Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
'yan albashi ne ga 'yar gudunmuwar mu don satin biki ba muyi albashi ba" Bilkisu da Abdul suka yi godiya, Abdul yace "kana son kayi mana tsiya ne kawai to karka manta Amina ce bare duk kanawa ne don haka za mu iya da kai" duk gaba daya aka kwashe da dariya. Aminu ya tafi office, Bilkisu da Abdul dinta suka wuce da niyyar karfe hudu Amina zata je su yi bankwana. -91- Aminu ya kai ni gidan su Bilkisu na tarar duk ta hada kayanta tsaf a cikin store, kayan sawa kawai ta dauka. Bayan mun gaisa da mutan gidan, Bilkisu ta dauki Aminu har falon babanta. Alh. Usman ya yi mana nasiha yadda ya kamata, a nan ne Alh. Usman yake ce mana "kar kuga Bilkisu bata nan kuce baza ku fada mana zancen aurenku ba", "Baba Insha Allahu zamu sanar da ku komai." Bilkisu ta jani wani daki a cikin gidansu kayane irin na mata babu abin da babu wanda ya shafi kitchen da kayan jere ta ce "Amina wannan gudummuwata ce, don haka ina son idan zaki tafi ki nunawa Hassan gidan ku don ya kai miki in yaso tunda ga babbar mota nan ta office din Baba sai ya kwashe su a cikinta." "Kai Bilkisu na rasa wanne irin godiya zan yi miki" "a'a Amina ba bu godiya tsakaninmu ai wannan taimakon kai ne tunda burina ya cika ai shike nan." Muka koma dakin Bilkisu ta bani hotuna ita da Abdul babba, ta dauko leshi guda biyu da shaddodi dinkakku ta ce "to wan nan kiyi fitar biki da su ga wannan inji Abdùl ya ce na baki ta shi gudummuwar" "haba Bilkisu banda taki hadda ta Abdul?" "Don Allah Amina kar ki saka komai ki dauka ni da Abdul da ke duka 'yanuwa ne, karki saka komai a ranki, kada kuma muna can idan kina da bukatar wani abu ki yi shiru, ga lamba ta +1280678252 dan Allah ki tambayimu komai ba wai ki ringa tambayar mu lafiyarmu ba, don muma za mu -92- dinga kiran amarya da ango muji lafiyarsu" ita da kanta ta kwashe da dariya mun yi sallama da Hajjiya su Bilkisu, Hassan ya dauke ni don na kasa tsayawa muyi sallama da Bilkisu tunda akace lokacin tafiyar yayi, wai jirgin karfe biyu za su shiga amma tun shidda Abdul ya turo ta tafi gidansa, nima lokacin na fita na kama hanya shike nan na rabu masoyiyata mai kauna wadda ta nuna min kauna da iyayena basu nuna min ba, ba abin da zance da Bilkisu da ita da minjinta ban da nayi mata addu'a. Ina hanya Aminu yayi min waya wai ya tazo daukata nace "ia na taho gida". Hassan ya ajiyeni yace "idan Allah ya kaimu gobe zai rako masu kawo kaya" nace "na gode" Tunda Aminu ya kawo Yusra, don haka yau ba ni da sukuni ina ta faman hidima tun kafin nan, don ma bata zo da yaraba. Ina son halin Yusra saboda dannewa da take, harda cewa "karma yanzu ajamu a sake korarmu" nace "to ku dage da addu'a kar a sake koraku". Ko a yanzu nasan Aminu zai karemin mutuncina tunda lokacin da bani da gata bai kwashi Yusra ya kai mini ita ba sai a yanzu ina cikin gatana duk da ance ba a shedar namiji to inganin zan shedi nawa mijin. Kamar yadda yace, bai zoba sai bayan sallar Magariba, a cikin irin kayan turarukan da Bilkisu ta bani tun kwanakin na dau guda hudu na bawa Yusra, mun rabu muna wasa da dariya. Bayan na idar da sallar isha'I nayi addu'o'i na godewa Allah da ya sako 93- min kunci lokacin daya ya kuma saka min waraka lokaci daya, don yanzu duk inda na juya sai dai godiyar Allah komai ya zama tarihi, tundå duk mai mace fargabarta da mai kishiya shi ne halin kishiyar, ba dole ne ba kana son zama lafiya itama tana so, amma ni cikin ikon Allah ita take son zama lafiya, don haka dole duk fitinata nima na zauna lafiya na kuma godewa Allah da Aminu ya ce ba zamu zauna gida dayaba tunda idan gida daya ne dole wata rana a bata, yanzu fa kullum a marmarce zamu hadu. Aminu ya yo min da waya wai "sunyi magana Inna za a hada daurin aurenmu gaba daya da su Hadiza, don haka ni tun dazu na bayar da aikin buga kati, Amina ina son kema ki shirya next week Sunday ki tare don kin san bazan iya hira ba ace kina gida da aurena”. Ban bashi amsa ba don maganar tasa ta daure min kai, wai har da cewa yana ji kin ti shiru? Nace "Aminu mai kake so nace maka tunda kariga ka zartar da abin da kake so, ai ko kunyi magana da Inna nima ya kamata ka nemi shawara ta" nan da nan ya zafita "Amina idan ba kya so na ki gaya min, wace shawara zan yi dake tun da nayi da nagaba da ke?" "Allah ya huci zuciyarka." Kawai na kashe wayata. Na yi shiru da waya a hannuna nace "idan bama zuciya zamu ringa yi ba, in ba haka ba ai kamata yayi tun da aure dai da shi ne ya nemi shawarata ba wai yace shi ya je ya gama, ni sam na so ya nemi 94- shawara yace da baba yaso a bashi nan da sati biyu saboda zai yi shiri, in yaso su sai ayi musu nasu tunda komai biyu aka tanada don haka bana son a cusa kanmu a cikin harkar. Binta ce tayi sallama, wai nazo inji Aminu. Ko gaisuwata bai amsaba "Amina mai yasa kike so ki mayar min da hannun agogo bayane? Kin san dai bai kamata na nuna gazawataba, ba don haka nema na zo akace an bani, don me zanyi sanyi akan lamarin?" "ni bance ka yi sanyi akan lamarinka ba, amma ni gaskiya anyi saurin amince maka kamar wadda aka gaji da ita kawai sai ace yau saura kwana hudu daurin aure, ai kusan tayi yawa kamata yayi ace kayi kamar wata biyu sannan ace ka fito." "Ni wallahi kin ban dariya Amina, ina son ki kwantar da hankalinki in dai ni Aminu ne bazan wulakantaki ba har abada, nasan kina tsoron mazan nan wanda idan basu sha wahala ba suke cewa dama ana neman kai ne da ke, to ni.Amina ki ga ne duk namijin da zai wulakantaki to daman can yana da niyya, idan kuwa mutumin kirki ne ko ranar da ku ka hadu washegari aka daura muku aure to zai rikeki, ni ina ganinki kamar mai wayo ashe ba ki da wayo?, baki san idan aka dade ana soyayya duk soyyayar karewa take a waje, ba gara muyi aurenmu tun yanzu ba idan muje gida mu karashe, haba amaryata dan Allah ki dai na taurin kai." "ni wallahi har ka bani dariya naji na -95- fahimceka, Allah ya nuna mana lokacin", "yauwa tawan, duk abin da nace aringa cewa to, kinji ko?" "TO." An daura aurenmu ranar lahadi 27th Mar 2005, misalin karfe daya rana AMINU DA AMINA, ALH. RABO.DA HADIZA, KABIRU DA BINTA.Abin gwanin ban sha'awa, Alh. Rabo ya yi kaya kai daya da mu da mazanmu duk shadda blue, abin yayi tsari sosai. Alh. Rabo da Kabiru sun hada party a Abuja Garden, sun sa kaya iri daya Kabiru da Binta, Alh. Rabo da Hadiza ni da Aminu ne ba muyi wani kwalliya iri daya ba, saboda bamu san komai akan tsarin bikin ko kuma nace na sune ba namu bane be. Washe garin daurin aure aka kai ko wacce gidanta, Binta Maiduguri aka kaita yabzu mijinta a can yake, ita kuma Hadiza anan Abuja aka kaita. Baba yayi kokari sosai don anyi musu gado na gani na fada tunda kowacce gadonta ya kai dubu saba'in, duk abin da akeyi a kicin an yiwa amaran. Nan muna zaune a wurin party sai ga Shamsu ya zo yace "Amina ga wata jarida ki gani" ina budewa hoton Nura ne da abokansa wai an kashesu, nan da nan naji duk garin ya isheni nace da Aminu "Ina zuwa, wata kilama zan kima gida" yace "lafiya kalau?" "babu komai" yace "Amina ko mainene bai kamata ki boye min ba, in wani abu ne zo muje daga cikin can ga wasu kujeru can." -99- Mun zauna, to anan ne na nunawa Aminu hotunan su Nura na kuma gaya masa dangantaka da shi, don ada ba abin da ya sani, dalilin kaduwata itace nina yi masa sanadiyar tafiya lahira, Aminu ya ce "Amina, gaskiya gaki kamar mai zuciyar maza amma kuma kina da tsoro, ke kika san iyakacin mutanen da ya kashe, ke kanki kika san niyyarsa a kanki, don haka karki damu kanki ba shi da awani hakki a kan ki. Halinsa ne ya kaishi ya baro shi." Gaskiya na gode da miji gwarzo irin Aminu, ya kawoni yana yi min fada akan shaye-shayen da nake, gaskiya Aminu miji ne, Allah yasa mu zauna lafiya. Ba a tashi daga gurin party ba sai karfe shida na yamma, magariba ta kawo kai, kowa ya kama gabansa. Amare kowa ta kama shiri, washe gari duk suka watse saura ni kadai na rage, tun washegarin da suka tare duk gidan ya gundire ni, naje dakin da kayan da Bilkisu ta bani na ringa dubawa daya-bayan-daya naga duk wani electronics na kitchen babu wanda bani da shi, plates da cokula da tukwane, filas din cin abinci duk masu tsadar gaske, gaskiya dolene na kara godewa Allah nayi dace da mutuniyar kirki kawar arziki, bari ma naje na duba gudummuwar da tace Abdul,kai lallale ina da sake inda wani ya dauke a gurin bikin nan, ashe check ne na dubu dari, lallai masoya sun hutar min da iyayena. Don yanzu zanje Yanyan na zabo gado da kujeru ne -97- kadai ya rage min masu gara kawai. Tunda muka dawo daga wajen party Aminu bai sake zuwa ba sai dai waya, don haka ni kadai naje na zabo gadona da kujeru masu bala'in kyau, dama Baba ya bani kudi dubu hamsin saboda siyan labule da zanen gado, acan na bar gadon nace idan za а kaini anzo a dauka, na wuce kasuwa na siyo zannuwan gado da labulaye iri daya nasa aka dinka min zanin gado da labulaye iri daya, pganin yadda na shiryawa kaina kayan alatu naji har na matsu ranar tarewa tayi. Ban dawo gida ba sai karfe biyar nayi salloli da wanka don na kasa cin abinci saboda gajjiya. Ina bude wayata naga missed call har biyar, biyu Aminu ne daya kuma Hadiza sauran biyun Bilkisu. Ba shiri naje nasa-credit a wayata na buga mata, cikin sa'a kbugu daya na sameta, tana tayi min tsiya wai na manta da ita, nace ba haka bane muna shirin tarewa ranar Sunday "lallai abin ya matso, yau saura kwana uku, ina angon?" nace "nima sai waya yake min kawai"tace kila yana shirinsa ne" nace "nima ina ganin haka" mun dan sha hira har katin ya kare. Ranar tarewa tun da wuri su Mairo da maman Khalifa suka iso don suje suyi je da wuri, amma har sha biyu Aminu bai turo mota ba, da muka gaji da jijra muka yi masa waya yace muyi hakuri yana zuwa, da ya zo babu wata motar kaya babu komai. Ya ydauki Mairo da Maman Kalifa -98- wai suje su ga gida, gaskiya gidan ya tsara komai nasa, babu dakin da ba gado, daki uku da falo duk ya cikasu da kaya, falon kansa ya cika shi da kujerun alfarma, babu abin da bai šaka ba na a cikin gidan, yadda Haj Mairo suke fada har kitchen an shirya masa komai don haka Aminu yace da kayan sawata kawai yake son naje gidansa. Nama rasa abin da zance, to yanzu ya zanyi da gadon da na siya hadda kujeru, idan naje nace su bani kudina ai baza su yarda ba, da na fadawa Aminu cewa yayi "ki bawa Inna ta sa gadon a dakin ta kujeru kuma ta sa a falonta, na falonta ki sayawa Isa, kinga don son kai naku sababbi shi kuma nasa sun tsufa.""to duk abin da kace haka za a yi" "daman ina son in gaya miki yau da daddare su Hajiya za su zo su kawo kayan lefe, ko ya kika ce?" "yaushe su Hajiya suka zo daga Kano?" "ai tun washegarin daurin aure, abin day a hana su zuwa saboda dasu ake ta faman shirye-shiryen dakin naki." Akwatina uku Aminu yayi min cike da kaya masu tsada, set din gwal hudu aka saka, 'yar zobe dozin biyu ta kwance biyu duk dubai, kwal fasion kala biyu da warwaro mai shida, kai komai kiyayyar da kakewa Aminu sai ka yaba da kayan da yayi. Na tare ranar Lahadi kamar yadda akayi, amma sam naki yadda ayi wani party, don gaskiya wahalar da Aminu yayi tayi yaw. Baban Bilkisu ya bada dubu dari biyu a siyamin wani abu, buhu -99- ashirin akayi min goma shinkafa biyar masara biyar gero, maja garwa hudu man gyada ma haka, macroni kwali biyar taliya biyar maggi kwali gishiri buhu biyar shima, dan Baba cewa yayi komai ya yiwa Aminu bai biyashiba. Ranar tarewa yini muka yi da Bilkisu a waya kamar yadda muka yi da ita, anyi mini alkaki, nakiya, tsatssafa, dubulan, aljacagis da tayota. 'yan uwanmu na Mobi duk sun zo saboda sun ji haushi ba a aika musa da na su Hadiza ba. Yau ni Amina, na godewa Allah daya nuna min wannan ranar don ko a mafarki ban taba zaton zan tsinci kaina a cikin wannan halin ba, yau gani ga Aminu na, wanda ya bude min ido, yau ga shi ya aureni ya rufa min asiri, da duk maza haka suke irin Aminu na da sai n ace babu matar barikin da zata wulakanta, to amma an sha bambam, don mazan yanzu idan sun ci moriyar ganga suna yadda ita, sai kaga yarinya karama namiji ya koya mata bariki ya yadda ita tana ta faman wanga ririya daga nan kuma hanya ta bud eta zama abar kyama a gurinsa, bayan kuma shine ya buda mata ido baya ko tunanin tasa 'yar, yanzu wanda ya yiwa Karima ciki ga shi ya cuceta tunda gashi ko saninsa ba a yi ba, kuma gashi su Inna suje nemanta, 'yar matar da Inna ta sani to yanzu babu wanda ya san ko wace ce, sai dai in anje lahira Allah yayi hisabi muga ko waye uban acan. To nima Aminu na haka ya yarda dani, ai Allah -100- kadai yasan halin da zan shiga. Dan haka babu kakkautawa kullum zan yiwa ioyalan Aminu addu'a ta musamman, Allah yak are masa su kamar yadda ya nema, irin maganin matan da Aunty Nafi ta ba su Mairo ta hado min yasani jin kaina kamar ban taba neman mazaba, sai yau zan san namiji, Allah ya sakawa masoyana da alheri don duk da taimakonsu ne na sami wannan matsayin da nake ciki. Yanzu wata na bakwai kenan, hadiza tana da tsohon ciki ita da Binta ni ko batan wata ban yiba, amma kwanciyar hakali tasa na yi fari nayi kiba, idan naje naga yadda Inna da Baba suka canja dadin da nake ji ya isa, yanzu daga su sai Isa da Sadiya a gurinsu, yanzu Isa yana level 3 а university ita kuma Sadiya ta gama secondary school, tana son ta shiga school of nurse, Baba y ace tayi kokari ta fito da mijin kafin ta gama. Ina cikin kwanciyar hankali don Aminu bai taba damuwa da rashin haihuwarmu ba. Yau kwana biyar baya nan, ga gurin da ya tafi babu service din Glo, don haka sai na bude waya na ringa karanta text message din da ya rubuto min, ina karantawa ina jin dadin kalaman nasa, kna farko -naci karo da wannan kalamin Hi! Baby let me tell you a story of how lonely I used to until you come into my life and set my sprit, free U always there when I needed U, U made me real special when I was felling blue. Thanks -101- Baby 100% I care, 20% I nid, 30% I love U, 40% I cherish you, 50% I think of U, 60% I dream of U, 70% 1 admare U, 80% I missed U, 90% I luv U am missin U again. Wannan text din washe gari a gidan nan yayo min da ya fita office. Bari na ga akwai wani da nake so sosai yace "hi! Baby life is like a book which day is a new page, may ur book a best sellers with advantages 2 tell, lessons 2 learn and takes of good dead 2 members. Whatever is meaningful, whatever is beautiful, whatever u desire, whatever brings u peace & joy be yours 2 day and forever" ina jin dadin kalaman da Aminu yake turo min kullum idan ya tafi office, don tsabar text din Aminu har memorin wayata ya cika saboda haka sai na goge wasu san nan wasu su shigo. Na bugawa Bilkiosu waya tana ta faman yi min mita wai cikinta yana damunta da motsi, nayi tayi mata dariya "wace irin mai rikicice ke, an gaya miki a sama mama ta sameki, kwara ku dandana kuji yadda aka haifeku", "ke kin huta" "a'a ba hutu tunda nima so nake, sai dai likita yace bazan haihuba wai mahaifata baza ta iya rike cikiba." Ina ta zuwa Fiad Islamiyya nida Yusra kullum Asabar da Lahadi, abin mamaki wata rana mun'tashi ita kuma Yusrå bata fito daga ajinsu ba ina waje ina jiranta sai naga Baraka da uniform itama tana zuwa makaranta, ban san lokacin da na -102- je na jawota muka rungume juna tace "ta yi aure ta auri daya daga cikin samarinta Ali, anan zone 3 take da zama" "Baraka, kin haihu?", "a'a likita y ace bazan haihu ba wai mahaifata baza tad au cikiba", "daman ina kin taba haihuwa ince ki kai ni inda aka baki magani nima a bani, don na san ko meye tare muka yi, kin san ina jin kokain din nan ita ta lalata mana mahaifa" "nima ina zaton hakan abinda yasa ni abinma baya damuna sosai don Aminu baya Inuna mini damuwarsa." "To ni Alina ya damu amma yanzu yaya zai yi sai dai in aure zai kara" "lallai Baraka kinji haushi tunda kike tunanin kishiya, in da ne ai ba zaki yarda ba amma yanzu baki damu ba." "To Baraka sai gobe kinga kishiyata can ta fito za mu tafi", "gidan ku daya?" nace"a'a muna tahowa tare ne saboda ni ban iya mota ba, sai na zauna a gidan da yamma Aminu ya mayar da ni gida wani lokacin ya na koya min mota, Baraka Allah ya kara shirya mu" "Amin Amina". Yau aurenmu da Aminu shekara biyu, Hadiza ta haifi 'ya mace Amina sunan Inna, Binta ta haifi namiji sunan uban mijnta Ibrahim, Bilkisu ta haifi twins Hassan da Hussaini sun sa musu suna Muhammad da Ahmad, ta aiko min da hotunan yaran renon turawa kamar turawa manya-manyadasu kamar sun fi shekara. Ni kuwa da nawa angon kullum soyayya kara karuwa take, yanzu na iya mota babu inda ban a shiga, don haka -103- ya sai mini mota irinta Yusra 206, ni da Yusra babu wani sabani don ta sake haihuwa ta samu mace, ansa mata sunana ana kiran Mimi,yanzu haka ta kusa dawowa gurina saboda shakuwar da muka yi da ita, munje dinnar ni da sweetie, ina waigawa kawai, sai ga Samira tayi baki ta lalace kamar ba ita ba, tayi kamar zata yi min Magana ko kunya taji ta fasa. Shi ne naje na same ta ita da sauran kawayenta ana ta faman shan giya, na gashesu saboda yanzu na san na fita duk da a buge take, kunyata take ji don ta san yanzu bad a bace "ina aunty Hafsatu?" "tayi hatsari kafarta ta fita, don haka ta koma gida da zama yanzu haka ita a gidan" daman na tambaya ne don na ji komai, nace "to Samira Allah ya sauwake, sai anjima. Ban ko ce mata ga mijina can ba, don nasan halin matan bariki ko ita ko ukawayenta. Yanzu na dawo da Shamsu mai sahayi gidana ya na yi min wanki da guga ni da sweetie na, muna biyansa dubu goma don na san yafi shayinsa da kwanan titi. Allah na gode maka da halin da na tsinci kaina don yanzu babu Surar da bazan iya karantawa ba a Qur'ani, addu'o'i kuwa ba a magana, bana yafa mayafi sai hijabi don haka ko yanzu nasan babu abinda yafi aure daraja, gaskiya Bilkisu tunda ta rabani da jahilcin da nake fama dashi, tunda idan naji ana wa'azi a makaranta, idan naji an tabo irin abinda nayi a baya na kanji tsoron lahira -104- babu wanda nake tasuayi irin karima, kwara ni yanzu na sani na kuma tuba, Allah ka shiryemu baki daya, kasa masu hali irin na mu za su daina kar ce sai an samu miji irin Aminu a'a indai aurene, kowama aka samu ayi hakuri dashi Allah zai bada lada, komi kuma lalaceawarsa yafi bariki, ba zai ki baki abinci in zai barki ki nema to ki aure shi, sakamakon ki yana can lahira, don ita ce madauwami duniya duk ruduce. Allah ya sa mu gane. Zan so naji ra'ayin makaranta, wa yafi baku haushi, tausayi, burgewa da kuma me yayi muku dadi sosai. Na gode masoyana ku saurari littafina mai suna DUK HALINSU DAYA 08035803200 MATA KAWAI -105- An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 11 of 11