Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ko?" Rufa'i ba saurin "Gaskiya zan yi yanke hukunci ba, saboda Aminu dai nasan halinsa tun tuni to ya kamata a ce nasan na matarsa itama tasan irin matar da zata żauna da ita, kaga haka shi ne zai sa zaman lafiya a gaidan, ni gakiya ban ji dadi ba da Aminu ya boye min ya na da mata". "A'a Amina", Aminu yasa hannu ya dakatar dani yace "ni ban boye miki ba tun da ki ke kin taba tambayata, ace kinsan ina da iyali, saboda mutum kamata ban rasa ci da shaba ina da wadata gwargawdo ace na kasa rufawa kaina asiri, don aure rufin asiri ne tunda yana dadawa mutum mutunci idan za ki tuna dama inason rufawa kaina asiri, tun da nace inason rufawa kaina asiri tunda nace ina sonki, da aure na nemeki, don an hana ni ne bayan nan ban dade ba na yi aure. na don haka tunda yanzu kin kawo hujjarki ta son kiga matata zan kaiki har gaidana kiga iyalina itama ta ganki, Allah-ya kaimu Abuja zan kai ki har gida kiga Iyalina, inyaso sai mu tashi daga inda mukatsaya. Muka yi sallam da Rufa'i ya bani kyauta a leda munyi sallama da Umma da mutanen gida munsha tsaraba kya-kaya. Bamu bar mubi ba sai karfe sha biyu na rana, tunda muka taso Aminu yake ta kwara gudu ba mu tsaya a ko ina ba sai a Fadan Karshi, mukaci abinci muka yi salloli nan ma muka kama hanya, nan ma muka kama hanya, nayi manakin zuwan Aminu da wuri mubi don ranar juma'a ne, nan ya ce "wai ai ya fito biyar na asuba."Bamu iso Abuja 41- ba sai karfe goma na dare. Kowa ya gaji don haka sallah kwai muka yi kowa ya kama makwancinsa, kajin da Aminu ya siya mana babu wanda ya taba ko wanka kasa yi muka yi, da safe Aminu kafin yaje office ya biyo ta nan don ko tashi ba mu yi ba, mun yi sallar asuba mu koma bayan ya sa an táshe mu yace daman yazo ne ya gaya min na shirya idan ya dawo da yamma zai zo ya dauke ni ya kai ni na ga iyalinsa, na ce Allah ya kaimu, tun lokacin bacci ya kaurace min, ni kadai na saka wannan na kwance wancen, wajen karfe goma sai ga Baraka, nayi makmaki don da sauri na tambayeta "me ya kawo ta? yanzu ina office din?" tace "wai tana hutu taga kwana biyu" nace mata 'jiya muka dawo daga mubi," munsha hira irin ta kawaye anan nake gaya ya mata Aminu ya ce zai aureniduk da nasan Baraka bata son Aminu, na fada mata ya na da mata da yara biyunan da Baraka ta hau fadawai bani da hankali zan auri mai mata har da yara biyu ai na daukowa kaina aiki, ina zaton zai so ni ne ya na kai ni gidan sa shi ne zai fara tona min asiri bacin ya san komai nawa ai ita ko ba shi ida mata ba za ta aure shi ba tun da ya san asirinta ba bu yadda zata auri wanda ya san sirrinta, wanda da kansa zai zauna ya gaya mata sirrinki, gorima ya isheki a tsakar gida duk motsi a ringa cewa karuwa dan haka ni dai shawarata karki fara shi yasa ya matsa miki ya rabaki da gidana don ya cusa ki gidansa ya hada ki da wahala in aure ki, ki so ki nemi wanda bai sanki ba. Ba wanda yasan kiba tun kina -42- yarinya. Haka muka kare hirar mu da Baraka ta kama hanya ta tafi, masifatuwa Hadiza tana jinmu, ina dawowa daga rakiyarta tace "to ta kaiki ta baro, don ita tarasa shine take son ta hana ki naki a renko? Ina zaki?, zauna kiyi tunani gwara ki zauna Amniu shi yafi kowa sanin sirrinmu, amma duk da haka bai yi kyamarki ba yace yana sonki babu abinda mahafinmu bai yi ba akan idon Aminu, amma yace yaji ya gani, idan zai tona maki asiri tun yanzu zai fara ga iri halin daya fito dake daga gidan duk da haka yana manne dake don so kawai, banda husuma irin na mutane menene aibun mai mata tun da ya rike an gani ai yafi lalube a cikin duhu, duba duk wahalar nan da Aminu ya ke miki bai taba cewa zai dauke ki kuje yawon banza kamar sauran samari, ai Wallahi Amina babu rufin asirin da yafi namiji yace zai auri mace mai zaman kanta don ya rufa mata asiri, don kuwa rufin asiri ne babba, banda rufin asiri Aminu idan ya aureki har jahadi yayi, tunda ya fitar dake daga kangi." Nasihar Hadiza ta shigeni don haka ni yanzu na barwa Allah zabina kawai. Kamar yadda mukayi da Aminu magariba nayi sai gashi na yi kwalliya dai dai gwardwado nasa wata Holland fara da Aminu ya yi min lokacin da zamu tafi mubi nasa Hadiza ta shirya tsaf, doguwar riga ta sa, ita ma Aminu ne ya siya mani, tun daga nan na fara yiwa kaina fada nasan Aminu gatan mune tunda daga ni har kannena mun zama akarkashin Aminu, Rufa'i abokin Aminu a ledar da -43- ya bani turarrukane guda uku da man shafawa "SoWhite" set na dauka cak da niya nima naba matar Aminu. Bamu zame ko ina ba sai Asokoro Aminu ya yi hon maigadi ya bude kofa, katon gida harda gareji tun daga falon na fara tsorata ganin yaran Aminu da suka zo tarare kai kace 'ya 'yan turawane saboda kyau ga fara fat, tabbas kowa yaga yaran nan yasan uwarsu mai kyau ce dan duk cikinsu babu mai kama da Aminu, kamar ba 'ya' yan sa ba ma wanda zai ce Fahad da Fairus ba yan biyu ba ne, ina ta sake sake Yusura ta fito tace manyan baki sannunku da zuwa ko gama gaisuwa bamu yi ba har an cika gaban mu da kayan ciye-ciye, ba bu ko shakka da kallan Yusura kasan ta hada iri da shuwa ko fulanin asalin, don babu makusa a jikinta doguwa fara siririya hanci kamar ka tureshi ya fadi, da gani akwai natsuwa a tare da Yusura da alama tana da zurfi ilimi. Basai ka tambaya ba kana gani ka san akwai tsaftatacciyar soyayya tsakanin wadanna ma'aurata. Aminu ya kalli Yusra "Uwargida ga amaryarki" ta kalleni tace "Allah ya bada zaman lafiya, Allah ya sa mu zauna lafina idan ta zo", koba har ranta take maganaba ai naji dadi, don kuwa idan kissace ma to ta gwanance ida makirceine to karatunsa tayi, gaskiya da duk mata haka suke kamar Yusra da kudin boko ya huta, mun sha hira da barkacwanci da Yusra da Aminu, Hadiza kuwa tana ta fama da Fairu wajen tambayoyi, muna zaune har tara tayi muka fito, nazo mota na dauki ledar dana -44- kawo mata naba Hadiza nace ta ashe itama ta na can tana faman nata hade-haden tazo har mota ta kawo mata tace "Amina ki rike amana karki yaudari Aminu kinga tsakani da Allah yake sonki ina fatan baza a same ki da rashin birki ba." Tabbas mata masu danne kishi irin su yusra abin sone da dai nasan bazan iya ba ko banza yayi amfani a illimnita ta daure kishin ta wanda ko wane namiji zai yi alfahari da mace irin Yusra wanda take daure fitinar ta, mun biya ta Natalizer mun yi take awy na chicken shawarma da ice cream, bayan mun dawo gida mun dade da Aminu muna hira yana tambayata "yanzu yaya nake ciki tunda nace sai naga matarsa, to naganta meye ra'iyina?" Na saki murmushi "Aminu gaksiya na yaba da Yusra matuka, dole ne kayi alfahari da ita, Allah yasa nima idan na shigo gidan, nayi koyi da hali irin nata sweetheart, kuma ba sai ka tambaya ba ka san ina sonka tun tuni, na san bani da miji sai kai don haka ka ya femin abin da nayi a baya in sha Allahu zaka sameni mai ladabi da biyyayay a tare da ku" cikin jin dadi yace "amin, amin, aminu" yace "gaskiya Amina ba wani abu bane ya sa duk inda ki ke a duniya zan neme ki in kin yarda zan aureki, saboda tun tuni daman in kin tuna da aure na nemeki mahaifinki da shedan sune suka sa har ta kai ni da afka miki, dan haka na dade da yin nadama, Amina hakan da na yi miki shi yasa bana tsantsanin duk halin da na ganki, kullum ina zargin kaina dan ni na jawo miki tunda ni na bude miki ido. 45- Na riga na yi tunani naga babu abin da zan miki ki ya fe min, irin na aureki don Allah Amina ki rikeni da amana nida iyalina, don Yusra bana jinta don ban boye mata komai akankiba da saninta na dawo na nemeki, kinga yanzu in zakiyi tunani ni ne mutumin da nafi kowa can-canta da na aureki duk wanda za ki aura bayan ni basu san iyayenki ba, don haka zasu yi miki kallan marar gata ni kuwa kin ga nasan kina da gata. Kinga idan kin zo zan saka ki a islimiya kamar yadda na saka yar uwarki." wannan shi ne an sosa min inda yake yi min kai-kayi nace "daman Yusra bata aiki?" ya girza kai yace "sam bata aiki, islamiya kawi take zuwa ta dai yi karatu kafin tazo gidana, amma bata zuwa ko ina sai islamiya Monda to Friday, yaushe Amina zan bar matata take aiki? sam bazai yiyuba ina da kishi don haka bazan bar matata ta ringa cakuda da maza tunda ina aikin office ina ganin yarda akeyi". "Amma gaskiya Aminu kana son kanka da yawa, ai tunda kake kallon matan wasu kaima sai kayi hakuri a kalli naka" "a'a Amina karki yi min sharri bana kallon matan kowà, ni duk duniya akawai dan gata irina wanda Allah ya yiwa baiwa. kiga fa irin baiwar da Allah yayimin da mata kyawawan mata kamarku, dan haka babu wasu mata da suka isheni kallo", "Hm Allah yasa maganar da ka ke fada har cikin zuciyarka", "Amina ya kamata ace ke ce mutum na farko da zaki shedeni" "hakane, ina maka wasane na yadda da -46- kai". Ina ga nin mun kai karfe goma da rabi muna hira da Aminu na amince zan auri Aminu dari bis dari don na auna naga duk wahala gara zama da Aminu akan zaman da nake yi yanzu in da Aminu ya kubutar da ni, bansan irin halinda zan sake tsaintar kai na ba tunda gashi a dalilin Aminu Baraka ta daina kulani, sam in ban da ta tsaneshi ne, da haka nayiwa kaina fada tunda in zan tuna labrin Baraka, rashin samun miji ne ya sa ta zama 'yar bariki, duk kawayen mu wanda muka shekewa da su kowacсе ta shirya ta kama gabanta, su maijidda tun yaushe sukayi aure, ai naje auren kowacce duk cikin su babu wacce ta samu miji irinAminu na. Wata nayi Aminu yazo nace "na amince yaje ya sami inna da mutanan sa ayi maganar aure" yace "to nagode Amina sai dai akwai hanzari, ba gububa ina son ace baba mahaifinki shi ya daura mana aure ko ace bazai dauraba da yardarsa" "Hm!!!" wata doguwar ajiyar zuciyar na yi kana nace "Aminu, kai yanzu kasan inda zaka sami baba? Gaskiya ko ka sani nasan abinda bazai yiyuba kenan, inaga aure yanzu basai samu ba, tunda kai kafi kowa sanin yadda muka rabu da mahaifinmu, don haka na tabbata har yanzu mahaifinmu yana nan kan bakansa, ni dai ina son ka janye zancen neman mahaifinmu, idan Allah ya yi zamu hadu wata ran zamu hadu, idan kuma sai a lahira to Allah yasa mu dace." "Amina naji maganarki, amma sam ban yarda da maganarki ba, ku mata tunaninku kadan ne -47- abinda nake son ki gane anan shi Uba Ubane don haka abinda yayi muku dole ne ku nemeshi tunda ya haifeku tunda ke kin taba ganin inda akayi ado da uwa sam, Iba ki ji hausawa na cewa da ubanka ko gyartai ne shi ne ubanka, Amina ba'a sake uba idan, ana sake uba me ya sa ba'a kiranki da wani sunan ina kowa ya tashi Abubakar din nan da shi ake amfani, bari na gaya miki in ba dan na sanki tun kina yarinyarki da ba bu yadda zan yarda na aureki band san mahaifinki ba, don ko` kin ce min ya mutu dolene ki nuna mini dangin mahaifinki ko sau dubu ki ka nuna min mahaifiyar ki idan ba ki nu na min mahaifinki ba babu-yadda zan amince, abinda zan dauka ke 'yar-rariya ce baki da uba, to kinga duk wanda yake son ya shiryawa kansa arziki dolene yanemawa 'ya 'yan sa uwa ta gari mai Asali. Dan haka Amina nida kaina zan nemo inda mahaifiku yake, in ya so zan zo na dauke ku muje ku kuma kuroke shi gafara duk da kuna ganin ya yi muku laifi, tunda ya koreku, sannan muyi masa zancen aure idan ya yarda to idan yaki kamar wance sai mubi ta wata hanyar mu nemi wanda muka san zai bashi hakuri har sai ya amince sannan muyi aure ya kikace?" "Naji ban amince ba, inaso abani kamar sati abin da na yanke zan fada maka", Aminu ya yi murmushi yace "ba bu damuwa za'a baki ranki ya dade ko wata kika ce za'a baki ballantana sati, Allah ya kaimu". Ya mike ya je yashiga motarsa, nasan ransa ya baci yá danne ne kawai, kamar yadda na nemi sati guda, Aminu bai zoba bai kuma aiko da -48- wani dalilinsa ba, tunda duk bayan kwana biyu yana aiko abokinsa da ya ke unguwar mu, ya kan aiko da kudi ko da kayan abinci da kayan cefane, amma babu ko note ballantana wani bayani mai gamsarwa, nasan dama fushi ya yi to ni dinma haka, don a cikin satin nan na ziyarci maman kalifa inda nayi mata karyar tafiya ce mubi ta sameni babu shiri shi yasa taga shiru bana zuwa, a karyar tawa har da cewa jiya don naga har tana tambayata ya umma nace tana nan lafiya kalau. Ban boye mata komai ba game da Aminu har nemana da ya yi daga farko mahaifina yaki yarda muka rabu dashi, yanzu yace sati amma sam ya share tunda na dawo daga mubi yaki zuwa, don karta dagoni nace tanda nadawo daga mubi. Hajiya kamar yadda ta saba tace "Amina ina son ki gane aure nan shi ne mutuncinki, kuma Aminu yana da gaskiya da ya ce zaije gurin neman mahafinki, yanzu abinda na keso da ke, ki kwantar da hankalinki, idan ya gano inda muhaifinki yake to mu da baban kalifa sai muje mu gan shi, muje masa da maganar auren, idan yace ya amince, kema sai mu kai ki ku sasanta, idan kuma yana nan akan bakansa sai a kyaleshi aci gaba da addu'a har Allah ya kawo karshen abin sai azo baban kalifa ya daura ko kuwa?, Idan kuma Aminun ya kafe akan sai ya yarda zai aureki, to sai muzuba masa ido muga abinda zai biyo baya ko ince muga yadda zai yi karki damu Allah yana tare damu ke dai ki da ge da addu'a. Ranar da kwana bakwai yana cika Aminu yazo yace dani "ya ya nake ciki don shi yana nan akan bakansa". Haushi ya zomini wuya nima nace "ina nan 49 akan bakana, inaga bai kamata ka matasa aka maganar babana ba tunda ni bashegiya bace, idanzaka tuna da shi ne ya koreni bani na kori kai na da kainaba, don haka da yana bukatar mu yasan inda zai nememu don haka idan har in da gaske ka ke tsakani da Allah kakesona ai ni zaka aura ba mahaifina ba, abu mai sauki ina ganin ka je ka nemi baba buba ya daura mana aure nidai tawa shawarar kenan." Aminu yace "to naji taki shawarar sai dai munsaha ban ban ana, amina kamar yadda kike ganin babu wanda ya isa ya cenja maki ra'ayinki haka nima don haka zabi ya rage naki, in kina ganin kin kafe nima haka na riga na gayamiki bazan aúre ki ba saida yarda mahaifinki kinga tafiyata wacce kike ciki kya nemini". Haushi ne, takaici ne duka babu wanda babu, don haka na yi kuka na share, nayi alkawarín nabar Aminu har abada, tunda tun yanzu haka har tana faruwa a tsaknin mu, nasan idan munyi aure abin haurshin sai yafi haka, don gwara da ya nuna min tun anan nasan idan aure na ya yi, akan kankanin abu zamu ringa batawa dashi tunda yana da kafewa ni dai nan na fishi gaskiya, da ace baisan iyayena ba in ya fadi haka to ba zan ga laifinsa ba, idan ba ya sona a fasa auren, ya dada cewa daga bangeran mahaifina aka samu matsala, mai yasa zai kafe, to yaje na hakura, Allah ya kawo mini rabona, don ma banda kaddara ina zan iya da wannan makirar -50- matar da shi ni ba kowa ba, ba kuma 'yar kowa ba na cusa kaina inda akafi karfina, ni daman a tsorace nake dan na san ina aurensa, zai koma gindin matarsa da 'ya 'yansa, ya zauna ya ajiye ni a gefe, tunda ni na şan ba haihuwa zan sake yi ba, ko haihuwa zan yi yaushe zan haifi 'ya 'ya kamar wadannan yaran masu kama da 'ya 'yan larabawa. Duk kukan da nake Hadiza da Sadiya su na kollo na ba bu wanda ya ce da ni ci kanki, haka na ci gaba da rayuwa kamar da, don yanzu kusan wata duga Aminu bai zo ba, bai kuma aiko komai ba, don haka mun koma buga-bugar mu, tun da bakin da Allah ya tsaga ba zai ha na shi abinci ba, irin kudin da Aminu ya ke ba ni na hada dubu goma na siyo indomie da kwai kiret goma na ce shamsu ya rinka sayarwa yana aje mana riba, to wannan ma yana taimakon mu sosai tunda muna cin abinci ko ba dadi kamar da. Hadiza ce muna cin abincin dare tace "wai don Allah Amina yanzu me ya hadaku da Aminu?, Kusan wata guda ba labarinsa, ni da na san office dinsa da naje na bashi hakuri, na sanki da zafin zuciya, don haka ba sai na bincika ba, na san halinki, tunda Aminu tun kafin ya aureki ya ke son ki, idan kuma zugar Baraka ne har yanzu, to ita ta zagaya ta aure shi ta samu tsuntsu daga sama gasasshe Allah ya bata." "Hadiza na gaya miki ke yarinya ce, ba bu 51- wata Baraka da zata zugani akan Aminu, yaushe rabona da naganta ma, kamarki ki alhakinta ki rage mata kaya, Aminu halinsa ya hadani da shi tunda shi idan ya kafe akan abu ba bu wanda ya isa ya canza masa ra'ayi, don haka ya sauka lafiya Allah ya kawo min wanda zamu zauna lafiya mu ringa ba juna shawara." Ba'ayi cikkaken wata biyu da rabuwar mu ba, naje gidan maman kalifa na gaya mata yadda mu kayi da Aminu da dalilina na saurin yin fushi, tayi min fada sosai akan na ringa hakuri, muna zaune ne baban kalifa yazo ya ke gaya mini ai yanzu daman zai sa a nemoni don ya samo mini aiki. Shi ne office din da muka hadu da Bilikisu, shi kuma wannan gurin abin da ya sa nabar gurin saboda ogan nawa yana matsa min, lallali yana sona yana son ya mai dani matarsa, matarsa ta rasu ni kuma na ki sam, dan bana son irin wannan rashin kama kan kullum in ganin 'yammata kala kala ana fita dasu, don haka nan danan muka fara fada da shi, tunda na kwanta rashin lafiya sai ya aiko min da takardar kora daga aiki, nima kuma ban je ba ballantana na bashį hakuri. Duk da cewa ya na jin haushi na naki bashi hadin kai, amma ya hada baki da wani bazawarina, wani tsahon mutum a kalla zai kai shekara sittin da biyar, haka a yadda ya gaya min, matarsa ta mutu ta bar shi da 'ya ‘ya, yana zaune a kaduna, anace masa Ambasada, ya nuna kamar -52- zai aureni, to shedanci yasa na afka cikin wannan wahalar, don watarana yazo Abuja ya sauka a Nycon, na san dakin da yake sauka don haka dana tashi daga aiki sai na wuce gurinsa na gaya masa ba ni da lafiya na sha magani, ina son zan kwana a gurinsa. Ransa bai soba don haka ya bar min dakin ya dawo falo yana karatun Al-Qur'ani, a haka muka kwana, washe gari sai na dada langwabewa tun da babu in da zani ya dada komawa falo, sai na biyoshi falon na ringa aibatarsa har na sami kansa ya afka min, to tun daga wannan lokacin ya mayar dani kamar matarsa, duk lokacin da shedan ya gaya masa sai ya kirani idan yazo Abuja, ko kwana nawa zai.yi tare za muyi sai ya tafi zan dawo gida, hartakai ta kąwo idan bazai sami zuwa ba yana turowa in je Kaduna weekend ya kama min daki, saboda yaransa ba na zuwa gidansa, to da haka sai ya sa ni a gaba kullum yana cikin waya office din mu kar na fita, yasa aka samin ido ban isa na kula kowa ba sai ya ji, mu yi ta bala'i ya sa ye wani abokin aikina na zama bani da sukuni nawa na kaina, da haka ya samu ya shiga gurin ogan nawa, to daman abinda yake nema, don haka ogan ya danne kishinsa ya sani a gaba ko waya aka bugo min sai ya ji wa ye, sannan zai bari na dauka to da haka suka koreni daga office din, yanzo kuma ya gujeni bai aureni ba don yanzu bana ganinsa sam". "To Mairo da Bilkisu kun ji dalilin su -53- Samira suke mini wulakanci, su ma gani su ke su suka dace d asu zauna da aunty Rahma ba ni ba, ita kuma ta ki saboda shaye-shayensu", Bilkisu ce tace "wai sannu Amina kin wahala, babu laifi amma wani abun hadda zuciyarki don in nice ke ba bu abin da zai hadani da Aminu, zanbi shawararsa, sai dai mahaifinki tunda shi ya haifeki ke ya kamata ki nemeshi bashi ba, don yansu ina da abin yi akanki idan harkin yarda, na farko kibar gidan nan dole, na biyu ni da babana zamu biyo sawo dole a nemo inda mahaifinki yake, ko da ba za ki auri Aminu ba ya kamata kiyi aure, ballantan Amina kin yi kuskure Aminu shi yadace daki aura tunda ya fada miki. gaskiya duk mutumin daya ganka a wannan yanayin yace yana sonka haka toba karamin masoyika bane." "Bilkisu mahaifina kuwa nasan inda yake har gidansa na sani ka wai zuwa ne bazan yi ba, su sadiya idan sun hadu suna gaisawa, amma ni gaskiya ban taba haduwa da shi ba, yanzu dole ne na koma Yanyan da zama don Karima tana nan bata da lafiya duk wasu kuraje sun fito mata tana fama da mugun ciwo ciki, don haka na ke son in koma don in taya su Hadiza jinyarta, tunda baka kula ta mutum, ko yanzu idan za tayi bankali ai tayi tunda tafi wata shida bata je Yanyan ba, amma da ciwon ya kamata sai suka dauke ta suka. kaita cen." "To ku ga idan tana da tunani bata da -54- kamar mu, tunda abokan harkar ta ta kowa ya gujeta, yanzu ma idan naga komai ya yi zafi zuwa zan na dauko Inna, tunda babu yadda za ta yi da ita, ita ta haifeta dan haka yanzu ina son duk wata magana a barta mu gama da shifin karima tukuna" Bilkisu "tace gaskiya." Mairo ta nunfasa tace "Amina saboda kaunár dake tsakanina da ke, zanje can na taya ki kula da karima kafin innarki tazo", ban san lokacin da na fada kan Mairo na fashe da kukan murna, mum samu uwa, na hada sauran abin da aka bar min na koma Yanyan ni da Mairo. Bilkisu ta ajiye mu ta shiga ta ga yadda Karima ke birgima akan katifa, tace za taje gida tunda dare ya yi zata dawo da safe. Abin mamaki shi ne koda was aunty Rahma bata nuna damuwarta na barinmu gidan, ba wai daman ta sani tunda taga kwanan nan kullum muna daki muna kus-kus harda cewa "mairo ai sai ki bari na mayar dake inda na daukoki tunda daman amana aka bani", Bilkisu dake yar bokoce tace "a'a babu komai aunty Rahma na ajeta, na hutarsheki" muka biya muka yi wa aunty Nafisa matar kinin Mairo bayanin komai sannan muka wuce Yanyen. Karfe takwas na safe sai ga Biliksu tazo don ni ko tashi ban yi ba saboda ina fashin sallah gashi mun kwana bamuyi bacci ba saboda ihun da Karima take. Bilkisu na zuwa ta ce "to kuzo muje Hospital, National Hospital ya kamta a kaita" nan 55- kuwa muka dosa da karima, ko taka kafarta bata yi, sai da ma'aikata suka zo suka dauketa. Nan da nan aka shiga daukan jini, fitsari, kashi, harda yawunta sai da aka auna ckin minti talatin aka zo da result wai tana dauke da wani ciwone a cikinta, shi ba HIV ba, yawanci mata na daukar ciwone a wurin mazajensu, don haka ta samu ne wajen mijinta. A raina nace "wajen samarinta dai" duk mun damu, likita yace zai yi iya kokarinsa amma wai abun ya dade ajikinta don haka saukinsa sai a hankali. Duk kuraje sun cika mararta ganin yarda take faman ihu a hospital din sukayi ma ta allurar bacci duk wahalar da ake yi Bilkisu ta ke yi, don mu babu mai ko sisi a cikin mu. Abincin da zamuci damu da karima duk Bilkisu ta kawo mana, 'yar isaka Hadiza ko kusa da mu bata zoba wai tasan HIV ce, dan haka bata aike taba, tun a gidata bar mana daki da ta ho Asibiti, Sadiya ce ta fito da komai na dakin ta wanke komai wasu kuma ta baza a rana wai karta dau ciwo. Mun wuni muna sintiri a Nationa Hospital, asibitin da inba dalilin Bilkisu ba, sai dai na shiga dubiya don duk Abuja babu hospital mai kudinsa da kyauta. A hospital din gwamnati kwanan mu uku sai ciwo ya yi kamar ya tafi sai ya dawo, likita ya yi kirana yace "idan muna son ta warke sai anyi mata operation an yanke inda ciwon yake don ya dade a tare da ita, amma sai mun bada kudi dubu -56- dari da hamsin", nace "to naji na dadi ma da Bilkisu bata nan ya fada, da na rasa inda zan sa kai na", don haka da safe Bilkisu na zuwa na ce" zanje mubi na kirawo Inna don ta ga halin da karima take ciki, san nan itama Mairo ta samu taje gida," Bilkisu bata gaji ba ta dauko dubu biyar ta bani tace "sai kin dawo". Ban je mubi ba sai karfe tara na dare, Inna ta ce "Amina da daren nan, har hankalina ya tashi", nace "Inna babu komai motar dare

Chapter 8 of 11