Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tun kuma ranar bai zoba balantana musan matsayoin shi ya kyalemu ko kuma yana nan 70 akan baker sa nasai munbar masa giadansa akullum gari na wayewa kowa zata kama gabanta neman abinda zamuci ya yanmu maza kuwa tun wanda akayir rigima nan muka rabu a gidan Baba Maryam bamu sake ganin kowa acikin suba itama karima duk tayiwa hudubara Inna kunnen Uwar shegu tun da muka dawo randa Inna ta tafi wani saurayinta yazo tabishi haryau yanzu dagani sai Hadiza muke ta fadi tashiAllah ya taimakeni Aminu yace zai biya mini kudi nayi karatun Computer don haka yanzu komai inaga zai zo mini da sauki ina ta zuwa gida ina wannan tunanin ashe facin rain a gabana tunda ina zuwa kofar gida naga motar mahaifinmu ina tura kaina cikin falon naganshi kwance a falo nayi sallama bai koa amsaba na shiga a tsorace kamar barayon da aka kamo yayi sata. Na tsugunna a kasan kafet nace ina wuri Baba ya wurgeni da mugun kallo wai ku wane irin mayu ne ban ace kuabar mini gidana ba to karkubar gidan ni nasan matakina da zana dauka akanku Allah ya kaimu gobe. Ina shiga na tarar Hadiza tana dakia a zaune tayia tagumi na tambayeta ko Baba yayi mata wata maza na tace sam ita baisan tana gidan ba saboda sanda yazo ina bandaki don haka inaga har yanzu bai samba ina nan. Nace to tayi shiru mu kwanta karya jimu in yaso in Allah ya kaimu gobe Aminu yace zai bani kudi zan shiga computer school in yaso idan ya bamu sai inje in nemo mana gida haya ko ince daki koda a Nyanya ne. 71 To wannan shine dalilin dawo warmu yanya ita kuwa Karima mun kusa wata daya a Nyanya bata samba inda muke sai sannan Hadiza tazo wani kanti sannan taganta ta gaya mata muna Nyanya ita Sadiya a lokacin tana makaranta kwana don haka da akayi hutu naje na daukota na nuna mata inda muka koma shikenan shi kuma mahaifinmu muka rabu bama ganinsa baya ganin mu, daki biyu muka kama kusan nace diya kaganmu ne diya kuma anan muke kwana, kayan fa bawasu kaya bane abinci cine da yar tarkacan kwanika wanda Innarmu ta barmana, duk mun samo inda 'ya'yanmu maza suke mun kuma gaya musu inda muke koda yake suna sun kasu kowa da inda yake Usman yana karo yana aikin gyaran wuta Moh'd kuma yana makaranta Poly nasarawa don haka yakoma ma nasarawa da zama wani abu kinsane ya dauki nauyinsa wanda muke nan unguwa daya don haka kusan ince yadawo gidan su abokin su suke masa kome Ibrahim kuma yana nan gareji yabi yana tuka mota Isah ma anan yake sai dai shi yana aikin bada takardane a tashar yamin kunga kowa ya watsu. Ita kuwa Karima ta zama kyakykyawar karuwa don in akazo aka dauketa sai tayi kwana uku babu ruwanta da kowa tunda ko zuwa tayi to in wani abuta samo babu wanda zata ba ko wahala zata kasheka inta dafa abinci ba zata bayarba don haka ban dogara da itaba sam kullum nafita zan samo mana abinda ya samu da haka harna tara kudi na shiga computer cikin wata tara na hada diplomer duka don haka bansha wuya ba nasami aiki. 72 nawa property inda muka hadu dake kenan Bulkisu inbiki muntaba ja haka na kame mutunci na, narufawa kaina asiri dani da 'yan Uwana duk sanda sa'adiya zata tafi makaranta babu abinda take nema ta rasa inayi iya kokarina akanta don karta shiga wani hali kamar yadda muka shiga haka Hadiza duk data gama karatunta da tace tana son ta shiga aikin dansanda nayi iya baki kokarInna na samo mata ta tafi don haka da kowa ya kama gabansa dana dauki kudi karshen wata nakama hanya naje mubi naga mahaifiya tayi tausayin Innar mu saboda yadda naga ta rame tayi baki babu alamar yinwa ko rashin kyaun makwanci a'a sam babu tantama rashin ganin mune da tunanin yanzu awane hali muke har kukan tausayi nayiwa kanmu tunba da tace tunda tazo ni kadaice nazo gurinta babu wanda ya taba zuwa a tunanina 'yayyanmu maza suna zuwa tunda naga kowa yana da rufin asirin sa amma ina kowa ya kama hanyarsaAllah ya shirya addu'ar Inna kenan. Koda yake banga laifinsu ba irin renon da aka bamu ne dole yasa kowa baya tausayin kowa haka najiyo nadawo da tausayin Innata fal cikina nazo na nemi kowa nagaya masa naje mubi Inna kuma tana gaishesu nayi hakane don insun mantama da ita to sutuna karkuma wataran wani yace ace ina zuwa suga kamar ina musu wani zagon kasa ne. Allah cikin ikonsa ina nan Nyanya ina kuma aikina na kuma kama kaina don harnayi 'Istibira'l'Allah ya hadani da wani bawanAllah Nura abinda yahada mud a anura kuwa fili yazo siya nan office namu to tunda yazo sau daya yasiya shi ken an kuma duk sanda ya 73 tashi neman fili sai yazo office namu yakan bugo mini waya yace yana nan zuwa idan yazo mukan gaisa amma babu wani wasa saboda shi nura mutum ne shi mai jin kai, don haka ni kuma nake dauke kaina idan yazo tunda na fuskance shi wani lokaci ma idan ogana yana nan ko kalon inda yake banayi tunda in bayanan dole aikin sai dani anna haka ashe shi nura wai sona yake don haka ra'ayinsa in yanason abu sai yaja masa aji . Ni kuma ta bangare na ina sha'awar hakan don banason mazan nan masu rawan kai don nasan babu komai acikinsu sai neman mata hakan da nura yake sai nake masa kalom kamili don haka kafin nura ya furta min yana sona tuni sonsa ya dada a zuciyata don haka nura ya furta mini yana sona ne ta hanyar waya ya tambayeni numbers wayata a kan cewa yazo neman oga nane bai same shi ba shine yace na basa number office namu yana fita ya bugo mana waya kasancewar yasan ni zana dauka ina dauka ne yake bayyana kansa a wuri na yana sona da aure mun dau lokaci muna hirar fahimtar juna tun daga nan dai muka fara fahimtar juna don nura ya bayyana mini bai taba yin aureba nima kuma naga hakan, don shi namiji mai iyali in ka gansa kasan shi ba wani abu bane ba yasa nura ya shiga raina lokaci daya sai kwarjininsa nura ba fari bane bakine bakinmu irin wulik yana da idanu kwala - kwala bashi da wani kyau wanda zam fasalta muku nura bashi da surutu bashsi da irin kananan maganganu duk matar da takeson ta aje namiji mai kwarjini zata so ace nura mijinta tane don kuwa kwarjini yanasa a mutunta 74 namiji cikin dan kankanin lokaci muka amince da juna nida nura min yiwa juna alkawarin aure cikin wata uku. Lokacin da bikina ya rage saura sati uku lokacin ne na rasa wa zai zamo mun Uba ko Uwa a harkar cikin ikonAllah na nemi Baba Maryam yayi mana ya kuma amince na dauki Nura na kaishi gidan Baba Maryam da Hajiya Haliama da sunan sune iyayena Nura yasan gidan da nake a Nyanya bai taba tambaya ta ba ni kuma bance masa komai ba tunda ni ai nafison hakan Hajiaya yarda akayi muka hadu da Hajiya wato yaya Anty Ramatu anan Nyanya cikin gidan da muke zaune dake dakuna ne har guda shida mu munkama biyu Hajiya kuma suna zaune aguda hudu ita da mijinta da yaranta guda biyar kusan nace na dauki Hajiya tamkar Uwata tana da 'ya mai suna na don haka take cemin 'yata son yarana ne ya dada hada jininmu da Hajiya tsananin shakuwar mud a Hajiya tasa duk wata damuwata inagaya mata don duk wani sirrina kamar kudInna da abinda nake ciki da samarina asalima Hajiya ita tabani shawara nayi Istibira'I don haka babu abinda nake boyewa Hajiyanema na da Nura babu abinda bata sani ba Hajiya tasan labarina kusan nace tana farkon dawowanrmu gidan da aurena ya tashi Hajiya tayi Uwa tayi Uba ko ince baban Khalifa yayi Uba sun tashi haikan don sharemin hawaye tunda nake a duniya bantaba ganin mutane masu mutunta mutane irin yau Babura Hajiya uwarta mutumiyar Baburace uba daya suka hada da Anty Ramatu mijinta tama mutumin Babura ne don haka naga karanci gurin 75 mutanan nan zo ku gansu sai kice bikin yarsu ta cikinsu ake. Ran aurena da Nura baba Maryam aure kawai ya daura ya dako gudun mowa dubu Ashirin yabani amma Hajiya da Baban Khalifa sune gado kujeru kayan kichin duk wani abu da zaʼayiwa yarinya dai – dai gwargwado bayin Allah nan sunyi ranar da za'a kaini dakina ne Baban Khalifa ya zaunar dani kamar yadda kowane uban kwarai yake wa yansa ya faramin wa'azi kamar haka wajibine gareki yake yar uwa musulma kiyi biyayya ga mijinki da kyautata masa manzo Allah (S.A.W) yace idan mace tayi sallarta biyar kuma ta kiyaye farjinta, tabi mijinta to zata shiga aljanna ta kowace kofa take su daga aikin kofofin aljanna to kinga anan babu wanda aka hala tawa aljanna cikin sauki irin mata don haka Amina ki kiyaye tunda ni aganina kin auri mutum kina sonsa yana sonki to maizai hana ki kayutatta masa ko bazaki sami ladaba saboda kaunar dake tsakanin ku ballan tana banda lada harda aljanna. Yaci gaba da cewa Amina bai halatta ga mace tayi aure ba alhali mijinta yana tare da ita said a izininsa kuma kada tabawa wani dammar shiga gidansa sai da izininsa hakan manzonAllah (S.A.W) yace idan miji ya kira mtarsa zuwa shinfidarsa batazo ba har ya kwana yana fushi da ita, to mala'iku zasu yi ta tsine mata har gari ta wayi. A wata ruwayan kuma manzon yace babu wani namiji da zai kira matarsa shinfidarsa sanan taki amsa masa face (Allah) wanda yake sama yayi fushi da ita har sai mijin ya yarda da ita. 76 To mata nagari masu biyayya ne gamazajensu kuma masus kiyewa ne ga kansu da asirin mazajensu da dukiyoyinsu lokacin da basu nan saboda kiyayewar daAllah ya dora musu wanna yana wajabta wa mace tayi biyayya ga mijinta a komai na hidima da tafiya tare da shi, dab a da kanta gare shi da sauran abubuwan kamara yadda manzon Allah tsira da amincinAllah su tabbata agare shi ya nuna. Allah madau kakin sarki yace mata ma suna da hakkin akan mazajensu irin yadda miji yake dashi akan matarsa acikin shari'a daga kyan zama da rashin cutarwa ance maza masus iko ne akan mata to idan mace bata yi masa hidima ba, maimakon haka ma shine mai hidimar, ta zama itace mai ikon a kansa ke nan Allah ya wajab tawa namiji ciyar da ita, da tufatar da ita da samara da matsuguni gareta, akan shi yafi dadi da ita kuma tayi masa hidima da abinda al'adar zaman aure ta gudana a kai sannan kuma duk wata yarjejeniya tsakanin mutane ana yinta ne aka abinda al'ada ta gudana a kansa. Abinsa al'ada kuwa mace itace take hidima da kula da ayyukan cikin gida. Ba dai - dai bane a dai - daita tsakanin mace mai matsayi da wanda bata kai taba ko tsakanin mai talauci da maiwadata gadai wadda tafi duk matan duniya matsayi itace fadimatu, yaddar Allah ta tabbataa gareta ta kasance tanayiwa mijinta hidima har tazo wajen manzon Allah tsira da amincinAllah su tabbata a gare shi ta kawo kukanta kan wahala da take sha wajen aikin gida amma bai dauke mata shi ba Amina ina shawarar ki daki nemi izni wajen 77 mijinki ki shiga islamiya don zaki fahinci abubuwa da yawa zan iya ce miki ban gaya miki komai ba gamai da zaman aure wannan na gutsura ne don nasan baki san komai ba game da aure tunda baki taba yiba. Don haka kid age ki nemi sani gurin wanda suka sani ki rokeshi ya sakaki in kuma baya so to shi ya koya miki in bashi da lokaci ya samo mai koyar dake kinji ko na daga kaina jeki mutane na jiranki Allah yayi miki albarka da Inna ta matar wanta da take wurinsa a can Mubi da Hajiya sune mukashihe mota kai amarya dasu gidana a garki II dan karamin gida ciki da falo da bandaki a tsakar gida kichin da sito duka a hade an shirya mini dakina da faloa duka babu abinda Hajiya da baban Khalifa basuyi mini ba tunda kusan sai nace kowa gudun mowa ya bayar sune sukayi komai Innata daman dake ba komai gare taba sai ido da godiwa Allah. Inna tayi kuka har kuka wa Hajiya da baban Khalifa kan abinda sukayi mini tayi musu addu'a da fatan Alhairi Inna take gaya mini bata bakin ciki da bacin rai irin na karima takaicin abinda karima take Inna tace zata dashe bata zo ganin muba saboda batason tazo taga yadda karima ta mayar da kanta, Karima ta mayar da kanta mashayiya shangiya taba kwaya a gaban kowa wani abu ban tsoro daf da bikina Karima ta gamu da wani saurayin dan koken nan day a mayar da ita yar koken shine abinda ayafi daga wa Inna ahankali tunda ranar wurina duk mutane sun cika gidan Karima ta shigo a buge tasha koken ta bugu ko ince ta shaki koken din tana zaune ido yayi mata jajir Inna sai kuka take yansanda sukai 78 mana sallama wai suna nemanta an kamasu da hodar ibilis itada saurayin ta yanzu haka saurayin yana hannunsu don haka itama zasu tafi da ita. Inna tana kallo aka kada keyarta aka tafi da ita babu kuma wanda zai bita donshi baban Khalifa daga shi har matarsa basa harkar karima don haka har aka gama bikina atana can a kulle da wannan bakin ciki Inna ta wuce Mubi. Zamana da Nura zama wanda tunda na shiga gidan bangane kansaba matsalata ta farko itace nura bai san addinin sa basa rigimar farko da muka farad a nura baisan yadda ake kwanciyar aure ba yadda Allah da manzonsa sukace miji ya kwanta da matarsa yasha baban da yadda nura yakeyi duk dare sai naci duka kafin nura ya kwanta dani sai yace sai dai ya nemeni ta dubura wanda duk da bansan komai ba nasan hakan ya sabawa addinin mu to idan naki yakan mini duka ya nemeni ta karfin tsiya, Da safe idan ya tashi fita yakan bani kudin abinci da zanci na safe ya auna mini abincin rana da dare iya ciki na kwai idan nayi baki sai daia nabasu na hakura idan yana gida magana kadan ta hadani dashi duka, ya hanani aiki sam bana fita ko ina bayason yaga kowa yazo gurina idan ya fita ya dawo ya ringa tambaya suwaye suka Zo. Wani abu da yake bania haushi da Nura wanda kuma na rasa fahimtara Nura baya fita yawo sai karafe ukun dare yayi wata shiga yasa bindiga ajikinsa ya fice idan yana shiri zai fita yasa son ko kadan naji motsi nima yadda akayi nagane kullum idana na tshi da asuba zanji sallah ko kuma idan na 79 farka zanyi fitsari naga baya nan shine arantan na hana idona bacci ina ganinsa yana shiryawa don haka ranar zuciyata ta bani Nura dan fashine, Asalima Nura baya son maganar iyayensa sam yayi min alkawarin idan munyi biki zai kaini garinsu yace dani iyayensa sun mutu don haka da aka tashi bikinmu ma abinda ya gayawa Baban Khalifa kenan sai wasu dattijo ya kawo wan 'yan uwan Baban sane yanzu kuma na gane karya ne dan fashi na aura tun sanda Nura ya fita na tashi nayi alwala nake ta kuka kamar an aikomini uwata ta mutu. kamara Ni Amina ina zansa raina ina ganin nayi aure na huta da yawan wahala ashe ba hutawa nayi ba wahala nashiga zabuwa tunda gashi na auri wanda zai gurgunta mini rayuwata yana nemana ta inda zai lalatani gashi ya hanani aikina ya hanani kowa yazo gurina kullum duka ga babban matsala wannan fitar daren da yake yi wanda na tabbata fashi yake zuwa tunda na taba kamashi ya dawo yana cewa bacci nake ya zauna yana kirga kudi masu yawa na tsorata tad a ganin yawan kudin nan nama rasa yadda zanaga Hajiya in gaya mata matsalata idan kunan na dage nace zanfita da karfi nasan bazai sakeni ba kar kuma na gudu yazo ya kasheni hargida islamiyar da baban Khalifa yace ya sakani itama ya kicincine to shima bai yiba tayaya zai sakeni koya barni nayi. Kawai wata yarinya makociyar mu kusan kullum yarinyar inta dawo daga makaranta tana shigowa muna gaisawa har takan kawo mini littafai na hausa ina karantawa to ahaka rannan ta shigo nake gaya mata inason ta kawo na addini inrinka karantawa 80 kona samu karuwa na kuma sami addu'oin d azan ringa yi saboda dai kewar wani bakin ciki. Na kuwa sa'a ta kawo mini harda wanda nake nema na addu'oi da wani littafi mata muminai naji dadin littafin tunkan na fara karanta shi dana duba abubuwan dake ciki nazo kurin da aka rubuta. IDAN MAСЕ ВАТA SON MIJINTA KUMA BA TA SON CI GABA DA ZAMA DA SHI YAYA ZATA YI? Da sauri na tafi nemo inda topic yake fako abinda marubucin yaceAllaha madaukakin sarki yace idan kunji tsoron cewa ba za su tsaida doko kin Allah ba, to babu laifi agare su cikin abin da ta fanshi kanta dashi (Bakara: 229) Al-hafiz Ibnu Kathir yace acikin tafsirinsa idan ma'aurata suka saba da juna matar bat a wa mijin hakkinsa ta ki shi kuma ba zata iyaci gaba da zama dashi ba, to ya hallata gare tat a fanshi kanta daga gare shi, ta bashi abinda ya bat a babu komai akanta idonta bashi kumashi ma babu komai a gareshi idan ya karba wannan shine KHIR"I sake - saken duniya suka cika min ciki nayi imanin wannan mutumin na dako sadakinsa na bashi kasheni zaiyi babu abinda ya damesa sai dai shima a kashe shi. Gashi idan ya fita da safe wani lokacin sai ya dawo sau wajen hudu yanzu haka tunda yarinyar nan ta kawo mini wannan littafin bata sake zuwa ba tunda yanzu ya lura tana zuwa ta debai mini kewa don haka idan zai fita sai yasa mukulli ya kulle ni. Abin ya fara isata don ko na fara tunanin manfurta wa rana laraba ya manta bai rufe gidan ba yafita ya 81 barni a bude nasa kayanaa ko wanaka banyi ban a fada gidan su yarinyar nan sunan ta Usaina tana ganina tana tsakar gida tana wanke - wanke tayi sauri ta tareni tace lafiya Amina nace don Allah idan kina da kudi ki dako mini dari biyu da sauri muna tsaya mamarta ta fito tasame mu tace ina zaki nace mana Asibiti zani Usaina tayi sauri yaje ta dauko mini dari biyu batare da mamarta tasan halin da muke ciki ba, mamar Usaina ta kalleni taga irin shigar da nayi ta kuma lura kamar a tsorace nake tace Amina ina fatan ba wani abu bane ta faru tsakanin ki damai gidan nayi saurin wangale bakina nace, haba mama babu komai asibiti kawai zani shi yasa nace bari na gaya miki zan kuma ba Usaina mukulli in yazo ta bashi koda ban dawo da wuri ba. Mukayi sallama da mamar Usaina, Usaina ta biyo bayana ta bani dari biyu muna lekowa kofar gida ina cemata saina dawo juyawar nan da zanyi Nurane a bayana Usaina ta fada gidan su da sauri da karfi yasa hannu ya jawoni tundaga kofar gidan su Usaina har cikin gidansa yana dukana da kafa tun ina bashi hakuri harna galabai ta nayi shiru bakina jinni ke fita idona ya juye ga yunwa na gallabata babu abinda naci ya fita yabarni kwance niba suma nayio ba niba mai raba yayi maganganu masu yawa bazan iya maimaita suba saboda duk kunnuwana dasu - dasu nake jinsu. Ban farko ba sai wajan karfe uku na yamma na rarrafa naje kichin na dauki wata guntuwar miyata ina dagarin kwaki na dauka na cakuda da niyar ko ruwa ban saba ina kaiwa bakina taunuwa ya kasa samuwa balantana hadiyewa bashiri na furzar da 82 abinda yake bakina nasan na shiga wani yanayi wanda bansan dashi ba. Na zauna zanyi kuka duk naji makoshina yarike naga wannan bazata kaini ba tunda bashi da magani don haka na tashi cikin mayen yunwa da wahala ta duka na dago tagar dakina naga gilas ne na duba agogo na ga karfe biyar na tabbatar Nura ya kusa dawowa na tuna furucinsa wanda kunnena ya jiyo mini wanda yace dukama sai nadawo na tabbatar shi agurinsa wannan ba wani, abu bane, na zabura da karfin zuciya na dako tabarya a kichin na daki gilas din dakin ya fashe tatsatsa na zura kafata sai danaji ni a kasa sannan na zura sauran jikina daman kudin da Usaina ta bani na sashi acikin rigar nono na, nan da nan na fada wani lungu wanda zanyi saurin bulla titi ina zuwa bakin titi naga bus ana maraba yanya nan da nana nafada na fito da kudin da Usaina ta bani dari na mikawa mai karbar kudin mota bai tambayan ba ani kuma ban gaya masaba ana zuwa Nyanya dai - dai kofar gidan mu sai wata mata tace akwai na nan ina dubawa naga nima inda zan saukane don haka na sakko na karbi canjina. Ina shiga naga dakin Hajiya Wasu kabilune namu dakuna na duka a kulle da makulli na bude baki zanyi magana inason na tambayi kabilun inasu Hadiza suke naji bakin ya rike wuyana ya rike sam bazan iya magana ba to anan hankali nay a dawo jikina na fashe da kuka na tabbatawa kaina wannan mutumin ya fasamin wani abu a wuya na nayi kuka kamara raiana zai fita tunda nake ban taba kuka kamar haka don tun ina gania har nazo bana gani 83 idon ya zama dusu - dusu dolene nayi kuka waje zai tsayamin na sami magani? shin wai waye zai bi mini hakkina akan nura? su Hajiya da nake takama dasu bansan inda suke ba to in nagansu ma yazasu dani tunda ba iyayena bane dole suma suna da nasu "ya"yan. yanzu idan na tsaya anan nasan dole Nura yazo nema na idona - idon Nura kuwa zai iya kashse ni don haka dole na tashi naje neman inda zan fake ko naje wajen Baba Maryam in kuma nemi su Moh'd duk da nasan ba zuminci zne damu ba baran tana wani yayi tunanin wani zai taimake shi koda yake banga lefinmu ba ukubar da mahaifinmu yasamu ita tasa kowa baya tausayin kowa. Na sake komawa kan tunanina nada dolene ko bazan iya magana da za'a gane ba bari naje gurin maman iyabo in yaso ko rubuta mata ane nayi ta gaya mini inda su Hajiya suka koma don inaga ko zan nemi Baba Maryam ya kamata na nemi su Hajiya tunda su nasan zasu boyenin in yaso Baban Khalifa yayi mini jagora zuwa gurin Baba Maryamn. mairo ce ta nunfasa tace turkashi lallai Amina kin sha wahala to ya akayi.? 84 Nagode mu hadu a MAHAIFINA NA 2 SARATU LAWAL NUHU GSM-08028405320 wannan littafin goron sallah ne ga dukkanin dauka cin musulmi Allah kasa abinda mukayi karbabbene kuskuren da mukayi Allah ya yafe mana amen. 85 MAHAIFINAH 2 ANA SARATU LAWAN NUHU 'YANKANNENA Aishatu Lawan Nuhu Farida Lawan Nuhu Balikisu Usman Ummatu Sabo Samira Nasiru Usaina Usman Ina ba makaranta Littafin Mahaifina 1 hakuri akan kura-kuran da aka samu daga Na'urar Computer ne, misalin -Amaryakar maimakon Abubakar - Baba Maryam maimakon Babura da kuma wanda baza'a rasaba. -3- Na duba naga biyar saura kwata na tabbata dai idan Nura yazo yaga bana nan zai taho nemana gashi kuma bani da bakin da zanyi magana, na fito bakin titi gurin Shamsu mai shayi tunda nasan ya iya karatu najashi gurin kasa na rubuta masa INASON KAKAINI GIDAN HAJIYA MAMAN KALIFA. Shamsu yagigice sai hawaye yace "Amina yaya maiyafaru? yaya naga kin dawo haka bakya iya Magana?" Na daga kaina, anan yace tsaya ina zuwa, yaje ya sallami mutanen dake siyan shayi ya sami wani yaro yace ya tsare masa yana dawo wa. Banyi mamakin halin danaga Shamsu ya shiga akainaba, don shakuwar da muka yi da shi kuma a dalilina yake aje kayan shayinsa a dakinmu. Asalima nina bashi jarin shayin da yake yi, don haka akwai dangantaka mai karfi tsakanina da Shamsu. Banyi mamakin kukan da naga Shamsu yanayi don ya ganni cikin wani haliba, munje bakin titi mun shiga motar maraba, bamu dadeba tunda babu nisa tsakaninsu yace "akwai na nan”, Shamsu yana rike da hannuna kamar wata yarinya har cikin gidan. Shamsu yana yin sallam maman kalifa na tsakar gida tana shara ta taso ta rikeni "lafiya? yanaga haka? mai ya faru?" Shamsu ya sake fashewa da kuka yace: "Hajiya yadda kuka ga -4- Amina haka naganta, inaga ko Magana batayi don nima rubutamin tayi tace na kawo ta nan gurin ki." Hajiya ta kalleni tace: "lafiya? mai yafaru baki Magana?" Na dagawa Hajiya rigata ta fashe da kuka mai ruri, duk da lalurar danake fama da ita sai da naji tausayin Maman kalifa a raina, naji wani farin ciki ya kamani don ni na san ina da gata tunda na sami uwa mai tausayina ha tana kuka saboda ni, ga kuma Shamsu kanina shima na samu, tunda dole nace shamsu kanina nasan shekarunsa bazasu wuce ashirin da uku ba. Shamsu ya koma da niyar gobe zai zo yaga halin da nake ciki. Yana fita hajjiya tace: "bari baban kalifa yazo muje Asibiti" kafin ta rufe bakinta ya shigo, maman kalifa tayi masa bayanin abinda ta gani yace: "ai babu zama sai asibiti." Duk ta rude tana cewa "Amina ai dukane" haka baban kalifa ya daka mata tsawa yace: "wane irin rashin hankali ne haka uwani kibari ta samu baki mana komai zata ansa" Mun iso general Hospital da misalin karfe bakwai na yamma, munyi sa'a likitan yamma bai tafiba don haka ya bamu gado ya shiga dubani ko ina. Dr ya yi kokarin yaga nayi magana kona daga wuyana, kafin Dr ya bar kai na, sai da ya tabbatawa su maman kalifa duka ne kuma yana kyauta zaton an taka mini wuya ne 5- don haka yanzu zasu rinka min allura za kuma su sa mini ruwa, saboda bazan iyacin abinciba. Baban kalifa yace: "don Allah likita ina so ka rubuta duk ciwon da kagani ajikinta don ina son na kaiwa police report." Baban kalifa ransa ya baci fada yake yana cewa "wallahi ko waye bazan yarda ba", ina daga kai na nan baban kalifa ya da da harzuka yace: "wallahi sai naga wanda ya tsaya masa". Ni dai ina kwance abinda ya dameni shi ne ko ina ciwo yake mini ina son na gayawa Hajjiya idan Şhamsu yazo ta gaya masa kar ya sake ya gayawa Nura inda nake, amma dole na hakura babu yanda zanyi tunda ko na rubutawa Hajiya ba zata iya karatawa ba. Saboda alluran da aka yi min da ruwan da aka saka mini a maimakon abinci, nan da nan bacci ya dauke ni ban farkaba sai da safe. Bangaren Nura kuwa karfe bakwai na yamma ya dawo ya tarar bana nan yaga ta inda na fito, nan da nan ya fada gidan su Usaina ko sallama babu ya tarar da Usaina a tsakar gida yace: "lallai sai ta fito masa dani ko kuma

Chapter 5 of 11