Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
na shigo", shi ya sa na gaisa da kowa harda tsarabar lemo da ayabar da na yiwa Innata, kuma na je na sanar da ita halin da muke ciki da karima, ban nuna mata ance ciwon ya yi tsanani ba, a'a abin da na nuna mata ina son taje saboda Mairo ta samu ta dawo itama gida gurin 'yan uwanta innata tace "to duk da kince Bilkisu tana wahalar komai amma bazan je hannu haka ba don haka dole tafiya sai jibi, don zan tsaya gobe in siyar da ragunana guda biyu in yazo ko kudin abincine an samu. Da sassafe aka dau raguna zuwa kasuwar mubi, tausayin inna kawai na ke, wanda saboda ba bu wanda zai maka wannan sai uwarka, duk wanda yace sai raba tsakanin da da mahaifi ya hada kansa da wahala ga irin rashin kulawar da karima tayiwa Inna, tunda inna ta dawo mubi a 'ya 'yanta kowa yazo ya ganta ban da karima, amma yanzu ance da inna karima ba bu lafiya har tana yunkurin siyar da kadararta don so, ni ina -57- zaton inna tafi son karima fiye da kowa a 'ya 'yanta, gaskiya ne da ake cewa yawancin mutane sun fi son wanda baya kulasu. Sai wajen karfe biyar na yamma aka dawo daga kasuwa, duk da girman ragunan nan ba su yi tsadi ba sosai, don duka kudin dubu goma sha biyu ne, wanda idan lokacin layyane sai dubu ishirin-ishirinm, haka inna ta kulle kudin nan, washegari da safe kárfe shida mun bar gida, munyi sa'ar mota karfe bakwai dai dai muka iso Abuja, sai da muka tsaya a Yanyan tun da kan hanya ne sanna muka wuce hospital, Mairo tana zaune tasa karima a gaba tana ta faman jan carbi, ita kuma an sa mata ruwa tana ta faman barci. Na lura hankalin inna ya tsahi- matuka yadda taga karima ta dawo, ni da mairo mun rufeta da dadin baki ta fara samun sauki don yanzu tayi kiba, a na haka wayar Bilkisu ta shigo, bayan mun gaisa na ke gaya ma ta mun zo da inna tace "to za ta zo da dare ita da Abdul dinta, ya dawo tun ran da na tafi mubi. Bayan mun yi sallama ne Mairo ta ke gaya min jiya maman Bilkisu da babanta sun duba karima sunje sun sami likita sun ce duk abinda ya taso ya yi musu waya, Mairo ta nu na da hannunta tace "ga kayan da suka kawo can", na je na janyo leda kifin gwangawani da lucuzed da kayan tae. Wadan nan mutane mai za muce musu sai dai Allah ya sa albarka, Allah ya kara arziki. Tun da aka yi sallar magariba inna ta yiwa -58- Mairo godiya tace "tafi gida, Amina ta raka ki" Mairo ta ce "ba bu komai inan jima matar kaninta za ta zo don jiya ma sun zo sun ce za su dawo yau, in sun dawo ma tafi tare. Kuma godiya da kike ai da na kowa ne, fatan mu dai Allah ya bata lafiya kawai." Yau naga Abdul din Bilkisu wanda aka cikani da labarinsa yana can America yana karatu, sai yanzu ya gama. Bilkisu kowa ya ganta ya san tana cikin murnar ganin Abdul, daga ganinsa mutum ne mai tausayi don ya tausayawa karima sosai har yana cewa Bilkisu kamata ya yi a fita da ita waje don su suke da kayan aikin irin wannan ciwon. Sun je sun sami likita, anan yake gaya musu daman yace tuntuni idan bamu da kudin fita waje to za'a yi mata aiki don yanzu haka sun bayar da kudin a yi mata aikin a gani in babu sauki sai a fita da ita. Yau alhamsi don haka yau saura kwana hudu kenen a yi aikin. Mairo ta koma gida sai dai tazo ta wuni, mu kuma mun dukufa ga addu'a Allah yasa a da ce kullum Sadiya za ta zo ta wuni amman Hađiza sam sai dai tazo ta gaishe da inna ta wuce wai karta dauki ciwo, ba na ganin laifinta don idan karima ce za ta yi mata abin da yafi haka. Biliksu da iyayanta da masoyinta suna ta ci gaba dayi mana dawainya. Har yau karima bata san inna ta zo ba don tana bude idonta lokaci lokaci amma sam ba ta gane mutane. Ranr hittinin da safe aka shiga da karima tiyata wanda a daren ni da inna kwana muka yi 59- muna Addu'a. Abdul din Bilkisu shi ya biya kudin duka, tun bakwai likita ya zo, muna zaune bakin kofar dakin har san nan likita ya fito sauran ma'aikata suka janyota aka je aka kwanatar da ita a wani daki, suka ce mu kyaleta nan da awa biyu. Karfe daya dai dai wata ma'aikaciya tayi kiran mu muka zo muka tarar da karima tana ta faman shure-shure na fita da gudu na kirawo likita yace "babu komai za ta dawo dai dai, idan allurar ta saketa" Bilkisu ta bugo waya "yaya jikin karima?" nace "Bilkisu ga ta nan an mata aiki amma bata farka ba" tayi mana Allah ya sauwake, ba za ta samu damar zuwa ba saboda saura two weeks, don haka za su wuce Dubai ita da innarta za suyi kwana hudu. Na yi-mata godiya da fatan Allah ya dawo da su lafiya. Karfe biyar na yamma sai ga sadiya da Muhammad, Usman, Isah da Ibrahim duk ta nemo su ta gaya musu Inna tazo ga kuma halin da karima take cik, i naka-naka ne inji bahaushe yace ko ba zai baka kamai ba, duk kanin su duk da maza ne sai da idanun su ya yi ja sobda halin da suka sami karima duk da an yi mata allurar baccі, saboda rashin dawowarta dai-dai shi ya sa har yanzu ba'a cire mata rigunan tiyata ba, basu bar asibiti ba sai da aka yi kiran sallar magariba, munyi sallam da su akan za su da wo washegari da safe. Tun karfe ukun dare bacci ya kaurace -60- mana saboda bige-bigen da karima take likitocі uku ne akanta, amma abin ya faskara, can wajen biyar saura karima ta farka kamar ciwon ya tafi, ba bu kowa sai ni da inna, ta budo ido tace "inna yaushe kika zo, don Allah ki yafe min na san ban kyautawa kaina ba, ni na kwasowa kaina ciwon nan, na san mutuwa zan yi ba bu wanda ya iya magana sai kuka, da karfi karima take magana kamar nace mata rage murya, duk Kalmar shahadar da nake mata wai ta fada, amma ya gagara a bakinta iyakacinta da tace mu yafemata karfe shidda saura dai-dai karima ta daina shureshure tayi shiru sai kunfa da take fita daga bakinta na ruga na kirawo likkita, ya na zuwa ya yi 'yan aune-aune yace "to Amina sai ku yi hakuri. karima ta rigamu gidan gaskiya, Allah ya jikanta" sai naji kunnena ya na gaya min ba dai-dai ba, don haka yana fita naje na sake kirawo wani likkitan, yana taba ta ya ce "oh Jesus karya ne, babu inda za ta", shi ne kuma wanda ya yi aikin ya tsaya yana ta faman ma ta Addu'a irin tasu. Hankalina ya dawo jikina sosai na gane wan can doctor Muhammad gaskiya ya gaya min, karima ta mutu shi wannan yana son dulmiyar da ni ne, don haka na fita na gayawa su inna babu karima, inna ta shigo da sauri tasa zani ta rufe gawar, naje na sami doctor Muhammad na ce "don Allah ya zo ya sa hannu a bamu gawar kar ace sai ankaita mutuware," ba a ata mana lokaci ba ya sa aka hada mana komai 61- aka bamu, motar asibiti din ciki aka saka gawar. Allahu Akbar rai bakon duniya muduba muga irin sharholiyar da karima tayi lokacin rayuwrta, babu wanda zai ce ya yi farinciki da rayuwarta. A dalilin karima inna ta hadu da hawan jini, gaskiya kukan da nake ba kowa nake waba sai kaina, yanzu mutum ya yi mutuwa irinta karima, a rayuwar duniya ace babu abin da ka fuskanta dan gane da lahirarka?, to me zaka cewa mahaliccinka?. Ni dai abin da ya tsoratar da ni haushin karan da na ji Karima tana yi ka fin ranata ya fita, tun daga duniya ma ke nan a zatona karima ko sallah ba tayi don tunda na ke da iťa ban taba ganin tana sallah ba, gaskiya duniya ba abun shagala bace, yanzu ta tashi tun tana karamarta tana faman bin samari, to yanzu a sakamakon da suka bata tunda sun hadata da ciwon da suka aikata lahita ba shiri, abin mamaki inda zaka kara tsorata da duniya tun da karima ta kwanta ciwo samarinta har mugayen kawayen nata duk sun kai ta sun baro. Innace ta katse min tunani tace "to sakko" muka sauka aka dauko gawar aka shiga da ita, Hadiza da Sadiya suka kwalla kara, nan da nan mutane suka cika gidan ana ta faman kururuwa. Babbab abin da ya fara damu na a ranar, jahilci, daga ni har inna babu wanda ya iya wankan gawa, mutane kuwa da suka cika gidan duk yawancinsu -62- arna ne, da farko shamsu ya je ya kirawo wani malami yazo ya gwanda mana, ya tafi ya siyo likkafani nan fa ya tafi ya barmu da gawa ba mu san yadda zamuyi mata komai ba. Can sai ga kungiyar su muhammad gaba dayan su kamar yadda suka zo asibiti, inna tace kuzo kuyimata wankan gawa, muhammad ne ya fara magana yace "gakiya ban san yadda ake wankan gawa ba", su Ibrahim ma kowama yagirgiza kai anan Shamsu yace ai akwai wata tsohuwa ana biyanta dubu biyar, idan namiji ne dubu goma, don haka idan da kudi sai ya je cikin maraba ya kirawo ta. Inna ta dauko kudin taba shi tunda kudin ragunnata babu abin da ta yi da su, mun fi awa daya da gawa a gaba ba bu shamsu ba bu mai wankan gawa, malamin daya kwadata bai dawo ba daga dinkin likkafani ba, sai arna ke ta faman yi mana ife-ifen, can muhammad yace "yana zuwa" minti isirin bai yi cikkake ba, sai ga shi da mahaifinmu, wanda gurin kowa ya yi tsit har arna da suke faman ife-ife, ko baka sani ba kasan shi ne mahaifinmu, tunda duk inda kama ta ke to su na kama da Karima mai mutuwa da kuma Muhammad, don haka duk arnan suka fita suka bar dakin dagamu sai shi, sai kallon-kallo suke shida inna, ya yi shigar manyan kaya shaddace tasha aiki bulu, hularma kalar kayan, banda siraran hawaye babu abin da yake, mu kanmu ya samu kukan wiwi, yauwa da inna ta kawo masa 63- را ruwa mai dimi zai wanketa Muh'd ne ya hado ruwan, yace “baba ka koyawa inna ta wanke ta" yace "ai wankan gawa kamar wankan tsarki yake, sai dai shi ba'a niyya, don haka ke da Amina za ku iya." Sai da muka kusan gama wankan gawar, sai ga matar wata wujiga-wujiga da ita, ganina ko sallar ta bata cikawa, na godewa Allah da mahaifinmu ya wanke mana jahilcinmu, ya kawo turare ya gwada mana duk inda za mu sakamata, malan mai likkafanin ya kawo aka sakata, mun shiryata tsaf nida innata duk zuciyata ta bushe kukama da nake na daina sai kokarin a kawar da ita kawai nake. Babu wasu mutane su shamsu ne da abokan hirarsa, sai mahaifinmu dasu Muhammad, sun yi shinfida za suyi mata sallah da su kazo daukar gawar ne mahaifinmu ya dafa makarar yana kuka yace, "Karima Allah ya yi maki gafara". "Ya Allah ka daukaka darajarta a cikin shiryayyun bayi, ya Allah ka gafartawa karima zunubanta wanda ta sani da wanda bata sani ba, ya Allah kar ka tuhumi karima da laifin da ba ta da masaniya aka shi, ya Allah ka haskaka mata kabarinta, Allah duk sabon da karima ta yi maka ni na jefata ciki, ina rokon ka da ka yafe mana baki daya, ya Allah ka wanke karima daga laifuffuka kamar yadda ake tsaftace farar tufa daga dauda, ya Allah ka tseratar da ita daga fitinar kabari da -64- 3 t Π 1. + f L azabar wuta." Mahiafinmu yana wannan addua'ar yana kuka haka su Muhammad, suka fita da gawar, aka yi mata sallah. An dau karima zuwa gidan gaskiya!, Allah! Ka kyauta namu zuwan, Allah kasa mutuwar karima ta zama sanadiyar shiriyar danginmu baki daya. Mahaifinm shi ke jigilar kawo abinci kullum, tun bakwai na safe yake zuwa sai bayan sallar Isha'i ya ke komawa gida, ban da akin kuka ba bu abin da ya ke, na san kukan ba ya wuce mutuwar Karima, minti ashirinashirin yake shigowa ya na tambayar inna me muke bukata. Ranar sadakar uku, ranar Binta ta zo, kuka ya dawo sabo don ta dawo da mutuwar kamar ranar aka yi ta, tunda ita tafi kowa dadewa ba ta ga karima ba. Mutum ba'a bakin komai ya ke ba, jahilci shi ne ya sa muke daukar kanmu komai, kalli duk yadda karima ta shiryawa kanta jin dadin rayuwa, ta sa kayan da taga dama, kullum kanta cikin gashin doki, don kwalliya kawai Jakarta cike take da kayan kwalliya, ba ta awa daya ba ta fito da madubi ta yi kwaliya ba don jin dadin duniya, yanda karima ta jiyawa kanta dadi ba ta cin abinci in ba mai dadi ba, dai kusan karima sai tayi wata ba ta cin abinci in ban a restaurant ba, babu abin da ta tsana irin zafi, kullum cikin raba take, don in ka ganta a gidanmu 'to şamirin nata basa nan ita kuma bata da kudin zuwa Hotel din, -65- yadda kawaye suke binta kai kace wata matar wani sarki ce. Amma abin mamaki, karima ta kwanta ciwo har sati biyu ba wanda yazo, gashi ta mutu har yau daga samrin har kawayen babu wanda ya leko, ni abin da yake bani mamaki ma shi ne, irin kayan da karima take sawa masu tsadar gaske, amma yanzu babu ko daya ina kyauta ta zatona kawayen nata suka kwshe, tun dama komai nata yana gurin kawarta Habiba, tun dama ta kawo man ita har yau bata dawo ba. Gasikiya duniya gaba daya rudu ce, ga shi dai yadda ta rudi karima. Babana ya katseni yace "Amina sai hakuri, kunyi rashin 'yaruwa, Allah ya ji kanta" Sadiya tace "Baba yanzu kana ina? kasan gareji kawai muke haduwa", ya ce "Sadiya mantawa ki kayi nace nan bayan garejin gaidana ya ke, ai ranr bakawi duk zamu tafi can Insha Allahu." Mahaifinmu yake tambayar Inna ina 'yar ginda karima? Inna tace "tana can gidan marayu, da na daukota daga baya na ga wahala tayi min yawa na mayar da ita, idan tana nan zan ganeta". Ranar kwana bakwai da sassafe mahaifinmu ya zo akayi Addu'a kowa ya kama gadansa, ya rage daga mu sai baba da inna. Mahaifinmu ya shigo ya zauna kusa da inna ya ringa kuka sosai wanda ko randa ta mutu bai yi irin sa ba, duk muna zaune muna kallonsa, inna ta tashi tace ita zata wuce Mubi kar dare ya yi ma ta. -66- Babanmu yace "dan Allah Amina kiyi hakuri karki wuce, yau kukan da nake na godiya ga Allah ne da ya sa ban mutu ba ku ma baku mutuba, zan rokeki gafara akan abinda nayi muku, nasan na yi jahilci kai na kuma na yi sabo babba na wulakanta baiwar da Alah ya bani na rungumi wacce ba tawa ba. Amina cuta na san na cuce ki kuma duk wanda ki ka ji ance ya yi hakuri to an cuce shi ne, don haka nasan na cuceki don Allah ki yafe min, nina batawa yarana rayuwarsu, saboda na barsu cikin yunwa, rashin sutura, kishirwa duka don haka dolene suje suyi ko meye, babu yadda mutum zai rayu babu daya daga cikin waddan nan ballantana su babu duka ma. A rayuwata arziki bai karamin komai ba sai halaka, don haka kullum Addu'ata Allah yabarni da talucina saboda na samu rabo babba. Annabi (SAW) da kansa yace "Mu nemi tsari da talauci don haka to ni ban ji dadin arzikina na fi jin dadin talauci don haka zan iya cewa talauci shi ne arzikina tunda shi ne na ke sa ran zan sami rabo babba dashi, Amina na wulakanta ki ke da 'yanuwanki lokacin da kuke tsananin bukata ta, amma da Allah ina rokonku da ku yafe min, rudin duniya ne da sharrin shedan yanzu na canja nagane na sake halina. Kowa ban ji kowa ya yi magana ba sai Sadiya ce tace "baba yanzu baka da mata?" yace "Sadiya bani da mata, mum dade da rabuwa da 67- Igala, wanda itace sanadiyar rabuwa daku gaba daya, tun lokacin da aka koreni daga aiki, ta kwashe min kudi masu yawa, kafin ta kwashi kudin sai da ta siyar da motocina, duka san nan ta kwashe mini kudina na America, wanda sune arzikina, inaga da Kudin nan suna nan ya isa nayi wani company nawa na kaina, a garin komai sai da ta rabani da komai, duk da gidan da take ciki siya ma ta nayi, ta siyar ta gudu garisu, har dan da muka haifa su duka, baifi sati uku da suka wuce ba ta aiko wani dan uwanta da ya ke garin nan da wasu wai dan ya mutu." Yadda aka yi na sai gidan da nake ciki don lokacin duniya juya ta min baya kuma kay abasa tsada don na siyar da kujeruna da kayan kallona, gadona kawai na bari nazo na siyi wannan gidan, abokai na duka sun guje ni duk cikinsu babu kamar. Buba, tunda shi ya fi kowa sani na, don haka, da ya ga yadda na yiwa iyalina ya fita harkata, ya na gani aka koreni daga aiki shi kuma sai da lokaci gama aikisa ya yi, don haka na tsane shi, nace ko yaje ya fadawa manyan mune, sai daga baya na gane sam ba haka bane hakkin iyalina ne ya kamani. Na dawo abin tausayi a cikin Abuja tun da abincin da zan ci ma ya gagare ni, yanzu dubi yadda na dawo, ni ba almajiri ba ni ba mahaukaci ba, sai na yi kwana biyar ban yi wanka ba, bani da kudin sabulu bani dana abinci. Haka na ringa 68- rayuwa sai da nayi kusan shekara a haka naga zama ba zai kaini haka ba kullum ina cikin gidan ina kuka kamar mace na fito gareji gurin masu mota, a nan naje na sami ogansu nace ina son ya taimakeni ya bani aikin da zan ringa yi ya na biyana, yace shi gaskiya na yi girma duk ma'aikatansa yara ne, don haka ba zai daukeni ba. Makocina wanda gidana ya ke jikin nasa, yana da shago a kasuwa naje na zauna a kofar gidansa ina jiran ya dawo, yana zuwa ya ganni a kofar gidansa yace "malam Abubakar lafiya?" nace "ba kalau ba", ban boye masa komai ba na gaya masa bukatata ta son na ringa binsa kasuwa nayi masa yaron kantinsa, yace "ai ni ca nake ka na da aiki" na ce "gaskiya da ina da aikin yi, ritaya suka yi min, shi ya sa nazo na sai gida acan da kudin da suka bani gaba day." Ban ce masa korata aka yi ba, don kar ya ce wani laifi ne ya ji tosron taimaka mini, yace "babu komai malam Abubakar, Allah ya kaimu gobe, sai ka shirya muja kasuwar a gwada a gani, ka san komai sa'a ne, idan Allah ya sa anan abincinka ya ke shi kenan." Washe gari da safe muka tafi kasuwa, sunansa Alh. Idris, shagonsa ya na cikin babbar kasuwa, ya na siyar da atamfofi da shaddodi, idan an zo ni na ke dauko kayan ina siyarwa, a haka nake samun kudin da zanci abinci da sutura. Mun kai wajen wata shidda dashi a haka, har ya fara -69- bani kudi ina zuwa kano ina masa sarin kaya, to yanzu duka baifi wata hudu ba da ya bude min wani shago anan kasuwar Garki, yanzu hakanma yadda muka yi da shi idan Allah ya buda nim, kantin ya na son na ringa biyansa kayansa na mallaki kanti. Tun da muka hadu da Alh. Idris yadda ake zuba masa abinci a gidansa haka nima nake da kwano, dan haka ba bu abin da zan ce masa sai Allah ya saka masa da alheri." Duk gaba dayanmu mukace Amin. Mahaifinmu ya kalli inna yace "Amina ya kamata kizo muje gidana gaba daya in ya so sai ki koma mubi, ku kuma kowa ta kwaso kayanta mu koma can", ya kalli mazan yace "haka kuma akwai dakin maza banda kải Muhammad da Ibrahim tun da kuna da mata" Usaman yace "baba nima ina da mata"yace "to me ya sa baka kawota gidan mutuwa ba" ya sunkuyar da kai yace abin da yasa ba musuluma bace" mahaifinmu ya dafe kai yace "usman bą ta sallah kwata-kwata" ya daga kai alamar E baba yace "to mai ya sa ba ka yi kokarin ka ga ta musulunta ba? 'ya 'yanku nawa?" yace "yaron mu daya Salwa ko shekara biyu bai cika ba", baba ya ce "ba bu komai muje dai can gidan nawa zanyi bincike baba yace babu komai muje dai can gidan nawa zanyi bincike akan abin." Inna tayi shiru abin ya bata mata rai sosai, don kowa zai ji a ranasa sai ya zo ya sami Inna ta zo bikin amma babu wanda bai kai matarsa -70- Mubi amma ban da Usman, ya na da aure har da da, a gakiya abin ya bata mata rai don haka ko magana ta kasa. Mun rankaya gidan mahaifinmu da kafa tund nan cikin Yanyan ne, ni kadai ce daman ban san gidan ba sai Binta da bata gari, cikin rufin asiri ba bu abin da bai saba a gidan, dakuna ne guda hudu, biyu a hade da falo da bandaki, kitchin ya waje a tsakar gida, da kansa yace "duk ginin nan daga baya ya yi su, don haka kullum addu'arsa Allah ya kawo masa ranar da zai hadu da iyalinsa. Ya sa aka je gidan abinci aka kawo mana abinci har da lemu, kowa ya fadi abin da ya ke so aka kawo masa, dadi ya ke ji ko Inna ma da take daure fuskarta nasan tana jin dadi a ranta, tana haka ne don karta nuna masa ko kuma ta tsoro ne kar a kuma, bayan munyi sallah ne Inna tace "ya kamata mu tafi", to anan usman yace wai gidansa yana nan bayan gidan mahafinmu, Inna ta so mu je, muka kama hanya mu duka Allah ya jikan karima da tana nan da yanzu tayi fada da wani. Takun da muka yi kadan ne, matar usman mai suna larai, daga ganin matar kasan suna wahala, larai mutuniyar kirki mijin ne dai, Asalinta 'yar kaduna ce arniyace, saboda usman ta musulunta, inda Allah ya kama usman mun sameta akan abin sallah, duk 'yan uwanta sun gujeta saboda ta koma musulma, don haka yanzu bata zuwa gurin kowai sai usman, tabbas ba sai -71- mutum ya tambaya ba ka san usman ya na zalintar larai, daga ganin aikin Usman makanikane, tun yana yaro ya ke da tabe-tabe, har Allah ya hada shi da wani uban gida na kirki ya koya masa aikin sosai, Usman yana samun alheri sosai amma da gani baya wadata iyali, babu wata alama anci abinci a wannan gidan, daga dakin kadai zaki tabbatar, saboda ba bu ko shimfidar kirki a cikin dakin, ciki daya ne da falo, falon ko leda ba bu, bạn da halin tsiya irin na usman tun da ka rabata da kowa nata aika san baza a yi mata Komai ba, shi ne ka barta cikin wahala. Ba dan yana son Salwa ba ya sata a makaranta mai kyau ya siyamata kaya masu tsada, da sai nace Usman ya gaji mahafinmu. Usman kuka ne kawai bai yi ba ranar, saboda fadan da mahiafinmu ya yi masa, babu abinda ya batawa mahaifinmu rai irin yadda ya bar falonsa babu ko leda don shi babanmu tunda yakema ya na son tsafta, wata al'adar banza da yake kullum idan zai fita sai ya bada kudin abinci 'yar iţa kuma uwar gari zata jika tasha, 'yar kuma a siya mata abinci mai kyau uwar kuma oho, ka ji azzalimi. Ranar dai yaga fada iri-iri don saida baba yace ya je ya dauko duk kudin da ya aje ni kuma ba haka ya nuna masa karuwa sa, yace shi baya nema mata, da aka matsa masa yaje cikin dakin matar ya bude cikin kayansa ya dauko kudi har -72- 1. Π 1 1 1 dubu dari da goma, kaji macuci nanfa akan karkashi daga Muhammad aka rubuta komai, kujeru, leda, kayyan abinci, sabulun wanka dana wanki, katifa tun da gadon babu katifar kirki itama laran kayan sawa, ya na ji ya na ga ni aka ba muhammad da Isa suka tafi siyayya, muka kama hanya mukabar gidan, matar har kuka take don murna, baba ya ce "daga yau ni ne ubanki, ki rabu dasu, kar ki fasa yi musu biyayya addininsu ne dai kar ki yarda ki shiga", har muka fito inna bata yi magana ba. Muka kama hanya zuwa tsohon gidanmu da niyar washe gari zamu je mubi mu duka, karfe bakwai Muhammad da Ibrahim sun zo da matansu, matar Muhammad Rashida da man mun santa ta na zuwa zaman makoki, yaran ne bamu taba ganinsu ba, Abubakar da Amina watau baba da inna, daga ganin Muhammad kasan yana rayuwa mai tsafta da iyalinsa. Ibrahim ma ya kawo matarsa umaimatu ita ma daman mun santa kyakkyawar gaske ga kunya kamar mijinta, don kullum tazo bata iya hada ido da inna, duk tsokanar da za muyi mata bata tankawa, baba ya zo da Isah tun da daman tare suka tafi, har an hakura da jira za'a tafi abar shi sai gashi yazo da matarsa Usman, inaga haushin kudin sa ne ya sa da bazai zo ba oho masa. Duk mai sonmu yayi murna da ganin mu a mubi, baba yaje gurin manyansa, anzo an hadu da kannan inna wanda take gurinsa, an mayar da 73- AUREN INNA DA MAHAIFINMU, ranar asabar da safe kofar gidan su inna ko in ce kofar gidan kannenta duk murna muke, ita dai inna gata nan ni na tambayeta nace "inna me ya sa bakya murna?" tace "gaskiya uwani ba dan ku ba, ba bu abin da zai sa na sake auren wannan mutumin, ba bakya ganin idan kudi suka shigo masa zai sake wulakantamu?" Ni na rufeta da nasiha na ce "inna kamar ki kawo wannan a ranki da fa ace ya ji dadi ne, kigafa-har yanzu ba da hakuri ya ke, ya na nadamar abin da ya yi, ki ji fa irinwahalar da ya sha a baya, insah Allahu wanna zaman na har abada ne, muma mu koma gidan ubanmu muyi aure koma samu namu 'ya 'yan", har na sa inna tayi murmushi tace "Allah ya kawo na gari", su Hadiza suna can suna faman yawo, mahaifinmu ya shiga dakin inna, na tashi na bar shi da amarya da ango su sha hira. Kwananmu biyu a mubi, san nan muka koma gidan mahaifinmu, ya yi mana dinkuna daga mu har inna, abinci kala-kala ba ka tunanin matsala

Chapter 9 of 11