Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya kai karar babanta" Usaina ta kwala ido alamun bata san komai ba, tana masa rantsuwa mamanta ta fito tace: "mike faruwa? Nan bakasan gidan matan aure bane? zaka shigo mana ko sallam babu, da izinin wa ka shigo? To bari na gaya maka kafin ka kai baban ussaina kara shi zai kai kararka, 6 tunda shi a tsarinasa ba'a shigo masa gida bada izini ba". Mamanta ta juyo cikin bacin rai tace da usaina: "ina bandake do shige-shegenki ma ta ya ya za a yi wannan mara hankalin ya shigo mana gida? Kai kuma ka fice ka bar mana gida ina rowan mu da matarka da har zamu barta ta shigo mana gida har mu boyeta? Kaje can inda ka kulleta ka nemota, ka saba dukan 'yar mutane kullm har 'yan unguwa suna jin kukanta shine zaka zo kana wani zare ido wai usaina ta nemo maka matarka, ai masu son matansu basa dukansu lallashinsu suke." ta nuna masa hanyar waje da hannunta, ya fitajiki babu karfi. Maman usaina mutunce mai mutunci wanda babu ruwanta da ruyuwar kowa yadda na fuskanceta koda yake ba fita nakeba amma yadda usaina take bani labarinta duk wanda ya shiga gonarta bata kyalewa don haka Nura yana fitowa ya kama hanya ya tarar su Hadiza sun dawo ita da Sadiya yace maśu wai su fito masa da ni, Hadiza da yake mafadaciya ce ta tashi tace: "kaga karka gaya mana maganar banza yaya zakace mufito maka da Amina bacin mu a gidansu muka santa, sau nawa muke zuwa gidanka sai dai muyi Magana da ita ta windo mu tarar ka kulleta, ko don kaga ba wanda yayi maka magana don da di ya yi maka yawa za kazo kace wai mu fito maka da Amina. Dan Allah malam ka fita, ka kuma fito da 'yar uwarmu don gobe zan zo gidan in har na tarar 1 1 bata nan, sai dai muhadu a station don bazamu yardaba. Nura ya fito yana huci yazo kamar zai tambayi Shamsu ya tarar da masu siyan shayi sunyi yawa don haka ya karasa can gun wata mai kosai ya tambaye zulai mai kosao tace ita rabonta da taga Amina tun kafin ayi mata aure. Cikin sauri da zafin rai yaje ya hau motarsa ya koma gida yana neman mafuta har ya yanke cewar ya daina neman Amina kawai, zai kaiwa yan uwanta takardar sakinta ya dakko biro da takarda ya rubuta saki uku har ya sa a embilan wata zuciya ta gaya masa "idan har ya bar Amina tabarsa to zata iya tona masa asiri tabbas hakan zai iya karshen rayuwarsa, don yasan Amina ta gane sana'arsa gashi kuma bai mata dadi ba, don haka haushin abin da ya yi ma ta zai iya sawa 'yauwanta su zugata ta kai karaarsa police station, don haka yau operation din neman Amina zamu yi, an nan ya dauko bindigarsa zuciya ta yanke hukunci. Karfe ukun dare Nura da abokan aikinsa suka dirkawa gidansu usaina cikin tsoratarwa irin kaga barayi, aka bude musu ko ina suka duba babu Amina, wanda basu nunawa masu gidan Amina suke duba babu, sun nuna kudi suke nema duk da cewa ga kudin amma basu daukaba, soboda bashi ake bukataba, karfe hudu saura kwata suka dawo gidanmu na Yanyan suka tarar hadiza, sadiya, kasimu, duk suna nan suka ringa bi suna cajewa 8 ko zasu ganni duk da badda kamar da Nura ya yi sai da hadiza da karima suka ganeshi yazo bakin kofa zai fita karima ta bude zatayi Magana hadiza tayi sauri ta rufe mata baki Allah yasa bai gani ba ya juyo yasa kafa ya make hadiza yace: "daga ganinki zakiyi tsiwa." wani daga cikinsu yace: "yallabai wannan inaga bai kamata abartaba don inaga kamar tana da magana kamata yayi kafin tace wani abu ace mata" Ya daga bindiga zai narkawa karima Nura yasa hannu ya kare, "rabu da ita babu abinda zasu iya don basuda gata". in Nura ya koma gida kamar tsohon mahaukaci da takaicin bai sameniba bai kuma san inda zai sameni ba don yama yanke hukuncin ya ganni kwai kasheni zai yi don ya san na gudп ne don na tona masa asiri, kwana nura ya tsananta bincike a kaina Wanda nikuma a bangarena ina cen a hospital, nama fara samun bakin magana don haka na sami dammar yiwa Hiajiya da baban kalifa bayin halinda na tsinci kaina tunda nake gidan Nura, ya rubuta tsaf ya kaiwa police report, bayan ya kaine suka neni hoton Nura dan life camp ya kai da haka suka rasa sauran police station kuma sun tsananata bincike akan Nura, sun sha kaiwa gidansa farmaki basa samunsa, don haka aka baza matakan tsaro masu sanin yanda za'a kama shi. Ta bangaren Nura kuwa, bayan ya kaiwa 9- su Hadiza farmaki da su Usaina bai sameni ba duk da haka bai hakura ba sai ya rinka zagaya unguwa akoda yaushe har gida, kai kace wani neman arziki yake min don haka ya daukeshi har gidan Hajiya Amara, yayi sa'a ya sami baban kalifa ya fada masa gaskiya yace "Amina tazo amma kwananta daya ta gudu, suma tashi suka yi da safe suka tarar bata nan don haka su yanzu shawarar su je police station su kai report da hotonta idan anganta," har Nura ya yarda da shawarar baban kalifa daga baya wata zuciya ta raya masa kamar hadin baki ne ana son aikai shine. Don haka ya tashi yace da baban kalifa zai dawo gobe suje da safe, Allah ya kaimu. Ya fita wata zuciya ta gaya masa lallai ya zo operation gidan baban kalifa da daddare su tsanan tashi duk inda take ya nemo masa ita, to shima baban kalifa ya yi wannan tunanin, don haka yaje life camp ya sanar da 'yan sanda. yadda suka yi da Nura da yazo, sukace kar ya sami damuwa in dare ya yi za su kai ma'aikatansu su tsare gidan don kar ya kawo hari. Dare nayi Nura da mutanensa suka shirya suka farmaki gidan baban khalifa kiri-kiri Nura ya tsare baban kalifa da bindiga wai ya gaya masa inda nake in ba haka ba yanzu su aika shi ba shiri, yana cikin wannan magana ne 'yan-sanda suka fado wanda daman sunga sanda suka shiga sun barsu ne saboda suyi musu saukin kamawa, ba -10= don Allah yasa 'yan sanda na da yawa ba da su Nura sun kashesu don dan sandan da ya taba fada Nura lokacin da ya sawa baban kalifa bindiga a kunne yana juyawa ya harbi shi, take ya mutu ko shurawa bai yiba. Nan da nan police suka yo kansa duk suka kamasu suka sa su a mota, da safe baban khalifa da ya je asibiti yake bamu labarin yadda sukayi da Nura, dòn haka a nan take muka nemi sallama wanda zaman gudun kar Nuran yazo ya kasheni ne yasa mukaci gaba da zama a hospital din, sai da nura ya yi kwana uku a police station sannan aka turo neman baban khalifa wanda bayan yaje ne akace masa anan son ganina. A nan 'yansanda suka sakani gaba da tambayoyi, tambayoyin uwa sune: "mai na fahimta da sana'ar Nura? Na taba sanin office dinsa?" Sannan sukace "suna son nagaya masu abokinsa daya da na sani" daga karshe suka tambayeni "shin ina son cigaba da zama da shi?" Nura Ibrahim shine sunana da naji ko nace naga yana rubutuwa tun kafin muyi aure da haduwarmu da Nura zuwa aurenmu har kawo wa yau ina ga zai shekara daya da wata biyu, yallabai kamar yaddan kuka nemeni tunda nake da Nura ban sanshi da wani aboki ba wanda zan nuna tun sanina da Nura shikadai na ganshi har muka yi aure da Nura zan iya cewa lokcin da aka tsahi bakin mu da Nura mutanen da sukazo basu wuce 11- wadannan wanda naga an kamasu tare ba, amma tunde nakeda shi bai taba kai mana suba gidansa don haka nima tun a bikinmun ban kara ganin suba inba yauba. Yallabai, sana'ar nura kuwa lokacin kafin na aure shi zan iya cewa suna'ar da na san shi da ita itace siyan fili ya siyarwa don nima kusan nace office din da nake aiki yake zuwa siyan filaye ta haka muka hadu da shi mukayi aure sai naga abin ya sabawa abin da na sani don kuwa baya fitar sana'arsa sai dare yayi kullum karfe ukun dare yake tashi yayi shiri da wasu bakaken kaya ba ya wuce awa daya biyu yake dawowa sai ya tabbatar ina bacci ni kuma bai san na taba kamashi ba nayi shiru ne don saboda jin tsoron kada ya kasheni in yaga na gane babu kuma hanyar da zan gayawa wani tunda kullum in zai fita kulleni ya ke yi saboda jin tsoron kada ya kasheni in yaga na gane, babu kuma hanyar da zan gayawa wani tunda kullum in zai fita kulleni ya ke yi saboda kar na fita kuma kar wani ya zo wajena, yace "karma na kara barin wani ya shigo masa gida”. Wani daga cikin 'yansanda yace "ya taba gaya miki wani abu game da gidan da ya sakaki, misali ya taba fada miki na shi ne ko na office?" "Gakiya a'a don tunda na zo gidansa wata bakwai kenan babu wata magana ta arziki data shiga tsakanina da shi". Daya dan-sandan yace: "kin taba ganin wani makami a hannunsa?" nace: -12- "sam banda wata binidinga guda daya, ita kadai nake gani kuma tun kafin muyi aure an nemi ya turo iyayensa ya turo wasu mutum biyu manya ya ce "daya babansa daya kanin babansa, mahaifiyarsa kuwa yace ta mutu, yace min su kauyensu yana wajen Kaduna, amma tunda mukayi aure har yau bai kara yarda munyi maganar data shafi hakaba." "Yallabai maganar zama da shi kuwa ina son araba mu daga yau bana son ko hanya mu kara haduwa sai lahira in anzo mana hisabi." Suka yi dariya gaba dayansu, 'yansandan suka tambaye ni "yarinya yanzu kinji wahala kike son rabuwa dashi da ai kudi ya nuna miki yace yana sayarda fili ko?" Inji wani police duk suka sa dariya. Duk maganar da nake yi Nura ya na zaune ya na kallona wani lokaci ya sunkuyar da kai idan yaji na fadi wata maganar ya dago kansa yanzuma tunda nace ina son murabu kwala min ido ya yi har yanzu bai dauke kansa ba daga kaina wanda nima kalon nasa nake kallo na takaici da haushi ina masa Allah ya isa a raina ta wani bangaren kuma ina masa godiya ga Allah da zai rabani da kaya. Wani daga cikin yansanda ya kalli Nura yace: "to kai kaji yanzun matarka ta ce bata son zama da kai don haka yanzu tana son ka saketa ya kace?" Nura cikin karkarwa don kowa ya kalli Nura yaşan ya sha duka ya ce: "to Amina na sakeki, Allah ya baki miji nagari ba irina ba." nace "Amin", bafa don naji dadi bane 13- don kuwa ina tsoron fitowar Nura daga police station don haka nace da yansanda inason ayimini tsakani da nura wanda ko ya fito babu ruwansa dani sukayi dariya sukace ba zai fito ba wanda ya kashe rayuka shima. kashe shi za'a yi Nura ya yi kwalakwala da idanu ya ji ance za'a kashe shi yasan kuma babu mai fito da shi. Ni da baban khalifa haka muka fito muka kama hanya da niyyar zuwa gidan baba Buba mu sanar dashi halin da ake ciki, muna zuwa muka tarar wasu ne a gidan ba shiba wai ya yi ritaya ya koma mubi, muka jiyo duka babu kwarin jiki. Su Hadiza kuwa sun rasa inda zasu same ni don itama hadiza tun sanda Nura ya kai musu ziyara suke ta faman nemana matsalar basu san gidan Hajiya ba don haka babu wnda ya dòshi can, da muka dawo da baban khalifa yace: "ya kamata ki tsaya kiga 'yan uwanki ki gaya musu abinda kike ciki in yaso koda da yamma ne sai ki dawo" yace: "ga wannan kin sayi wani abu in kuma zaki dawo kya shigo mota kin dawo." nace: "to na gode." Ina zuwa na tara Hadiza da Sadiya suna zaune, sai suka bani tausyi saboda halin da na samesu, ina sallama duka suka taso suka rungumeni har hawaye nayi don tausayin mu. Bayan na zauna ne suke bani labarin halin da suka shiga saboda rashin sanin inda nake da kuma irin shigar da Nura ya yi ya zo musu har da police din da Hadiza taje ta gayawa, nima na kwashe duk abinda yafaru har da zuwa gurin Baba Buba da na yi. Bayan nan nace -14- musu yanzu ni da Nura mun rabu. Bayan komai ya lafa, na tambaye su ina karima? Shi ne sadiya ta се tun sanda nura ya zo bata sake kwana ba tana gidan samarinta, sai dai ta zo ta kwashi kyanta ta wuce, ina zaune har la'asar wajen karfe hudu da rabi 4:30 Shamsu yazo daukar kayan shayinsa, da yake dama cen a nan ya ke ajjiyesu, shi ne ma dadin dangantarkar mu da shi, shi ma ya zauna yana jajinta min har yake gaya min ai shi Nura ya tambaya gidan Hajiya, yasa shi a gaba ya raka shi har gidan nan dai na gayawa Shamsu mun rabu da Nura don haka ko gaba yazo nemana kar ya sake yace zai nuna masa inda nake. Biyar da rabi dai-dai nayi sallama da su Hadiza na wuce maraba muka rabu da niyyar zasu kawo mini ziyara tunda ni ina idda kuma kowa yasan a ka'idar musulunci anason mace in har ta rabu da mijinta ana son ta zauna a guri daya har sai ta gama iddarta, badan komai ba aka gindaya mata hakan don cika ka'idar iddar tun ba'a son wani ya gan ki kuyi zance idan kunyi haka kunyi zance kan aure don haka ko tagama idda babu aure tsakanin su. Nayi zama na jindadi da kwanciyar hankali a tsakanin Hajiya da baban kalifa wanda duk iyayen da suke son 'ya'yansu haka za su yi musu, jikina ya dawo nayi fari nayi kyau ranar da iddata ta cika ranar nayi sallam dasu baban halifa halifa sai mubi don gano innata itama innata naga tayi farin cikin ganina don a zaton ta ina nan a gidan mijina don haka abinda akeyi bata sani ba, inna take bani -15- labarin itama daman za tazo Abuja ta ganni ta kuma gaya mana zata yiwa binta aure nan da sati biyu harta tambayeni Nura nace: "yana nan lafiya ban gaya mata kome nake ciki ba har nayi wanka nayi sallar magariba sai dana tabbatar duk kowa na gidan ya kama gabansa ya barni dagani sai innar tawa saboda tausayawa da ya ke tana cikin matan 'yan uwanta don haka tana tare da habaince-habaince irin na matan kauye don gudun haka nema yasa sai na yiwa kowace mata tsaraba da kudin da baban kalifa ya ba ni. Na kalli innar tawa a karo na farko na tausaya mata nace a sanina yanzu idan na gayawa innta nima aurena ya mutu, don haka dole ne na gayamata ban gama tunanina ba ta kalleni tace "kuna dai zaune lafina ko?", Inna babu abinda zan boye maki gakiya yau watana uku kenana rabona da Nura don nagama iddah na kwashe komai nagaya mata tun farkon aurena da Nura har rabuwarnu inna tace: "Allah ya zaba miki abinda yafi alheri”. Inna tace ni yanzu babu abinda yake damuna irin karima tunda nazo garin nan yarinyar nan bata taba kawo min ziyaraba sai dai ni naje kinga yarinyar nan bata taba aika sabulu saboda ita ba balanta ni duk da haka ban tunzur inna ba nai ta bata hakura da kuma shawara duk abin nan da take ta ringa yi mata addu'a Allah ya shiryeta, ki daina sa bacin ranta, fishinki zai iya sawa takara fandarewa. Da irin wanan dadadan maganganu nayi tayiwa inna har ta dan saki ranta muka cigaba da hira kwanana uku a Mubi nadawo Abuja. Tunda na dawo Abuja na gaji na dawo gidan -16- 1 Hajiya don na huta, don haka ina son Bilkisu da Mairo suma su huta, "Bilkisu kin ga magariba ta yi, kin san kuma mama bata son kiyi dare, yanzu sai ki tashi ki tafi gida in ya so kya dawo gobe na karasa muku ko in nasami dama sai kizo na karasa baku labarin ko kuwa Miaro?" Mairo tace: "gakiya haka ne, don ya kamata a ce יי munyi sallah tunda magariba ta yi kafin ki wuce. Bilkisu tace: "Mairo ina hutu" ta na fada ta na dariya "gobe idan Allah ya kaimu karfe goma zanzo don jin karshen wannan labari". Da Mairo dani muka yiwa Bilikisu rakiya har bakin mota. Gaba dayan mu ni da mairo muka yi alwala muka yi sallar magariba muka zauna wuridi har aka yi Sallar Isha'i, san nan Mairo ta je ta dakko mana kula da faranti ina gama cin abinci nace: "mairo gaskiya zafi nakeji, bari naje nayi wanka." Da na fito ne daga wanka kafin nä shiga dakinmu na leka nace da aunty sai da safe, anan ne ta tambaye ni "ina bilikisu?" nace "ta wuce tun dazu mun leko kina toilet" "to baza ki yi kallo ba?" na girgiza kai nace "gaskiya aunty na gaji bacci nake ji". Washe gari tun karfe goma Bilkisu tazo don ni ko tashi ban yi ba, sai naji ana dukana, na tashi naga Bilkisu, "gaskiya kin fiya sammako" "ai dole nayi sammako, don kuwa na matsu nasan abinyi akanki, ai ni kin cuceni, tunda duk tsawon zamana dake baki bani wannan labarin ba." 17- Amina ta tafi ta yiwanka, bayan ta shirya tace da Bilkisu "zo muje mu gaisa da Anuty" da muka dawo daga dakin aunty ne Bilkisu ta wuce mota ta fito da kuloli guda biyu da flask na tea, kulolin waina ce masa, daya kuma farfesu kifi ne shi kuma flask din tea kuma kunun gyada ne hadadde mai makon rowan shayi. Amina tace "ke ki ce da abincinki ki ke tafe." Bilkisu tace "mai ya yi min zafi tunda ina son labarin, dole na cikawa mai bani labari cikinta da abinci ta koshi don kar yinwa tasa ta ringa bada labarin gaibu." Na dauko flate da kofina na zubawa Aunty nata da Mairo, ni kuma na zuba mana namu nida kawata Bilkisu. Bayan mun gama mairo ta kwashe kwanikan ta kawo mana ruwan sanyi, bilkisu tace "wai Amina kafin ki fara bani labari zanyi miki wata tambaya, mai yasa har yanzu bakya gidan Hajiya?" "Kwanana biyar a gidan Hajiya, bayan na dawo daga Mubi na tattare kayana na koma asalin gidanmu Yanyan, inda sauran yan uwana suke, Hajiya ta so ta hanani komawa yanyan don dai babu yadda za tayi tunda ba gidanta bane dole ta hakura nida kaina nasan baban kalifa bazai tasheni ba, amma a tsari ya kamta na koma inda nafi wayo, ba dan komai ba don su Hajiya su ci gaba da zama a matsayinsu na iyayena kar wani abu ya hadani dasu." Kafin na tafi na roki baban kalifa daya -18- samo min aiki, Hajiya ta hada min goma ta arziki, kayan abinci kala-kala. Baban kalifa ya bani dubu biyar tare da nasiha nayi hakuri da halin dana sami kaina kada na yarda shedan ya auręni na koma bin samarin banza, duk abinda nake so nazo gurinsu in Allah ya yarda za su yi min dai-dai iyawarsu. Nayi godiya nakoma cikin yan uwana da zama. Zama na cikin su Hadiza na fuskanci matsala da bakin ciki iri duk kayan abincin da naje da shi har da kudin dake hannuna muka hada muka halaka har da karima, tunda a 'yan kwanakin bata fita ko ina ba, a satin ne karima ta sami aiki munyi farin ciki kamar ba zamu mutu ba saboda lokacin dana same su suna cikin yunwan don babu mai aikin yi duk abinda naje da shi gidan ba'ayi sati biyu ba ya kare, muka dawo kamar almajirai, muna faman cin bashi a gurin shamsu, don ma hadiza tana da wani saurayi bakano to idan yazo muna samu mu biya Shamsu a haka muka zauna duk abinda muka samu mukaci sai mu ragewa karima komai kan-kantarsa ta zo ta samu, amma abin mamaki wata na cika karima ta karbi albashita muka nemeta muka rasa kwana biyar duk hankalinmu ya taşhi sai ana shida sadiya ta ganta a kofar wani guest house ita da saurayinta suna hira, ta karasa kusa da su wai ita mai 'yar uwa, amma mai zai faru, karima sai tayi kamar bata santa ba, sadiya da sauri tace "karima baki ganeni ba? nice sadiya" ta juyo a yatsine tace "na 19- ganeki, menene?" Suka hada ido ita da saurayinta suka kwashe da dariya, sadiya yarinta sai ta tsaya tana kuka, da suka ga zata tara musu mutane suka tashi suka bata wuri, da ta zo gida tana bani labarin abin da karimatu ta yi mata banyi mamaki ba saboda ta yiwa uwarta mu kuma su waye? Kwanci tashi har na kai. shekara guda rabona da aure babu aiki babu kuma miji sai samari yan taya hira, lokaci-lokaci ina zuwa ina gaisheda maman kalifa wata juma'a akan hanyata ta dawowa daga gidan su maman kalifa muka shiga mota daya da wata baiwar Allah muna zaune zaman mota, har muka fara hira itama take gaya min anan yanyan take, yadda ta kwatanta min gidan da take babu nisa da namu gidan, tana fadin gidan da take na gane marar gata ce ko ince mai zaman kanta ce irinmu, don gidan babu wata mai aure, gwara ma namu mu kadai ne. Mun rabu da Baraka akan zamu ringa kaiwa juna ziyara, ita ta fara kaimin ziyara tun washe garin da muka hadu; Baraka irin mutanan nan ne masu kirki, don haka Allah ya ke wasu, tana son mutane, ga kyauta tun haduwa ta da ita bata barni ba na biya kudin mota ba, haka da zata kawo min ziyara sai da ta ciko leda da kayan shafe-shafe hadda alawowi, munsha hira har la'asar ta gayamin ta na aiki a kamfanin lemo, ba ta da aure amma a yadda ta nuna mini bata taba yi ba, a yarda na fuskance ta shekarunta zai kai talatin da uku, don haka nasaki -20- jiki da ita tunda komai ta fini don haka bana tsammanin mummunar shwara daga gareta. A cikin sati guda mun shaku sosai da Baraka kamar mun yi sheharu, in ka ga ba ma tare, to Baraka ta tafi aiki da zarar ta dawo za ta zo, kwanciyar bacci ke rabamu. Wani abu dana fuskanta da ita tana son kula samari kala-kala sannan kananan yara wanda basu kaitaba, kusan nace kannanta 'yanyara wasuma ko sakandare basu gama ba, kirkin da Baraka take min yasa bana son na yi mata mummunan fahimta, sai dai kawai zan iya cewa munsha bam-bam tunda irin samarin da Baraka ke ma'amala dasu narainasu, dan ni ko duniya banza tsakanina dasu aike, aiki lokaci-lokaci idan muna hira da ita, ina bata shawara akan kananan yaran da take kulawa, amma Baraka taki sam, da hakan takance da ni wai kula manyan-maza shi ne ya ke tsofar da mace da wuri, duk da haka ban yarda ba, ban kuma yarda na biye mata ba, sai ran nan da la'asar an gama ruwan sama mun zauna kowa ya takure saboda sanyin daya shigo na yamma ga ruwa. Baraka ta zuba wani abu a kofi daga kicinta ta kawo mana tace "Amina ku sha wannan maganin sanyin da muke jine", na karba ina kaiwa bakina wani irin wari da daci, na furzar nace "Baraka meye wannan" "ke dai ki sha in ta fara yi miki aiki kya ji", raina ya baci nace -21- "Baraka giya ki ka bani gaskiya baki kyauta min ba, don ni ban taba shan giya ba", tayi wani murmushin da ya bata min rai "inda kin san maganin da ke dauke da giya da baki ce na cuceki ba, kin ga dai tana maganin tunani ko wane iri ne, ba wanda zai saki damuwa da rashi aure, tunda kinga ni kaina inda ba dan wannan ba zaki ganni haka ba, ga yadda kika rame, kin damu duk kin zama kamar wata tsohuwa, kin sawa zuciyarki damuwa, mace bata da ranar magani kin zauna baki da aiki sai kula tsofaffin maza, wanda ba za su kare ki da komai ba Sai cuta, banga amfanin namijin da ba zai yi min magani ba, tunda kinga tsohon namiji daga gare ki ya ke neman lafiya, to daman zan je gun wanda zai karu dani, a'a kina wahalar da kankine, Amina duk namijin da ya ce min aurenki zai yi karyane, wanda ma yaron in kina dabai-bayeshi koya aureki, shifa babba tsohon dan iskane kawai so yake yayi amfani da yarintarki na murje ya kara lafiya. "Inda kin kai shekuru irin nawa, da baki hanani hulda da kananan yara ba, don yazu zancen da nake maki shekarata arba'in da biyu, babu wanda zai ce na girmeki, duk kin tsufa". Na yi kwanto ina kallon Baraka na faman lakca, ina rike da kofin giya ni ban sha ba ni ban aje ba. Ita kuma ko a jikin ta ta ci gaba da cewa "ni Baraka Mansur kaunace ta hadani da ke na ji ina kaunarki kawai a raina, mahaifina Alh. -22- Mansur da mahaifiyata Haj. Basira duk kanninsu mutanen Gombe ne, babu talauci ko rashin gata a tare da ni, don mu uku ne kacal a gurin iyayenmu, mahaifinmu ya taba rike controller na costom a nan Abuja, Allah ya bashi dukiya mai yawa yayata wadda na ke bi yanzu haka tana aure a Legos, tana auren tsohon gwamnan sojoji, kanwata itama tana aure a Kaduna, auren manajan kamfani ... yanzu haka ni kadai ce Allah bai ba mijin aure ba, mahaifayata ta tsangwama min, kullum cikin gori duk abin da na dauka a gidan nan sai anyi min gori ni da gidanmu, ba ni da izinin na saka abincin da zan ci, tsoron zubawa na ke, ina karatu a A.T.B.U Bauchi duk san da nazo gida weekend kafin na tafi sai raina ya baci, ni ina son na ringa zama a can amma innarmu bata son ta bani kudi da kayan abinci isasshe, don haka kwana biyu komai ya kare inna dawo karba wani a ringa yi min fada ana fada min magana wai ni mai bakin jini har yau na kasa samun miji, sai in masu miji sun kawo abu na kafa zalama, kinji kamar ba ita ta haife mu ba. Ire-iren wannan takaicin yasa kullum nake tunanin barin gida to keda kan ki kinsan bariki ba kamar aure bane, babu wahala samun abokin yi, Alh. Sanusi shi ne mutum na farko da ya karbi budurcina ta-hanyar zina, yana da mata uku ban san iyakacin yawan 'yaʻyansa ba, yana yawan zuwa makarantarmu wata rana na zo fita a bakin -23- get din fita anan muka hadu ya rage min hanya zuwa cikin gari gidan yayata, a unguwar lemon Hauwa'u, da dare yayi yazo ya daukeni yake tayi min siyayya tarkacen kayan ci, ya kawo kudi dubu goma ya bani, naji dadin kudin nan don haka ko zance gombe banyi ba, washe gari da yamma yazo ya kaini

Chapter 6 of 11