Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
wani abu ya samu Iyayena don Allah." Ta faɗa tana me fashe mishi da kuka, "inji Nassif ɗin yace zai yiwa iyayenki wani abu?" Ya tambaye ta, yana miƙawa tsaye. "Wallahi ya ce sai ya kona min su, Saif na gaji kai ma janyo min magana kake, idan ka je ka zauna da danginka zan koma wurin iyayena" "Gimbiya saurare ni, don Allah kada ki min haka. Zan koma tunda laifina ne, ba zan kuma yin abin da za a miki magana ba, zan zauna sai kin yarda na dawo." "Ko kai fa, sai an jima!" Haka ya shirya ya bar hotel, ya nufi unguwar su. A compound din gidansu ya hango Nassif, kallonshi Nassif yayi, cike da takaici. Yana nufar shi ya dunkule hannu ya sakar mishi naushi a gefen fuskarshi. "Ni ka nausa?" "Ka godewa Allah, da ba fille maka wuya nayi ba, banza dan iska." "Zagina kake?" Sai ya tambaye shi a fusace, "an zage ka, kana da abin da zaka yi ne? Wallahi ka sake wani abu ya sami Gwaggona, sai na batar da shegiyar matarka idan kana ganin karya ne, shege kafasa." Daga haka ya shiga motar ya bar gidan, shi kuwa jikinshi a mace, ya shiga falon gidan babu kowa. Har dakin Ummi ya isa ya same ta, daga ita sai Aunty Mariya da Basmah, auta baya dakin, tana zaune a tsakiyar gadon ta dafe kanta da hannu bibbiyu, "Ummi ga Akhi din ya zo sai ki daina kuka." "Meye amfanin zuwan shi, bayan ba zai amfane ni da kome ba? Saifullahi-Khalid da na sani, me tausayi ne da jin kai. Mutum ne mai gudun b'acin raina, wannan da yake gabana, bai damu na mutu ko na rayu ba, ya je na sallamawa duniya..." Rufe mata baki Aunty Mariya tayi, tana girgiza kai. "Wallahi baya cikin hayacinshi, Ummi addu'a Saif yake bukata, don Allah ban da baki don Allah." Kukan da ta ƙasa yi, tuntuni shi Ummi take da dukkan zuciyarta. Kuka take kamar ranta zai fita, haka take kukan jikinshi yayi sanyi, ya kasa bata hakuri karshe fita yayi ta kalli Mariya da idanunta suke zubda kwalla ta ce mata. "Ya tafi!" "Ummi sai hirji da addu'a, da salatin Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama, ba zamu bar shi haka ba Ummi." Ɓangarenshi ya koma a can ya kira gimbi a waya suka sha hirar soyayyarsu, sannan ta umarce shi da ya kara niman Khalwat tana tausayinshi bata kusa da shi, dake munafika ce, sai da ta tambaye shi, taji halin da ake ciki. Aikuwa ya gaya mata abinda yake faruwa, murmushi tayi, a karon farko da ta bashi umarnin ya dauki Khalwat su tafi Istanbul, amma ya biyo da ita ta lagos su gaisa. Jikinshi har rawa yake, yana amsa umarninta. Haka kuwa ya aiwatar da abinda tace, bai tausayawa Yarinyar nan ba haka ya je mata kamar ba mutum ba, ya biya bukatarshi sannan ya kwanta ya barta ita ta sani, a ranshi yana tausayinta. Amma yana tsoron kada Gimbi ta ce ya zake. Don haka ya tsalleke ta ya koma dakinshi ya kwanta. ★★★ Bauchi Washi gari. Tun asuba Malam ya taso Tahir ya mai da Nazneen dakinta, duk abinda ya faru akan idanun Goma, bayan Tahir ya fito suka nufi masallaci da Malam, bayan sallah asuba Tahir yake gayawa Malam mafarkin da yayi, murmushi Malam yayi ya ce mishi. "Anya ba yar gida zamu yi ba? " "Baba malam kenan." Daga haka Malam ya ce mishi. "Ba mafarki kayi ba, da gaske ne abinda ka gani " cike da mamaki yake kallon Malam, ya ce mishi. “Baba Malam, kana nufin abin da na gani ba mafarki ba ne zahiri na gani? Kenan Aisha na gani tare da wasu irin halittu." "Ka daina wasa da azkar, yana da kyau sannan kana yawan addu'a kafin ka kwanta Allah zai kare ka daga jin duk wani abinda zai dame ka cikin dare, sannan idan zaka yi sallar dare ka tashi da kyakkyawar niyyar ibadar babu abin da xai razana ka, zan saka an jima a zo a maka ban daki a cikin dakin ba sai kana fitowa na waje ba " "Allah ya saka da alkhairi, ya kara lafiya da nisan kwana." "Amin Ya Allah!" Suka shiga cikin gidan a tare, suna tattaunawa. Dakin Hajiya Innayo suka wuce, tana tsaye a kan Nazneen da bokitin ruwan da ta sheka mata, amma wani ikon Allah ruwan bai sauka jikinta ba, sai a jikin bango ya zuba. Har ila yau tana barcinta cikin nutsuwa da dadin rai. "Innayo me kike yi kenan?" Tahir da ya leko dakin ya hango Innayo a tsaye kamar gunkin da aka dasata. Kai hannu yayi da nufin tab'a Innayo aka daki kirjinshi ya hadu da kofar dakin ya fad'i a wurin sumamme.. "Innalillahi'wa'inna'ilaihi'raji'un, Tahir!" Malam ya shigo dakin, yana kallon Innayo da take tsaye har zuwa lokacin. "Fita yayi zai nimo waɗanda zasu taimaka mishi, sai ga Ahmad Rufa'i, ya shigo gidan. "Lafiya Malam?" "Ina lafiya Uwarka da Tahir dake kwance maza fito min da shi." Da sauri ya shiga dakin, ya ga Innayo a tsaye da bokitin ruwan, ga Tahir a kwance da Bismillah ya d'ago shi, suka fito waje ya zauna da shi a shimfidar da Umma tayiwa Malam, "kada a kwantar da shi Malam ya ce, a zaunar da shi kawai." Jamilah ta faɗa, tana mishi fifita. "Ikon Allah! Kome ya faru oho." Fitowar Malam daga cikin dakin shi, suka zuba mishi idanu, zama yayi ya fara magana. "Ku taso min Nazneen ɗin!" Mikewa Rufa'i yayi zai tafi, Malam ya ce." Kada ka nufi dakin babu ayatul qursiyu a bakinka." "Tow Malam " haka ya nufi dakin, da sallama yana me karanta ayatul qursiyu. Har ya shiga dakin babu kome,. Innayo tana tsaye a wurin. Tashin Nazneen yake amma kamar matacciya. Haka ya fito da ita a kwancen. "Malam taki tashi!" Nuna mishi wuri Malam yayi ya ajiyeta ya ce masa. "Innayo fa bata motsi!" "Kyaleta sharrin da ta nufi yarinyar da shi ne, ya haifar mata da haka." Haka Malam yayi ta addu'a, yana karatu amma babu alamar zasu farka. ------- A hankali ya juya yake waige-waige, har yayi nasarar hango Innayo a gindin wani irin bishiya an daure hannunta da wani irin igiya me dauke da wasu irin kwari, sai hawa fatarta suke, tana ihu amma baka jin me take cewa. Da sassarfa ya nufe ta, har ya kusan isa wurinta aka rike hannunsa. "Kyaleta bata da kirki, bata isa hana kome ba, wacece ita da zata na niman azabtar da yarinyar da babu ruwanta." Zube gwiwarshi yayi tare da cewa. "Don Allah ku kyaleta, " Tahir ya faɗa yana rokonsu, amma ina sai kara habaka abin suke suna cizonta. "Zamu kyaleta, amma kasan yadda zaku rabata da gaban Innayo domin kuwa muguwa ce bata sonta ba iya ita ba, kowa da yake gidan idan ka cire Goma bata kaunar kowa." "Naji zata bar wurinta." Kwance Innayo aka yi ta zube a kasa tana nishi. ----- Tari Tahir ya fara, "Alhamdulillahi!" Duk aka furta, ana mishi sannu. Kallon Nazneen da take ta barci har lokacin. Kai hannun Malam yayi zai tab'ata ya rike hannun Malam. "Aljanunta ba gama garin Aljanu ba ne, idan ka tab'ata suna iya taba' mutum gwargwadon yadda ka tab'ata. Malam kyaleta tayi barcin, yana daga cikin lafiyarta." Kallon karin bayani Malam yayi mishi, ganin yadda Goma tayi kuri da idanun, ya cewa Malam. "Zan maka bayani." Dakyar ya mike, ya sab'i Nazneen sai dakinta. Ya kwantar da ita, sannan ya ja mata mayafi ya rufeta. Yana shafa kanta. "Queen of demon!" Ya furta a hankali, tausayi da wani irin abu da yaji ya tsigar mishi wanda bai san dalilin ba, ya ji yana masifar tausayinta. Innayo tunda ta dawo hayacinta, da rarrafe ta juya dakinta, wani irin zazzaɓi ya rufe ta, dakin Rufa'i ya shiga ya ganta cikin mugun yanayi, dole ya fita ya gayawa Malam, aka wuce da ita Asibiti.. Shi kanshi bai san yadda al'amarin zai kasance ba, amma tabbas Innayo ta tab'a Nazneen, mutanenta sun tab'a Innayo. Haka ya gayawa Malam. Sai wurin karfe biyu Nazneen ta farka. Kwanakin Innayo asibiti goma sha biyu, aka sallame ta. Tunda ta dawo Goma ke hidima da ita, Nazneen bata shiga harkanta,asalima makaranta take zuwa. A hankali Goma ta cigaba da zuga Innayo, da aibanta Nazneen. "Wallahi ina gaya miki, Innayo abin kunya kan an yi fa, domin kuwa ina jin Sa'a tana cewa jikanta ya janye jiki daga yarinyar nan me sufar aljanun, idan naga halin da kike ciki, kullum sai na zubda kwalla. Ai Uwar yarinyar nan tsinanniya ce, domin Wannan yarinyar bata yi kama da jinin gidan nan ba." Hmm ai kuwa yadda Goma take, ziga Innayo ya dinga saka jininta yana hawa, sati biyu da suka biyo bayan, Jamal ya kawo zancen biyawa Hajiya Lami Umra ita da Umma, Wayyo ina wutar da za a saka Umma da Hajiya Lami, domin kuwa habaici babu wanda Innayo bata musu ba, babu wanda ya ce mata cikanki. Domin sun san ba yinta ba ne, lokacin da Malam yaji labari ranshi yayi mugun b'aci, domin bai ji labarin ba, sai da su Hajiya Lami zasu bar Bauchi. Ai kuwa bayan tafiyarsu yayiwa Innayo barazanar sakin ta, haka yasa ta kara jin tsanar Nazneen, yadda ta uzurawa Alhaji Adamu, yasa babu shiri ya biya musu har da Nazneen, lokacin da ya fadawa Malam har da Nazneen a tafiyar. Yayi farinciki sosai. Don ma yarinyar tana da kwakwala ba karamin ɗaukar karatu take ba, koda aka kaita makarantar basu kaita primary section ba, kai tsaye suka kaita Secondary section, aka bata jss one. Sannan suka ce Tahir su nima mata kome na primary section, dake me makarantar Igbo ne, kuma wani abin dadi, Nazneen na shiga cikinsu, ta juya harshe. Sai gashi kafin wani lokaci ta hada kawaye Yaran Igbo da suke makaranta, sannan abin da kake kara musu sonta yadda kanta yake ja. Islamiyya kuwa a gaban Malam take yi, kuma yana jin dadin yadda take daukar karatu, shima kuma kara bata lakanin karatu yake, domin ta gaji gidansu ta bangaren Ilimin addini. Sati biyu cif Hajiya Lami da Umma suka dawo, ai kuwa Nazneen tasha tsaraba domin itace karamar Y'a a cikin gidan sannan rabin guzirinsu Alhaji Adamu ya basu. Haka yasa suka jibga mata tsaraba. Sannan wani abu daya kuma, suna son yarinyar domin idan ta dawo makaranta Innayo ta koreta a bangarenta, sai ta wuce falorn Hajiya Lami, ta je ta kwanta abinta. Ko dakin Umma, har faɗa suke da Tahir akan gadon. **** Abuja. An dauki lokaci kafin aka samu visar Khalwat, kafin ya fito suka zo azare da Saifullahi-Khalid, kowa ya gansu sun matukar dacewa, ba karamin dadi dangi suka ji ba lokacin da suka ga Saif da Khawlat. haka suka kwashe sati guda, sannan suka wuce kano, a can suka kwana sannan suka nufi lagos. ------ Tun a Azare ya kira Gimbiya ya gaya mata gasu nan zuwa, don haka ta nufi gidansu Jessica ta gaya musu ga Saif da Matarshi. Wani daki Hanne ta nufa, ta dauko mata wata ƙatuwar Mage bakakiririn da idanunta fari kwal. A wuyarta wani abin wuya ne na zinari, a jikin kwadon an rubuta. *Luse*, "wannan ita ce Kashim bayar ganin bayan duk matar da Saifullahi zai yi, gata nan ki riketa da aminci, mahaifar mutum take ci, da fatan zaki nima mata...... _NAAZNEEN, GENERAL NASIR ZAKI, BINTUN BATUL TOP-NOTCH TEAMS NA KUDI NE! BAKI DAYA UKUN 1300 NE_ BIYU=₦900 DAYA=₦500 0008219237 Azizah hamza Jaiz bank CHAT ME IDAN KUNA BUKATA: 08130269641 _KASUWA A KAI MIKI DOLE_ *Nesa tazo kusa, ko kun san Muzafa World collections. Sun zo muku da kayan zamani babu ruwanki da zuwa kasuwa. Yar uwa, kayanmu daya yake tankar da dubu. A rashin tayi akan bar raha, haka kuma bahaushe ya ce a rashin kira karen bebe ya b'ata. Tow ga dama ta same ku, domin kayanku ya tsinke a gindin kaba, kayanmu sun haɗa da Dubai Abayas, yan kunne da abin wuya, takalman Manya da Yara, lace masu kyau da inganci. Hajiya nesa da ake ce miki tazo kusa babu ruwanki da shan rana da kura, kayanki yazo inda kike! HAJIYA Abu me kyau ke sayar da kanshi* *08130269641* [11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥* EXQUISITELY BEAUTIFUL #Mai_Dambu Chapter 20 Last page A hankali ta dauki magen, tana jin wani sabon farinciki yana kara lullubeta. "Na gode sosai." Ta dauki magen zata fita Jessica ta ce mata. "ki kula da ita kamar yar cikinki, domin ba kasafai ake samun irinsu ba. Ki kula da rayuwar luse." "Zan kiyayye, kamar yadda zan kiyayye rayuwata na gode sosai yan uwa." Sannan ta fita daga gidan, bata tsaya ko ina ba, sai wani best eatery a kusa unguwarsu, ta sayi abincin da Saif da Khawlat zasu ci, sannan ta wuce gida, ta fara gyara gidan domin yayi kura, rashin yarda irin na Gimbi taki amincewa ta dauki yar aiki. A hankali take aikin har ta gama, sannan ta ajiye kome ta wuce dakinta tayi wanka, ta dawo falo tana kallon luse da take ta lashe kanta. "Luse ina son na fita na nimo miki abincinki, amma ina tsammanin Saif suna hanya." "Meow meow meow!!" Ta faɗa tana lashe jikinta, "na tafi kenan?" Gimbi ta tambayeta, sake mata kuka tayi da haka ta fahimci tana son abincin, don haka ta juya ta fita, tare da luse suka nufi motarta. Bude mata get din gidan akayi ta manna a guje. Can wani asibiti ta nufa, anan ta samu wata lebura da take shara a asibiti ta bata kudi, ita kuma ta je bola ta kwaso mata sabin mahaifar da zuba mata a leda, sannan ta bar Asibitin,. Lokacin da ta koma gida su Saif basu iso ba, sai wajen karfe biyar na yamma, suka shigo gidan tana dakinta kamar me barci. Suka shigo gidan, sai wani dauke kai yake kamar ba tare da Khawlat suke ba. Haka ya wuce dakin Gimbi ita kuma ya barta a falon, tunda ya shiga ya sameta kwance, zama yayi a bakin gadon, yana jin wani irin kewarta. "Princess!" Bude idanun tayi, domin taci uban kwalliya kamar me zuwa wurin biki. Tana ganin shi, ta wani rungume shi har da shashekar kukanta, ita yayi kewar shi. Haka tunda ta rungume shi, suka shiga wata duniya na daban, don dama an jima ba a hadu ba. A can falorn kuwa, zama a Khawlat tayi a daya daga cikin kujerun falorn, tana kallon yadda gidan ya hadu, dama haka yake da bala'in kudi, tana yi tana kallon kowani kusruwa ba gidan, a can bayan kujeran kuwa Luse ce da ta gama cinye sauran mahaifar da ta zuba mata. Jinin da yake jikin mahaifar ya gama ratsata. A hankali tayi ta sanɗa da bin bayan kujeran, Khawlat bata sani ba kawai shegiyar magen nan, ta dira a kafadarta tare da sake wani fusattacen gurnani a daidai kunnen Khawlat. Ihun da tayi tare da wurgi da luse ya katse abin da Saif da Gimbi suke, suka fito daga dakin. Luse ta kara nufar Khawlat da gudu,. Ita kuwa ta arta da gudu wurin Saif da ya riga Gimbi fitowa. Jikinta yana rawa, turus yayi tsigar jikinshi yana tashi. "Subhanalillahi, waye ya kawo mana mage gidan nan?" "Luse!" Gimbi ta kira sunanta, wuce su tayi ta nufi wurin Gimbi tana gurnani. "Magenki ce?" "Eh tunda ka tafi, bani da abokin hira shine ranar na fita na bude Uwarta ta mutu, shi ne ta bani tausayi ua daukota, ai bata son mutane kuma ban gaya mata zaku zo da Auntynta ba ne, Luse kin gan shi nan, shi ne Dad ɗinki. Ni kuma Mom ɗinki, ita kuma wannan Auntynki ce ba zata na dafa abinci tana baki, gobe ma zasu wuce honeymoon, don haka kada ki kuma razanata kinji." Ta faɗa tana daukar lusen, "meow!" Lusen ta juya tana kallon Khawlat da take bayan Saif. "Sorry sister, Luse tana cewa kiyi hakuri." Gyada kai Khawlat tayi tana faɗin. "Ina tsoron mage ne, shi yasa amma ya ce, Ina wuni aunty Gimbiya!" Zama tayi a daya daga cikin kujerun falorn, ta daura daya akan ɗaya tana faɗin. "Lafiya lau, ya amarci? Saif da fatan kana kula min da kanwata?" Washe baki yayi yana kara jin son Gimbi na cika zuciyarshi, bai zaci zata sauko haka ba. "Muje na nuna miki dakinki domin nasan ko kin dawo ba zaki koma Bauchi ba, kawai ki cigaba da aikinki anan." "Tow Aunty!" Gimbi tayi gaba dauke da Luse, Saif dauke da kayan Khawlat har cikin dakin da ta gyara ta tsaface shi. Da sallama a bakin Khawlat ta shiga dakin. Tana murmushi "Dakin yayi miki?" "Gaskiya yayi min, na gode sosai Aunty." Murmushi Gimbi tayi sannan ta juya ta fita, abincinsu ta sake dumamawa, sannan ta kara gyara ko ina, ta shirya ko ina, sannan ra raka Saif har dakinta yayi wanka ta ciro mishi kaya, yana kallonta. "Ban zaci zaki amshi Khawlat hannu bibbiyu haka ba, na zata ko don baki son kishiya zaki ki bata fuska. Gaskiya na godewa Allah da ya bani ke, domin ba karamin sa'a nayi ba. Allah ya miki albarka." "Amin Ya Allah!" Haka ta taimaka mishi ya shirya, sannan suka fito falo, ita ta wuce dakin Khawlat, da ta shirya cikin riga da skirt, tayi kyau murmushi Gimbi tayi ta ce Mata. "Kin yi kyau Amaryan Saif, zo muje kici abinci." "Tow Aunty Ina zuwa, ban yi sallah la'asar ba ne." "Ok ba damuwa!" Ta fito tare da bin dakin da wani mugun kallo, sannan ta fito falo, ta zauna wurin Saif bai tambayata ba, gudun kada ta fassara shi yasa shi cigaba da cin abincinshi, "baka tambaye ni ina amarya ba?" "Oh, Baby gaya min ina take?" "Tana sallah, yanzu zata zo." "Ok ta kyauta nima dake na ganki, ban yi la'asar ba. Amma ina gamawa zan je nayi sallah domin dai kin san ci na gaba da sallah." A ranta tace. 'Ai ko zaka yi, ba zaka tab'a yin shi akan lokaci ba.' suna zaune a wurin Khawlat ta iso, ta ja kujeran zata zauna luse ta tawo da gudu ta haura kan kujerar.. "Baby Girl, sauka aunty ta ci abinci." "Meow" ta faɗa, tana me sauka daga kujeran, ta nufi wurin da take zama ta zauna. "Kai magen nan, tana jin magana ga hankali." Saif ya faɗa, yana kallon Luse da tayi kalar tausayi. "Haka kowa yake faɗi. Idan nayi baki suka ga yadda nake mata magana tana yin duk abinda na ce, sai su ce dama sune da ita." Ita kan Khawlat bata ce kome ba, ta cigaba da cin abincin ta, wanda take cusa shi kamar dole, dakyar ta mike ta ce musu zata shiga daki yayi sallah magariba ta karato, sai lokacin Saif ya tuna sallah la'asar ta wuce mishi, sai da idanunshi yayi jajuur don bakin ciki. Daga nan ya wuce yayi alola, ya gabatar da la'asar, sannan yayi Sallah magariba. Dakyar Gimbi ta barshi yayi Sallah isha, babu dogon addu'a suka fada duniyar maji dad'i. Kusan wannan daren Khawlat bata rintsa ba, domin Luse ta hana ta barci. Domin ta rasa ta yadda magen nan take shigowa, bata samu barci ba sai karfe biyar na asuba, ta nime Luse ta rasa bayan ta idar da azkar ɗinta, ta koma ta kwanta. ....... Wurin karfe sha daya na safe, Saif da Gimbi suka fito daga dakinsu. Lokacin Khawlat tana can, tana fama da wani irin mafarki ko nace idanu biyu, na wata mata me rabin jikin Luse, tana kokarin caka mata wuka, amma tana ta addu'a tare da dambe. Shigowar Saif dakin yaga tana ta kokuwa da kiran sunan Allah, ya isa wurinta da sauri yana me d'agota yana kiran sunanta. "Khawlat!" Ya kira sunanta da mugun ƙarfi, bude idanu tayi akan shi. Da wani irin sauri ta rufe fuskarta a kirjinshi, tana me fashewa da kuka. "Yaya Alhaji ka maida dani wurin Ummi don Allah!" "Ya isa, hala baki yi addu'a ba, kika kwanta ko?" Ya faɗa yana bubuga bayanta. Shigowar Gimbi dakin tana faɗin. "lafiya kuka zauna baku fito ba?" "Princess, Kanwarki na samu tana mafarki shine na tashe ta." "Ya Salam! Sannu kinji." Ta faɗa cikin matukar ban tausayi, "Kiyi wanka sai ki fito." Saif ya faɗa, yana kokarin barin jikinta. "Amma ai da ka taimaka mata, koda haɗa ruwan ne yadda take a firgice nan ai ba zata iya ba." Wani karin mutuncin Gimbi ne ya kara tula a idanunshi, ya sake murmushin farinciki ya ce mata. "Ina godiya da Ubangiji ya bani ke a gefena, Na gode." Fari tayi da idanunta, sannan ta ce mata. "Bari na hada mata kawai." Haka ta wuce ta haɗa mata ruwan bayan ta zuba abin da zata zuba, ta fito ta ce mata. "Sannu Khawlat shiga ki yi." "Tow, na gode Aunty." Daga haka ta fita ita kuma ta shiga tayi wankar ta fito, ta gyara jikinta. A hankali ta shirya cikin doguwar riga, na material lace yayi mata kyau. Sannan ta gyara dakin, kafin ta fita wurinsu. ....... Tana fita falon ta samu sun gama, ta zauna ta fara ci, Saif da yake can tsakiyar falon ya ce mata. "Ki hanzarta domin zamu tafi yau ne." "Ok" ta ce mishi tana cin abincin, Gimbi tana jikinshi tana zuba zamaninta. Har Khawlat ta gama, suka fito tare da rakiyar Gimbi har airport, har jirginsu ya tashi tana nan, murmushin mugunta taii tana me juyawa zuwa gida da gudu domin idda sauran aikinta. Ba karamin dadi ta ji ba, domin tun jiya Luse ta cire mata kurwan Khawlat. Tana zuwa ta ta nufi dakin da take aikinta, ya cire mayafin da ta rufe madubinta. Cikin raha ya kira Mamanta. Tare da tura mata wata yar kaza, ta ce mata. "Ga kurwa kishiyata." "Lallai kin fini kokari, yanzu dai miko min ita, na duba ko tana da ciki " "A'a bar min ita, nima zan iya ji da ita " kiri-kiri Gimbi ta hana Uwarta kurwan Khawlat, ta rufe labulen ta fita ta kira Jessica, ta gaya mata. "Zan turo miki da wani flowers pot guda biyu, daya zakina zuba mishi ruwa ne, daya kuma zaki na zuba mishi runshi ne, a gefensu zaki saka wani wani flowers, anan zaki daure kazar. Sai kina barin Luse tana aikinta a kanta." "Da fatan na zata mutu da wuri ba?" "No ba zata mutu ba, ai ke zaki cinye abinki. Sai luse da zaku bata hanjin da kudun. An gama da tarihinta amma zaki cigaba da azabtar da ita." "Na gode sosai!" Wurin karfe tara na dare, aka buga mata kofar, tana budewa ta ga flowers pot din nan dai amma babu kowa, dauka tayi ta kai can backyard din gidan, ta ajiye ta yi yadda aka ce mata. Sannan ta fito zuwa dakinta, ya dauki kurwan Khawlat da take yar karamar kaza, ta je ta daure. Duk da wani zuciya tana bata shawaran ta barta wani zuwa yana bata shawaran ta kashe ta haka ne hukuncin duk macen da ta rab'i Saifullahi. ★★★ Saudiya. Friday morning Za a iya Cewa, Allah yana tare da Nazneen ne, kawai amma Innayo bata ki ita

Chapter 11 of 12