Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
"Mtsew! Kada ka min magana, kuma wallahi ba zan kuma hawa motar nan ba." Shiru Saifullahi-Khalid yayi domin yasan matuƙar ya biye mishi, abin kunya zasu yi. A zafaffe ya juya yana kallonta. "Kin ja baki kinyi shiru a ina za a ajiye ki?" Kamar tayi kuka, domin Nassef akwai daukar dumi. "Hey ka mata a hankali, mace ce fa sai ka razana ta ai tayi kuka?" "Zan zage ka, mara mutunci uban me na mata? Ta jima bata yi kuka ba!" Ai kuwa kamar jira take ya kai aya ta fashe da shashekar kuka, "Ya isa haka! Meye sunan unguwarku?" "Kasan Allah ba zan bika ba, ajiye ni idan kaso ku je duk inda yayi muku." Haka kuwa yaje y ajiye shi, a gidansu Saifullahi-Khalid din da yake Sir kashim g.r.a dake bikin class mate dinsu ne, yasa suka tawo tare. Sannan ya ciro hanky ya mika mata, ta amsa. Saifullahi-Khalid yana da matukar tausayi da kirki sosai. Mutum ne sa yasan darajar mutane, duk da Naseef ma haka, amma akwai abubuwan da ya banbantasu... "Sunan unguwarku?" "Idan ka isa winti ka ajiye ni, domin muna da nisa!" Ta faɗa tana shashekar kuka. "Ok!" Ya fada yana cigaba da da tuki, a tunaninta zai ce a'a ya kaita gida ne, sai taji akasin haka. Haushi ya kamata kamar ta ce ya wuce da ita gida, amma ganin dare yana yi, yasa ta hakura ta kuma san bai zama dole su kuma haduwa ba.... [11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥* EXQUISITELY BEAUTIFUL #Mai_Dambu 'Top-Notch Season 3 بسم الله الرحمن الرحيم Chapter 6 Love@firstsign Ba karamin mamaki ta sha ba, lokacin da ya ajiye ta a winti, ya juya yayi tafiyarshi. Tow kuma me take so ya mata? Wani bangare na zuciyarta ya tambaye ta, shiru tayi tana nazarin abin kafin ta tari abin hawa ta nufi gida, tunda ta isa ta kasa rintsawa, idan ana neman love at first sight shine ya faru tsakaninta da Saifullahi-Khalid. Al'amarin da ya gigita Gimbi ai ba karami ba ne, don haka koda gari ya waye bata leka ko waje ba, asalima wani irin zazzaɓi ne ya rufeta. Washe gari Linah da Siyamah suka zo mata, ganinta suku-suku yasa suka matsa mata da tambaya. "Baby lafiya?" "Ku bari kawai, tun ranar da naga gayen nan na rasa meke min dad'i, domin kuwa kamar na zauce nake ji a raina." Sakin baki sukayi suna kallonta, kafin su ce mata. "Ina honorable ɗinki?" "Bana son bura uba, ni ba shi nake nufi ba. Ina gayen da ya bude taro da addu'a a wurin bikin nan?" "Eyeeeee!" Suka fada bayan sun ware idanu akanta, "Kinsan me kike faɗa kuwa? Saifullahi-Khalid?" Hadiye yawu Siyamah tayi tana faɗin. "Hala hauka kika fara? Gayen da bai kula mata shi ne kike tunanin zai so ki?" "Haba Siyamah, Gimbiya kawarmu ne wannan karon ta ga abu tana so me zai saka ba zamu taya ta nemanshi ba, Gimbi matukar kina sonshi zan taya ki." Kamar tayi kuka haka take kallon Linah ta ce mata. "Wallahi ban tab'a jin haka ba, sai wannan karon." "Na sani, amma ku sani Linah akwai hatsari. Saifullahi-Khalid ba gama garin mutane ba ne. Yana da addini sosai, sannan yasan abin da yake wallahi ba zai tab'a yarda yaso Gimbi ba." "Zai so mana, yanzu abin da zamu yi dole daga yau mu fara niman sanin waye shi. Kafin mu cimma shi." Dake Linah tana da mugun shige-shige, babu abinda yake razanata. Haka suka shiga fafutukar sanin waye Saifullahi-Khalid. Sosai suka binciko waye shi, sannan suka shiga tufka da warwara. Kafin kuma suka shiga bin Malamai. Duk inda suka je babu wanda yake iya nimo musu koda kurwanshi balle kuma a san waye shi. Karshe dai sai da suka tafi har kaltungo, suka dira wurin Ba Allah, yana ganinta ya kwashe da dariya,kafin ta bashi labarin kome ya bata labarin abin da bata sani ba , sannan ya ce mata. "Aikinki kala uku ne,na farkon kayanshi na sawa, rigar shi da wandonshi sai takalmi da hula, na biyu zaki bashi abu yaci domin ta haka ne za a same shi. Na uku za a mishi kiranye, domin ana gab da hada shi aure da yar Kawunshi gata nan!" Kallon hoton tayi yarinyar ta hadu ta gaji da haduwa. Tana kwance a kasa ta ce mishi. "Ba Allah, taya zan samo kayanshi?" Murmushin mugunta yayi kafin ya farawa kanshi kirari. "Sai ni na deluwa baban Korau, uban dan tsugudidi baban ifiritai, Mijin aljana angon shaidaniya. Na ci dubu sai ceto. Ni ne nan ba Allah!" Kwanciya tayi sannan ya ce mata, "zan duba miki cikin gidanshi domin yana rayuwa ne daga shi sai masu mishi hidima, zan tura yan aikina domin su duba mana waye me son zuciya a cikin mutanenshi." Suna zaune kuwa aka nuno gidan Saifullahi-Khalid a madubin gabansu, babu wanda aka nuna yana da son zuciya sai da aka kusan daina nuno gidan, sai ga me mishi girki, yana leke leke, sannan ya ficce da wasu kaya a hannunshi. Murmushin mugunta Ba Allah yayi sannan ya ce musu. "An gama, yanzu na baki nan da kwana ashirin ki tafi har can, ki nimo kayanshi sannan ki bawa mutumin wannan abin ya saka mishi a cikin abincin shi. Wannan kuma ki tabbatar ya binne a cikin gidan, wannan kuma ki nimo inda kika san ana girki ba dare ba rana, ki saka. Wannan kuma ki nikashi ki zuba a cikin mazubi, kina sakawa a idanunki. Amma sai ranar da zai zo. Wannan kuma ki zuba aman shafawarki, kina shafa shi. Wannan duk ranar da zaku haɗu, ki turara jikinki da shi." Gyada kai take, don ma Allah ya taimaka duk abin da ake bata, Linah tana rubuta mata, suna gamawa ya ce musu. "Da me zamu biya sadaka?" "Bakin karfe da jan kare, bakar akuya da jar akuya, da yar kasa gajeruwa. A kai duk inda aka san ruwa yana taruwa. Da carton din giya, jar dawa da farar dawa. Jariri wanda aka haifa yau sabo fil!" "Jariri?" Suka tambaye shi, a razane jikinsu yana rawa. Murmushi yayi ya ce musu. "Jimawa kaɗan zaku haɗu da shi, don haka a hada min da shi, aikinki yana bukatar jinin Dan Adam. " Wani irin tsoro ne ya kama ta ce mishi. "Ina tsoron kada a kama ni?" "Hhhhhhh! Babu mahalukin da ya isa kama ki, sai na ga baya shi, maza b'ace min da gani!" Daga haka suka mike zasu fita ya ce mata. "Nan da sati Uku, ki tabbatar aikin ya kammala ki sha mamaki." Haka suka fito daga dutsen jikinsu a mace, suna jin kamar ba cikakken mutane ba, a cikin sati daya da ya wuce Gimbi ta shirga karya, bayan ta nimo address din gidan Saifullahi-Khalid, har da inda yake aiki. Kukunshi me suna Wasim, dan kabilar igla ne, sai dai mutum ne mai shegen son kai da son zuciya, bai da kirki sannan shi kanshi Saifullahi-Khalid yasan cewa yana mishi barna, amma hakuri da taushin zuciya yasa yake tare da Wasim, amma da ya bi na zuciyar Nassef tsaf da ya kore shi, Wannan yasa shi kuma Wasim yake ganin kamar ai Saifullahi-Khalid bai san kome da yake yi ba, kasancewar ba unguwar yake ba, zuwa yake da sassafe da wannan damar Gimbi taci gallabar bashi kudi me yawan gaske ya kawo mata kayan me gidanshi, sannan ta bashi wanda zai na saka miishi a cikin abincinshi. Wannan lamarin ba karamin dadi ya mata ba, domin kuwa yadda taso haka ta yi. A cikin kwanaki goma sha takwas. Suka dawo Bauchi da kawayenta, ranar da suka cika kwana biyu da dawowa, aka tsinci jariri a makarantarsu, dama abun da suke fata kenan, Siyamah ta shiga makarantar taji ana an samu Jaririn, kafin ace wani abu ta tafi ta sace jaririn a asibitin makarantar, sannan ta kawowa Gimbi. A can makarantar aka nime Jariri sama da kasa, ganin dama suma gidan Marayu za a kai shi, yasa babu wanda ya wani damu. A bangaren Gimbi da Siyamah da Linah, kuwa duk abinda aka bukata sai da suka saya. Sannan suka ajiye bakin ruwan dumduma.. sannan suka wuce kaltungo , suka kai kayan kome, kallon jaririn Ba Allah yayi ya tashi ya amshe shi sannan ya saka Gimbi ta durkusa, aka fara buga tsafi me sunan tsafi, da kayan Saifullahi-Khalid. Da wannan jaririn haka yayi ta aikin, musamman aka yanka Yaron babu tsoron Allah ko imani, haka suka yanke shi, aka binne shi da kayan Saifullahi-Khalid, sannan aka dawo jinin jaririn Ba Allah ya mata wanka da shi, ya kuma dauko wasu irin tattabaru guda biyu aure ya yankesu, aka ɗauki hular Saifullahi-Khalid aka saka su a cikinshi, sannan aka dauko budurwar kare da saurayin kare, aka yanke su jininsu aka zuba aka cikin hular, aka haka rami aka binnesu. Kafin ya kalleta. "Ban tab'a aiki me haske irin naki ba, don haka tashi maza ki je, nasara tana gaba kada ki sake ya zo ki bashi fuska kai tsaye, ki bashi wahala da zai gane ke ba kanwar lasa ba ce." Gyada kai tayi tana faɗin, "Godiya nake ba Allah" daga haka suka bar kokon dutsen, ajiyar zuciya ta sauke tana faɗin. "An gama kome" "Ya zaki yi da honorable?!" Tsaki tayi tana faɗin, "ke kyale dan wahala, ba abin da zan iya mishi." Suka kwashe da dariya, sai dare suka iso Bauchi, suka.ajiye ta a gud'un sannan kowa ya kama gabanshi. *** Azare. Unguwar Zaweeya. Unguwa ce me dinbin tarihi a garin Azare, unguwar manyan hafizan Alqur'an, uwa uba kuma manyan malaman mazahabar darika, Unguwar da ta kasance kamar quarts kasancewar kafin boko ya shiga cikin su, manyansu da Yaransu anan suke zama kuma anan suke auratayyarsu. Gidan Sheikh Saifullahi Goni, marigayi domin ya rasu shekaru takwas. Ya bar mata uku, Hajiya Mariyah wacce suke kiranta Hajja Mari. Sai Hajja Maliyyah, suna kiranta Mama Hajja, sai Hajja Kubrah wa. Gidan Sheikh Saifullahi Goni yana da yara goma sha huɗu ne, kofar Hajja Marih tana da Yara biyar. Alhaji Mansur Saifullahi katagum Hajiya Adamah Saifullahi katagum, sannan Gwana ta shekarar talatin da suka wuce domin ta shiga musabbaka ta karamar hukumar katagum, sannan tayi na jahar Bauchi, sannan tayi na kasa baki ɗaya. Hakan yasa aka mata lakabi da Gwana tana da yara biyar, dukka mata kuma abin burgewa mahaddatar Alqur'ani ne. Alhaji Abideen Saifullahi katagum, shugaban kamfanin wutar lantarki na shiryar arewa maso gabas, yana garin Jos da zama. Shi wannan asalin dan boko ne Yaranshi uku , Hajiya Na'imatullah Saifullahi katagum, itama gwana ce, Yaranta hudu maza. Alhaji Yahuza Saifullahi katagum, shima nan alaramma ne,.mai jan baki a duk watan azumi, ga Sheikh Abubakar Goni. Shine karaminsu, yana da Yara kusan goma sha. Domin matan shi uku ne rurus, kuma haihuwa suke kamar me? Hajiya Maliyyah, Yaranta biyu ne rak kuma duk mata, suna nan cikin zaweeya da yaransu, Hajiya Ummulkhairi, yaranta takwas itama gwana ce, shida maza manyan kenan biyu mata. Hajiya Sadiya itama gwana ce, har tana koyarwa a high Islamic dake nan azare. Dakin Hajiya Kubrah, Mama Hajja. Mace me kirki da barkwace da son kowa nata ne, mace me ilimin addini, duk abinda zata fada sai ta saka Allah kafin ta kawo Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama, macen da duk inda ta shiga sai ka fahimci ana yiwa Muslunci da muslamai hidima, mataimakiyar shugaban Fomwan, uwa uba sakatariyar Da'awa ta yankin arewacin Nigeriya kungiyar nasarul Islam. Mama Hajja akwai ilimin addinin kamar me, tana da Yara bakwai. Hudu maza uku mata. Dr Khabir Saifullahi katagum yana garin Bauchi da iyalinsa suna aiki a asibitin Ni'ima, Matar shi daya da Yara uku. Alhaji Awwal Saifullahi katagum shi kan Custum ne yana garin katsina a iyakar bodar Nijeriya da nijar. Matar shi bata jima da rasuwa ba, don bata samu haihuwa ba, sai daga baya, kuma tana haihuwa ta rasu, ta bar mishi Y'a mace Rukayya Saifullahi katagum Nurse ce, ita kan Allah bai bata haihuwa ba, har yau. Sai dai sun san lokaci ne. Mubarak Saifullahi katagum, gwani ne yana garin Lebanon da matar shi inda yake aiki yarshi daya. Zakiya bata jima da aure ba, don tana da tsohon ciki ma. Itama gwana ce amma tana karatu a nan Bauchi, a Atbu. Fatihatulkhair wacce aka yi bikinsu tare da Zakiyah don kusan babu tazarar shekara a tsakanin juna. Jalaludeen dan auta baki daya a cikin gidan, domin ya rasu Jalaludeen bai wuce shekaru goma a duniya ba. A wannan shekarar da aka yi musabbaka Jalaludeen shi ya lashe gasar a garin Qatar. Gidan Sheikh Saifullahi katagum idan aka ce babu tarbiyya tow an ci amanar Malam, domin baki daya yan gidan Malam ya daura su akan tafarkin Allah, kuma ya koya musu soyayyar Manzon Allah. Kuma suna kan daura yan bayansu akan soyayyar Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama, Duk cikin gidan ba zaka tab'a banbance Yaran Mama Hajja da Yaran Hajja Maliyyah ba, domin kowannensu ya rungume Yaran gidan, Hajja Mari tana matukar kunyar Yaran Ambassador Mansur Saifullahi katagum, daga kan Mariya Shamsiyah da Saifullahi-Khalid, tana matukar kunyarsu, ita kuma Mama hajja saita Rungume su, ita kuma Hajja Kubrah ta rungume Yaran Mama Hajja, ita kuma Hajja Marih ta rike na Hajja Marih ta rungume Yaran hajja Kubrah, saboda tsananin zumunci da hade kai, kome iyayen suke so ba tare da gulma ko tsegumi ba, zasu tattauna abinsu. Iyayen sun rike junansu, Babu batun kishi ko tashin hankali, ba kyashi ko hassadar Yarana suke kaza, matan gidan sun fi mazan Yawa. Mazan gidan Allah ya albarkaci rayuwarsu ba kadan ba. ----------- Sukuku Mama Hajja ta tashi, hannunta rike da casbi. Tunda tayi sallah waalaha. Ta kishingida. D'aga labulen dakin Hajja Mari tayi cikin zolaya ta ce mata. "Mata a gidan Malam Alhaji, me ake roka mishi ne?" Tashi tayi a kishingida ta sake murmushi ta ce mata. "Hajja Marih kenan, Bana jin dadi ne, amma in sha Allah gobe juma'a zan saka a daka min fura, yau zan tura a kira min Yalwaji...... [11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥 * EXQUISITELY BEAUTIFUL #Mai_Dambu 'Top-Notch Season 3 بسم الله الرحمن الرحيم Murmushi Hajja Marih tayi, tana faɗin. "Ba dai kiranye zaki yiwa mijin da baya cefane ba?" Murmushi tayi ta bude baki zata yi magana Jalaludeen ya shigo a kidime. "Baku ji rasuwar Sheikh Ibrahim Goni ba?" "Innalillahi wa inna illahirirajuun Ubangiji ya amshi bakonshi sa." Inji Hajja Marih, "Ai bashi daya ba ne, harda Hajiya Nana!" "Ikon Allah, hatsari suka yi ko?" "Eh." Ya karasa bakin famfo yayi alola. "Ina zaka yanzu?" "Zamu jana'izarsu ne." Baki daya mutuwar da aka yi, ya mantar da Mama Hajja abin da zata yi, asalima kamar an shafe tunanin kome a ranta,amma a yanayin da take ciki tana bukatar nazari ne babba. ★ Friday. Gimbi Kusan sati biyu babu labarin Saifullahi-Khalid, kamar tayi hauka haka take ji, ta kira Siyamah da Linah yafi sau dubu, abu daya suke tabbatar mata tayi hakuri indai aikin ba Allah ne, sai ta sha mamaki. Amma ina kullum wayewar garin duniya zuciyarta kara nesantatta yake da Saifullahi-Khalid, ga honorable ya tasota a gaba da zancen zai turo maganar aure. Amma haka tayi biris da shi, ta masifar ramewa ta fita hayacinta. Ranar wata talata ta shiga kasuwar wunti domin sayan gashin kitso, da za a mata kari. Har cikin laushi ta shiga, tana shagon tana sayan wig da sauran kayan kwalliya, aka damfa kafadarta, juyawa da zata yi suka yi ido biyu da wata kawarta tun na secondry. Me suna Amina Nuhu Giyad'e, "Gimbi Yusuf Bogoro!" Wani harara suka sakarwa juna, kafin suka saka dariya, ta ce mata. "Shegiya kin yi aure ne?" Gimbi ta tambaye ta, wani fari tayi da idanunta, sannan ta ce mata. "Da saura nazo zan wuce ne, na ji muryar kamar na san Mai ita. Shegiyar ashe kece." "Allah sarki, ya su Sadiya Badar?" Tayi tambayar kamar me jin tsoro. "Bikinta nazo zata auri wani dan misau, amma abuja yake aiki can zamu kaita kin ga abinda ya kawo ni " "Ikon Allah, Ayya da na sani da wuri da na shirya zuwa bikin." "Why not? Idan har kina son zuwa sai muje ki zabi ashoben." "Ke bani da kudi " "Banza waye ya gaya miki, sai da kudi zaki zo bikin Sadiya Badar!" "Allah ko?" "Wallahi muje ki dauki kayan." Amina Nuhu Giyad'e, Gimbi ta cire ta a jikinta, amma irin kawayen nan ne masu yiwa kawaye hidima, matsalar Amina da Gimbi, ita Amina irin matan nan ne waɗanda basu da fasalin halittar fuska nan ne, domin idan ka ganta zaka dauka ba mace ba ce, sai tayi magana. Amma yanzu da take gaban Gimbi ba wancan bakar mummunar da suka sani ba ce, domin wannan tayi karatun aikin jinya (nurse) ce, kuma tayi bleaching ta koma fara kwal. Dake tana son Gimbi babu abin da ya dame ta, kashe mata kudi tayi kuma ko da suke makaranta kusan, ita ke kashe musu kuɗi. Daga nan wani shagon ɗinki suka kai kayan, sannan suka fito kasuwa sai a lokacin idanun Gimbi ya sauka kan motar Amina Nuhu Giyad'e, "ke ni kinyi aure?" Wani fari tayi da idanu, sannan ta ce mata. "Da saura, wani dan wahala ne da yake son aurena ya ba ni kyautar shi ranar birthday na!" "Gaskiya ya kyauta." Gimbi ta shiga, tana yaba motar cikin jin dadi, suna tafe suna hira anan take tambayarta ko tayi aure ta fito ne, Gimbi ta girgiza kai tana faɗin. "har yanzu dai ba a dace!" "In sha Allah za a dace, kiyi hakuri lokacin ne da saura." Haka suka yi ta hira zuwa kasuwar mata, da yake railway. Gimbi ta ce mata. "sauke ni anan, zan amshi sakon Mama!" "Ayya don Allah ki gaishe ta," da zata fita Amina ta cire dubu biyar ta bata, tayi ta godiya har suka rabu, baki daya kan Gimbi sai wani irin tashin hankalin take ji, domin kuwa shi nave though da yarinyar da suke bawa wahala, a junior class ita ta koma haka, Amina ta sha wuya a hannunta, domin gani take ai alfarma tayi mata da take barinta shiga cikin su, daga karshe aka maida Amina FGGC Bauchi, ajiyar zuciya ta sauke bayan ta amshi sakon Mamanta, ta wuce gida. A madadin Saifullahi-Khalid ya zauce, sai gashi Gimbi ita ce tayi tattaki har kaltungo. A lokacin Ba Allah ya sha mamaki da aikin shi bai tasirantu ga Saifullahi-Khalid ba, ya kurawa hoton idanu, kafin ya ce mata. "Kada haka yasa kiyi tunanin kamar aikinki bai ci ba, ya ci amma akwai wani abu da ake bukata. " Zane zane yayi ta yi, kafin ya juya gare ta yana faɗin. "Dole sai kin hadu da shi." "Ba Allah, haduwa taya kenan? Yana Lagos ina Bauchi. Bai zama dole mu hadu ba." Shiru yayi kafin ya ce mata. "Ki je zaku haɗu!" Haka ta bar ramin bokan jikinta a mace, har suka dawo gida, tana takaicin wannan lamarin, sai da aka yi kwana biyar da dawowarta Amina Giyad'e ta kirata suka fara shige da ficcen biki, a hankali tayi ta haduwa da maza amma baki daya, zuciyarta tafi kwadaita mata Saifullahi-Khalid. *** Abuja. Unguwa Maitama. Shigowa dakin Nassef yayi tare da d'aga labulen dakin. Ya juyawa window baya yana rike da counter. Idanunshi a lumshe. Zama Nassef yayi a bakin gadon, yana me tattara dukkanin nutsuwarsa ya ce masa. "Har yau baka gaya min me ke damunka ba?" Ajiye counter din yayi ya kalli Naseef. "Ba kome, kawai ina son zaman kadaici ne." "Ba dole ka zauna kadaici ba, yo ko ni da nake kaunar mata masu manyan mazaunai. Nakan zauna na wani lokaci balle kai da baka saba kallon mace kai tsaye ba." Kurawa Nassef idanu yayi, wallahi ba don suna da dangantaka ta jini ba, ba zai tab'a yarda wannan Nassef din da yake gabanshi baya bin mata. "Da wannan b'arin zancen me zai hana kayi aure?" Murmushi yayi yana faɗin. "Ina son koda zan yi aure na auri yar shekaru goma sha shida, wacce tana tafiya nonuwar nan suna ragajau ragajau." Yayi wani irin rawa da hannunshi yana girgiza hannun. "Wai kace alamarinka ya kazamta haka? Tow Allah ya takaita maka." Gyara zama yayi sannan ya ce masa. "Wato na samu mace, wacce ko tafiya take mazaunan nan kamar ana girgiza musu ruwa." Rike wandonshi yayi yana muzurai. "Ke kwanta, lissafin yadda zamu sha lilo nake mana." "Innalillahi, Ya Subhanalillahi, fita min a daki kafin ayi girgizar ƙasa." Saifullahi-Khalid ya tashi daga gadon, yana me fadawa ban daki yana dariya. "Na gaya maka, idan aure kake so kayi magana amma ka tsaya wasa da damarka." Kallon fuskarshi yayi a madubin banɗaki, yana shafa fuskarshi da ta b'aci da kasumba. Baki daya ya rasa me ke mishi dadi, yana son tuna wani abu me muhimmanci da yake nima, amma ya rasa. A yan kwanakin nan aure yaƙe son yi, amma ya rasa matar da yake bukata. Domin wani lokaci ji yake kamar ana tursasawa zuciyar ga son wani abu na daban. Sai da ya gyara fuskarshi, sannan ya yayi wanka, ya fito. Shiryawa yayi cikin riga da wando, senator suits. Yar tafiya yayi ya iso compound na gidan, domin part dinshi yana da dan nisa da na iyayenshi. Dan tafiya yayi kaɗan, ya ji baki daya ya gaji. Dakyar ya isa part din ya nime wuri ya zauna a entry na gidan, yana jin wani irin bala'in ciwon kai. A hankali yake ambaton Allah tare da dafe kirjinshi idanunshi a rufe. "Habibi!" Yaji an kira shi, a hankali ya juya yana kallon matar. "Na'am!" Ya amsa mata, bata bashi damar wani magana ba, ta cilla mishi tambayar da ta fito bakinta. "ayn kunt mundh alsabahi?"(ina ka shiga ne tun safe?) A matukar gajiye ya ce mata. "umat 'ana la 'asheur bialraahati. dafaeani 'iidkhal nassif" (Ummina bana jin dadi ne, sai da Nassif yazo ya tashe ni) "Ya Allah , marhaban laqad adhiataka? marhaban 'aw nadhhab 'iilaa almustashfaa؟" (Ya Allah, sannu ina ke maka ciwo? sannu ko zamu je asibiti ne? ) Girgiza mata kai yayi, kafin ya mike dakyar zufa na karyo mishi ya nufi cikin gidan, a falon ya zube yana sauke ajiyar zuciya. "Me ke damunka?" "Ummina zazzaɓi ne fa" "Zazzaɓi? Wannan ai ba karamin ciwo ba ne, bari na kira Family doctor!" "Basmah;" ta kwala mata kira, yasan halin Umminsu kafin ya dakatar da ita, ta tara mishi mutanen gidan, har da yan aikin gidan sai da suka taru a falon, Abbiey da yake wurin aiki, an kira shi ya kai sau goma. Aunty Mariya da Shamsiyah kuwa, sun kira sau kusan uku uku, karewa ita Aunty Shamsiyah da suke Abujan kasa hakuri tayi ta tawo gida a guje ta yo gidan, Nassif yake kokarin barin abuja zai koma lagos shima kiran shi goggonsa tayi tana gaya mishi ga Saifullahi-Khalid bai da lafiya. Yadda take ruruta al'amarin zaka dauka, kana zuwa gidan zaka same shi yana nishi ne ko baya ganin wanda yake kanshi. Dukkansu haka suka taru a falon, ta fito daga kitchen, hannunta dauke da bowl na porridge din dankalin turawa, wanda yayi mashing dinsa, yayi laushi. "Ku matsa ku bani wuri. Kun wani zuba mishi idanu, sannan Habibi." Langwabe kai yayi, Nassef ya kalle

Chapter 4 of 12