Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya ce mata. "Na same ku lafiya? Ina Abba.? Aunty Mariya ya kuke." Duk sai ya basu tausayi suka kasa magana. Kallonshi kawai suke kamar sun samu talabijin, mikewa Nassif yayi ya fita domin bakin ciki ya ishe shi. *** Gimbi tunda ta shiga ƙungiyar cult, baki daya ta tattara Siyamah da Linah, ta watsar domin yanzu basu da ikon isa da matsayin da take basu isa taka inda take ba, ta wuce matsayinsu da darajasu, a wannan lokacin ta hadu da mata mayyu kuma gogaggun yan boko, domin duk wani mayye matuƙar ya hadu da d'an uwanshi, ana kulla abota tare da karawa juna sani, ranar da suka dawo suka hadu da wasu manyan mata biyu, daya yar arewa ce, irin christan arewan nan domin yar Kaduna ce. Daya kuma yar south Africa ce, tunda suka hadu, Gimbi ta hangosu ta fahimci dukkansu mayu ne, sannan a cikin Mayun su manya ne, don haka ta shiga binsu da idanun. Daya me suna Hannatu, ita ce ta fara zuwa inda Gimbi take, ta zauna tana murmushi. "Wancan ustazun mijinki ne ko?" Gyada kai tayi tana wani yatsuna fuska. "Ga wannan idan kina son ganin mu." Daga haka ta bar wurin, har suka iso lagos matan sun burgeta,. Shi yasa koda suka dawo bata yarda ta kuma zama ba, bin matan nan tayi ta nimo su dakyar. Lokacin da ta isa gidan, dakyar aka barta ta shiga, koda ta shiga cikin compound na gidan, ta kuma gigice domin taga inda Arziki yake, don haka ta ajiye motarta a gefe guda, sannan ta fita sanye take da abaya, tayi kyau sosai sannan ta nufi cikin gidan. Koda ta isa bakin kofar shiga entery ba gidan bude mata kofar aka yi, a hankali ta shiga cikin gidan, babu kowa a falon, amna kamar an san da zuwanta. "Hello!" Ta faɗa tana leka cikin falon, wani irin maciji ne ya faso mata kai, idanunshi jajjur, sai fito da wani irin harshe yake bakinkirin, murmushi tayi tana faɗin. "Sannu ina mutanen gidan?" "Gamu nan!" Aka faɗa, suna saukowa daga upstair. "Gimbiya Baby, ya kike? Ya aka yi kika san wannan me kula da gida ne?" D'ago idanunta tayi, da suka koma sak na mage ta ce mata. "A duk inda naga namu, ai ba boyewa yake ba, ya bayan rabuwa?" Murmushi daya tayi ta ce mata. "Zauna ga wuri bari na kawo miki abin sha." "Anya na koshi fa." "Tab, kizo gidan nan ki kasa cin wani abu ko sha, ai ba maita ba ne da zamu hanani." Dariya suka saka su uku, haka Hanne ta kawo mata, abin sha da naci aka ajiye mata. Kallon juna suka yi,suna faɗin." Sha ruwa mana!" Dauka tayi ta bude ta sha. "Idan kika cigaba da takura Mijinki, zaki iya rasa shi fa." Burza da ruwan bakinta tayi, ta kura musu idanun da suka yi jajjur kamar runshi. "Ban gane ba." "Zaki rasa shi, domin kuwa iyayenshi suna tsaye akanshi kamar yadda kike tsaye, kowa da kike gani, yana da abin da yake so ya mallaka, amma talala akewa abin. Sannan yadda kike mishi ba a san Mayu da rashin biyayya, muna iya kama kurwan mutum mu koma muna taya shi sannu sannu. Har ya mutu, sannan mu taya Uwarsa kukan rashinsa. Da ace kina da wayo ba zaki rike Saifullahi kina bashi wahala ba, ai kina rike shi, a gaban uban kowa biyayya ce zata shiga tsakaninku. Har ta kai duniya idanun kowa ya rufe akanki, amma yanzu kina rike shi sai an nime iziniki? Gaskiya kin bawa mayu kunya, koda yake Jessica mayun gargajiya ne, su haka suke kome yana tafiya da zamani da wayewar." Inji ɗaya, gyara zama Gimbi tayi tana kallonsu. Taya suka san abubuwa dayawa akanta? "Kina Mamaki ne? Ai mun san abubuwa dayawa akanki, ki bar mamaki." Inji Jessica, sannan ta cigaba da cewa. "tunda kina son zama da shi, dole ki bar danginshi su bashi damar aure Aure, amma dake jahilci yana cin kanki ke aurenshi zai amfana ba shi ba, kike kokarin lalata shirinki? Ga ki kamar wayayye amma baki da wannan wayewar. Ni nan mijina Senate na a can south Africa, yana da mata uwargidanshi, a boye mukayi auren. Tunda matar shi ba zata tab'a yarda muyi aure ba, ina aurenshi na kwantar da ita tana can tana jinya, kuma ni da shi kullum muka hadu ko na kira shi, ina tausaya mishi. Sanadin haka yasa shi amincewa ya gabatar da ni a idanun duniya. Kin zata kowa bai da dark side ne? Gata nan Mahaifinta shi yasaka a bariki, ta hadu da mutanen arziki karshe yana can a gida a kwance yana jinya, kuma ita ke daukar nauyin shi bayan ta auri wani attajirin mai kudi anan lagos, and wani abu na dark side dinmu, muna haduwa da mutanen manyan da kanana muna niman kudi. Babu abinda bama yi, so ki waye yanzu an daina wannan mallakar ki mallake shi yadda ba zai tab'a ganin laifinki ba, amma ba Mallakar da zaki hana danginshi sanin halin da yake ciki ba. Ai ke abin alfahari ne yasan baki da matsala da danginshi, kin wani tantame dan mutane, ki sake shi idan ya kwanta da wancan yarinyar tana samun ciki mutuwa zata yi, kece da riba. Yana kara auren wata kece a sama, sam hauka ya cika Miki kai." Zaman dirshan tayi tana faɗin. "Yanzu kuna nufin zanyi kudi idan na shiga tafiyarku? Sannan na sake Saifullahi babu wanda zai zarge ni ina wani abu?" "Hanne ci min Uban wannan yarinyar, wawuya. Na farko kin hana shi zama da wata mace, na biyu kin hakura kin zauna da danginsa baki shiga harkokinsu, na uku kina kasuwanci ciki da gefe waye zai damu dake, misali ko Dubai kike shigowa da sunan kina kasuwanci waye zai saka miki idanu? Waye zai damu da cewa kece kika shiga rayuwarshi da matarshi. Kina daura mata ciwo ki rike sana'arki." Sake baki Gimbi tayi tana kallonsu, sannan ta ce musu. "Ni ina tsoron wani abu,. Ba zan iya bawa mutane kaina ba." "Meye baki aikata ba?kin kashe mata biyu da ciki, sannan kin ce ba zaki iya kwana da namiji ko mace ba, kasuwanci ne fa zaki samu kudi zaki hadu da manyan mutane, idan ba zaki iya mu'amala da maza ba, ai ba laifi bane akwai mata da suke ko ina a duniya zasu biya miki bukatarki, kuma account ɗinki zai yi nauyi. Kawayenki zasu zama kamar Almajirai a gabanki sai kin watsa musu wani abu, tsakaninki su kin tab'a musu kyautar ban girma?" Girgiza kai tayi sanan Hanne ta ce mata. "ki basu kyautar ban mamaki,ki bude manyan shaguna ki daurasu a kai kin biya abin da suka miki, amma ke a kare shi mijinki a kare gashi yana da kashin arziki, haduwa dake kin kasa barinshi ya nutsu balle ku ci arzikin da toshe kome na shi yana hannun dan uwanshi, ina gaya miki dole ki cire mishi abin da kika mishi da haka zai kara bunkasa yadda babu me kallon abinda kike aikatawa. Sannan duk wanda yasan sirrinki kashe shi zaki yi babu ruwanki da wani abu." Kiran da Nassif yayi mata ya saka kallon wayar tace musu. "Mijina ya kira ni." Nan ta dauka tana jin muryan Nassif ranta ya b'aci, sai da ta gama haukarta basu ce mata kome ba,har kirana biyu ya shigo ta ce ta bashi sati daya. Dariya Hanne tayi sannan ta ce mata. "kin bashi sati daya, idan iyayenshi suka so a kwanaki uku sai su lalata miki shiri, maza tashi mu tafi wani wurin ki ga abin mamaki domin kwanyarki baya ja." Fita suka yi basu tsaya ba, sai wani gida me kyau, a can apapa. Danna horn suka yi aka bude musu kofar gidan, sannan suna shigar da motarsu. Cikin gidan suka shiga, wata mace ce ba zata wuce sana'ar Gimbi ba, tana zaune a gaban wani mutum sai ladabi take mishi kamar ta kwanta ya bi ta kanta. "Barka da gida Sir!" "Hanne keda Jessica ne, Barkanku da zuwa. Ai gara da kuka zo, Angela ta hanani fita, sai lallabani take kamar kyau, ni kuma ina da Meeting da shugaban kasa." "A'a angela ya haka? Sir tafi a binka." Tashi yayi yana dariya. "Baby da gaske tafiya zaka yi ka barni?" "Sweetie na hakura da tafiya!" "A'a muje ka tafi kawai!" Ta mike tana me raka shi, sanye take da wani hatsabibin riga da wando, kana ganin yadda manyan mazaunanta da gidiga gidgan boons ɗinta suke juyawa,. Ta raka shi har waje ta dawo falon. "Wash Hanne bana son iskanci, taya zaki kora min mijina." "Gimbiya kin ga yadda ake lallaba miji, ba a takura shi musamman ka kama shi ta hanyar asiri ko tsafi...... _KASUWA A KAI MIKI DOLE_ *Nesa tazo kusa, ko kun san Muzafa World collections. Sun zo muku da kayan zamani babu ruwanki da zuwa kasuwa. Yar uwa, kayanmu daya yake tankar da dubu. A rashin tayi akan bar raha, haka kuma bahaushe ya ce a rashin kira karen bebe ya b'ata. Tow ga dama ta same ku, domin kayanku ya tsinke a gindin kaba, kayanmu sun haɗa da Dubai Abayas, yan kunne da abin wuya, takalman Manya da Yara, lace masu kyau da inganci. Hajiya nesa da ake ce miki tazo kusa babu ruwanki da shan rana da kura, kayanki yazo inda kike! HAJIYA Abu me kyau ke sayar da kanshi* *08130269641* [11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥* EXQUISITELY BEAUTIFUL #Mai_Dambu Chapter 18 Kusan itama Angela abin da ta gayawa Gimbi kenan, tow kusan ta yarda hakan, amma fa daga gidan nan wani gida suka wuce, inda aka yi ta gabatar da ita ga wasu manya mata, masu manya mazaunai. Har dare ya raba raba suka dawo da ita a galabaice suka dawo da ita gida, suka ajiye ta a falo, sai da suka gama bin gidan da idanu sannan suka ce mata. "Gaskiya kina bukatar gyara na musamman domin ba zamu iya tafiya da mace irinki ba, ki gyara alaƙarku da shi domin tafiyar tayi mana kyau." Juyawa suka yi suka bar gidan, ★★★ Watsa mata ruwa suka yi, tare da kura mata idanu, suna jiran su ga me zata yi. Tana farkawa ta shiga waige-waige. "Goma tashi ki min rawan sabada." Wani irin ware idanu tayi tare da yin baya tana nuna su da yatsarta. "Goma kin ga wannan Yarinyar duddiya rabonta da tayi dariya tun shekaru tara baya, yau kuwa kin sakata murmushi shi ne nace ko zaki kara sakata dariya baki daya." Ita kuwa duddiya tayi mici-mici da idanunta, kamar zata yi kuka. Kallon gabas da yamma tayi, ta kuma juya ta kalli kudu da Arewa, bata san lokacin da ta takarkare ta fasa ihu ba. Kallonta suka yi suna mamakin me yasa ta fasa ihu haka. "Goma!" Suka kirata da wani katoton murya. Rarrafe ta fara a gabansu tana faɗin. "Ranku shi dade, kune kuke ganin mu bamu ke ganinku ba, wannan sakon daga fadar kurzazzu kurkurazu, uban shadanun zungururru." Kallon karami Duddiya tayi tana faɗin. "Karatu take ko addu'a take ?" "Kinga ni kaina ban san me take fada, Goma yau a dakinki zamu kwana domin ki koya mana karatunki nan" inji karami, "kurzazza ko?" Inji dan tsirit, da ya leko ta silif din dakinta. "Au ashe baka yi nisa ba, tow sauko mu kwashe zabon ilimi!" "Ai matsalar shine ni kwarkwatan da yake kaina nake son a rage min, Goma zoki kifara aikinki." "Me zan maka bawan Allah!" Ta faɗa cikin wani irin bala'in karyewan murya. "Me zan muku?" "Eyyeeee tambaya kike?" "Goya ni zaki yi!" Duddiya ta faɗa tana mika mata hannu. Tuntsirawa Goma tayi, suka kwashe da dariya. "Kato ya zamu yi da ita." "Ai ko mun samu wurin hira, a maida mata kome kamar mafarki tayi." Suka dauki hijabinta suka saka mata, suka gyara inda ya sake fitsari lokacin da ta razana. Sannan suka dawo wurin Nazneen da take tsakar gidan, akan rijiya zaune kallonta suka yi. "Me za a miki?" "Babu kome yawo nake son fita." "A wannan daren?" "Zo nan dan dukunnunu!" Ta kira shi da hannu, bayan Kato ya koma ya boya. "boye ni, domin ba zata min ta wasa ba." "Ai muma bai zama dole tayi mana ta wasa ba." Duk suka shiga guje-guje a tsakar gidan, suna buruntu. A can dakin Tahir, bai yi barci ba yana karatu, domin har ya kwanta ya farka ya fara barci, ya tuna zai yi karatu tunda an tura shi internship asibitin specialize Bauchi. Wurin sha daya na dare yana karatun, har sha biyu yayi. A lokacin ne yaji muryan Yara suna ta wasa, karatu yake amma haka suka raba mishi hankali gida biyu, dole ya mike yana me d'aga labulen dakin, Nazneen ya hango tana bin wasu abubuwan da gudu. "Me yarinyar nan take cikin dare?" A hankali ya sake labulen tunda bai da me bashi amsar, fita yayi zuwa wurinta. "Aisha!" Juyawa tayi tana kallonshi. "Me yasa kika fito waje a wannan lokacin?" "Wasa muka fito yi!" Ta gaya mishi tana cigaba da abinda take, "wuce maza ki kwanta." "Tow ai bana jin barci ne." Ta faɗa tare da hawa saman rijiya. "Ke!!" Yayi maza ya fisgota. A madadin ta fado sai yaji kamar irin ya girgiza katon bishiya durumi ne. Juyawa yayi ta kalle shi, sannan ta kai hannunta saman hannunshi, ta ce mishi."Ka tafi ka kwanta, sai da safe kada ka tuna kome." Babu musu ya wuce dakin ya kwanta, ita kuma ta saka abokanta suka yi ta dibo mata ruwa suna zubawa a wani katon daro, ta shiga cikin ruwan tana faɗin. "Kai Jama'a, ina son ruwa haka nayi ta wanka s cikin shi." "Nazneen ya batun Maman Uchenna?" Bude idanunta tayi da suka kad'a jajjur, ta ce mishi. "Dole yau na bar gidan nan domin ba zan yafe mata ba." "Babu hanyar fita a gidan nan." Shiru tayi kafin ta ce mishi. "Zamu fita,muje ka taso Tahir shi zai bude mana kofar gidan." Gyaran muryan Malam suka ji, a bayansh da gudu suka boya ban da Nazneen da take tsaye a bakin rijiyar. "Aisha!" Juyawa tayi ta gashin kanta da suka tsaye a tsaye, bayanta kuwa hasken farin wata yana haska baƙin duhun da yake tsaye a saman kanta. Dauke idanu Malam yayi yana me niman wuri ya shimfida farar buzunshi ya zauna a kanshi. "Zauna mana!" "Fita zanyi." "Tow jeki mana!" Ya fada bayan ya tadda kabbara, ihu ta fara tana tsalle me mugun shiga cikin kai, bai fasa sallah ba, itama bata fasa ihu ba. Haka ya cigaba da sallah, yana gayawa Allah buƙatarshi, kamar zata mutu haka take ihu,har garin yayi wani irin tsit baka jin kome sai ihunta da buge-bugenta. Lokacin da Malam ya zauna yana addu'a, a lokacin ta fara wani irin karkarawa. "Malam!" Ta fada da wani katuwar murya. "Malam ka daina azabtar damu, ban tab'a cutar da ita ba." Nan ma malam yayi banza da shi, ya cigaba da addu'arshi. "Na rantse ban tab'a cutar da ita ba, kawai abin da na sani ina tsaron zuriar kakaninta ne, wannan shine aikina na tsawon shekaru sama da dari ina kare zuri'arsu." "Tow ka tafi tana cikin ahalinta." Malam ya faɗa da dakakkiyar murya. "Zan yi farin ciki idan mutuwa nayi, akan na bar jikinta. Domin na samu faduwa sau biyu, itace ta uku da nake tsoron faduwa akanta mutuwa zan yi." "Kana son na kashe ka!" Durkusawa tayi a gaban Malam, ta ce. "Zan yi farincikin mutuwa a hannunka, akan na fuskanci al'ummar da suka bani amanar kare zuri'arsu." "Waye kai?" Wani irin kuka yake yana ihu, yana dukar fuskarshi. "Kada ka tambaye ni, waye ni." "An umarce ka ne da idan ka fadi gaskiya mutiwa zaka yi?" "Sanin waye ni, zai saka boyayyen sirrin da yake makale da zuriar ya bayyana har duniya ta san su waye su. Ita kanta ko nufarta aka yi da sharri zai koma kan mutum. Nayi alkawarin ba zan kuma bayyana na cutar da ita ba, amma ba zan bari wani abu ya cutar da ita ba. Har na tsawon karshen rayuwata." "Kenan ba zaka fita?" Malam ya faɗa yana me tofa addu'a a jikin katuwar calbinshi. "Malam abin da na sani, zuri'arsu suna daga cikin manyan mutane a kasar Tanzania da Afirka ta kudu, zuwa kasar Malawi har ya dangana da Ethiopia, ita din jininsu dauke yake da kunshin arziki da daukaka, Mahaifinta zai zama abin mamaki. Gaba za a tsayar da shi matsayin shugaban kasa. Mijin da ya aureta duniya zata so nimanshi domin jinin da suka hada, bayan haka Malam Malami, ba zan gaya maka kome ba." Daga haka ta zube a wurin, tashi Malam yayi ya gyara mata kwanciyarta, sannan ya saka farin alkyabbarshi ya lullubeta, ya cigaba da ibadar har asuba ta gabato. –★– Abuja. Kamar wani mara gaskiya, haka Saif ya kasance a cikin gidan, koda dare yayi Nassif ya raka shi ɓangarenshi, inda amarya ta sha kwalliya da wanka, da zasu shiga Nassif ya mika mishi ƙatuwar leda, ya ce mishi. "Saura ka je ka nuna mata, cewa kai mace tafi ƙarfinka, ya kamata ka fara new life, new beginning. Don Allah kada ka lalata wannan daren, domin yana da muhimmanci a gare ka." Gyada kai yayi, domin Saif ya koma kamar wani karamin Yaro, duk abin da aka ce shi yake yi. Har Aunty Shamsiyah ta bar gidan, Ummi kuka take dama Aunty Mariyah zuwa tayi, baki daya ta tausayawa Ummi. Haka suka yi ta rarrashinta suna nuna mata kome zai wuce babu abinda ya tab'a tabbata, kome yana tare da lokaci ne. A can bangaren Saif kuwa, kusan Umarnin Nassif yake bi, a falon shi ya same ta, d Alamun an maida wurin bangarenta ne, don haka ya ajiye ya zuba mata idanu. "Kici ki dauro alola, sai ki same ni a dakina." Ya fada tare da barin fakone. Tsayawa tayi tana kallon kayan, kafin ta dauka ta wuce dakinta, sai da ta ga akwai nama da madara, ta kai kitchen ta adana su, sannan ta wuce dakinta ta kuma gyara jikinta, sannan tayi alola ta nufi dakinshi. Kusan ba zata ce bata san wahalar daren ba, amma kuma zata ce gangar jikinsa ne a tare da su, amma ruhinshi yana tare da matarshi, domin kowani yanayi bai gaza furta sunanta da karfi ba, haka ya fahimtar da ita cewa kawai ta kawo kanta cikin wata duniya ce na iya ita kaɗai zata rayu babu soyayyar namiji. Babu laifi, shi kanshi yasan tana da kamunkai, domin ya samu nutsuwa da ita fiyye da yadda ya zata, sannan ya tashi yayi wanka, tare da ce mata ta tafi dakinta. Haka ta mike ta nufi dakinta, a can tayi kuka kamar ranta zai fita, dan tararayen da akewa mata a daren farko, bata samu ba babu wani tausayi ko kulawa daga gare shi ba. Washi gari, da sassafe ya bar gidan bai zame ko ina ba, sai Minna domin akwai wani makarantar da suke son budewa, wanda a iya Minna zasu fa. Sun so a bude a garin Abuja, amma ina tsadar fili yafi karfinsu. Idan ta nashi ra'ayin ne da ya bude a Bauchi, amma ganin akwai masu bukatar ya bude a nan Minna yasa shi saka hannu. Kusan tunda ya bar gidan yake jin kamar an sauke mishi wani katon dutsen da yake kanshi. Haka yasa shi niman Gimbiya a waya, bata dauka ba. Har rana yana nimanta,. Kafin ya samu ta dauka. Wani irin ajiyar zuciya ya sauke yana faɗin. "Princess kiyi hakuri, ina ta kiranki baki dauka ba." "Ok me kake so?" "Kawai ina son naji muryanki ne." Ya fada kamar ya fashe da kuka. "Ok yanzu kaji?" Ta faɗa a dakile, "Eh na ji!" "Ka kwanta da yarinyar nan ne?" Wani abu ta hadiye, cike da kunya ya ce mata. "Kiyi hakuri, Nassif ya sani dole na kulata." "Kace kaji dadinka, ka samu sabon wuri kayi yadda kake so?" "No princess, ke daya nakewa rawan jiki!" "Karya kake Saifullahi karya kake Saifullahi katagum, wallahi kai munafiki ne, Azzalumi ka samu sabuwar budurwa shine kake kirana domin ka gaya min yadda ka kwana da ita?" "A'a Baby!" "Dalla ka min shi, azzalumi macuci, shi yasa da aka ce min kada na auri bahaushe naki, amma shi ne daga zuwa har ka kwanta da ita, yarinya karama kaci Saifullahi ko kunya baka ji ba? Baka ji kunyar kwanciya da yar yarinyar da bata wuce 21 ba a duniya?" Wato bai san lokacin da yaji wani abu ya tsarga mishi ba, ya ce mata. "Kiyi hakuri, nima na tsani kaina nayi abin kunya, don Allah ki rufa min asiri, kada wani yaji abin da na kaita." Yadda Gimbi tayi amfanin da kananun shekarun tana nuna mishi illar kwanciya da Khalwat sai ka zata zina yayi shi kanshi yana hango kuskuren shi a kwanciyar da yayi da ita kamar yayi wani zunubi, a shakarun shi abin kunya ce, balle ita gimbiya da take niman shakaru talatin da uku a duniya." Shi kan yana ganin kamar,abin kunya yayi baki daya rayuwanshi. Duk haka yaki komawa gida, hotel ya zauna yana kallon kanshi a madubi, shi ɗan kimanin shekaru arba'in da daya a duniya, kallon kanshi yake kamar ya aikata abin da za a kai shi gaban jama'a a bayyanawa duniya yana mugun abu, kasa kallon kanshi yake yana kara jin tsanar Khalwat, domin aurenta yasa shi mutuncinshi ya zube a idanun gimbiya (🙄🤣😂) _NAAZNEEN, GENERAL NASIR ZAKI, BINTUN BATUL TOP-NOTCH TEAMS NA KUDI NE! BAKI DAYA UKUN 1300 NE_ BIYU=₦900 DAYA=₦500 CHAT ME IDAN KUNA BUKATA: 08130269641 [11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥* EXQUISITELY BEAUTIFUL #Mai_Dambu Chapter 19 Wasa-wasa Saifullahi ya makale a hotel, yaƙi dawowa gida. Hankalin Ummi ya tashi, duk ta d'aga hankalin mutane. An kira wayarshi fir yaki d'auka. Wannan abin ya fusata Mahaifin shi Alhaji Mansur Katagum, da ya cewa Ummi. "Ce miki aka yi ya damu da damuwarki ne? Tow damuwar kansa bai damu da ita ba balle ta wasu. Don haka ko mutuwa zaki yi sai ya ga dama yayi kuka. " Ya faɗa yana haurawa sama, ran Nassif yayi mugun b'aci, don haka ya bar falon, harabar gidan ya nufa, kiran Gimbi yayi. "Me yasa ka kira ni?" "Idan kin san Saifullahi-Khalid yana tare dake maza ki saka ya dawo gida, idan kuwa kika sake raina ya b'aci wallahi, zan saka yan iska su kona min Iyayenki, ai iyaye basu fi iyaye ba, nan da awa biyu Saif ya dawo, idan ba haka ba na kona iyayenki na kona banza babu wanda ya isa ya ce min don me nayi haka. Kin fahimci abin da nake nufi!" Kashe wayar yayi yana Safa da marwa a cikin gidan. Yana yi yana kallon agogon wayarshi. ------ A hotel kuwa, Saif yana kwance kiran Gimbi ya shigo mishi, dauka yayi yana faɗin. "Baby kiyi hakuri, gobe zan dawo." "Kana ina?" Ta tambaye shi. "Ina hotel ne?" "Kai da wa?" Ta kuma wurga mishi tambayar, "Ni ɗaya!" "Ka koma gida, domin brother dinka ya kira ni yana min barazana da rayuwar Iyayena, Saif ka rufa min asiri, kada

Chapter 10 of 12