Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
nunamin ababuwa komai ya gane insha Allah aikin sati nan zai turo mutanen gidan su, hakan kuwa akayi kwana uku da magana Bello yaturo mutanen Hadeja akasa ranar aure wata biyu. To fa hankalin kande ya tashi don kullum kwanta da tashinta mai zatayiwa Maryam wanda zata bata wannan aure da farko ta sata daukar tafashahsen ruwan zafi a katon bokiti taje da ruwa 34 akanta ya zubo mata duk ta kone jikinta har kanta yarinyar ta kwanta jinya ni da kaina bansan halin da take ciki ba sati wajen biyu tana kwance babu abinda take ko ina jikinta ya kwale banda fuskarta amma har kanta duk da haka kande bata kyaleta ba tana cikin jinyar taje ta cire mata wanda ta dauki kandir wanda ake kunwa ta caka mata a matuncinta kamar yarda ta saba caka mata danyatsa yanzu kuma kandir kaji rashin imani irin na wasu jahilai don kuwa wannan jahilci ne tsanatsa duk wanda yake da ilimin bazai taba yiwa dan uwansa musulmi wannan izayar ba. Kafin kace wannan, jini da mugunyar kuna yana ta fita ajikin wannan baiwar Allah nunfashin ta yana neman daukewa annan ne kande ta tsorata tasa magajiya taje tayi kiran, tare muka taho da magajiya kanin dake yana gida kafin mu karasa Maryam tuni ta suma na rasa inda zana fiskanci ciwon ne farko dai ga kuana duk ajiki to kuma wannan jinin na mai yake kwarara haka? na tambayi kande wai itama haka ta gani kwai yana fitowa shi yasa tace a kirawo ni nasake tambayar ta dama ta kune tace wai da ruwan zafi ta dafa zatayi wanka, naga dai duk zan batawa kaina lokaci idan na tsaya ina saura rana karyar kande nace da kanina ya shigo mu kamata muka kaita babban Asibiti na nan aikin cikin garin babura nan da nan aka bamu gado dakin da aka barmu mu kadai ne, aka samata ruwa, suka sako kayan aikin su suka guge wurin kunar suka satsaka magani tare da allurai. Muna zaune da yarinya har magariba tun safe amma bata farfaduba akwai wata ya rinyar kirki acikin yan aikin zalamatu nace don Allah ta kirawo mini likita a 35 duba idan babu rai kamata yayi a abinne ta muyi ta zama da gawa agaba, yazo yayi aune - aune sa yace tana da sauran rai yanzun hakama tana jin duk abinda ake cewa tana ji kawai magana ce bazata iyayi ba saboda azabar ciwo saboda ta wahala sosai ana magana sai ga Bello yazo yake gayamin wai murtala ne yake gaya masa bata da lafiya shin kullun idan yaje sai ace masatayi lafiya babu wanda ya taba gaya amsa bata da lafiya, yake tambayar baba mai ya same ta ance Bello banda wannan kuanar babu abin da zan dara sai dai ina Allah yasa ta tashi ta fada mana abinda yafaru. ya dafa kafadar likita yace likita kana ganin zata tashi likita ya kalleshi. Ido yayi yajir yace insha Allah ka kasa nace namiji karka karyawa tsohuwa raia nia kwa Amina zuciyata ta bushe ko ka dan banajin kuka araina tuni ma nasawa raina Maryam ta mutu kawai dai muna zauna ne daga wane. Don dai anki yarda ne kwai da salla insha'I kenan ina jan carbaha nabar Bello nan zaune yana kallonta sai naji yace Baba tana motsi kafin nada ko kaina Maryam ta bude idon ta wanda yayi jajir ta kalleni tace Baba mairo ki yafe min Inna kande tana son ta kashi ni kinga abinda tayi mini bazan iya zama ba ta kwaramin ruwan zafi yau sati biyu ko zama banayi barai komai babuya wanda yabani magani gashi kuma yanzu abinda ta saka mini sai ta kalli Bello ta fashe da kuka shima Bello kukan yake ni kuwa ido nane yayi jajir na kasa kukan, Bello ne yakatse mana yace Maryam tashi yanzo ki sha koda madarar nan nace wallahi bazan iya tashi ba yakalleni yace baba mutasheta nayunkura 36 zan dagata daga yadda bayanta ya manne kana ganni naman jikinta gashi ta kasa hada kafafunta sai bude su takeyi kasan cewar banason Bello ya gane domin a tunani na ko kande wani katon ta dauko yazo ya burmata da karfi dayaji don haka nace Bello mukeleta tunda naman jikinta ta zalla ana ganin sa duk da maganin da aka samata anan asibiti nai kukarin dagu kanta a filo ahaka na danga bata madara da Bello yakáwo mata har tace ta kushi na mayanta na kwantar. Na tashi na fita na basu wuri Bello ne ma ice mata Maryam kiyi hakuri ina tare da duk wahala sanan duk wannan abubuwan yana samun kine saboda ni Insha Allah idan munyi aure sai munzama a abin su ga kowa kuma insha Allahu gobe zanje kano zanyi magana da likita na, idan yace a kawoki inyaso zan kai ki can Asibitinsa ya kalleta cikin tausayi da kuncin zuciya in kana son bu kagan sa a wani hali kiyi hakuri samu sauki don haka gobe bazan zoba sai da yamma saboda zuwa kanon gawannan kudin ko zasu ne mi wani abu Allah ya baki lafiya ina dada fada miki ina tare dake duk halin da kika ciki sai na dawo to bayan fitar Bello ne Maryam take bani labarin abinda kande taimata da kendir nadagata naga yadda baganta ya rure yayi zajur har yanzu kuma bai dai na zubar da jinni ba hankalina ya tashi sosai cikin sauri naje na kirawo likita na nuna masa halin da take ciki nan da nan yasa wata safar hannun sa yasaka hannunsa a matancinta Maryam don zafi takasa buda bakinta sai hawaye take zubarwa don azaba anan likita yaga shi kendorden ya karye aciki ya janyoshi bansan lokacin 37 dana fashi da kuka da karfi kukan danake hankalin likita ya tashi sosai yace Baba kiye hakuri zata samu sauki akwai allurai da zamu yi. Washi gari da safe Murtala yazo harda kayan shayinsa bayan mun gaisa ya tambaye ni yaya mai jiki lokacin Maryam tana ta sharar baccinta takaici bai barni na bashi amsa ba nakalle shi kallon, banza murtala ka cuceni akaci amanita wannan yarinyar daka ke wulakantawa idon Allah ya tashi kamaka mahaukacin kasuwa ma sai yafi ka daraja, tana zamanta a gurina kazu ka karbeta kaje ka kunata kana kwance a gida har sati biyu amma bakazu kace dani komai ba ba ka kuma nemomata magani ka bata ba. To yanzu komai ya kare Maryam tabar gidan ka har abada kande ta satai duk kutun da ta dace ba zata koma dagi don kada zama ba tana neman kasheta kanji kana gani don ita takawo rashin imani duniya shine ta dauki kendir ta sokawa wannan yarinyar a matuncinta tana neman kasheta har lahira, to zamanta a agiadanaka yakare sai dai taje da yawo yayi kasake da kai yace babu damuwa Baba Allah yaba ta lafiya. Washe gari har yamma sai wajen magriba Bello ya dawo daga kano kamar yadda ya gaya mana zai gayawa abokinsa a kano, to haka akayi don abokin yace lalle a hanzarta kai Maryam ya ganta gari na wayewa Bello ya kawo mota, muka kama hanyar sai kano. Aminu Kano gurin abokinsa Dr Nasser inda suka bamu daki mu kadai dagani sai ita. Bello ya biya kudin komai da komai nan da nan ka fara fesa mata maganin nika jikinta allurai kuwa a kan lokaci badon kar nayi karyaba sai nace ammata ta 38 fi hamsin Allah cikin ikon sa kwana uku yarinya ta sami sauk: so sai har tana zama, tana kuma cin abinci sosai muna da kwana hudu ne maurtala ya zo duba mu yace Bello ne yagaya masu tun randa muka tahu, yanzu kusan nace komai yayi dai – dai a Maryam banda tafiya bata iya tafiya nayi - nayi da ita sai tace ba zata iyaba wai gabanta yana mata ciwo tana najin kamar zai fado idan ta tashi zata taka. To anan na fara fahimtar lahanin da kande tayi matane don haka nayi amfani da basirar mu ta mata nan da na ringa gasata a cikin rowan zafi sau uku arana kamar yadda a kewa mai sabuwar haihuwa cikin ikonAllah Maryam fita da ita filin Asibitin mu zaga ya, wani lokacin ma Bello ke dauketa yazagaya da ita, a haka said a muka shafe wata biyu cif a Asibitin Aminu Kano. BAYAN MUN DAWO GIDA Da sati daya Bello yazo yasameni yace baba ina son nan da sati biyu zan aiko komai. asa Bikinmu amma banason asa da yawa inason kamar sati uku idan ta kayan da za'a kaiwa Maryam ne zan saka mata komai agidan ta don inason na waresu banason hadasu saboda banason fitina inma zan hadasu sai in sun saba, duk wannan maganan da yakeyi ni dai nayi zugun na zuba mai ido ina kallonsa a raina inata sake - sake anya inyaji abinda ya samu Maryam zai yadda ya aureta kuwa? amma bania dai inji ta bakin shi tunda dule in gaya masa abinda ake ciki aure yawuce wasa. Na numfasa nace dannan dama akwai wata magana inaso ingaya maka (akan wannan yarinyar) watau wannan konewan da tayi banda ita akwai wani ciwo 39 daban da na rula ban gaya maka ba, ya dago kanshi da sauri yace wace magana ce Baba?. Na numfasa, kamar ka na fada to amma na riga na fara zancen kawai sai naci gaba, ai Bello ita, wannan mata da kake gani kande. .nan na kwashe labari irin mugun abinda tayiwa Maryam, kafin in kai karshen labarin bawanAllah sai naji kamar yana sheshekan kuka, naja dogon numfashi nasa gefen zanina na goge kwalla da suka tara mua idona nace sai fa hakuri. Bello. Ya dago kanshi yace mun Baba idan ahar a duniya tayi haka don ta rabani da Maryam ne tayi a banza don bazan taba daina sonta a raina ba, ita kuma muguntar ta Allah ya mayar mata kayanta Inna shiriyane kumaAllah ya shiryeta. nadago kaina nace amen bawan Allah, Allah yayi maka Albarka. Bana wata gudu da maganar mu da Bello akayia biki Maryam da Bell wanda kowa yayi sha'awar Bikin banda makiyarta, kande da murtala babu abinda ya fita na gudunmuwa saboda tsoron kande sai kudin sadakinta atana daya rinke wanda ranar daurin auren Maryam wanda baisan abinda ake bama ya sani saboda har ana daura auren akan sadaki dubu goma Murtala da kani na su suka fara shi ga aikin gida su Maryam budar bakin kande malam nawa ne sadakin yace dubu goma da saurin ta sai catayi koma kace sai dubu ashrin ya juya da sauri sai kace wani karamin yaro wai zaice a dawo ya fasa ya mayar dubụ Ashirin nan da nan akanina ya zuciya yace baza'a karaba abinda kiyi niyyar bata koa fasa mu Allah zai huremana yadda zamuyi to abinka da 40 sai wanda sai yadda akayi da shi haka mukayi iya kokarinmu duk na sayar da kiwona muakai mata kaya duk da Bello yace kar aje da akomai amma said a aka samu wani ta wajen dangin ubanta, wani kaninsa mai zuciya, kuma babban ma'aikacin gwannati yace in hara aka kaita ahaka ai sai a sai amata agori koa mun mance tanadaa akishiys ne? shine ya sanya mata duk wani abu da za'a gain adakian kowace ayargata. Nidai da naje naga dakin Maryam naga irin dukiyar ada aka shirya mata sai danayi kuka na kuama ce Allahamdulillahi. Zaman Maryam da Bello zamne mai tsafra wanda duk wanda yagani zai yaba tunda Maryam tana masa biayayya dai - dai gwargwado, Maryama ta samu tarbiyya maia kyau a wurina tunda bana sakara mata hasalima bana mata wasa irin na jika da kaka, ata wajen kande kuwa zan iya ce ta samu tarbiyar aiki tukuru da rashin son jiki, koa karkani bata dauki aikace aikacen cikin gidanta bakiana komai ba. Shi kuwa Bello, sai son barka tunda bai rageta da komaiba najin dadin rayuwar duniya, yana tattalinta ya kuma saketa a islamiyya anan unguwar tasu, gidan Maryam can dutse jihar Jigawa yake ita kuma kishiyar Maryam tana Hadeja garinsu Bello, saboda Bello ya koma can dutse da aiki yabar Babura. BAYAN WATA TAKWAS DA BIKI A lokacin Maryam nada ciki wata bakwai ciki mai laulayi mai wahalarwa da gasken gaske ganin haka Bello yazo ya dauki ni kullum Maryam cikin wahala take tayi baki ta rame batacin komai sai 41 madarar ruwa irin ta bature shima sai nam a mata take sha cikin na da wata takwas ne ciwo yayi ciwo bata ko zama batayin komai sai na mata, kofi,tsari zatayi sai na kaita. Bello ya matsu tuntuni muje asibiti nace naga asibiti bashi da amfani tunda anje - anje babu sauki to amma duk da haka Bello sai da yarinja yeni mukaje asibiti a daren wata Alhamis da ciwon yayi tsanani cikin yarina yin sama yana turowa mata kirjinta idon ta duk ya kafe ni dai salati da kuka duk nake hadawa saboda na tuna yadda mahaifiyata tatafi muna zuwa asibitin babban asibiti ne a dutsen suka turata a wani gado suka shiga da ita wani daki shikenan Maryam ni dai a wannan daki suka ye tsoke sokensu wannan ya wuce da farar riga wannan yasa safa a hannua duk ina kallonsa suna hada baki sona ta turanci sai dai wannan ya leko yace sannu Hajiya tun inajin Maryam har na dai na ji, muna zaune munyi zugum ni da Bello wata tazo tayi masa turanci ya tashi da sauri ya shiga dakin da aka kai Maryam ashe Maryam rai yayi halinsa. Allah yaji kanta yakauta zuwan mairo na kano dana share hawaye. Amina nace mai cewa ina labarin kande mairo aka ninfasa kande kowa itace mai labari don Lami ta haife musu da namiji ta gudu tabar musu ita kuma ta zama kasuwar gida kinga alhaki kwukkwuyo ana cewa Maryam yar iska anga iskanci ita kanta kande hakkin bai barta haka ba tunda ta zama abin kyama ga kowa tunda wasu kuraje ne suke fito mata sai suyi ruwa banda doyi babu abianda take don wani zuwa da muka yi bayan mutuwar Maryam gidana kansa ya cenfa tunda shi murtala sakamakon kulawa da 42 yasamu daga Bello tacan yin gurin aiki tasa ya sake aure ya kama wani gidan don haka yanzu sai yaga dama zai kalli gidan da kande take. kullum makota cikin rabon fada ita da magajiya babu wanda zaki tausayawa shin yaron da lami ta bari saboda baya samun kulawa ko kadan ita kakar wato kande kenan tana fama da kuraje yadda kuma ta mugunawa "yan uwanta babu wanda yake zuwa inda take tunda dama abinmda yake kawo su sabodaa murtala yana musu to itama ya barta, shi kansa murtala duk da cewa asiri kanade tayi masa akan Maryam din daban rokar masa Maryam ta yafe masa ba, da ya shiga wani hali. Shi kuwa kanina shine ya sami cigaban aiki ya dawao nan ita kuwa matar gidan nan Hajiya Rahma ita kawai matar kanin nawane Nafisa don haka da tace tana son wadda zasu zauna tare na amince don kawai na ringa motsa jikina tunda ita amatar ganina nawa bata barina nayia komai akinji dalilina na zuwa nan gidan Bello kuwa har yanzu yana zuwa gurinmu don yaso naci gaba da zama dashi nice taki tunda dai wanda ta hada ta mutu. yanzu haka mun kaia shekara rabonmu da Babura don haka bazan iya ce miki ko kande ta mutu ko tana da rai murtala yakan zo mugaisa amma ban taba tambayarsa kande ba saboda bana son komai sunan tan a karaji balan tana ita. Don haka Amina a duniya kayi gaski karka dauki wani ba naka bane inhar kana da tunani shine naka don sai kaga baka mori naka ba kamori nawani wallahi mata mu kulla don irin wannan kuskuren daga gurinmu yake tasowa idan kin to zarta danwani 43 kin wulakanta shi to kanki kikewa kunga da kande don sharrin son taga Maryam taje iskanci babu irin azabar da bata mata don kawai taje ta nemi maza ace yar iskace daya keAllah ba ruwansa kinga duk da irin gatan da takewa "ya"yenta sai mugun nufin da tajefi Maryam ya koma kan "ya'yanta alkairin da ta nufi 'ya'yanta ya koma kan Maryam da tayi gaskiya tad a duk haka bata faruba don haka mata mukiyaye mu saniAllah baya barci. Yana jinmu yana ganin yana kallonmu duk inda rauke karmu yarda duniya ta rudemu ta kaimu ta baromu don komai kika samu ko kike dashi anan zaki barshi babu inda zaki dashi daga ke sai likafaninki zaki yan uwa ayi tunani a kiyaye. Gaskiya Mairo labarin Maryam labarine da yake da abin tausayi, amma duk da haka zan iyace miki labarin yafi na Maryam ban tausayi, al'ajabi, mamaki don ni duk wanda yaji labarina zaiso ya ganni ido da ido. Nikuwa badan babu kyau bincike bad a zance zanso nasan labarin ki don inaga ci yan dubarun mu na tsofaffi ba za'a rasa shawarar dazan baki ko kuwa? ina fatan ba zakiyi tunanin idan nasan sirinki ko zan yi miki wani abu kamar juya baya ko tona asiri in zaki duba ki gani ina da hankali, sannan yarda ita take kawo komai don kuwa yarda dake da nayi ita tasa na kwashe labarInna nida jinina wato Maryam na baki. Haba Mairo duk wadan nan tunanin ma bai kamata kiyi ba domin kuwa idan har banyi niyar baki labarin ba da bazan fara furta miki ina da wani siri a zuciyata, don haka mairo zan baki labarin zuciya 44 daya babu komai araina dake sai dai inason ki bari sai jibi don kinga yanzu dare yayi tunda ana kiran sallar naje gidan kanwata Bilkisu saboda inason tasan nan gidan don tunda ta dawo nan bata zo nan ba saboda rashin sanin gidan inaga kuma zankai yamma don haka labarin sai jibi idan Allah ya kaimu. To Amina ta Allah ya gwada mana ganin jibin Mairo ta fada cikin sanyin murya da gani kasan badan taso ba dadin manya kenan duk yanda kake dasu sun ya danne damuwarsu komin dacinta hakan Amina kota kula ta tashi na nufi bandaki don daura alwala magariba. Washe gari Amina na tashi wajan tara bayan tayi sallar Asuba ta koma sai karfe tara ta tashi ta share dakin da take kwance ta gyara katifara data atashi a akanta ta wauce bandaki tayi wanka tazo ta cada kwalliya da wata atamfa jah sabuwar fitowa mai suna three elephant tayi kyau ta kara tunda daman duk wanda yaga Amina yasan kyaukyawa ce don haka yau ta kara akan nada ta wuce kichin ta dako dumamen tuwo wanda yasha man shanu da yajin daddawa ga kuma rowan shayi bunu daman can Amina tun tana karama ba sem da safe taci komai inba tuwo ba don ita batason wani dankali ballai kwai. In babu sauran tuwo ne take siyar masa gurin wata mata ya Bauchi. Amina ta zauna cikin nutsuwa ta gama cin abinci ta mayar kwanan kichin ta wuce dakin Anty Ramatu ta sameta a falonta suka gaisa. Anty cikin fara'a ta kalli Amina gaskiya kinyi kyau sosai fita zakiyi ko kokuwa sirikin namune zaizo. Amina cikin 45 jin kunya ta rufe idonta haba Anty sai zanko zanyi bako zanyi kwalliya zanje gurin Bulkisu ne kinsan an kusa bikinta kuma haryau bata san nan gidan ba, ah ya kamata ki akaita nima fitar zanyi zanje har wuse II hanyarmu daya? Amina cikin dariyar farin ciki tace wallahi Anty harnaji dadi don banason zuwa gidan su Bilkisu a Taxi don tafiya lungu cikin maitamane, Anty ne maia cewa babu komai bari na doko jakata, itama Aminar cikin sauri ta shiga daki ta dako Jakarta da takalminta bakake da mayafinta jah kalar atamfata. Ta leka inada mairo take wanke - wanke tayi sallama suka fita, suna tafiya Amina nayiwa Anty nuni da hannu har zuwa kwanar gidan su Bilkisu ana zuwa bakin gate Amina tace to Anty koma daga nana ga gidan nan sukayi sallama da nufin inta gama hirar ta zata koma da kanta basai ta biyu mata ba. Amina na shioga get din gidana su Bilkisu tun a bakin masallaci taci karo da mutumin nata Hassan ya tabbatar mata da kawar tata tana nan kafin ta karasa ya rigata dan ta tsaya anan kasa tana gaishe da Hajiya Innar su Bilkisu bata bar falon Hajiya Bilkisu suka zo ita da malam Hassan nan da anan kawayen suka rungume juna don murna Hajiya hafsatu ta tsaya tana murmushi na ganin kawayen yadda suke son junansu nan dai suka hau saman Bilkisu, suna shiga suka taba hannu Bilkisu ce mai tambayar Amina ya Anty aid a gain nasan tana kular mini da ke yadda ya kamata kinga kika zama wata katuwa Bilkisu har yanzu dai kina nan da zolayar ki ke kuma fa itama Amina ta rama nan dai suka ringa yiwa juna tsiya kande mai 46 aíki gidana su Bilkisu ta shigo da kayan abinsha kaka - kala dana tandar baki irin dai na masu hannu da shuni. Haka kawayen suka wuni hira lokacin sallah yayi sukayi masallacin gidan sukayi sallah suka wuce kan table nacin abinci nan ma suka ci suka kuma dasa wata hirar sai wajan biyar sannan Amina ta yunkura tace zata tafi, shine Bilkisu da yanzo mota ita da Hassan suka tafi kaita gida lugue, unguwar dana koma kenan da zama yanzu gidan aAnty Ramatu. Muna zuwa na tarar da mairo ita kadai a tsakar gida tasa kujera 'yar tsygune tana ta sakatar hakorinta ita kuma Anty tana falonta tana kalon wani sabon wasan Hausa sansani, mairo da saurinta ta taremu duk da bata taba ganin Bilkisu ba abinda tayi mata a rannan naji dadi sosai tunda ta nuna kamar da dade da saninta har ita kanta Bilkisu yadda ta amsa taryar mairon naji dadi sosai. bayan sun gaisane muka wuce fakon Anty ni kuma na wuce kichin na dako mana ruwa sha da kunun aya, muka zauna muna tay Anty kallon film din yadda Aunty take jan bilkisu da hira yayimin dadi sosai, ko da yake dai daman banyi zatron komai daga Anty ko kare na kawo gidan inaga zata karramashi a yarda nake gani muna cikin hirarmu akayi kiran sallar shine muka tashi muka yo alwala nayi mana shinfidar abin sallah a dakina don a lokacin mairo harta idar da sallah tana lazumi. Ina idar da sallah naga wata katuwar jaka na ke tambayar mairo ko munyi bakune shine take gayamin Maryam ce kanwar Hajiya da kawarta suka zo amma 47 sunje cikin gari su dawo ta kaici yas. kasa daurewa said a na nuna bacin raina a fili don kuwa zuwan Maryam gidan nana yana dagamin hankali ita da kanta mairon ta gane banji ba dadin zuwan Maryama din don haka tace wania abine na dana saki raina nace babu komai. Bilkisu tana idar da sallah tace zata tafi gidan don bata tukin dare daddy ya hanata nayi - nayi dasuma su tsaya suci abinci sunce a'a na kaita sukayi sallama da Anty muna zuwa bakin mota Bilkisu tace Amina naga zuwan zakin anan ya tayar miki da hankali ko? akwai wani abune idan har kina ganin akwai wata fitina mu koma gidanmu da zama in yaso idan kuka tafi kya dawo a'a babu komai, ke dai Amina kina sonki rinka boyemin damuwar ki meyasa wallahi ba haka bane Bilkisu kina daya daga cikin mutanen dana yarda dasu haka kullum kike cewa Amina Allah yasa har ranki da gaskene to shike nan zan tabbatar miki insha Allahu acikin satin nan. Bilkisu tasa hannu a cikin mota ta mukowa Amina leda cike da kaya atace gashi inji Hajiya wannan kuma Handset ne nina hada miki saboda inason mu ringa magana numbarki 08034477288 insha Allah zanzo jibi in duba lafiyar ki zanzo miki damai gidana tunda ke kinki aure ta shige mota tana dariya na bita da godiya nace a araina Bilkisu sarkin zolaya Na shiga gida da farin cikin kyautar da akayi mini da akin cikin zuwa Samira don kuwa nasan irin masifar da take hadamin don nasa komai Allah zai shige mini gaba. 48 Ina shiga daki na saura sallar insha'I don na tarar mairon ma sallah take bayan na idar ne na bude ledar da Bilkisu ta bari naga ashema yikan shafawane da turaruka na jikia dana hamata nayi farin cikin kyautar Hajiya Hafsatu korai don duk abubuwab banita bani shine lokacin danake bukatarsa. Har muka ci abinci muka gama hirar mu muka kwanta nida mairo su samara basu dawo ba sai can wajen karfe sha biyu harda rabi naji su suna buga gida shine mairo taje ta bude musu suna shiga kasan a buge suke sunsha giyarsu sun koshi suna zuwa samira tazo bayan ta kwanta harda cewa wannan shegiyar maiyar haryanzu tana gidan nan ashe itama kawar tata haka ta sharbu a kasa mairo dai sai kallon ikon Allah kawai take tunda ita agurinta sabon a bune. Dana lura barci irin na mashaya ya kwashesu Maryam sai na tashi cak na koma dakin su.... tunda daman basa nan sunje hutu gurin dangin babansu. Tun asuba natashi nayi wanka na shirya don nariga ba yanke zan koma Nyanya da zama har sai sunbar garin zan dawo kafin ma su tashi naje na dumama tuwo na dauki karamar aakata na zuba kaya na kala uku da kayan shafe - shafe suma nadau wanda zanyi amfani dasu na sanar da mairo inason zanje Nyanya amma bazan dade ba zan dawo ko kadan mairo ba taji dadin tafiya ta ba, na leka nace da Anty an aiko nazone ana nemana da sauri na nuna mata wayata na sanar da ita number na wuce sai Nyanya. Ina zuwa nayima Bulkisu waya na sanar da ita idan dan ana nema na ina Nyanya kwanana biyar acan sannan na dawo 'don nasan iskacin Maryam ta 49 taji ina zuwa na tarar ta wuce amma tabar min sako don kuwa ta kwashe mini kayan manshafawa da Bilkisu ta kawo mini ta bude jakata ta dauki duk wani kayan sawata sabo ta kalma na bata bar su ba,yaba suma ta dauki wanda taga yayi mata, jakatama ta ratayawa guda biyu ta dauka ko miye dalilinta nayimin haka? Na duba gurin kayan mairo ban ga komai ba jikina ya bani lallai mairo ta kula Maryam akan daukar mini kaya harta bar gidan ai kowa yau komin dare zanje na nemo mairo na wuce falon Anty na tarar tana cikin daki nayi sallama ta amsa tacce na shigo ko gaisuwar kirki ban mata ba nace ina mairo shine take gayamin wai tun jiya da safe lokacin su Maryam zasu tafi ita dai batasan taka maimakon abinda ya hadasu ba taji dai samira tana ta zagin mairo. To kinsan nima ban karfin abinda yafi haka ba agurin Samira don haka naba mairo hakuri nace ta kyaleta ita kuwa samira sai kara zaginta take don haka na komo dakina na zauna bacin sun tafine na duba na tarar mairon ma tabar gidan don haka yanzu tunda kinzo ina ga yakamata muje gidan su mairo mu bata hakuri don nasan zatace na koma daki na kiwa samira magana kema kuma kinsan nima banfi karfin hakan ba. Amina da Antyinta suka dunguma gidan su mairo suna

Chapter 3 of 11