Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
baki su, kuma nawane. Hajiya dubu goma sha biyune, a'a a'a a'ah! Hajiya yaya kike bude baki haka? harda rausayar da kai? to Bilkisuce ta bani jiya da amuka tafi daga nan na rakata gaurin babanta ta karba ya bani dubu goma taban babanta kuma ya bata dubu biyu yace ta bani na shiga mota. kai! Kai! kai 'yata wadannan mutane masu mutunci 'yan wane garine? kuma a ina kika sansu?. Hajiya kenan zaki shiga wanka amma har kika kagu kiji labarin Bilkisu to ki bari sai kinshirya mana. Ina Amina bawani shiri, kawai bani nasha, To Hajiya. Su Bilkisu dai mutanen kano ne, Alh. Usman Dan batta shine mahaifin Bilkisu shi wannan bawanAllah mutumin kirki ne kwarai fiye da tunaninki, Danbatta wata karamar hukuma ne a jihar Kano, kamar yadda 14 ta taba gayamun waida Babanta Custom ne. amma yanzu ya dade da barin aiki, yan zu ofisshin kansa ne dashi a wuse II inda yake saida motoci inaga mafa kamar zakisan wurin don kusa da office dinsu Babana Khalifa ne, wani wuri da ake saida motoci an rubutu USMANIYYA MOTORS, ke! ban tari numfashinki ba shine babanta? Hajiya shine babanta a ke ko dole tayi kyautar dubu goma Hajiya tana fada tana kwantar da kai, nace wallahi Hajiaya har kin ban dariya. Hajiya Hafsatu itace mahafiyarsu itama mutumiyar kanoce, babanta tsohon alkali ne anan unguwar kan karokfi kamar yadda Bilkisu taga yamun mahaifi yarsu tayi digirinta, anan B.U.K tayi karatun tana Account don haka yanzu tana aikinta ne a 'Bank of the North' su Balkisu su uku ne a gurin Hajiya Hafsat da Alh. Usman. Bilkisu itace babba, sai kannanta Hassan da Hussaini wandan da suna nan suna makarantar sakandire yanzu haka Bilkisu yarin yace data gaji arziki gaba da baya don haka tasan darajar mutane, wani abu da yake burgeni da Bilkisu tausayi, duk inda kike tunanin mutum mai tausayi kika sami Bilkisu to koma ki zauna. don kwa nasha garin haka muna tafe da Bilkisu idan taga Almajirai sai ta tsaya yta basu sadaka, kin san wanbi abu Bilkisu har kayanta na sawa take ajewa a mota don intaga almajirai a hanya ta basu, wani lokacin kuma ta kanje Area 1 wajen masallacin nan ta rabawa almajirai kayan sawa da kudi, kar kice kayan tsafaffi a'a masu tsada kuma basu yi komai ba haka take rabar dasu. 15 Gidansu Bilkisu kuwa yana nana a maitama ta wajen federal Housing in kinbi kamar zaki shiga kwanar maitama store to sai ki mike kwanar farko shine gidan Bilkisu, watan Hajiya gidansu sama da kasane kuma bangare biyu daya bangaren Hajiya ce da Bilkisu da 'yan aikin gidan mata, daya bangaren kuma Alhaji Usman da Hassan da Hussaininsa, gaskiya Hajiya tunda nake a cikin garInnan na shiga gidaje da yawa amma ban taba ganin gida mai tsarin gidansu Bilkisu ba, babu abinda babu a cikin gidan nan, abinda yafi bani sha'awa sai yanda sukayi wajensu dana yaransu, a bangaren Hajiya Hafsatu itace a kasa dakin Bilkisu a sama haka nan shima Babansus a bangarensa shine a kasa su Hassan a sama. kinga wannan yana daya cikin tsarina Addini, tunda kinga hakan tarbiyyace mai kyau. Hajiya Hafsatu tana kula da shige da ficen Bilkisu, haka Alhaji usman yana kula da shige da ficen su Hassan da Hussaini wanda kinga in kika duba sauran gidajen mutanenmu ba haka abin yake ba, sai ki tarar iyaye sun ware nasus bangaren daban na yaranmu daban don haka sai kiga yaran sun tashi da muguwar tarbiyya sune shaye - shaye neman mata mugayen dabiu dai kawai don babu ruwan kowa da shige da ficensu, ba'a masan abinda sukeyi ba don tsabar rashin kula irin ta wasu iyayen har yaro yakawo budurwa ya kwana da ita a cikin gida sunanan da safe ya fita da ita amma sam basu saniba. Wani abun ai sai shiru tare da Addu'a kawai Amina amma tarbiyya kam ta gurbace sai gyaran Allah kawai, hm! haka nefa Hajiya, kinga in kjiana 16 shiga banagaren Hajiya Hafsatu kina shiga falone kato akwai wata karamara kofa daga cana cikin falon in kinbi tanan ne zaki shiga kicin mai katon store a ciki daga gefen falon dakin Hajiya, katon daki da aka shinfideshi da kafet na alfarma, gadon da yake dakin baiwar Allah nan ko film ban taba ganin irin shi ba, remote da kika sani Haijya shi ake dannawa gadon ya shige bango ya manne kamar ba'a taba yinsaba, idan kuma aka sake danna remote in anason ya fito kenan sai ya fito kamar ba'a taba komai a jikinsa ba, abindai sai kin gain da idonki kawai don idan bakin gain da idonki ba sai ki karyata. Dai dai kofar nan da zata kai mutum kichin matakalar bene take itace ta haura hard akin Bilkisu, dakin da take shima katon gaskeni don yaci babban gado da kujeru set manya, komai najin dadin rayuwa akwaishi a wannan dakin kan mudubi Bilkisu turarukan da suke gurin da man shafawa ya isa mai karamin karfi jari, a kowa ne daki da yake gidan akwai toilet shi kansa kayan ban dakin ban taba ganin irinsu ba, tunda randa na fara shiga kasa bude famfor nayi, inkin fito daga dakin Bilkisu akwai dakuna guda biyu a nan Hajiya take sauke bakinta. Daga gefen gidan ne jikin bangaren Alhaji aka yi dakuna masu aikin maza, duk da namijine yake musu abinci amma duk da haka suna da masu aiki mata saboda shara da wanke - wanke da gyaran dakunansu. Afilin gidansu Bilkisu akwai masallaci anyi shine a tsakanin bangaran mata dana maza don haka yazama dole idan anyi kiran sallah kowa ya fito, ata gefen kichin din akwai dining anan aka shirya katon 17 dining table doncin abincinsu don haka da angama abinci. Alh. dashi dasu Hassan za suzo nan bangaren Hajiya don cin abinci. To wai shin Amina a ina kika hadu da ita wannan Bilkisunne? inji Hajiya kenan take tambayata, nace Haj ya a inda muka hadu da Bilkisu dai shine awurin aikina anan Abuja Shopping mall a wani office na siyar da gidaje da filaye, shine Bilkisu sukaje da ita da babanta da mamanta don siyan wani fili. To agaskiya Hajiya Alheri yana da adadi don kuwa lokacin nayi kokarin dana taimaka musu naga na toshe duk wata kofa da za'a cucesu, kinsan sha'anin fili ba abu bane da za'ayi rana daya har dai a garin Abujan nan, don haka duk zuwan da za'ayi Bilkisu ce take zuwa to da haka muka saba da ita sosai, sai dai duk sabon danayi da ita ban bari tasan labarina ba. kinga yanzu inaga mun kai shekaru uku da ita amma sam ban yarda tasan labarina ba, duk da haka Bilkisu tana burgeni koda wasa bata taba sonjin labarin na don bata taba yimun tambayar da zata so tasan mai nake ciki ba wannan ma yana daya daga cikin abinda yasa nake sonta araina. Hajiya tayi wani goron ajiyar zuciya lallai "yata wannan yarinyar 'yar mutunci ce ta haifu kwarai don haka ake son harka da mai arziki don shi duk wanda ya gaji arziki to zakar same shi dan mutunci. Kinga babu abinda yasa Bulkisu ta hada duk halin da ake so sai Ilmi don da bata da ilmi zata kasance mai kyashi da kudin nata tana ganin kamar tafi kowa tanama wanda basu da shi kyashi sai kiga 18 ma tana neman ta rabaki da naki komin kan - kanton sa, gaskiyane Hajiya Assalamu alaikum gaba dayansu suka juya dan amsa sallama da akayi musu Anty oyo! yo: itama Anty da fara'arta tasha wani material mai fari da baki abinka da farar mace tayi kyau ba kadan bata karaso falan Hajiya inda suke zaune Amina kinzo lallai na makara wallahi dana mika yara makaranta shine na tsaya shan mai anan na bata lokaci, Hajiya ina kwana lafiya kalau ya yaran duk suna nan lafiya? iyi, lafiyarsu kalau, Hajiya ke tanbayar kanwar tata wai a kawo masa tace a'a wallahia na kosher nake kawai so nake na koma gida sabaoda abinci kafin lokacin tashinsu yayi". To shike nan ai babu wani abua iya kaci dai zan dan muku "yar nasiha Ramatu ga Amina nan Amana inason ki riketa tamkara kanwa ki uwa daya uba daya ban yarda ki rinki wulakantata ba kada ki dauketa tamkar 'yar aikinki domin bamuyi haka dake ba kinga dai ke kika zo har gida kika nemeta don haka inason ki rike ta amana idan kika ci amana wallahi sai Allah yaci amanar ki kina ji da kyau ko Anty Ramatu ta kyada kai tare da cewa insha Allahu zaki sameni mai rike amana Amina fiye da tunanin ki. Abu na biyu da nake son na gaya miki shine dole ki iya bakinki da kawayanki duk wanda ya tambayeki Amina kice musu yar uwarki ce idan ba haba ba kuwa babu inda zaman ku zashi don nasan sharin kawayen nan naku, wallahi Ramatu idan naji wani abu daga gareki ranki zai baci don kuwa babu abinda zakia sake zuwa ki nema kuma na shige miki 19 gaba. Ta juyo ta kalleni ni tace Amina ke amanace agurin Ramatu. Ramatuma amanace agurinki don haka inason ki duki Ramatu kamar 'yar uwarki Uwa daya Uba daya. idan har Ramatu tayi miki wani abu wanda ya bata miki rai da ita to babu fushi tsakaninki da ita ki gaya mata shine zama na gaskiya, kara kice zaki tsan gwami nna wa 'ya'yantta don kinga dai wannan abu taimıkon kaine koma nace ke ka rufawa asiri don haka idan kikace zakai daga mata ahankali babu dole. Duk da irin mutıncin da Hajiya take min sai naji zafin wannan maganar amma bakomai ba abinda ya jawo haka basai sanin sirrinn da tayi tunda da bata san sirrina ba babu abinda zai sa ta fadamun irin wannana maganar don haka yanzu tasa naji babu wanda zan sake yarda yasan sirrina ji abinda ta fada yanzu wai rufamin asiri za ayi itama da nake ganin tana share mini hawaye ma kenan, gashi akan 'yar uwarta don haka zaman nan ko zanyi shi bazan saki jiki dashiba tunda tun yanzu Hajiya ta fara nunamin banbanci akan 'yar uwata kwarama nayiwa kaina fada tun wuri nayia hakuri da 'yan uwana tunda duk tsiya babu wanda zai min gorin ya rufa min asiri ni yanzu ma na daina yarda da kowa tunda Hajiya tafara haka. Hajiya ace ta katsemin tunanina da cewa yakamata inwuce ina fatan dai babu wani naga kinyi shiru "yata inda akwai ki fada tunda ga nan na bata amsa da wallahi babu komai lafiya, mu wuce ko Anty tana fada tana duba mayafiyata tare da sakala Jakarta. Itama Anty Rahama, haka ta bita harda Hajiya tayi musu rakiya suna zuwa Amina ta zauna a mazaunin 20 mai zaman banza ita kuma Anty Rahama taja motar (CARINA 11) yah kai tsaye lugube muka nufa. gidan Anty Rahama gidane ma dai -dai ci kana shiga tsakar gida sai dakuna guda uku daya yana dayan kuma shi Anty ta nuna min da niyyar yazama nawa, dakin da Anty ta bani babu komai a cikinsa sai ledar tsakar daki ina ciki dakin ina gogo ledar. Rahama tacе abinda yasa na baki wannan dakin don ki sake inaga kamar idan na hadaki da yara kamar na takura miki Amina tace a'a babu komai Anty zan zauna acan dakin da kayana amma zana ringa kwana da yara, na fadi hakane dan nasan ina da kudina da Bilkisu ta bani, itama Anty ta amince da hakan na tambayi Anty abinda za'a dafa nan take tace dani taliya ta nunamin duk inda kayan dafa taliya yake na shiga kichin cikin minti arbain na hada taliya da busheshen kifi ina hada komai a cikin tukunya na wuce (toilet) na sheka wanka na fito dai - dai lokacin karfe daya dai - dai don haka na daura alwala nayi sallah naje na juye taliya a babban food flask na shirya tsaf cikin doguwar riga na dako karamin mayafi na yafa naje na sami Anty na sanar da ita inason zanje kasuwa, tace babu damuwa nima yanzu zanje dauko yara don haka bari na ajeki inda zaki samu mota. nayi godiya na wuce kofar gida gurin mata ina jira ta kulle gida mu wuce. Anty Ramatu ta ajeni gurin da zan samu mota nah au mota zuwa New Market. Ban zame ko inaba sai gurin "yan katifa muka rinka ciniki dasu su taya na taya harda muka dai - daita da wani aka dubu uku da dari biyar, nabar katifa anan na wuce gurin masu 21 zuba uban tagumi nace mairo kinajin karya ko ai ansan wannan kwai littafine yaya mutum zai yi haka lallai Dijon nan ta cika muguwa nasan akwai masu Kaman irin wannan amma ba haka sak, ba. Mairo ya naga kin kafa min idon ko kiftawa ba kya yi?"to mai zance miki Amina ai yau na san ke yarin yace tunda kika ce wai bazata yi haka ba to bari nagaya miki wannan nata mai sauki ne akan na wasu don idon kikaji labarin tawa jikara zaki sha mamaki don sai kice tatsuniya ne domin kuwa izaya da wahala ba wanda yarinyar bata shata ba ni har kinso narufe littafi ni kuwa zanzo naji wannan labarin ina da kawa maru buciya idan har kin yarda zanbata ta fadakar da jama'a wannan aia mai saukine yanzu ma idan kinshirya nima ana shirya, nikan mairo a shirye nake. Maryam shine asalin sunan ta don sunana ta ci kasancewar nina haifi mahaifiyar da ta haifeta bata ko daga kai ta kalleta ba ta ko ma ga ubangiji ta ta zauna ahannun na, na shayar da ita har takai shekara bakwai da can mahaifiyarta su biyune a gun mujinsu don haka tana isa amakaranta babanta yasa hannu ya karbeta ranar da zai karbita yarinyanan naga tashin hankali mutuka don kuwa nasan mugun halin matar nan kande. Asalin mu matanen Babura ne a wani kauye da ake kira kulfe Babura tana farkon karkashin jigawa State don haka ita mahaifinta yana nan garin Babura yarinyan nan ne don bani da ikon hanashi ita tunda ya fini iko akanta. Malam Murtala Malamin makaranta ne shine mahaifin Maryam mahafiiyar ta itace Laure nina haifeta itace yata ta biyu, tana da wa 24 shine ya mutu kafin ita kande matara uban Maryam tana da yaya uku amma a wani gidan ta haifesu sai dai tana tare dasu a nan gidana Maryam ita kadai malam murtala ya haifa don haka ya dora rai akanta muruka Maryam kwanan ta hudu a Babura gurin babanta ta fara fuskantar sabuwar rayuwa tana kwance tsakar dare kande ta tasheta ana nuka nukun sanyi irin na Babura matarnan haka ta dauko ruwa mai sanyin tsiya ta kwara mata tace wai tayimata fitsari kaji zalunci haka yarin nan ta kwana a tsugune da kaya a jike shi kuwa uban yana can bai san, bama abinda akeyi, to wannan ya zama jiki kullum al'adane da kullum indai anyi ruwa dole ne a tashi Maryam cikin duhu ta share ruwan gidan tas kamar yadda na gayamiki da sanyin nan kuwa tana barci za'a dauki ruwan tulu mai sanyi a kwara mata haka kawai, duk wani aiki da kika sani shara da wanke - wanke duk Maryam keyi daukar ruwa duk itace take yi. Wani abin kuma da yake bani mamaki matar nan bata bawa Maryam abinci sosai! da safe idan aka dama koko zai tasa yaran nan nata kowa yazo ya zuba yawun sa da majinarsa sannan ace da Maryam gashi tasha sauran yawun haka zata sha tana sha taje tayi amai amma babu wanda zai kula. wannan abubuwan da Kande ke mata babu wanda bai sani ba amma ankasa mata magana har shi kansa murtala sai kaunar zuci kawai yake don kuwa koshi bai fi karfin hakan ba agurinta don tsoronta da yake yi. 25 kwananta biyar kenan rabonta da wanka tun randa ta dai na talla bata karayin wanka ba. Duk wannnan bayani da nake miki Amina kande ce da bakinta take gayamin wadannan tun da kwana biyar ban ganta ba sai na biya nida matar kanina tawa nace muje mugani ko lafiya shine da muke je take gaya mana wai don rashin kunya harda cewa abinda yasa ta hana ta talla tana zuwa gurin wani ne a kasuwa mai lemo ita kuma tana tsoron kara taje tayi ciki ace don ba 'yarta bace. na kale ta kawai nace kinyi dai - dai amma ina ganin ai Maryam har yanzu yarin yace tunda bata wuce fadaba don haka ina ganin ai za'a iyayi mata fada a kuma je a tsawatarwa da mai lemon ba'ace ta fasa tallar gaba daya ba ko kuwa ni anawa ganin, ta wani yatsuna fuska to wazaije yana bin wani mai lemo kinsan shi Murtala babu ruwansa tunda ta fara wancan lokacin yace ba ruwansa da ita don haka ko magana baya mata, kwara su lami da magajiya sau dubu da Maryam gun murtala tunda ta nuna ita bata mada mutunci, kuma wannan abu Maryam dashi tazo gidan nan tunda tun farko zuwanta take kula gali mai shago yara suke cemin sun gansu tare nake karyata wa ashe da gaskiyarsu. Bansan sanda na harzika nahau fadaba nace dole murtala yace ba ruwansa da ita mana tunda ya sami wansa suka fita kuma iskanci gada tayi shi yasa take yinsa tunda ga uwata nan da 'ya'ya har uku ba'a taba ganin ubansu barantana danginsu kullum cewa ya mutu ake, ko ca kuke bamu san komaia bane shiyasa aka sami bakin gayamana maganan banza 28 nan danan idonta yayi zazur tace ni Inna in har maganar dana gaya miki ta baki haushi kiyi hakuri nib a haka nakenufi ba. bansan abinzai bata miki rai haka ba. Na tashi rai abace na je ni dakin garki na janyo Maryam tana hura wuta nace muje ko mayafi babu a ajikinta nace idan murtalan yazo ace nazo na dauke ta ni inasonta haka da iskancin nata tunda shi bayaso har baya mata magana akan kande tayi wata magana nabar gidan. Ina zuwa nasa salamatu matar kanina daura rowan zafi nasa Maryam ta tube kayanta na dauko sabullun gana nahada da ruwan zafi nan mai zafi so sai naje da kaina na gurje mata jikinta tunda ga kanta na fara har kafarta wallahi idan kinga kafar yarinyar nan kyace kullum a gona take wuni bukiti biyu nayi mata saida na tabbatar tafita tas sannan na kyale ta na dawo na dauki komai da ruwanka na mitsitsika mata duk jikinta na ci ka kwano da abinci tuwo shinkafa miayar Agushi nace maza cinye, amma sam ta kasa cinyewa saboda yunwar taci tacinye ta dole haka na kyaleta na bata fura ta kara akan meye wannan ta fara kyan - kyali don haka nace ta kwanta Maryam dai bacci harda munshari. Haka muka zauna cikin kwana uku ta murje har tayi fari kiba a binka da mai doguwar fuska nan da nan kyaunta ya fito na sakata a islamiyya kuma karatu sosai sallah bata wuce ta wanda da ko sallati bata iyaba ma. Babu maganar tallah in kinga Maryam ta fita to taje makarantar islamiya ne yarinya mai hazaka nan da nan tayi nisa a akaratun ta. 29 WATA UKU cur babu wanda ya biyo bayan ta daga gidansu nima ban damu ba da hakan don haka kanina ya bani shawara na rinka tura Maryam gidan yan matarsa safiya baza ta yi zaman ban zaba tunda mu a aganin mu yanzu Məryamu ta wuce musata a firamare don haka naringa tura Maryam gun safiya tana koyan dinki da yarinya mai hazakace nan da nan ta fara hada riga da farin karatun boko kwa tafara koyan wasika. A gida itama matar kanin na wa takan koya mata turanci abinka da mai hazaka nan da nan Maryam kamaninta suka canja tana samun ilimin boko tare da na sana'a nai kyauta nayi. cikin wata shida na siyar da ragona nahado da kudin hannuna na sai mata keken dinki duk tsawon watanin nan babu wanda ya waiwayo Mairo daga gidan muma haka yanzu kan mairo ta zåma buderwa tunda she karunta sha shida take aiki yanzu haka tana da izu arba'in da biyu a Qur'ani mai girma ta fanin boko tana iya rubutu duk binda kika ce ta haka takan karanta abubuwa da yawa. Ni kuwa duk wannan labarain da mairo take ina tausayawa Maryama amma ina gani nafita shan wuya tunda ita tana da wanda zai taimaka mata harya karbar mata yancinta na 'ya mace mairo ce ta farko dani daga tunani na da nake tace Amina duk har yanzu bangaya miki karshen tsiyarmu da kande ba. don kuwa saida kande tabani Maryam ta zama mutum sosai kowa yana sha'awarta yana yabawa da kyaunta da tarbiyarta mutane sun fara kai hari ana 30 sonta duk da dai bana barinta fita barkatai zance da samari saboda ina lura da ita Maryam din inda hankalinta yafi kwantawa akwai wani yana aiki nan local government, din Babura daraktane a wannan lokacin bakone ba hadejene to naga hanakalin Maryam din ya kwanta da kusan kowa dake garin nan yasan da mutumin yana neman ta. To abu kusan wata biyu har ya nemi yaturo iyayen sai nace to zanturashi yaje ya tambayi babanta tukuna, turashin nan da nayi gurin babanta Malam Murtala shi yajawo rigima da kande ta tayarwa da Malam Murtala hankali kan larai sai ya kawo Maryam gida wai sai ta dawo gidan ubanta da ke shima sakarai ne babu kunya babu tsoron Allaha yaje wai Maryam ta dawo gida yanaso idan ma auren zai mata yayi mata agabansa. Nayi niyar maye kanina ya hanani yace sam ba yarsa bace baiji kunyar duk shekarin da tayi ba baizo ko son yarsa ya dauakata amma da ga ita sai kayan jikinta. Har Maryam tasa takarmi zata bi shi nace da safe tazo inason ganinta ba komai yasa nafadi haka ba sai don inason kafin safe na taushi ganina akan don mun mata kaya ba wani abu bane. Kamar yadda nayi niyyar nasami shi kanin nawa ne masa magana akan kayenta yace shi bayana nufin ya hanata kayanta bane ba a'a yana son idan zatayi amfani dasu tazo ta dauka don yasan yaran kande sune zasu saka ita Maryam din baza bartaba ta saka ba nun ma naga gaskiyarsa nabata kekenta nace zan ringa aika mata dinkuna idan sun zamu kudin kuma zanci gaba da aje mata kamar sauran. 31 To wai mairo ita kande ina yayan nata suna 'nan?' ita lami an kai ta makarantar kwana tana aji hudu aka korire tada ciki wata biyu wai malamin sune yayi mata acan a makarantar. Magajiya kuwa ita da Jummai suna nan su suka maye gurbin Maryam na talla ai mairo da gaji kasan yaran nan babu wanda zatayi wani abun arziki ko wace ko sunan kirki ba'a akiranta da shi, wanda kowa a duniya anason dansa ya amsu suna nagari don nasan ran koyi dasu sunan nagari amma ita duk tabi ta bata yaranta da sunan banza to ni yarda kikaji nafadin nan haka nasani bansan suna sun agaskiya ba. To kuma Mairo ta barta ta auri wanda take son a'a bari dai tun da kin matsu na kara samiki nakara samiki labarin kafin lokacin sallah ya yi shi mai naiman nata Moh'd Balle ke nan wanda nace miki mutumin Hadija ne duk da walakanci da kande ta dinga yi masa bai damuba dak Allah yasa masa son wannan yarinyar sannin kanki ne duk mai suna Bello Allah yayi su da kwarjini da kuma bakar zuciya amma sanin halin matar ubu bai kula da halin mairo ba tunda idan tsiyarsa ta tashi idan yazo ai ta hana Maryam din fita ya gaji da jira yatafi da aka ga wannana bazai yiyu ba sai ta fara bin abin da kissa. Idan yazo sai a turo magajiya da kayan abinci da ruwa tazo tayi ta masa hira ita kuma Maryam din an hanata fita ana cusa mata wai yace ya fasa yace yanzon magajiya yake so don jahilci irin na kande kayan Maryam masu kyau wanda mukai mata za'a sawa magajiya tasa tafe take tana kararraya kusan akullum haka kande kewa Moh'd Bello ita magajiyar 32 tana amsa kayar wai Maryam an mata alkawarin aure da wani har ansa rana shiya sa ba zata fito ba. Da Allah yasa ba azzalimin bawan sabane ana da masa haka sai yazo ya sameni dayake ya saba dani da zuwa yace kaka kinji abin da akace dani a gidan su Maryam daman tafi sati bata fitowa zance sai dai magajiya ta fito ta tayani hira. kinsan namiji duk wanyonsa idan mace ta kulla masa wani makiraci sai kiga ya zama wawa, don haka wannan makircin ya samu karbuwa agurin Bello tunda yazomin da maganar ya janye zai koma gun magajiya tunda mun yaudareshi. Nasan dai karshen alawa kasa amma duk da haka bance masa komai ba naba shi hakuri nace yazo gobe zanyi bincike na yi alwala nayi sallah nafila na rokawa yarinyar nan abinda yafi alheri a rayuwarta nashafa mairo na zuwa gurin naji idona yacika da kwalla domin kuwa Maryam 'yar gatace tunda har tana dama wata addu'a gaskiya nafita shiga kuna'a rayuwata, Mairo tacigaba da labarinta a tunaninta ko labarin da take bani ne. ya sani kuka. Tunda harda acemin ihma kukama tukuna Amina. Watan! Amina na dauki mayafina sai gidan Malam Murtala muka gaisa da kande Malam yana tsakar gida a kwance dama yazo maka yasa nayi kirana Maryam nace Maryam haka zaki yimin ki ko yaran nan Bello kice karya kara zuwa ko? Maryam ta bude baki ta ce ta dafi kirji tace ni sam ba muyi haka dashi ba. asalima idan yazo ya daina kirana sam sai magajiya kuma inaga ni ya kamata nayi korafi da shi tunda abin da yamin cin fuskane mai nayi masa zaice 33 baya sona wai magajiya yake so ai babu abinda ya hadani da shi amma yace ya fasa kuma shine yafi yace miki nace bana sonsa tana fada idonta duk sun cika da kwalla nace duk maganar bata kuka bace, juya kan kande nace kande ya ishiki akan yarinya nan abinda kuke mini ya ishiki haka karkiga kinsa Murtala yazo ya dauki yarinyan nan ki dauka don kin isane dama munafarki kenan don ki rabata da mai sonta ko? to kinyi karya don kuwa Allah yafiki na kalli barinta wanda lami take kan keken Maryam tana ta jagwalgwalawa kawai don mugunta na tashi da sauri nace tashi mai uwa na kalli kande kici ga da yiwa yarinya nan mugunta zakiga yadda Allah zai mayarda don kuwa ba azzalimin bawarsa bane duk wannan fitinar kece kika hada to ki sani ai Bello mijin Maryam ne, sai ya aure ta akina arzukinsu in gama fadar wannan kande ta rushe da kuka mai karfi ba don komai ba sai don taga malam murtala yana nan kafin yazo ya batamin rai na dade dabarin masa gidansa don nasan yadda yake tsoaran ta duk abinda tace yayimin zai min. Washe gari da safe Bello kafin yaje aiki yazo muka gaisa nayi masa bayanin duk irin kuke - kulen da kande takes a tsakaninsu ya

Chapter 2 of 11