An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
[11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: Message Mai_Dambu on WhatsApp. https://wa.me/2348130269641
*NAAZNEEN❤🔥*
EXQUISITELY BEAUTIFUL
Top-Notch
Season 3
Chapter-2 Evilness
بسم الله الرحمن الرحيم
Balkisu ce take da wannan yanayin, amma itama sai da ta kara da mai da gyaran jiki, shi yasa ake tsammanin ai ita tayi gadonshi akwai dai farar fata.
Yau Alhamis.
A bisa tsarin gidan, yau ake yankar namar miya, wanda zaayi wata guda ana amfani da shi. Hajiya Innayo wacce asalin sunanta Aisha, domin dayawa suna tunanin Aishan Hajiya Lami sunanta aka saka, amma shi Malam bai ce musu cikanku ba. Fitowa tayi tana rike da wayar hannu. Tana me kallon wayar ta ce. "Jamilah zoki duba min, kamar Rufa'i ya kira ni ko?"
"Tow Innayo" gabanta ta isa ta amshi wayar cikin girmamawa ta ce mata. "A'a ko yaya Adamu ya kira ki!" Shiru tayi kafin ta ce mata. "Kira min shi na ji jikin takwara."
Kiran layin tayi ta mika mata, sannan ta bar wurin. Tana son taji meke faruwa. Komawa daki Hajiya Innayo tayi tare da sallama. "Assalamu alaikam!" A can ɓangaren ya amsa. "Wa'alaikimun Salam, Barka da safiya Innayo!" Ya faɗa,
"Ya iyalin da Yaran? Da fatan jikin takwara da sauki?"
"Da sauki Hajiya, dama na kira Malam naji wayarshi a kashe shi ne na kira ki."
"Ayya ai ya fita, amma nasan fada ya tafi. In sha Allah zuwa anjima zai dawo."
"Yawwa Hajiya, don Allah ki min addu'a maganar karin girman nan, yana nan ana dambarwa a kanshi. "
"In sha Allah, Ubangiji zai mana jagora ka yarda Allah yake badawa."
"Hajiya Na gode, ki yafe min ki kuma yi hakuri da ajizanci irin na d'an Adam!" Ya faɗa da bala'in raunin murya.
"Adamu idan ba mutuwa zaka yi ba ai kullum sai ka roke ni Allah ya shirya maka zuri'a."
"Amin Ya Allah!" Ya faɗa kamar zai yi kuka.
★★★
Kaltungo.
Sai da suka yi, tafiyar kafa me nisan gaske wanda har ka gaji suka yi. Su uku ne yan mata, biyu cikinsu daga su sai kayan jikinsu sai ita ɗaya da ta rufe fuskarta. Sanye take da hijab har kasa, ko ba'a gaya makaba yadda suke hawa duwatsu zai tabbatar maka da sunyi tafiya me tarin yawa.
Zubewa suka yi a kasa, suna nishi kafin suka juya gare ta, tana tsaye kamar doki. "Yanzu ba zaki zauna ki huta ba?"
"What hell fucking your stupid mouth! Gaya min taya zan huta? Taya ina ji ina gani waccen shegiyar tsohuwar tana shirin shiga rayuwata? Taya ina ji ina gani zan kyale shi ya koma gere su? Da ita da tsinannen balaraben nan sai na saka anci min bura ubansu. Ko zan yi yawo tsirara sai naga bayan duk wanda zai shiga tsakaninmu, mutum ko aljan, bani jakata, mun iso."
Ciro mata jaka suka yi, suka bata tare da komawa gefe suna kallonta, budewa tayi sannan ta ciro wani dan karamin madubi, ta taka gaban wani dutse, ta ajiye shi sannan ta ciro wuka da candles guda uku ta kunna, fari da baki da ja. Sai da ta kunna kafin ta koma gefe, ta cire nikab din fuskarta. Ba laifi kyakkyawa ce, doguwa me dan jiki.
Tana da hanci dan siriri, sai bakinta wanda yake babba ba laifi, a fuskance tana da kyau ba laifi.
Cire hijab dinta tayi, tana watsar da shi, sannan ta shiga ware zaren rigarta, kallonta daya budurwan tayi tana faɗin. "Gimbi tun daga Abuja dama haka kika taho babu riga sai nightwear?;" Banza ta bawa ajiyarsu, sannan ta cigaba da aikinta.
Cire kayan tayi ta watsar a gefe, daga ita sai pant. Ta cire shi tana zuwa gaban madubin ta zube a gabanshi. Warware wig din kanta tayi, ya sauka a gadon bayanta. Sannan ta dauko wuka yar ƙarama ta yanke hannunta, ta dunkule hannunta tana me zubda jini a gaban madubin.
Sai da jinin ya zuba sosai, sannan ta mike tsaye, tsirararta ta dafa dutsen tana wasu irin surutai kafin can kuma sai ga wurin yana girgiza. Kafin wani lokaci duhu ya lullube ilahirin wurin, iska me karfi yayi ta tashi har sai da suka bayyana a gaban wani kasurgumin mushriki. Zubewa tayi a gabanshi, a lokacin sauran yan matan suka cire kayansu.
"Gimbiya kenan, dama mun san zaki zo tabbas zaki dawo nan. Shi yasa ban dauki matakin b'acin rai a kanki ba."
"Tuba nake nima ba Allah, na san nayi kuskure ba Allah, amma wannan karon zan shiga duk abin da kace. Fatana ka karasa min aikin da ban gama ba, Ba Allah."
Ƙasaitacciyar kazamar murmushi yayi, sannan ya ce mata. "Kin yarda ba Allah?" Zubewa tayi a gabanshi tare da kwanciyar rubda ciki ta ce miishi. "Dubu bisa dubu domin naga haka"
"Kinsan sharadin aikina!" Murmushi yayi yana kallonta, idanun shi kur akan guduma guduman duwawunta. Gyada kai tayi tana faɗin. "Ba Allah na amince!" Ta faɗa kamar zata yi kuka. "Shegiya tsinanniyya. Na zata zaki ki ne? Kuma da kuke tsaye ke Siyamah don ubanki ba Alhaji Mamman ya ki saya miki motar ba, karshe da kika masa magana ya ce kada ya kuma ganinki?" Zubewa budurwar tayi tana faɗin. "Anyi haka Ba Allah, me dogon idanun duniya."
"Feenerh ya muka yi dake akan, haduwa da minista? Nace zaki hadu da shi. Amma sai kin sadaukar da wani abu, tunda kika tafi baki kuma dawowa ba, sai bin kananun yan iska kuke da sunan masu taimakon.
Daga karshe zan gabatar muku da kungiyar Ba Allah. Amincewa suka yi tare da kwanciyar rub da ciki. Juyawa yayi kan matar farko ya ce mata. "Saifullahi-Khalidu Mansur Katagum, ko ba shi ne tsaye ba?" D'ago kai tayi tana kallon madubin gabanta. Muryarta na rawa ta ce miishi. "Ba Allah shine wallahi."
"Kutumar ubanki ni zaki rantsewa da Allah? Bayan nan wurin ba Allah."
"Tuba nake, ba zan kuma ba a yafe min!"
"an yafe miki shegiya!" Ta cigaba da kwanciyarta, wani abu ya shiga watsawa a wuta. "Aure zasu mishi, musamman Amininsa. Wanda tun farko ya nuna adawa da aurenki. Ita kuma tsohuwar guzumar tana can, tana raba abinda take da shi akan ya dawo gare ta." Ya cigaba da aikinshi sannan ya ce mata. "Zaki samu nasarar nisanta shi da kowa amma ki sani bai zama dole ya manta da su ba. Musamman wannan dan iskan Yaron!" Aka hasko mata hoton wani kyakkyawan balarabe. Rike da littafai yana tafiya.
"Zan shafe tunaninshi a duniyar Mijinki, amma shi ba zan yi aiki akan shi ba." Ya faɗa yana kallon bangon. Domin shiri yake babba akan mutumin.
Suna kwance ya gama aikinshi, sannan ya ce mata maza ku tashi. Ki dauki wannan kwaryar ki ajiye a bandakin ki, kina wanka da ruwan ciki. Wannan kuma ki haɗa da kunzugun hailarki, kina sarrafa miishi wani abu, sannan wannan a nima miki. Bududdugi. Ki saka a bakinshi a rufe ki binne a makabartar kiristoci. Wannan kuma ki samo guzumar saniya, a zuba mata a cikin dusarta ta ci, idan ta fadi sai a binneta da ranta, magana ya kare. Ladar aikinki kuwa kema kin san kome."
Gyada kai tayi tana faɗin,. "Na gode ba Allah!" Sauran kuma aikinsu yayi sannan kowacce sai da ya kwanta da ita, idan ka cire matar farko wato Gimbiya, ita baya kwanciya da ita, domin auren da tayi. Amma akwai wani abin da tsakaninsu kawai suka sani ita da shi. Yana gama musu aikin suka fito. A gajiye suka fito bakin titin kaltungo. Wurin karfe biyar na yamma, daga nan suka bawa motar wuta, sukayi ta gudu akan titi zasu zo Bauchi.
Karfe bakwai da rabi suka iso garin Bauchi.
Gud'in na sayawa.
Koda yake kafin gud'in ya samu rabuwar kai, an samu tashin hankula tsakanin mazauna unguwar da hausawa. Asalin mazaunan unguwar sayawa da Fulani ne kasancewar yayi baya da garin Bauchi sosai. A unguwar motarsu Gimbiya ta tsaya, a kofar wani gida da ya banbanta da sauran gidajen unguwar, domin kowa yaga gidan, yasan nera na numfashi a cikin gidan.
A hankali ta fito, tare da kallon yan matan. "Tow ni dai sai gobe zan koma Abuja!."
"Ke Ba Allah bai gabatar mana da kungiyar Ba?" "Yana sane, domin zai nime mu " sannan ta juya zata bar wurin. Siyamah ta ce mata ta. "Gimbi hankali sai ya kwanta, Mijinki zai fasa aure!" Juyawa tayi ta wani yatsina fuska, ta ce mata. "Hmmm! Ai ba zaki gane ba, sai mun hadu." Daga haka ta juya ta barsu wurin, jan motar suka yi a guje.
A nutse take takawa, har ta isa cikin gidan, Uwarta ce gaban wasu yan mata, suna tatan gasarar kunun zaki. Baka ce doguwar me jiki. Kallon yar tayi ta watsar sannan ta ce mata. "Ban da iskanci, daga zuwanki, wancan shegen mijinki ya kira ni ya kai sau goma! Gimbi ba zaki dake ni, ki hanani kuka ba, tunda kika jajjubo mana bahaushe na daina ganin dai-dai a harkata."
Banza tayiwa uwar, ta wuce wani daki, ta leka tana kallon mutumin cikin dakin. "Sannu Baba Allah ya baka lafiya!" Daga haka ta wuce dakin uwar har can uwar dakar, ta ajiye kayanta sannan ta zube tana kallon shirgin Uwar. Shigowa tayi dakin daga gefe. "Gimbi kenan, na gaya miki. Babu wanda zai taimaka miki, kamar kanki. Tun ba yau ba nake gaya miki. Babu amfanin zuwa nima a wurin wani ki nima da kanki."
"Gaskiya ba zan iyaba, Gara na lallaba da haka, kina ganin ina tattaro shi yana kwace min, saboda tsinannun da suke tare da su." Ta faɗa tare da tura baki. Cikin kwantar da murya, Maman Gimbi ta ce mata. "Ki barshi yayi auren, kinji." Wani irin ware idanu Gimbi tayi jikinta yana rawa, ta ce mata. "Na gama cin uban wahalar hawa dutsen Kaltungo sai ki ce na barshi yayi auren? Anya kece kika haife ni?"
Murmushi tayi, jajjayen haƙorarta suka bayyana ta ce mata. "Na miki alqawarin ba zan tab'a barin yayi rayuwa da wata ba, ina son na tsaya a matsayina ne na mahaifiyarki na tayaki yaki. Yaron nan yana da nasara, sai dai cikon nasarar shi baya tare dake?" A razane tayi baya tana nunata da yatsa. "Mama kina sona kuwa?" "Kaf duniya babu na biyuna, domin cikar burinki na nad'e ubanki akwai abin da ya kai haka, matakin kauna?"
"Ya zanyi da kayan ba Allah?"
"Yanzu aka fara, ki shirya gam aure babu bashi. Domin na san Hausa na kuma san halinsu, basu tab'a yarda da faduwa, kullum cikin sallah suke da niman biyan bukata, ki shirya yaki ne ta ko ina."
"Amma Mama akwai wanda zai saka ya manta kowa na shi." Murmushi uwar tayi sannan ta ce mata. "Kin basu damar tashi tsaye a kansu kenan, yaron nan, yana da nasara dole ki barshi yayi aure, domin yin auren shi zai bani damar samun abin biyan bashin da na dauka, Ba Allah ya miki tayi amma na hana shi domin bana son ki matsa ko ina, ina tare dake. Idanuna yana kanki."
"Na bar shi yayi aure?" Ta fada tana me fashewa da kuka. "Na gaya miki da kanshi zai daina, ki barshi yayi ke ce ma me shirin auren na shirya kome yau zaki halarci taron kungiyar mu na farko!"
Gyada kai tayi tana jin wani irin kwarin gwiwa, tabbas zata barshi matukar zata mallake shi a iya duniyarta.
Enugu.
Tunda ta baro church, ta zubawa yarinyar idanu. Wacce ta gama ihu da birgima kafin tayi barci. Ta zubawa yar idanu, tana tsananin tausayin rayuwarsu. Ta bar kowa da kome ta bar danginta, hawaye ne ya zubo mata. Amanda ita ce ƙaddararta ko da yake ba dan yarinyar ba, ita kanta da ta zama tarihi domin kuwa rayuwarta abin tausayi ne, daga ranar da ya shiga rayuwarta shi kenan kome nata ya tsaya cak. Kallon Amanda tayi da take barci, buga mata kofar dakin akayi tasan landlord ne, jikinta a mace, ta ce mishi. "Yes Mr Uchenna " ta fita cikin sanyin jiki. "Nne Amadan, the month is coming end and I never see you." (Maman Amanda wata ya kare banganki ba,)
Zubewa tayi a kan gwiwarta. Tana hada hannunta "I beg you for the sake of God,
i'm sorry, all the money I get a spent it for Ama, ." (Na roke ka da Allah, kayi hakuri duk kudina sun kare akan Ama ...)
"I know now, but the house is not my own.!" (Nasani mana, amma kuma ai gidan ba nawa bane)
"Nne!" Wato mama, ta kira sunanta, juyawa tayi jikinta yana rawa, domin bata cika son bayyana Yarta sosai ba, matukar ba kasan wacece ita ba. Da sauri ta tura yarinyar daki. "Ama what happened?" Mika mata ledar tayi, ta ce mata, "Go and give him!" Karba tayi. Tana juya ledar baka ce, kafin ta ce mata. "Ama who give you?" Juyawa tayi tana kallon jikin bango. Ta nuna mata. Kallon wurin tayi tana faɗin. "i don see anything!" "But he is there!......
*KADA A JI TSORO YANZU AKA FARA🙄🤣🙄*
#Mai_Dambu41
[11/19, 7:01 PM] Queen BeeBee: *NAAZNEEN❤🔥*
EXQUISITELY BEAUTIFUL
Hakkin Mallakar
®Mai_Dambu
Top-Notch
Season 3
بسم الله الرحمن الرحيم
*Mun fara da sunan Allah, Ya Allah ya bamu ikon sauke nauyin da muka dauka. Ayi hakuri da abin da idanun ko kunnuwa zasu gani, ban yi alkawarin kyautatawa zukatar kowa ba. Zan bada abin da naga zan iya ne, ba labarin mun irin na yau da kullum ba ne. Labari ne da yayi arashi ga rayuwarmu ta yau da kullum. Bana ce abin da yake faruwa ba ce, kuma ba nace kirkira ba ce. Labarin zai yi gogayya da zahiri da badili!*
_Labarin wani bangare ne na Arewa maso Gabas din Nigeria! BAUCHIN Yakubu..... Garin masa_
Chapter-1_Exorcist
Catholic church Enugu.
"In the name of father, the son, the holy spirit and virgin Mary lead us to not into temptation, but deliver us. From evil"
"Hhhhhhh! Father Christopher."
Ta kalle shi tana dariya me d'aga hankalin da wani irin bala'in iska, baki daya church din ya kaure da mugun duhu wanda ko tafi hannunka baka iya gani, wani tsoro ne ya kama wasu daga cikin malaman Catholic church din musamman masu aikin cire evil spirits, kafin su fahimci wani abu, an shiga buga su da kasa, suna wani irin azababben ihu.
"In the name of Jesus Christ, I command you." Dariya ta kuma kyalkyalawa ta ce mishi.
"Ba zaka iya kome ba, ba zaka tab'a rabani da jikin Amanda ba, ba zan tafi ko ina ba. Am the only angel of guardians, she can't live without me! I'm like breathing in her body. Ba zan taba fita ba, amma zan muku abin da. Ba zaku manta ba."
Aka faɗa ana tsinke chain din da aka daurawa me maganar.
"Saint Michael the archangel defend us in battle. May you cast out Satan and evil spirits who roam the world to curse souls!" Kusan abin da suke nanawata kenan, amma ina watsar da chain din aka yi,. Gaba daya dakin Ibadar yayi duhu.
"Ka gama ihunka, ba zan fita ba, amma zan gaya maka wani abu ko garin nan zaku hada ba xan tab'a barin jikin Amanda ba. Sun yi laifi wanda ita zata dauki zunubansu. " Ɗif aka yi shiru, haske church din yayi, malaman Catholic din suna gefe cure da juna, wani dattijo tsaye rike da bible Idanunshi rufe yana jan crossing. Yarinya ce a gabansu wacce bata wuce shekaru tara ba, rike da chain ta murde shi a hannunta. Kafin su ankara ta shiga zane su da chain din tana faɗin. "Kunyi karya, ba zaku iya min kome ba!"
"Wayyo Father Matthew ka taimaka mana zasu kashe mu." Inji Malaman.
Bude idanu yarinyar ta juya kanshi, a fusace tare da kai mishi bulala, wani azzababen ihu da rawa jikinshi yake. Ta kuwa cigaba da zanesu. Bude kofar shiga church din, wata mata tayi kanta daure da dankwali, "No....no Amanda don do this for me!" Ta fada tana diba a guje, taje tasha gabanta, lokacin Father Matthew yana cin uban duka, domin ya hadu da jagwal. Zubewa tayi a gabanta. Ta fashe da kuka,
"Please don do please, I beg you for the sake of son of God!" Ta faɗa tana hada hannunta wuri guda. Sake chain din tayi tana fadin.
"Nne!" Ta taka jikinta, da sauri ta bude mata hannun. "Don let her hug she is evil demon!" Da sauri yarinyar ta fada jikin Uwar, tana me bude idanunta, ta kalli father Matthew. "You can't change the destiny!" Ta faɗa tare da kura mishi idanunta. Wanda suke kore me had'e da wuta wuta, fasa ihu yayi yana burgima shi yasan azabar da yake ciki, "Mu dai ki fita mana da yarinyarki a church!" Ya faɗa yana kallon yadda baki daya cross na cikin church din ya juyasu upside down.
Bai san lokacin da ya zube a gaban babban gunkin virgin Mary ya fara addu'a ba.
" I cut the ties between your inner demon and outer demon. May the holy spirit cast you into the abyss, let all evil spirits be cast into hell"
Samun tsakiyar bayanshi aka yi, aka sakar mishi dundu, tare da kara make kanshi. Ya tintsira can, ba shi daya ba, hatta sauran malaman binsu aka yi da mugun rankwashe sai da Father Andrew ya saki fitsari, tare da fashewa da kuka.
"Nne take me out zasu kashe ni." Ta faɗa a daidai kunnen Uwar, cikin matuƙar gajiya, da son lallai ta kawo karshen matsalar diyarta ta juya a hankali, ta goyata. Suka fita daga church ɗin. Kamar dama jira ake su fita. A cigaba da zane malaman tare da basu wahala, musamman father Christopher da yake finsu zakewa, mari kawai ake sake musu.
★★★
Garin Bauchi.
Unguwar Jajja, daddaden unguwa ce a cikin garin Bauchi, domin tana cikin gari, bata yi waje da garu ba, sannan akwai manyan mutane a unguwar, masu karfi da ma'aikatan gwamnati, sannan yan kasuwa tare da babban gidan Malami Alhaji Sani Jajja, wanda ake kira Malam Malami Jajja.
Dattijon da yayi kaurin suna a koyarwa da tafsirin Alkur'ani mai girma, babban Malamin da yake da tarin almajirai kamar me a cikin unguwar domin manyan gidaje hudu gare shi na kwanan almajirai.
Banda taimako da yake bawa mutane, hatta yan siyasa ba karamin cin gajiyarshi suke ba.
Babban gidanshi me dauke da mata hudu rus, kuma kowacce ta zuba Yara kamar meye. Sannan wanin abin burgewa Malam Malami Jajja Yaranshi maza da mata suna karatun Alqur'ani da na boko, kowacce yarinya zata gama secondry school, kafin ayi aurenta. Mazan kuma har jami'a suke yi, ya danganta da abinda kake so ne, idan baka son karatu zaka kama kasuwanci ko gona. Domin ya yarda da in baka nemi ilimi ba, ba makawa zaka yi kasuwanci.
Matan gidan Malam Malami Jajja, har yau da girma ya kama su, suna da mugun kishi, da kafkaf da Yaransu. Domin Allah ya bashi ikon gargad'an su, bai yarda wata mace ta sauka akan Hanyar da ya dace ba, ba zai hanasu kishi ba, amma ya zama dole a garesu. Kada yaji kada ya gani wata ta tab'a mishi yara da asiri domin zai iya mata abinda ba zata iya kwatar kanta ba. Haka ya haifar masu da zafin kishin juna.
Don haka suka rufawa kansu, asiri kada wani yasan meye yar wancan take ciki. Hajiya Innayo, ita ce uwargidan Malam, tun auren fari. Tana da yara biyar domin tana yin wabi ne.
*Dr Adamu Malami Jajja
Shine babban danta, kuma yana zaune a garin Abuja, yana aiki da iyalanshi.
*Ahmad Rufa'i Malami Jajja
Babban lecturer ne, a federal polytechnic Bauchi. Yana zama a tambari housing estate da iyalinsa.
*Nurse Uwani Malami Jajja
Tana aiki da asibitin specialize Bauchi wato bakas tana da Yaranta, suna sabon unguwar railway da Yaranta.
*Nura Malami Jajja
Soja ne yana nasarawa state da Matarshi da Yaranshi,
*Hawwa'u Malami Jajja
Suna kiranta da Yar Bauchi, domin ta kware a masa, kasancewar tana aikin girke-girke a government house Bauchi, sannan tana da babban gidan cin Abinci na ta na kanta, tana zaune a tudun salmanu da Yaranta.
Hajiya Umma matar da take bin Hajiya Innayo, mace me matukar mutuncin da hakuri sanin ya kamata, kawaici da dattako, babu ruwanta, da hayaniyar matan Malam, su suka sani tana da Yara uku.
*Abdullahi Malami Jajja.
Dan jarida ne, da yake aiki da babban gidan Radio BBC, yana can London da zama, da iyalanshi, tsakaninshi da Dr Adam wata shida, kusan sa'io'in juna ne, shi kan ya riga su aure, domin yana da shekaru goma sha tara aka mishi auren zumunta, kuma shi ne me Babban D'a a gidan.
*Usmanu Malami Jajja
Yana aiki a ministry
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 1 Chapter of 12