Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
zaranda Hotel, yasa aka kawo mana kayan ciye-ciye, muka zauna muka sha hira kasancewa matsi da kuncin da maihaifiyata ta sani shi yasa na yi saurin amincewa da Alh. Sunusi, tun daga wannan ranar na zama kamar matarsa inna sami hutu yana daukata muna yawo gari-gari yawon bude ido, da haka na sallama gidanmu, sai nayi wata uku banje ba, abin mamaki da naje ko mai ya sa baki zoba ba ace min ba, ga dukkiya an ganni da ita, nayi dunkuna kala. Na dinga yin abinda babu tsoro babu fargaba. Tunda na san babu wanda ya damu dani banda Alh. Sanusi, na sami wasu' abokan haraka, a cikinsu a kwai wani Ali da kwara tantirin yaro ne, Ali kowa ya san kwarori ba bu wanda ya kaisu fitina, to Ali tasa fitinar har da shaye-shaye haduwata da Ali ta sa na yarda duk samarina ta haka ya koya min shan giya, tun ina sha ina jin daci kamar yadda kikace yanzu, har na goge naga babu abinda ya kaita huce takaici da sa zuciya sukuni irinta, tun randa na fara shan giya babu wani damuwa da nake kwana da ita, dan haka ina baki shawara da ki sha giya ki kula kananan yara -24- ki huta da wahalar da kan ki wajen manyan mutane." "To Baraka ya ya aka yi ki ka dawo Abuja?" Tun da nagama A.T.B.U Bauchi na koma gombe naga baza mu shírya da Innata ba tunda ita bata sa min idoba, amma abinda take min gwara sa ido, ina da kayan biyan bukata a gidan babu abin da nake nema matsalar duk wanda yazo guna sai tace a kirawo shi yana zuwa tace wai lallai ya je ya kirawo iyayensa, inba haka ba kar ya sake zuwa, ko kuma in ta ga abin duniya tace bata son wanda bai kawo ba ta fita tana zagezage, niko giya bata banani sha ba don inaga ko na sha bata ganewa, to da irin wannan damuwar tasa muka yanke shawara da wani saurayina Gali ya samo min aiki anan Abuja ban sha wahala ba, da nace mata zan dawo Abuja, to kinji dalilina na zuwaAbujа." "Yanzu haka kina zuwa ko bakya zuwa?" "Ina zuwa ina kai mata kayan alheri ta na kuma farin ciki bama tayi mini zancan aure ma." Na yi shiru zancen Baraka ya ratsani, ita kuma uwar tace ta matsa mata gashi ta sata ta shiga wani hali kwara ni daman uba ban sanshi da tausayi kamar uwa ba, tun da shi baya shan wala kamar uwa, ita uwa itace mai daukar ciki, itace mai shayarwa da reno duk da haka banda son abin duniya irin na mutun, ya ya mutun zai wulakanta dansa ya guje masa saboda abin duniya?, gaskiya -25- iyaye na sake wajen amanar da Allah ya basu, to yanzu in sunje wujen Allah mai za su ce Masa akan amanar da Ya basu ta mu, ranar lahira da kallo kuma in ina ganin duk abinda mukayi su Allah zai tuhuma don haka bari na sha giyata kawai. Tun daga ranar na fara shan giya da farko na wahala daya baya na saba kullum da yamma sai mun fita nida Baraka mashya, anan ma munyi kawaye iri-iri kamar su Bashina da Maijidda kusan nace kullum da yamma nan gidan Baraka muke haduwa randa bama son zuwa sai mu bayar a siyo mana mu zauna musha mubugu tare da samarinmu. Don yanzu na bi shawarar Baraka ba na kula manyan maza sai kananan yara dan na hadu da wani yaro dan shekara ashirin da hudu har ya koyan shan taba, kusan nace na bar gidan mu na dawo gidan Baraka dan ko tafiya tare muke dan tsabar shakuwar mu, yaron da ya koya min shan taba Misbahu, yaro ne fari dogo kyakkyawan gaske dan naji dadin haka kwarai da gaskiya da Musbahu, ta haka ya koya min shan taba, na san na fishi nesa ba kusa ba, amman in kinga shagwabar da nake masa kin san bariki ba kyau, a wannan lokacin holewar rayuwa babu irin wanda bamuyiba. Yan kannena Hadiza da Sadiya da suka ga na canja sai suka ja baya da ni, na daina neman 'su maman kalifa duniya ta yi dadi. Kwance na ke akan three seater ina kallon A.I.T suna English drama ina jin dadin wasan sosai wata yariya ta shigo wai ana kiran Amina kafin na ba -26- ta amsa Baraka ta bata tace "ki ce wa mai sallama ya shigo”. Ga kwalbar giya a gabanmu muna korawa, wa zun gani, Aminu wanda mahaifina ya hana shi aurena tun ina yarinya ko ince Aminun da ya koya min harka, na kalle shi kallo irin na bugagiya yace "kwarai da gaske, gaskiya Amina na sha neman ki tun tini na rasa inda zan sameki, lokacin da na samu wanda ya nuna min gidanku sai aka fadan kinyi aure, to yanzu kuma nazo wucewa na shiga shi ne sadiya tace min auren ya mutu kina ma nan gida." Na kalleshi a buge nace "yanzu da wace ka zo?" Aminu ya yi murmushi alamar ya san ba a cikin haiyacina nake ba ya ce "Amina na zo da wacce kika san ni" na mika masa kwalbar giya nace "to bismilla" ya girgiza kai yace" na gode, żan barki ishan Allahu zan dawo gobe kamar yanzu". Washe gari da safe sai ga Aminu ko tashi bamu yi ba sabanin yadda yace da yamma da alama Aminu bai yi bacci ba, da ganin idonsa. Haka kwa akayi dana fito na sami Aminu a falo, na kalle shi idona cike da bacci na dafe kai nace "lafiya dai? da safe haka kamar mai bin bashi" ya saki murmushi yace "Amina ai bashin na ke bi tun da jiya banyi bacci ba, halin da na gan ki wai ke Amina ke ce ki ka dawo haka", kallon shashasha nayi masa nace "Aminarka a ina?" Ina Magana ina busa masa hayakin taba, na lura bai kula ba da abin da nake, ya sake kallona yace "Amina don Allah ina son kiyimin alfarma guda daya idan zan samu, ina son ki shirya mu fita wani guri", nace "mai zai bana, -27- ina zuwa" na shiya cikin siket da riga ko dankwali babu nace "muje ko?" ya girgiza kai yace "gaskiya Amina kisa mayafi, idan kuma da doguwar riga kisa don bazan so a ganni dake da wannan shigarba," na juya na dauko dan mayafi wanda hausawa ke ce masa rakani karuwanci, nace" doguwar riga kuma babu, in bazaka ba shike nan" duk tunanina ya bani shi ma layata zai dauka yace "to bisimillah" muna fita kasuwa wuse ya zarce dani ya tsaya a wani kanti da ake sayar da dogayen riguna yace na fito ya nunan wasu guda uku yace ki dauka idan sunyi miki na dauka ko godiyar kirki banyi masa ba tun da ba wando da riga ya siya min ba, ni sunfi doguwar rigar a gurina. Na lura Aminu ya gane ban yi farin ciki da rigunan daya siya min, amma duk da haka ya kawar da kansa bai kula ba ya kunna mota ko kallon ind nake bai yi ba, bai tsaya a ko ina ba sai a Abuja Garden, inda mukaje muka zauna a fararan kujeru da table fari a tsakiyarmu, ya tashi yace "ina zuwa tunda ya dawo bai ce dani komai ba, nima haka can sai ga wani mutun da leda baka ya kawo masa, a raina da naji dadi ca nake wani abinci ya bayar aka siyo mana don yinwa nake ji banci komai ba. Buda leda ke da wuya sai na ga' kwalbar giya da ganyen wiwi da kwalin taba guda daya ya kalleni cikin bacin rai yace "Amina ina son duk -28- kayan nan ki dauke su daya bayan daya kiyi min bayani akansu, da amfaninsu ga shan su."jikina ya yi sanyi sosai, abinki da zuciyar bariki wato bushashiyar'zuciyar ban ko kalle shi ba, nace "duk amfanin su daya, suna sa zuciya tayi sanyi". Shi ma yace "naji to kuma mai yake karawa a jiki?" na dauke kaina nace "jinin mutum ya na dawowa yana sa mutun lafiya, kyau" Amina dama jinin mutum yana tafiya ya dawo, abinda nake nufi da jinin mutum yana dawowa idan mutum yana shan wadanna abubawan yana sawa jini mai kyau ya dinga zama a jikin mutum. Aminu ya daure fuskarasa yace "Amina kar kiyi was dani kinji, kina magana son ranki, ki duba kiga yadda ki ka dawo, haka kike da? hunnunki da fuskarki da kafarki duk sunyi baki saboda hayakin da kike busawa jikin ki, mufara ta kanta, ita taba wanda mutane suke gani karamin alhaki to illarta babba ce, na farko tun kafin ta je ciki, fuskar mai shan ta musamman farin mutum za ta yi baki kirin, hannunsa haka, tafin kafarsa, kansa cikin bakin kuwa nanne farko da lebansa, to anan ga uwa uba ciki duk wanna hayakin da mutum yake busawa yana nan a zaune cikin huhunsa, za kiga duk wanda taba ta yiwa illa yana yawan tari musamman idan yana magana, dafin da take sawa cikin huhunsa, shi ne ya ke fita a fuskar mutum da tafukansa, ki yi tunani hayaki shi kadai idan ana gobara ya na kashe mutun har 29- lahira, ballan tana kiyi sheharu kan busawa cikinki, don haka kullum likitoci suna cikakken fadarkar da masu shanta, su kan su masu tallarta suna mai da ku wawaye tunda kullum sukanyi talla sai sun rubuta (The Federal Ministry of health warns that smoking is dangerous to health) shan taba harsarine ga lafiyar mutun, don haka Amina, ina baki shawara tun ba ta kama kiba ki bar ta. Giya bari na hada duka don wannan na ganki da gulder yau kuma naga kwalbar star don haka ban san wanda kike sha ba, star, gulder dandanonta kamar kanwa yake, to Amina tun ba'a je kan wata ba miye amfanin kanwa in ba a miya da duk wanda ya sha kanwa ta zame mai dole, miya kanta idan aka samata kanwa sai ta yi kunfa saboda zafinta amma Amina ace shi ne abinda zamu sha yana kara lafiya ki yi tunanni. Star wanda naga kulbarta a gurinki yau, tafi kowace karfi kinfi kowa sani wata illar babba da giya takewa mutane sai ka sha kwalba hudu a lokaci daya, uku lokaci daya, giya ta na sa rashin kunya, duk abin dan giya yake idan yasha yana sane illa dai kawai bazai fasa ba saboda fitsarewar da idonsa ya yi ba ya jin kunyar kowa, zata iya sa mutun ya je ya yi zina akan titi ba tare da jin kunyar kowa ba, saboda ya sha abind idonsa zai bushe, kana ji kana gani za ka kasa tashi kayi sallah, duk mashayi ya na barin sallah don babu -30- yadda za'ayi ya yi sallah, don haka Amina ki kula. Stourt mai kamar maltina tana da daci, amma ba mai kama baki ba, itace wadda likitoci ke cewa tana kara jinni don wani lokacin akan cewa kasha maganin fever, to bari na gaya miki Amina, duk abinda Allah ya hana ya na da kyau mu barshi, dan cikakken musulmi ba zai ce kije ki sha giya ba, kin ce maganin jini ne, don haka duk wanna yahudanci ne, kwara mu barshi, ita giyar nan idan mukayi hakuri da ita anan an tabatar mana da ita a aljanna, Allah (SWT) yayi alkawarin duk wanda ya sha ta duniya ba zai sha ta lahira ba, Amina mai ya sa zamu bari shedan ya rinjaye mu muyi zuwan zomo kasuwa (ya zo a guje ya koma a guje), don Allah Amina ki nemi lahira kibar duniya, ki tuna matsayin da ki ke, kamar marainiya ki ke, me ya sa bazaki rike maraicinki ba, ki kama kanki har Allah ya baki miji kiyi aurenki, ke bakya sha'awar yadda ku ke da yawa, kema ki samu naki, sai ki zauna ki na shirme duniyar nan babu wanda yazo zama, kowa da ki ka gani zai tafi, don haka ki yi kokari kafin lokacin tafiyar ki yazo ki figi wani guzuri da za ki yi ikirari da shi acan. Ganye wiwi kuwa nata daban da sauran, don ita tana tafarfasa kwakwalawa, da zarar kasha zakaji yunwa ta kamaka to idan ba ka yi kokari kaci abinci ba shine ka ke dawowa kamar mahaukaci, don ita lokaci daya take kama duk -31- was jijiyoyi na jikin mutum ta kuma kama kansa da ido yai jajur kan mutum ya ringa bugawa tana sa rashin kunya kamar giya itama. Amina don Allah don Annabi ina son ki yi min alkawarin kin daina shan wadan nan cuttukkan duka. Ki tuna Baraka tafiki gata, tana da kudin kanta ko ciwo ya kamata kafin takai ga halaka zata iya yiwa kanta magani ke kuwa Amina daina kulaki za tayi ta koreki don karki mace mata a gaida". Maganganun Aminu .sun shigeni, sai kuma idan na daina wannan harkar duk abokan harkar tawa gudu na za suyi to wazai kula dani da da bana wanna harkar kullum cikin roka da bashi nake, yanzu fa ba bu abinda da na nema na rasa wasu ma yi musa nake adalilin wannan haraka. Dan haka yanzu in na ce da Aminu na daina a gaskiya karya ne ban daina ba. Na kalli aminu nace "to na gode da shawarar da ka bani, Insha Allahu zan daina shan komai daga yau, amma ina fatan zaka taya ni da Addau'a" Aminu yace "ba bu damuwa Allah shirye mu baki daya, Allah kuma Ya sa wanna maganar har ranki in ma karya ki ke Allah ya sa mala'iku sun ams", haka muka rabu da Aminu lafiya ya dawo dani gidan Baraka, na san dai Aminu ba aurena zai yi ba sai dai ina mamakin yadda ya ke mini kullum da yamma idan ya taso daga aiki ya na tare dani amma kuma ko hannuna bai taba sha'awar ya rike ba, duk kuma abin da ya -32- san zan nema na bukatar yau da kullum ya na kokarin kawo min, a haka ya fara korar samirina. Hakan da yake min ya sa na ke shakkarsa sosai don in zanyi shaye-shayena nakanyi da daddare ne kamin safe komai ya bar jikina. Kawai ranar da Aminu yazo da safe ya kamani da kwalbar giya a hannuna kallo da yayi mini nida kaina na tsorata na rasa inda zan sa kaina, ya fito da ni ina tangadi nazo na tsaya a jikin motarsa nace "don Allah Aminu ka yi hakuri ba zan sake ba." ya daka mani tsawa yace matsa daga nan mayaudariya banza, ni zaki rainawa hankaki ana son a taimake ki, kina lahantar kanki, daga yau karki yi tunanin kin sanni, ki je ki yi ta barikin, tun da ki na ganin shi ne ya fi miki". Na kwanatar da kaina ina ba Aminu -hakuri, don nasan Aminu gata na ne, ko banza duk wanda ya san sirrina a baya bai kai aminu ba. Amma bai wulakanta niba, nasan duk irin mutanan da na ke ma'amala da su da sun san sirrina kamar Aminu da walakacin da za su ringa yi min yafi wanda suke mini ko banza nasan Aminu a gaskiya yake mani tunda banda wulakaci mia yake faruwa daren jiya said a aliyu saurayina yayi mini dukan tsiya bayan ya ya biya bukatarsa wi ina zagezagana irin na bugaggu shine na zageshi yanzu haka bayana du ciwo yake min ibabu kuma abinda na isa nace masa gobe ma idan yaga dama saiya sake ko kudin kwana bai biyanda, haka 33- ( rayuwar take watarana da sa'a wataran babu wani inyazo yabiyaka hakkika wani kuma yayi maka duka ya kama gabasa dolene nabi shawarar aminu idan inason rayuwa ta dawo irinta da. Aminu yasa hannu yatureni daga jikin motarsa ya ja kayansa na shiga cikin digan Baraka ina kuka na sami kwalabar giyar tawa na fartsa na dawo kamar maharkaciya ita kuwa Baraka tana can tana. aiki na shiga bandaki nayi wanka na kwanta baci mai karfi ya kwasheni irin na mashya giya tayi Musu kai tun sha daya na safe nake kwnce ban farka sai karfe ukku shima Baraka ta tasheni, nashiga kicin naci abinci nayi sallah ban yaga mata na yadda muka yi da Aminu daon nasan bata son sa don ko gaisuwa arziki basa yiwa juna tund ta gane inda ya nufa ina idar da sallah na sau jakat nasaka daya daga cikin dogaen rinunan da aminu yasaya mani ban zame ko inana sai din su aminu don nasan baya tsahi shidda yana zaune na kwankwasa kofa ya mansa batare da yasan ko wanene ba yana dago kansa da yaga nice ya bata ransa nagashe shi ya amsa a ciki na daure tunda na san bani da gaskya nace aminuy don Allah don son Annabi kayi hakuri kayi mini Addu'a Allah yarabani da wannan harka insaha Allahu bazan sakeba daga yau ya kalleni yace Amina karki sake yardarata kinji koke kanki kinsan ba ina yi donki bane inayi don Allah don kuma sanaya dake tsaknina dake don -34- haka amina yarage naki koki daina ko kici gaba tunda kema kin fison a ringa kwatace a kanki kamar karima wanda duk wanda yasanta yasan sunnata to shi ne kema kike son ki nadawa kanki wannan sunna tunda ita mai wannan sunan bata cika sai ta hada da wadannan abubuwan naa shaye-shaye sannan ta cika kasuwa. A durkushe nake a kasa nace "don Allah karka kaurace min, na san na yi maka laifi" Aminu "naji, Allah ya shirye ki, amma ina son mu yi da wajewa daga yau laraba in na sake ganin ki da kayan maye ba ni ba ke, kin gane?, saboda haka ki kula ba bu wani dan Allah don son Annabi ina son daga yau ki tattara kayanki ki koma gurin su Hadiza 'yan uwanki da ki ka gudu saboda shedanci.Amina kin cuci kan ki, kin yiwa kanki tabon da ba zai warke ba kije daddare ina zuwa gidanku ba gidan Baraka ba in har naga abin da nake son gani shi kenan zamu shirya." Na fita daga office din jikina a sanyaye da zulumin ya ya zan ce da Baraka daya kenan, 'yan uwana kuma wanda na wofantar dasu tun barina gida dawowata gidan Baraka, wane ido zan kallesu tunda sun sha zuwa ba na kula su, asali ma Hadiza har korar kare nayi mata don tayi min nasiha akan shan giya yanzu, idan na je za su saurareni ko suma za su koroni kamar yadda na yi musu. Yanzu abin da zan fara yi naje gurin su Hadiza kamar na kawo musu ziyara don naga yadda -35- 6 zasu karbeni, na yi sallama, na iskesu a waje, ta amsa a dakile kamar dole waton Karima tayi mini kalon sama da kasa tace "Amina daga ina, ko kuwa abokan harkar sun korcki shine ki ka lekomu?" ban ko kulaba tunda ba bakuwata bace in da sabo na saba da bakakar maganar Karima, na wuce kaina tsaye gun su Hadiza da Sadiya tunda su nakeyi ni sam ba na yin karima, ko ta kulani ko ta kyaleni, na wuce na yiwa kannena sallama, Sadiya da fara'arta ta amsa, Hadiza kuwa ta yi kamar barci take na zauna a sanyaye kamar mai jiran hukuncin alkali, nace "Sadiya, Hadiza barci take?" Sadiya ta girgiza kai tace "idonta biyu tana jin ki nasa hannu a tsaorace nace "Hadiza kina jina ki ka kyaleni?" bata ko motsa ba ballantana tace wani abu ko naji sanyi, nace "sadiya bari naje nayi alwala nayi sallah" Sadiya ta zuba mini abinci ina ci ne Hadiza ta juyo tace "Amina ki biyo mune kici mana wani mutuncin?" "To karki manta nan gidanmu ne ba gigan Baraka ba, don haka a kara gaba a gaida Baraka da sauran mashayan." Sai naji gabana ya fadi don kasa tauna lomar dake bakina na kalleta nace "don Allah Hadiza ki yi hakuri sharrin shedan ne ba bu kuma wanda ya fi karfin kaddara, ke kin taba zaton zanbar gidan nan har na zauna da wasu?, ki tuna yadda nake sonki ki tuna kaunar da na nuna muku a baya. Gaskiya Hadiza ba ki yi tunani ba, don ni yanzu Inshal Allah na shiryu yanzu nake son kwaso kayana zan dawo cikin 'yan uwana yanzu haka idan -36- na gama ina son Sadiya ta rakani na kwaso kayana gaba daya daga gidan Baraka na dawo nan. Marar kunya tayi shiru da maganganu da take tace "Amina, dama ai ke ki ka ja ban da haka muna nan kamar marayu, maimakon mu rike maraicin mu amman kowa ya kama gabaansa bacin kuna manya kun zama manyan banza kenan, karima ta kama gabanta kema da muke ji da ke muna faduwa muna tsahi kin kama gabanki kin bi sahunta, in har kin shiryu muAddu'ar kenan kullum" Hadiza ta bani tausayi saboda kukan da take tana Magana. Bayan na gama cin abinci muka je da Hadiza da Sadiya, na yi sa'a Baraka ba ta nan ta fita, ita da saurayinta don haka na kwashe yanawa-yanawa nace da 'yar aikinta tace nayi tafiya kawai don ma kar ta biyo ni, kamar yadda mukayi da Aminu dare nayi sai ga shi da alama ya ji dadin gani na a gida cikin yan uwana, ni kaina naji dadin canjin rayuwar don ya kawo mana kayan abinci har da su kaji da kayan shayi ya kawo mana, mun sha hirar duniya da Aminu da kannena baki daya, bayan ya tafi Hadiza tace daman ya na yawan kawo musu kayan abinci dana shayi, naji dadin hakan na fuskanci Aminu ya mayar damu kannansa ne kawai don ya sa idonsa akan tarbiyarmu, hatta shiga mutum ya yi sai ya lura da irinta idan ya ga bata dace ba ya hana shi. Yanzu da dawowar Aminu ya kai wata takwas, amma sam bai taba nuna min wani abu na so ko na fasikanci ba, a zatona ma Aminu yana da mata don dai bana son ya san na damu da nufin zuwansa -37- na barshi a inda ya tsaya. Kwana goma da komawa gidanmu, idan na ji kishirwar giya hankalina yakan tashi na rasa in da zan sa kaina na yi ta neme-neme wani lokaci na kan sha lemun kwalba haka mai dan gas, abin ya dan lafa min, idan kuwa damuwar tabace tafi komai daga min hankali, saboda duk lolacin da naci abinci ba bu abin da nake son nasha wan da ya wuce taba, daga baya dabara ta zomin nake cin goro na mayar dashi kamar tabar, da na fadawa Aminu cewa ya yi na dinga fadin Inna Lillah Wa Inna Alakim Raji'un isha Allahu abin zai zo da sauki, to kusan kullum haka na ke ta fama da innalillahi da haka har sati biyu ba tare da shan komai ba. Ina da kwana goma sha bakwai ne Baraka ta zo gaidan mu wai an ce mata nayi tafiya sati biyu, san nan har yanzu shiru nace "tun jiya na dawo, naje mubi ne, ina son na dawo nan da zama saboda su Sadiya ba ta da isasshiyar lafiya, tana fama da ciwon mara, idan ya tashi sai Hadiza ita kadai ta rasa inda zata saboda haka Inna tace in dawo kusa dasu." Baraka fuskarata a bace ta ce "haka ne amma ai ya kamata ki ringa zuwa koda da yamma ne munaa hira, ba dauke kafaba kamar mun yi wani abu" nima na bita da kissa nace "babu komai kawata, Insa Allahu zaki ringa ganina" ta fito da taba ta busa ta miko min guda daya, nan da nan naji yawuna ya tsinke, na shiga addu'a ba bu shiri har Allah ya taimákeni na cewa Baraka bana jin shan taba yanzu, na gode da haka muka sha hira ban nuna -38- mata komai ba don zamana da Baraka ba bu abin da zance mata tayi min mutunci yadda ya kamata, dan haka Baraka ba kashin yarwa bace. Hadiza suna ta fama dani akan naje gaida Hajiya maman kalifa, amma sam naki saboda yanayin da na jefa kaína lokacin da na sheke ayata, ban taba kula da yadda jikina ya dafe, koda Aminu ya fada jinsa nake kawai inaga yana fada ne kawai don na daina kawai, amma yanzu da hankalina yadawo jikina naga fuskata ta yi baki, idona ma sunki su dawo fari tas, kamar da saboda dafewar da sukayi sosai, don yanzu na shiga shafe-shafen babu gaira ba bu dalili akan jikina ya dawo dai-dai dalilina daya Hadiza tace Hajiya tazo nemana sau biyu sunce mata ina mubi. Soyayya ce, mutunci ne, kauna ce har yanzu ban fahimci ko daya ba nida Aminu, duk lokacin daya dawo daga gurin aiki yana manne dani har magariba, babu abinda muka nema muka daga ni har kannena kusan nace har Innata, don Animu yanzu yasan mubi yakan je shi kadai ma ba tare dani ba, a wannan satin ne ma yake cewa mu shirya dasu Hadiza zai kaimu muga inna muyi sati idan sati ya zagayo zai dawo ya daukemu. Haka kuwa akayi satin daya a mubi, zama irin wanda ba a taba yin irinsaba tunda bamu daurawa inna nauyin komai ba, Aminu daya kawomu sai da ya ciko mota da kayan Abinci ya kuma dauko dubu biyar ya ba inna yace saboda cefane munzaga mun gaisa da dangi yadda ya kamata mu ringa ya wadanda basu sanmu ba -39- yanzu sun sanmu don har dangin babanmu inna ta kaimu a wannan satin. Ranar juma'a gobe Aminu zai dawo muna cin tuwa mu uku inna tana gefen mu a dakinta hadiza tace "inna ya kamata kisa baki mu bamu san matsayin Amina da yaya Aminu ba kullum suna tare har yanzu kuma munji shiru babu alamar maganar biki", Inna ta dan yi murmushi tace "to Hadiza ku zaku zauna mata bakwa ganin irin matsayinsa yace shi yana da mata da yara biyu idan tana sonsa haka zai aureta nace "gaskiya inna Aminu yaso kansa don tunda muke tare da shi babu wata magana ta soyyaya da ya taba yi min ballan tana takai ga zancen aure don ni inba yanzu bama ban taba sanin Aminu yana da mata bama." Washe gari tun karfe daya Aminu ya karaso amma cike da kayan Abinci kamar sanda ya kawo mu, bayan yaci abinci ya huta ya je masaukinsa gidan wani abokinsa mutumin kano, wanda aiki ne ya kawo shi mubi tun da ya tafi saida safe suka dawo shida abokin nasa, bayan sun ci abicin safe ne muna zaune dakin umma daga ni sai shi da abokinsa mai suna Rufa'I, shi ne abokin ya ce min, "to Amina ranar wanka ba'a boyen cibi, kin riga kinsan abinda ya hadaki da Aminu tun tuni don haka yanzu ma ya dawo sai dai da iyali don yanzun Aminu yana da mata da yara guda biyu Fahad da Fairus yanzu haka suna zaune a Abuja, a Asokoro, ina fatan za ki yi joining dinsu as Amarya" gaba daya muka sa dariya Rufa'i yace "ba dariya za mu yi ba kin san dai nan -40 gida a kazo, don haka idan kin amince to mukara shiri akan na da

Chapter 7 of 11