Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
in ka tashi kayi wanka ka kunna kallon da ka keson gani, rayuwa kenan ashe muma zamu samu wannan?. Yanzu tunda komai ya natsa bari na nemi wanda suka rungumeni lokacin da ba ni da komai bani da kowa, Hajia maman kalifa da Bilkisu, na tashi naje bangaren mahaifinmu shi da inna suna zaune suna kallo, na gaya musu bukatata na -74- L kuma gayawa babana irin wahalar da suka yi da ni a baya, yace "to idan Allah ya kaimu da safe na shirya naje na samesu." Gidan maman kalifa na fara zuwa, tunda ko rasuwa karima bata sani ba ballan tana kо shamsu zaije ya gaya mata amma nima nayi shiru, ban boye mata komai ba na gaya mata duk yadda abin ya kasance, na bata hankuri akan rashin gaya mata rashin karima, hajia ta yi kukan rashin karima ta kuma ta ya mu murnar komawa gaban iyayenmu, ta yi min alkawarin zata ta yiwa inna da baba gaisuwar karima ita da baba kalifa, ban dade ba na kama hanyar zuwa gaidansu Bilkisu a maitama take, ita ma tana ganina ta fara cakwadi na dai dau laifina, na gaya mata karima ta mutu bayan tafiyasu da kwana daya, sun ji mutuwar sosia da ita da Abdul dinta, Hajiya Ramatu ta fito itama tayi min gasiuwa, can muka shige daki da Bilkisu nake. gaya mata mun koma hännun iyayenmu, yanzu nai mata kwatancen gidan, ta yi min alkawarin zuwa, sai mita take wai saura sati daya bikinsu duk abubuwa sun cakude mata ta rasa inda zata ganni ta buga waya taji shiru ta je gurin Mairo, Mairo tace bata san ba gidan, na ce "itama yanzu zanje, yau yawan zumunci nake da kuma ba da hakuri," Bilkisu ta so ta rakani, ta ki saboda Abdul ya'na zaune babu dadi Abdul ya bani dubu biyar, na ce mata "yanzu idan ta o bugo waya za ta sameni, daman a rufe ne saboda -75- mutuwa" tace "za ta zo ta daukeni na yi sallama da mamata na wuce cikin sauri. Ban zame ko ina ba sai gun mairo, wayyo mairo bata nan, ta tafi Babura sai dai aunty Nafi, ta gaya min ranar da zata dawo nace "zan zo na dauketa zuwa gidanmu." Anty Nafi ma ta taya ni murna, naso naje gun anuty Hafsat amma dare ya yi, dan haka na koma gida. Wani abu da ba mu saba dashi ba shi ne kulle, ba ma fita nan da nan, san nan kuma baba ya ce "kowa saita fitar da miji." Binta da take yarsanda a maiduguri tace ba zata koma ba aure za tayi, abin kunya duk cikin mu ba bu wata mai takamaimai sai Hadiza, don yazu Alhajinta bakano ya dawo ya tsaya tsakani da Allah zai aureta tun da ya ga iyayanta, da Hadiza tana neman taki, ni dai na bata shawara nace "gara ta hakura tunda Baba yace idan ya gaji zai bayar damu gun abokanan cinikinsa" ita matsalar Hadiza mata, matansa uku don haka bata sonsa, amma yace zai raba musu gida ita zai barta a Abuja, amma ita Hadiza tana ganin kamar ida anyi biki zai hadasu, sunansa Alh. Rabo dan, kundila ne, irin mutanan da suka shigo Abuja da sa'a ne a lokacin Abacha, ya dade yana wahala da Hadiza kusan nace shine mutum na farko daya bude mata ido, ban da shi ban ta ba ganin Hadiza da wani ba. To yanzu dai Hadiza ta yarda da shawarata, -76- 1 1 1 don Alh. Rabo ya yi tambaya an kuma ba shi, yanzu haka a wannan satin zai turo mutanensa daga gida za a sa rana. Ta bangaren mu kuwa ni, Binta da Sadiya ba bu bayani kwarama Binta tana tunanin komawa gidanta na da, ni ko a lahira ba na son Allah ya sake hadani da nawain ba wajen hisabi ba, tunda mijinta yazo sau daya take tunanin komawa kuma naga innama tafi son haka, wai daman uwarsa ce, ta kuma mutu, yanzu komai ya. rage min tunda sadiya yarinya ce, don haka ba dole bane a matsa ma ta tunda gamu. Washe gari da safe, maman kalifa ce ta fara mana sallam ita da baban kalifa....bayan ya yiwa inna gaisuwa, suka keba da baba a falon kofar gida, sun sha hira sosai har sai da baban kalifa yace "ya na so zai je unguwa, zai bar Hajiya a nan, idan ya dawo zai zo ya dauke ta, itama ta tausaya min, ta dau alkawari sakani a cikin addu'a Insha Allahu kema zaki tashi dai dai dasu. Hajiya bata tafi ba sai ga Bilkisu, maman kalifa ce ta kwashe komai ta gaya mata, Bilkisu ta yi dariya tace "daman wannan zance na ke son nayi amfani da ilimina, zan kuma nemo wanda nake son na ganki da shi duk duniya." Ido kawai na kafawa bilkisu ina kallon ta. Hajiya tace "to Bilkisu Allah ya bada sa'a, ai onasan aikin ki yafi da haka. Mutanan Alh. Rabo sun zo neman aure kuma an basu an saka -77- rana, saura sati uku, sunkawo kudin komai da ake kawowa. Binta ma dai abin ya kusa tabbata don mijinta ya dage da zuwa, yanzu haka har sun tsaida rana zai turo kanin babansa. Sadiya ma da bata kula kowa yanzu ta dage don ihar tana tunanin tsaida wani Tasi'u a matsayin mijinta. Yanzu ya rage ni kadai a filin ko yanzu nayi rashin karima don da tana nan da ni da ita zamu yi kwantai. Yanzu gidanmu shirye-shiryen biki suke nima kuma ina ta faman shirye-shiryen- bikin kawata, don yanzu saura kwana uku suka rage a kaita dakinta, munje mun siyo anko gwar-gwaron ne golden colour na kawayen amarya, kawayen mama kuma na su fari ne. Bilkisu 'yar gata, komai ya ji a bikinta, don Nicon Hotel aka kama mana don yi dinar, launching kuma a Sheraton, a Sheraton din ma a Ladi Kwale Hall, Hall din da ake takama da shi a duk hotel din, duk wanda ya hallarci bikin na ranar asabar, ya san bikin dan gata. da 'yar gata ake yi, maman Bilkisu ita ta kama'Sheraton ita kuma maman Abdul ta kama Nicon, wanda aure kowa yana ji da kansa. Baban Abdul shi ne Information Minister a yanzu ga bilkisu ita kuma abar milk, amma an tara an aje tuntuni, gata ita kadaice tilo, gwara Abdul naga su na da yawa naga yayyansa da kannansa, duk sun yi ankon wani jan leshi tunda nake da Bilkisu bata ta ba fadamin Abdul dinta dan information -78- minister ba ne sai a katin Biklinsu na gani, gaskiya duk halayen Bilkisu su na birge ni, ni kadai na je wajen launch, saboda haka na dare na ce da su Hadiza su taho muje gurin dinnar, da kyar ta bi ni wai ita tana shirye-shiryen bikinta. Mu duka muka je, ni da Sadiya, Binta da kuma mahaifinmu ya ba mu lokaci kar mu wuce goma, Allah sarki, duniya ba bu abin da ba zai wuce ba, in da ne ko da kwana za mu yi ba bu ruwan kowa da mu. Ina shiga hall din idona in ba karya ya nuna min ba Aminu ne na gani mijin Yusra, wanda ya so muyi aure Allah bai yi ba. Nan da nan na dauke kai na na yi kamar ban ganshi ba, mun samu, guri mun zauna nida 'yanuwana, ni kadai a zuciyata nake cewa ko dama Aminu abokin Abdul ne, in ba haka bamai ya kawo shi nan. A sani na Bilkisu bata san shiba, dan haka babu yadda zance ita ta gayyato shi, to Allah dai ya barwa kansa sani. Daga isar angó da amarya wajen, don haka kowa ya je ya zuba abincinsa bayan ango da amarya sun zuba nasu, mun je muna zubawane ni da Binta sai naji ance "ki zuba min nima madam" ban ma san da ni akeba sai da na duba bayana ina cewa Binta to bismillah, sai naga Aminu kawai, na kasa magana na mika masa plate din nawa, wani irin yar naji har cikin jijiyoyina tun da nake ban taba jin irin wan nan ba, na kasa maga kamar an kafe min bakina gam, haka naji lallai so masifane don ko ba komai duk -79- T 2 T gabobin jikina yau sun nuna min na kamu da son Aminu, gaba daya na yarda da zuciyata cew yau na hadu da mijina wanda jikina ya tabbatar min cewa duk duniya ba bu namiji da ya keburgeni yake bani sha awa irin Aminu, na yarda ba ni da miji isai Aminu. Ya ce "ki zuba wani" nace "na koshi” ya sa dariya yace "haka har da saurin sarewa, to zo mu ciwannan dinma." Mun gebe ni da Aminu mun zauna muna cin abinci ko da yake ni drinks na sha, tun muna zaune cikin mutane hira ta yi dadi, muka kebe daga da kujeru muka zauna. Ni da Aminu kowa kokarin ba dan uwansa laifi yake, shi ya na ni na koreshi, nima ina shi ya koreni, shi kansa ya yi mamakin da na tambaye shi ina ya san mijin Bilkisu, yace sam bai san shi ba, Bilkisu ce ta kai masa kati har office dinsa, lallai na yarda yau Bilkisu ‘yar jarida ce, ina duba agogo na ga goma, na tuna da gargadin da mahaifinmu yayi mana, don haka nace da Aminu zan je neman su Binta don ance kar mu wuce goma. Shi ma ya kalli agogonsa ya ce "da kyau, muje in kai ku," hall ya kacame da kida kowa sai rawa yake, amarya da ango suna tsakiyar makada, mutane sun lullube su bama su san wanda yake kansu ba, don haka ban bata lokacina ba wajen yi mata magana, naja su Sadiya muka kama hanya har kofar gida Aminu ya kaimu, mun da de a mota muna hira, ba bu yadda banyi da shi ba akan ya 80- do ya da bi k A b k d ra d n 11 g y 1 Π A t K 66 1 C 1 a Π shiga su gaisa da su Inna, ya ce "sam zai zo zuwan kansa ba yanzu ba. Mun yi sallama tare da bawa juna lambar waya, na shiga gida cikin farin ciki da walwala ba kamar da ba, tun da ko ba komai nasan ina da matayin hira, nima a yau na yarda da maganar Baraka tunda na fara gani da idona inna ta fara canja min akan su Hadiza, abu kadan ka ganta suna hira da na shigo sai ayi shiru, ina ji haushi kawai ina dakewa ne, saboda na san yadda zan yi da anga ba ni da kowa, to nima Allah ya kawo min nawa ko bal aureni ba ya tayani hira da haka har Allah ya kawo min abokin zama. Na shi go gida, ban ko fadawa Inna abin da nake cikiba, sallah kawai nayi na kwanta, da safe da muke falon su Inna wurin gaisuwa take tambayata "wa ye jiya ya kawo ku?"Nace "wani tsohon sauray nane" ban ce Aminu bane, Baba ya ce "to Allah ya zaba muku abinda yafi muku alheri" nace "amin, nagode" Hadiza bata gurin na tashi na koma dakinmu na duba wayata naga missed call, Aminu na share na kira Bilkisu ta dauka tana magana da kyar, da ka ji kasan akwai gajiya nace "kiyi hakuri na katse miki rayuwa", "a'a ba bu komai, wai jiya mai ya faru ko salama ba bu?" nace "Bilkisu ko me ye ai ke za a tambaya, wai Bilkisu ya akayi ki ka san office din Aminu" ta sa dariya tace "Alhamdu lillah abin da nake sonji kenan kuma na ji dadi tunda komai ya yi dai-dai", "to naji wa ya fada miki office din?" -81- "Ki tambayi Hadiza ita ta fada min inda gidansa yake ni kuma na je na tambayi mai gadinsa ya fadamin office dinsa, shi ne na kai masa card amatsayin kawarki, na kuma gode ya amsa kirana yazo, don Allah Amina ki sawa kanki nutsuwa ki auri Amimnu, kinga tunda yanzu komai yayi dadai, sai ku dai daita ni ina ganin Aminu ya so ya samarwa 'ya 'yansa uwa tagari ne shi ya sa ya dage, kinga yanzu za a yiwa kowa aure a gidanku danda ke, ko ni ban ji dadi ba shi ya sa na nemo Aminu don inganin duk duniya banga wanda ya cancanci ya aureki in ba Aminu, kin san bature ya ce true love never end don hakaki kwantar da hankalinki kawata, soyayyarku da Aminu ba zata kare ba, sai dai ta karu, bari na barki kar kudinki ya kare zan kira in anjima, bye bye!. Yau saura kwańa shidda bikin Hadiza da Binta don haka kullum suna hanyar kasuwa, yan zuma suna hira, ni kuwa yau shirin bacci bacci zan yi tunda mun gama namu bikin, Bilkisu tana ginta tunda a America za su zauna, don haka tana ta shirye-shiryen tafiya, andai shirya musu gida da komai da komai a Asokoro anan, bata tareba saboda shirye-shiryen tafiyar da suke yi. Har bacci ya fara daukata wani yaro yazo ya kwan-kwasa dakin da nake wai gashi inji wani abawa Amina, da saurina nace "yana ina?" Yace "yana motarsa", Aminu ya na so ya canja hali, ba zai so ya gaida su Inna ba? Gasgiya a rayuwata 82- d K bana son na auri mijin da bazai girmama iyayena d H D 1- d T 1 الا 1 i t 1 ba, na bude ledar naga cards guda biyar da turaruka, kowa ne card yana dauke da maganar soyayya kala-kala, kan na gama karanta cards din text message dinsa ya shigo, ya rubuta kamar haka "Hi! Darling how are u, please take this before i come back from office, bye" na ji dadin wannantext din, saboda na san ko yanzu Aminu ya na tare da ni, kai lallai zan yiwa Allah godiya ranar da na ganni a gida Aminu, na yarda da masu iya magana da suke cewa so baya tsufa Sai dai masoya su tsufa, har yau Aminu kullum soyyaya sabuwa ta ke dasuwa a zuciyarsa, naji dadi nace, bari nayi godiya "Thank you sweetie, may Allah give U a rainbow 4 every srom, a smile 4 every tears, a blessing 4 each treail, a sweet song 4 every sight and an answer 4 every question" ba aminu ba ko makiyina na yiwa wannaň text din na san sai ya saramin, shiru in cewa text din nawa bai shi ga, sai da na duba Acct di na ga har sun cire kudin text, zuciyata ta bani abu biyu, na farko na ce ko ya shi ga bai gani ba yana aiki, na biyu na ce ko shi bai yi masa dadi ba, na koma na ci gaba da baccina ban farka ba sai salla, ni kaina nayi mamakin baccin da nayi.lallai ba karamar gajiya na tara a harkar bikin nan ba, bayan nayi sallah, naji wayata na kara ashe Amaryace, mum dade akan layi take gaya min an gama musu komai na tafiya sauran kwana uku su tafi, wai tana so ta zo gobe ta yi -83- + 3 sallama dasu inna. "Lallai ba kwanan za'ayi bikin Hadiza da Binta, da", "suna cewa kwana shidda", "lalle kam, to ke kuma yaushe kuka sa mana?, gaskiya ina bakin cikin zaman AMERICA, naso na ganki a dakin Aminu" "ba bu komai haka Allah ya shirya", "amma Insha Allahu zan zama kamar ina nan, don waya zata daukar min komai, inaga idan na takura muku da waya har sai kun kasha," "haba dai Bilkisu, Allah ya sawake, inaga a rayuwata ba bu wani dadi da zai sa na manta da ke da Miro, maman kalifa don duk mutumin daya rungumi ka lokacin da baka da komai, to lallai zai goyaka idan Allah ya yi maka arziki" "haka ne, to mun gode bye." A'a, har mesege ya shigo muna ta faman suruto, dana duna lokacin na ga sha biyu ya shigo, lallai yau nayi bacci ban ko ji kara ba, "sweetie thank you very much, God belss you, I was given a heart only 2 love u, my hrt beats only 4 U, I was given Eyes only 2 u, u know I can't help my feelings it tought 2 live without you" cikin sauri na bashi amsa. "Oh! My baby I luv U, luv ur smile d way u call me! Oh Aminu just luv every tin about u take care and b mine 4ever." Karfe hudu dai dai sai ga amsar text dina daga Aminu "yes my baby I am on my way, I'll b with you soon. How prepared are you for." Nan fa -84- dУdЫKAHdrd1111d1a na fada wanka da sauri, na dauro alwala la'asar, ina idar da sallah na shiga shafe-shafe, yanzu kuma na mayar da dove maina, sahibata Bilkisu akwati biyu ta kawomin satin bikinta na kayan sawa harda set din dubai da abin hannu, duk akwatunan nan daga super sai less da kuma irin materials din nan masu tsada, banyi mamakin kyautar Bilkisu ba, don kuwa irin kayan da aka dankaromata da gwala-gwalai, abin kamar almubazzaranci koda yake naira ta isane shi yasa. Don haka na dau wani less pink kala na dau passion sarka pin kala itama, nasa jan bakinma kalar kayana, na san ni da kaina nayi kyau, don duk wanda yayi kyau ya sani basai an gaya masa ba, yaro yayi sallam da ni, lokacin biyar dai dai, ba sai na tambaya ba, nasan Aminu daga office yake direct, don haka naje kicin dinmu na zuba dambun shinkafa da akayi a kula, wanda na san ko inna da ita take yi tund da ita suke sakawa baba idan yana da baki, naje falons u inna don nasan ba'a rasa zobo a fridge dinta, na dauko a babbar robar swam, na shirya a babar folon, na wuce falon Isa na hanyar kofar gida na aje komai, sannan na fita waje gurin motarsa. Wani kallo da Aminu yayi min sai da naji yar a jikina, daga ni harshi kowa jikinsa ya tsinke babu wanda yayi magana, da kyar ya yi karfin hali yace "madam, har na dade ina jira", sai ni ma nace "don Allah ka yi hakuri, ka shigo daga ciki ko?" Ya biyoni a baya muka -85- C wuce falon Isah, sai ga su Hadiza da Binta sun dawo daga kasuwa da kaya niki-niki suna fama. Sai da na zubawa Aminu abinci san nan muka gisa yace "gaskiya madam, komai yau ya kai min, don inajin babu wanda ya kaini gata, ga abinici da na dade banciba, wanda nakeso, gaskiya idan ma baki iyaba wallahi ki tambayi inna ta koya miki tunda wurin." "balantam na iya" "to madalla tunda kin iya, don ina son sa, karfa kice santine" "a'a ba bu komai tunda dai akan kujera kake nasan zata kare min kai." "Yanzu dai mu ina wuni? Ya ya gaisa, aiki?" "Lafiya kalau rayuwta! Gaskiya Amina kinyi kyau kamar yau za a kai ki dakin nawa, kai! wannan randa aka kaiki kuma ai sai na sume, tunda yanzu jikina duk rawa yake." "Allah!" Nayi masa wani far da ido, dan nasan duk namiji idan akayi masa sai yaji a jinkisa, ai kasa daurewa yayi yace "don Allah karki sake min wannan kallon sai munyi aure, ai sai kisa naje ayi abin da ba shike nan ba," yace "to, saura kuma idan mun yi aure kiki yi min, don yawanci matan hausawa soyyayarku a waje take, inason duk abin da ake min a kara don nima karawa zanyi ba ragewa ba” "to Allah yasa da gaske ka ke, tun da ku maza haka ku ke, kuyi kamar zaku cinye mace a gidansu da zarar taje kun aureta shike nan sai kaga kamar baku ba." "to naji maganarki amma ina son daga ganki muga darasi duk muba mutane -86- masu irin wannan halin mamaki suma su daina." Muna cikin hira yace baiga karima ba nace "ay karima ta dade da mutuwa", Aminu ya yi shiru bai sake magana ba yace "to lallai na shiga na yiwa inna gaisuw ya kama ni, don koda wasa ban sani ba." Bayan ya fito daga gurin inna ne ya ke ce min ashe su hadiza suma aure za'ayi musu, wai yau saura kwana shidda inji inna, to ko muma muce ahada damu ne, Amina?" "A'a kabarsu sun tsara kayan su kawai muyi musu katsalandan, muma mu kirkiri namu" gaskiyarki fa." Sai shidda saura yayi min sallam ya tafi gida da niyar zai dawo bayan sallar Isah'i,. Na shiga na tarar da su Hadiza anata faman raba kayan da aka siyo a kasuwa, banko kula suba na shiga na cire kayana, Sadiya ce tace wai inje inji inna, nasan maganar bai wuce maganar Aminu ba. Amina yaushe Aminu ya fara zuwa nace "inna tin ranar bikin Bilkisu", "to yanzu da wacce maganr yazo" "da aure mana" "ai gara kiyi masa Magana yasa himma aiba tsayawa za a yi ba ana wasa dama ba ba bakone ba, don haka gara kawai ayi maganar aure idan yazo kice ina nemansa” nace "to inna amma ina maganar aure zakiyi masa da kinbari nima zan yi masa" "shi ke nan in dai za kiyi masa, ai daman ga ni nake kamar baza ki yi masa ba." Bari naje na je na yi sallah, inna idar da sallar magirba na yi wanka, nasa siket da riga, -87- siket din har kasa, na dauro alwalar Isha'i ko tashi ban yi sallar ba, wayata ta yi kara ina ganin lambar, nasan Aminu ne, don ina dauka cewa yayi "ranki ya dade ina waje" na dauki dan karamin mayafina na rufe jikina, yana jikin mota ya ce "wai yanzu wata sabuwa kira mai kyau aka yi miki ne, Amina gani nake kamar ba Aminar da na sani ba, komai nata ya canja sai kyau take karawa, anya kuwa zanbari su Hadiza su tashi su barni a gidan nan. Gaskiya gara naje na gayawa inna ina son a daura mini aure da matata hankalina zaifi kwanciya." "Haba dai ai idan aka yi haka an yi mini shigar sauri, ko aunty Yusra ma ba a kyauta mata ba, irin wannan shigar sauri" "a'a, ita abin da ya ke bakonta yanzuma ba gida daya zaku zauna don ke zaki zauna a gidana na Kwarinfa ne, kinga kuwa ai tarewa bata shafe ta ba" "haka ne amma ta na da hakki da hakkinta za a ba ta mana", "tun sanda muka hadu na gaya mata na sake haduwa da Aminata kin san kuma yušura ma ai bata da damuwa, yanzunma idan naje zance tazo ta yiwa inna da baba gaisuwar karima insha Allah gobe da safe idan zan wuce zan ajiyeta idan nadawo aiki sai na biyo na dauketa. "To mun gode, amma don Allah ina neman alfarma a bari sai jibi ta zo, don gobe idan Allah ya kai mu ba na nan, don Bilkisu za ta zo yiwa Inna sallama, nima kuma zan bita mu yi bankwana insha Allah, ka san jibi za su tafi", -88- “wan nan ba zai hana Yusra zuwa ba don kuwa ba gurinki zata zo ba gun Inna da Baba za ta zo" "ya kamata ace idan tazo na ta yata hira, tun da ka san baza ta sake da Inna kamar ni ba, ba ka son mu saba ne?, ai ko ba gida daya zamu zauna ba ya kamata ace muna zumunci." "Na yarda da maganarki ranki ya dade, don haka a hukuncin da kika yanke ya nuna sai jibi Yusra za ta zo. Amma ni zan so idan Bilkisu ta zo a kira ni mu yi sallama, ko ba a son sallamar da ni?" "a'a, ni nace, Allah ya kaimu goben". Ina shiga gida na saka rigar baccina na kwanta, ban yi minti talatin ba bacci mai karfi kamar wadda ta wuni ta na aiki, lallai na san gajiya ba bu kyau, duk gajiyar bikin nan ce taki barina, har yanzu ina da aiki tun da ga wani bikin a gaban mu yana tafe. Ai ko da safe na rigå kowa tashi daga bacci, tun kafin nayi sallar Asuba sai da nayi wanka don naji karfin jikina wajen sallah, ban bar kan abin sallar ba har karfe takwas na safe, ban da istigfari ba bu abin da nake, a lokacin abubuwa da dama sun fado min, na tuna muguwarrayuwar da na yi, yanzu ko ina su Baraka da Maijidda?, Allah sarki duniya, Allah yasa suma sun shiryu iyayensu suma su gane kamar yadda iyayenmu suka gane, nan da nan kuma lahira ta fado min, tunanin yanzu ya Karima take a lahira?, Duk da cewa ko yaya aikinta mai kyau yake, to itafa 89- Karima mun sani duk cikin abubuwan da aikata babu mai kyau, an kuma ce idan kuma har ka mutu to babu zance tuba, to yanzu kenan Karima tana can tana faman shan azabar kabari?. Ban san lokacin da kuka ya kamani ba na ringa rokon Allah da ya gafartawa Karima laifinta wanda ta sani da wanda bata sani ba, inda ma naji zuciyata ta dan yi sanyindan aka ce Allah ba ya kama mutum da bai sani ba, Allah ya sani rabin laifin da Karima ta aikata bata sani ba, Allah mun gode maka da ka shiryemu, Allah ka shirya 'yan bayan, idanuna sun yi hulu-hulu saboda kukan dana yi da na tuna da Karima. Na shiga gaishe da Inna take gaya min gobe idan Allah ya kaimu za su je gidan renon yara ita da Baba don neman inda yarinyar Karima take kamar ta san yau nima da Karimar na tashi nace "Inna inaga kamata yayi kiba Baba shawara duk karshen wata ya dinga sawa ana mata saukar Qur'ani don neman sauki akan zunubanta ko?" Tace "haka ne" bayan wannan ne ma yasa ake karanta mata hailala dubu saba'in duk karshen wata, saboda zunubinsa shima, Allah ya jikanta, amin. Dama ina son in tambaye ki, ya aminu bai ce komai ba?" "Shima ya ce shi a shirye yake, sai dai ni Inna ina neman alfarma kinga yau saura kwana biyar kuma ni babu abinda na shirya tun da kinga su babu shirin da basu yiba, don haka inga a -90- yi nasu ni nawa ko nan da sati daya ne a yi tunda dai ba wani biki zan yi ba ko Hajjiya da Mairo ma sun isa su rakani" "amma babanku yace yana son ya hada daurin auren gaba daya" "to ba damuwa zan fadawa Aminu ina yazo, Inna kisan gobe Bilkisu za ta zo ta yi miki sallama, ko bata samu zuwa ba ina son naje." Kafin ace na mayar da hankali na ci abincin safe har Bilkisu ta zo ita da Abdul, wai yau tana da abubuwa dawa, Inna da Baba sun yi musu addu'ar Allah ya kaisu lafia, nace "bari nayi flashing din Aminu ya zo ku yi sallama" Bilkisu tace "haba flashing ai harkar talauci ce, bari ai kiransa sosai ya zo", da wayar Bilkisu muka kirasa yace daman yana kan hanya, muka fito falon Isa gaba daya saboda abdul yana can, ba a yi minti arba'in ba ya karaso, an zauna ana barkwanci, muna musu tsiyar kar su je su manta da mu, suma suna mana tsiyar kar mu tashi biki muki nenamsu. Aminu ya dauko wani abu a kwali ya bawa Bilkisu ya ce "kin san mu

Chapter 10 of 11