sani idan na dawo zan tafi Malani!" Ajiyar zuciya yayi yana faɗin. "Shi kenan, zan yi duk abin da zaki bukata, please zan zo daukarki domin naji ran Mama ya b'aci." Ya faɗa yana jiran me zata ce, murmushi tayi ya ce masa. "Ba dole ranta ya b'aci ba, an tab'a mata yar autarta." A hankali kuma hiran ya koma na soyayya. Kamar ba zasu rabu ba, kafin suka yi sallah. Duk abin da suke a kunnen Mamanta, don haka ta daurawa ranta, ba zata tab'a barin Gimbi ta rabu da Saifullahi-Khalidu ba, domin kuwa ta hanyar shi zata maida yarta abar so a idanun duniya, sai ta mai da yarta zinariya a gidan aurenta.
Juyawa tayi ta koma dakinta, ta shiga surkullenta tana zaune, sha biyu yayi a lokacin dakin yayi wani irin haske ja. Juyawa tayi ta mike tsirara ta nufi dakin Gimbi, bata bukatar bude kofar, bangon dakin ta ratsa ta wuce. Sannan ta nufi inda Gimbi ke barci, shafa kanta tayi. Kurwanta ta mike, a hankali ta riko hannunta suka bar dakin, suna fitowa ta ga takalmin, komawa kanana suka yi, sannan suka shiga cikin takalmin. A hankali takalmin ya shura da gudun tsiya.
Tafiya suka yi kamar zasu bar duniyar, kafin suka isa wani kasungurmin daji, inda wuta takeci cikinta ganganga. Ajiye takalmin sukayi tare da nufar cikin dajin, Maman Gimbi tana cire kayan jikinta da suka kasance bakake, tana me watsar dasu. Kafin ta isa gaban wutar, tsirara suka kama rawa, idan suka yi rawa suka yi rawa sai su yi goho sai wuta ta fito ta duburarsu.
Wannan abin sai ya zamewa Gimbi kamar mafarki, domin bata taɓa sanin akwai irin wannan abin ba, duk da tasan Uwarta Mayya ce, amma bata kawo a ranta shaharan Uwarta ya kai har haka ba, tana tsaye suka yi rawa suka taka, kafin aka tsayar da kid'an. Wani irin dabba ya fito daga wani rami,shi ba damo ba, shi ba kadangare ba, shi kuma ba guza ba. Gashi nan jikinshi kamar kada, yana da hannu da kafa kamar ta tumakai.
Amma kanshi kamar na jaki, haka ya zauna yana kallon Gimbi. Bakinshi ya kai a kan kwaryar jinin da yake gabanshi ya tsoma sai da ya sha sannan ya juyo yana kallon Gimbi, wacce ba zata iya cewa tasan meke faruwa ba, rikota wasu karfaffan mata suka yi, sannan suka kawo ta Gabanshi, kwaryar ce ta tashi sama suna rike da ita, aka kafa kanta sai da ta shanye jinin tass, kafin ta fadi a kasa. Tana wani irin gurnani.
Zubewa Uwarta tayi tana murna, tana wani irin rawa, tana juyi kamar ba mutum ba."Gorumfa na gode, ina murnar Gimbiya ta shigo cikin mu, yau nake murna. Gorumfa dangin mijinta basu sonta, so suke su ga bayan aurenta. Gorumfa a bata karfin ikon da zata mallake shi har abada."
Yadda take rokon bukata wa yar zata baka mamaki, shi kuma dabban sai gyada kai yake, kallonta yayi. Kafin ya ce mata. "An lamunce mata, amma abu daya zata na kawo mana, mace me juna biyu."
Zubewa Uwarta tayi tana faɗin. "an gode godiya muke, mun kara mika godiyar mu!" Ta faɗa tana wani irin juyi kafin kace me ta koma bakar mage, wuluk. Sauran ma kowacce sai da ta koma irin dabbar da yake zane a gefen kugunta. Gimbi kuwa tana sume....
#Mai_Dambu
[11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥 <4>*
EXQUISITELY BEAUTIFUL
#Mai_Dambu
Top-Notch
Season 3
بسم الله الرحمن الرحيم
Zagaye wutar suke, suna ihu da waka wasun su,suna kukan halittun da suka koma. Kid'an da ake musu ne ya tsaya cak, kafin kuma suka koma suffarsu ta asalin, wani katon tire aka kawo musu aka ajiye a gabansu, cikin siddabaru wata karamar tukunya ta bayyana, a hankali aka dora akan wutar. Suna zaune sunyi jigum-jigun. Kafin kuma suka ware idanu akan tukunyar, yawunsu sai dalala yake yana kara sauka, saboda murnan zasu ci abin da yake tunkuyar.
A hankali dabban nan ya isa gaban Gimbi. Yayi wani irin tsalle ya dirka akan kirjinta, "ahhhhhhh!" Taja nishi sannan ta bude idanunta. Taga dabban ya juya yana taku ɗai-ɗai, cikin izza. Ya isa bakin wurin zamanshi ya zauna, tashi tayi ta
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 12