Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
9 / 12
kwari wato har da gupu ko? Muneeba ta yi murmushi ta dan matsa daf da 140 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria shi tace, "Sannu da dawowa ya Ofis", ya amsa a dakile "lafiya Lau" tasan ba wata hira da zata biyo bayan hakan sai ta juya zata bar dakin sai ta ji ya ce 'Ina son daga yau ki ringa yin girki, don Suwaiba ba zata iya ba kin dai san cikinta ya tsufa muna sa ran haihuwarta ko yanzu ko anjima. Ta juyo tana dubansa cike da bayyanuwar mamaki a fuskanta ta ce "Amma a gabanka fa nace ta hakura da yin girki zan dinga yi har Allah ya sauke ta lafiya" tace in barshi zata cigaba da yin abinta, ni to meye laifina ko kuma ta dauka girki da mijin zan amsa gaba daya? Wallahi ni ba nufina kenan ba, ko yanzu zanyi girki kaci gaba da kwana a'dakinta ni bani da matsala. Ta juya za ta fita ya sake magana, ki`je ki sama muku abin da za ku ci don bata girka komai ba bata jin dadi, ta ce "Allah ya sawwake żo mu je Baffa" Ta kamo hannun yaron uban ya dubeta a kaikace ya ce, barshi ki je ki yi aikinki tunda namanshi za gutsura idan kin barshi ta dubeshi cike da tuhumar kalamansa suna hada ido yayi saurin dauke kansa itama sai ta dauke nata kan tare da adiye kalaman da ta so furzarwa, taja jiki ta bar masa dakinsa. Tun daga ranar ita ke yin girki da hidimar komai na gidan, amma maganar rujia kwana dakinta kota kwana dakinsa duk bata danan sai Suwaiba. 143 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Wannan karonma aiki akayi wa Suwaiba data tashi haihuwa ta haifi diyarta mace mai tsananin kama da ita, haihuwar an kashe kudi sosai a asibiti saboda matsala da akayi ta samu da Suwaiban taki natsuwa dinkin ya warke shi yasa sau biyu yana budewa ana sake dinkewa saida tayi kusan sati uku sannan aka sallameta a lokacin Hajiyarta na Dukku bata da lafiya shi yasa Goggo ceta karasa zama da ita a asibitin har aka sallamesu suka dawo gida. Shirye-shiryen suna Suwaiba ke tayi, hakan ya tunzura zuciyar Goggo har ta 6ara tayi maganawa Suwaiban 'Haba Suwaiba wane kuma taron suna za'ayi ai kyaji tausayin mijinki irin wadannan makudan kudi daya kashe a asibiti sannan yanzu a sake kashe wasu a taron da bai zama dole ba haba a dinga yin abu da tunani ana tausayawa abokin zama". Wannan kalamai sun kular da zuciyar Suwaiba wato ita ga me da bata son ya kashe kudinsa to wallahi bata isa ba kudin sai ya kashesu, ko tana so ko bata so. Ba ta dubi ko inda Goggon take ba tayi maganganun son ranta, "Tabdi kada ayi taron suna, ai wallahi sai anyi tunda shi mai kashe kudin baıyi kukan bashi da kudi ba, haka kurun sai a ari bakinsa aci masa albasa, sai a bari yazo aga maganar wanda zaiji" Goggo ta sake tunzura dama ta 'ura da take taken Suwaiban kiris ya rage wata 144 Π WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ran ta lakucewa Goggon hanci tunda ta riga ta sami miji a hannunta, to bata isa ba za ta yi maganin rashin kunyarta. Ta ce, Lallai Suwaiba wuyanki ya isa yanka, tunda kika iya zakalkalewa kina min rashin kunya son ranki, uwarki ma Hajiya Harira za ki iya mata tunda mun bi dare munbi rana mun samo miki 'yanci a gurin miji wato za ki juya shi nima ki juyani to baki isa ba ni na haifi abina, na raini abina na sha wahalar da gwagwarmaya har sai da naga rayuwarsa ta inganta to ba kuwa zai yiwu rana tsaka ace za'a wahalar min da shi ba don an ga yana da abin hannunsa suna ne wallahi in ban amince ba ba za a yi shi ba gara ma abini a sannu”. Suwaiba bata sake tankawa Goggo ba amma sai kunkuni take yi tana fadan bakaken kalamai wanda wasu ma Goggon na ji amma ganin Munceba ta shigo dakin ne ya hana Goggo tankawa itama Suwaiban ta rage kunkunin da take yi amma da kallon fuskantar ka san an ta6o ta. Ruwan wan kan jaririyar ne Muneeban ta shigo da shi, ta dau co bahonta ta juye shi sannan ta dubi Goggon ta ce "Goggo kawo ta inyi mata wankan yau in hutassheki" ta wani dubeta cike da mamaki tace "Kiyi mata fa wankan kika ce? To ni dai ban ta6a ganin wanda bata haihu ba ta yi wa Jariri wanka ba, ki bari idan ki ka haihu "sai kiyi abinki ba mai hanaki amma ki daina wannan WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zana karanbanin akau jaririn wasu gara kiyi a naki in kin samu. Maganar Goggo ta Kona ran Munceba amma sai bata nuna ba tace "Gani nayi Baffa ma tun yana jariri nake masa shi yasa" ta cc, "Shi dinma ai saida yayi Rwari kike masa kuma lokacin na kom Dukku, wannan ma sai ki bari sai na koma ba za'a yi a gabana ba". Da Mujeeb ya dawo Suwaiba tayi sauri ta tareshi a dakinsa da maganar yin taron suna, ta lallaße shi har ta amshi kudaden da zata yi sayayya ta dawo dakinta ta zura idanu don ganin yadda zasuyi da Goggo, tunda sun riga sun gama shirya komai. Tana cikin dakin baccinta taji shigowarsa faionta inda Goggo take. Tzna jin hirarrakinsu har Goggon ta sako maganar suna ta nuna masa kada ayi taron suna don zai wahalar da kansa ne, banda wahalar kashe irdin asibiti da akayi ta yi ta kara da cewa, Haka yınyar nan ta zakalkale tana min fitsara don kawai nace a hakura da suna tunda ba dole bane, kuďi kam ai an kashc su a asibiti tunda ba hakosu ake a rami ba, su 'ya'yan yanzu sam basuda tausayi su dai a kashe m1 kudi turda basu zan zafin nemo su ba to baza a taro ba tunda ba b huwar fari bune, a na Baffa ai anyi" ta kare maganar cikin bashi umurmi. L WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Ya fanyi shiru, itama Suwaiba a daki shiru tayi ta natsu sosai don jin amsar da zai ba Goggo ta amincewa da umurninta ne ko akasin hakan, duk da tana da tabbacin ba zai taba ketare maganar da suka riga suka yi su ka gama ba har sun kai matsaya bata ankara ba sai ji tayi yana cewa Goggon 'Ina ganin Goggo hakuri zakiyi suyi taron sunan tunda ta kwallafa ranta tana son tayi maganar kudi ki daina damuwa bani da matsalar kudı sai muyi fatan ayi taroň lafiya a gama lafiya. Bakin cikin Goggo daya yadda Suwaiban taci galaba a kanta lallai aikin boka na tasiri akan danta tunda gashi yanzu kota bashi umurni, Suwaiban na'bashi nata zai tsallake na Goggon ya aikata na Suwaiban Tirkashi yau fa ta debo ruwan dafa kanta, dama tsuntsun dayaja ruwa shi ruwan ke yiwa tsinannen duka. Anyi taron suna da kashe kudi na ban mamaki wanda ba'ayi ba a haihuwar Baffa tunda ragamar gudanar da komai na taron sunan Suwaiba ya dankawa sabanin haihuwar Baffa da Muneeba ce Jagorar komai. Hatta da zannuwan da Suwaiban ta sa na fitar suna rantsattsune (Super Exclusive) ne guda biyu sai Lesuna manyan (Swiss) guda uku sai Shadda`da suka sha aiki an jera stones dinkin yayi kyau matuka guda biyu da Materiyal guda biyu masu tsada. 147 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Haka ta d nga shiga sutura tana sauyawa tambe wata amar kai da gani dai ta kama miji a hannunta. Muneeba kuwa ko Ingila bai jefeta da ita ba, Alla', yaca tana da sababbin dinkunanta su tasa ranar senan sh. yasa babu wanda zai gane ko anyi mata ko baıyi mata ba. To 6angare Sobeniyos din da Suwaiban ta raba ma wanda ta ga dama shi ta ba, haka nan 'yan uwa na Dukku wanda take shiri dashi shi taba duk wanda bata shiri dashi to ko kallon arziki bai isheta ba balie ta bashi. Wannan iskancin na Suwaiban ya tunzura Goggo matuka har ta yunkuro zata je dakin Suwaibar don ta ji dalilin hana wasu da tayi taba wasu, su fadima sunsan idan taje rashin kunyar Suwaiba zata iya mata shi yasa suka hanata zuwa har Zuwaira ta kara da cewa "Kinga waccan haihuwar ta Baffa da yake komai na hannun Muneeba ai wa ya samu, wasu ma har da kari wannan ko ya damka mta komai ai dole tayi wulakanci, in jinta da akace tava matar kawu Lawal da za su tafi, wai taron sunnan da aka bana ayi shine yanzu za a dameta taba mutane abin suna, ita fa taro don jama'arta tayi ba on jama'ar wasu ba naso in fita inci nutuncinta Goggo Hinde ta hanani, r iskar yarinya wato ta samu wuri shine zata baza shanyarta yadda takeso, to wallahi zan gyara mata zama. WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Adda Fadima tayi murmushi tace "Habawa kuma dai ai zaku gani indai halin wannan matsiyaciyar yarinyar ne dama ku kukc goyon bayanta, sannan ta samu Goggo na daure mata kugu tayi tsiyarta yadda take so yaushe Munecba za'a zo gidan nan ta hana mutum abu balle har ta gaya masa bakar magana ko da yake Goggonma bata kyaleba balle wani banza, ni shi yasa ba ma shiga shirginta balle ta rainani, wanda ko mijin daya ajeta bai isa ya rainani ba balle ita". Kowa fa a dakin yayi ta tofa albarcin bakinsa akan irin share guri da Suwaiban tayi ta mike kafa take baza abinda taga dama babu mai yi mata birki Goggo dai bata ce ta tafasa a sauke ba, saboda ita fa har yanzun bata san ana aibunta Suwaiba duk da irin rashin kunyar da take zubawa a gidan tafi sonta fiye da Munceba duk da cewar son da takewa kishin Mujeeb yana wa Muneeba yanzu babu shi, amma hıkan bai sa ta sassauta mata ba, sam babu gurin wa nda Muneeba ke jin dadi a gidan nan a halin yanzu. ***** ***** Wata sabuwar tashin tashina da taso a gidansu Munceba kuma tace kwace rikon Baffa a hannunta da Goggo ta yi bata mai da shi hannun uwarta, acewar Goggon tunda Muneeba bata zama kullum 149 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zara tana ysakaran to ba zai yiwu ba a dinga barinawer yaro a hannun Karime mai rainonsa, alhalin ga uwarsa a gida don tana takamar ance an bata shi, in gaskiya ne ita uwarsa ce kamar yadda lake iKirari toa dunga tasa shi a gaba tana zuwa dashi makarantr in kuwa ba haka ba to dole da ya dawo g rin u varsa. Muneeba sam bata gasgata zancen Goggo zai tabbata ba sai da ta dawo makaranta ta iske Goggo tasa Karime ta debo kayan Baffa tas dake dakinta wadanda tayi masa dirowa guda na komai nasa data dawo ta iske Karime zaune a falonta ta zuba uban tagumi fuskantar kunshe da damuwa, da ganinta zaka san wani abu na tashin hankali ya sameta kvi tsaye Munecba hayi ta shiga said a ta fito ne, sapuan ta lura da hulin da Karimen ke ciki. Ta matso kus. da ita tace, Karime lafiya na ganki haka? Ina Baffa? Don nasan in ba dalilin Baffa ba zan ganki hak. 'a?. Karime ta dan goge guntuwar kwallar dake idanunta tace "Dazun ne muna zaune a tsakar gida 11 Baffan yana ta yawonsa, sai Goggo tazo ta Jaukeshi suka shiga dakin mamansa sun dade a car., shine ta fito tace in kwaso tnasa kayansa dake dakinki kada in bar ko wando in kuma na rage ko aya Saya ne sai taci mutucina, shine na kwaso mala duka har da pampers dinsa data kalmansa da salabbin kayan da kika siyo masa duk na bata, wai 150 WATA KU'SAN 2 Rahmatu Hassan Zaria daga yau ya koma fakin mamansa, wallahi ni banyi masa komai ba. Nan da nan hawaye ka cika idanun Muneeba, tausayin kanta mai tsanani ya kamata Allah sarki duk fa akan rashin haihuwa ake mata wannan wulakancin da nuna iyaka, itama Suwaiban ai ba rawa tayi wa Allah ya bata ba ganin damarsa ne tana fatan itama ya bata masu albaka. Tayi saurin goge kwallar da tazo idanunta don bata son ta nuna butulcewarta ga Allah akan bai bata haihuwa ba alhalin ya bata wasu ni'imomi masu dimbin yawa da mul manci a rayuwarta, wanda in aka dauki guda daya kacal ya fi ni'imar a baka 'ya'ya misali lafiya kadai idan Alleya baka ya baka babbar ni'imar da ta wuce ka sami 'ya'ya. Takaicinta daya na yadda ake ce son rabata da yaron alhalin sunyi shakuwa irin ta da da uwa shakuwar da idan aka za'a rabashi da ita hakika an zalunci yaron itama an zalunceta saboda zasu shiga wani hali ko da yake so'akeyi aga iyakarta to amma zata bari wanda ya bata kyautar dan yazo taga hukuncin da zai yanke. Sam kasa cin abinci Muneeba tayi saboda rashin Baffa a tare da ita hakan ne yasa ta aje abincin ta nufi dakin Suwaibar sallamarta kawai Baffa yaji ya taso da gudunsa har yana faduwa yazo ya kankameta yana fadin (Maama) da na abinda ya iya fadi kenan sai wani lokaci yake fadìn Baba. 151 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Ta dauke shi ta rungume a jikinta wani sanyi ta ji ya ratsa zuciyarta hakika kauna ta jini daban take, ita kam tana jin a duniyar nan babu dan da zata so ta kaunace shi irin Baffa kai ko dan da zata haifo ne, sai dai soyayyarsa ta biyo bayanta Baffa. Ta risina gaban Goggo dake sakawa takwararta Rahina kayan sanyi tace, Sannunku Goggo kun wuni lafiya? Ta amsa a dakile tamkar mai ciwon hangui, Lafiya Lau. Muneeba ta kai hannu ta shafi kumatun jaririyar tace "Goggonmu har anyi maki wanka, ina kuka ana nan anayi? Daga Goggon har Suwaiban da ke gefe tana ninke kayan shanyar Jaririyar babu wanda yace mata ci kanki. Ta aje Baffa tana cewa Baffa na zaune in goya Goggo, Sarkin Kishi yanzu zakace baka yarda sai dai kai a goya ka "Ta dubi Goggon ta ce "Goggo tunda kin gama shiryata kawo ta in goya ta "Goggo ta girgiza kai tace A a ki barta kawai bana son a fita da ita a kwasar mata sanyi mura take yi shima wannan da ake gararamba dashi a hannun mai aiki yau na amso shi ya dawo hannun uwarsa đon ba zai yiwu ba ke ba kya zama shi a barshi hannun waccan yar yarinyar ca itama bata wuce ayi nata rainon ba, suna walagig a tsakar gida to ba zai yiwu ba, ko ta kama ta rufe su a daki ita dashi kamar wasu masu laifi shi yasa ni yau na dawo 152 이 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria dashi gurin uwarsa kuna babu wanda ya isa ya karya umurni na che!. Munecba idanunta cike da hawaye ta gurfana gaban goggo ta ce “Kiyi hakuri goggo don girman Allah in dai wannan shine dalilin amsar rikon Baffa a hannuna to zan dinga goya shi ina tafiya dashi makarantar, tunda ma na kusa gama karatun". Goggo ta kyabe baki ta ce, ai ko fasa zuwa karatun za ki yi saboda rikon Baffan ya dawo hannunki ba zai dawo ba, in fitsari banza ne kaza tayi mana in haihuwar a sama ake samu ki je ki haifi na ki sai ki mallake abinki baki mallaki na wasu ba ni na taba ganin inda akai haka: Gwiwoyin Muneeba duk sai suka saki tana durkushi gaban Goggo ta kasa mikewa saboda kalamanta sun soki zuciyarsa, shikenan ta san tun da goggo ta raba ta da Baffa to zance ya kare, Mujecb bai isa yace zai dawo mata da yaron ba, amına duk da haka zata kwatanta kai masa kokenta, ko Allah zai sashi yayi nasarar canza ra'ayin Goggon tunda shi ne ya bata kyautar yaron. Ta mike tana sharan kwalla rungume da Baffan zata bar dakin Goggo ta dubi ta tace, Aje shi kada ki tafi dashi yazo ya hanamu bacci anjima, duk da yanzu m ganinki da yayi ba zanıu iya tsayar da kukan da zai yi ba idan kik tafi ni na rasa jarabar da kike durawa yaron nan da har ba ya kaunar kowa sai ke, uwar ma da ta tsuguna ta haife shi baya 153 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Kaunar zama da ita balle mu wallahi kiji tsoron Allah!. Muneeba ta ce, wallahi ni ban taba bashi wani mugun abu don ya manta da wani ba, balle in bas hi ya guji uwar data haife shi, son da nake masa na jini ne kuma na tsakani da Allah. Ni kuwa meye ribar da zan samu idan na raba da da uwarsa? Ai da in zamo silar haka gara Allah ya dauki raina. Au sau nawa kuma akayi haka, ni nan da ban tashi tsaye ba ai da tuni kin rabani da nawa dan, sai Allah yasa kurwata tafi taku keda uwarki, to jikana yafi karfinku! Kamar yadda nafi karfinku. Muneeba ta kai iya wuya da wannan irin muggan kazafi da Goggo ke dora mata ita da uwarta kazafin yin asiri wanda a rayuwarta bata taba jin ko sanin Innarta na yawon asiri ba, amma kullum Goggo sai ta jefeta da mummunar Kalmar nan ta yin asiri bata san lokacin da bakinta ya furta kalmomi masu zafi ga Goggo ba" "Masu dai son rabaki da danki suna nan tare dake amma ni bana fatan in rabaki da danki tunda banyi gadon yin hakan ba da inga ranar gara Allah ya dauki rayuwata inje in hadu dashi satin-alin ban dauki hakin kowa ba". Ita kanta Munceba ba a san lokacin da bakinta ya iya furta wadannan kalamai ba kuma tana fadan su ta juya tayi ficew rta, tana ji Goggo na cewa, Dawo ki aje mata danta, tunda bake kika 154 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria haifar mata ba, ai shi yasa ma Allah bai baki haihuwan ba na wani ma kin mallake kina iko a kansa ina ga naki da kika Haifa vallahi ko kin tafi da shi zan zo in dauko shi tunda dakin naki ba bako na bane? Da Munceba bata dare da Mujecb ya dawo tunkare shi da maganar ba, saida ya dade da dawowa don a tunaninta Goggo zata yi masa maganar sai taga alamun bata yi masa ba, shine ta same shi a dakinsa tunda yanzu bata cika zuwa dakin nasa ba a dalilin ya kafa mata dokar in ba wani abu zata kai masa ba ko zata amsa ko wata magana to tadan saurara masa da biyo shi fakinsa da sunan kwana in yana bukatarta zai kawo kansa, a haka suke zaune kuma tun daga lokacin bai biyo ta dakinta ba balle yazo don bukatuwarsa sai ta zube masa ido kawai tare da Addu'ar Allah ya iyakance wannan matsala da suke fuskanta yana zaune bisa kujera mai zaman mutum uku (3 seater) tayi sallama ya amsa mata da kyar, kallo daya ya yi mata ya dauke idanunsa bata damu da hakan da ya yi ba, domin idan da sabo ita kam har ta saba da irin wannan ko'in kular na mijinta a gareta. Ta nemi gefensa ta zauna tare da yi masa sannu da hutawa ya amsa a dakile hankalinsa na kan jaridar da yake nazari ta (Blue Print) ta dan dube shi tace ni kam đai har yau na yi iya bincike na na kasa gano laifin da na yi maka, tunda kullum 155 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria idan na tambaycka sai kace ban yi maka komai ba, in kula shin an taba nuna wa mutum halin ko alhalin bai yi laifi ba? Wallahi ban jin dadin irin wannan zaman da muke yi nafi sabawa da zaman auren rayuwanmu ta bava cikin so da kaunar juna da kulawa da tarairayar juna ka tausaya mun na rame na futa hayyacina duk a dalilin juyamun baya dakayi shin da wanne zanji da matsalar data kunno a tsakaninmu ko kuwa da yanayin zamanmu da Goggo, na rasa mai na yi wa Goggo a duniyar nan ta tsaneni, tamkar ni ba jininta ba ce, tafison Suwaiba dani alhali nice dolen ta, duk irin rashin kunyar da take mata bata gani, sai ma dada fifita takeyi akaina, kuma hakan bai sa na daina yin mata biyayya ba, sannan yanzun ban san mai na yi ba ina makaranta ta ce Karime ta hado kayan Baffa a daki na wai ta maida rikonsa hannun uwarta, tunda ni ban zama sai dai in barshi gurin 'yar aiki, alhali ko da can haka ake yi tunda ko muna gida daga ni sai ita Karimen yafi yarda damu, da can duk ba'aga cewa da matsala ba sai yanzun da ake son rabani dashi alkawari ne ka riga kayi cewa ka ban Baffa, saboda haka ina rokonka daka dawo mun da shi, na yi mugun sabo da yaron ta yan la ba zan iya rabuwa da shi ba, kafi kowa sanin shal uwarmu don girman Allah ka tausaya min. Tun da take maganarta ai dube ta ba har sai da ta kai aya a sannan ya daga danu daga jaridar da 156 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria yake dubawa ya dubcta yace, Duk na ji bayananki, yanzu kin kawo mun karar Goggon ne a kan ta yi maki ba daidai ba ko mc?. Tayi saurin girgiza kai tace, Ni ba kararta na kawo ba, ina dai rokonka arzikI ne kasa baki a dawo min da Baffa wallahi yaron shine farin cikin rayuwata a halin yanzu, yana debemun kewa yana sani cikin nishadi da farin ciki rashinsa tare dani zai jefeni cikin Kunci da rashin walwala wallahi zan iya kamuwa da ciwo dalilin rashinsa kusa dani. Cikin maganganunta ya lura tana cikin matsanancin kunci saboda halayyar da suka shiga а zamantakewar aurensu, wanda shi baisan me ya same shi ba sam, sam ya ji bata cikin zuciyarsa ko kallonta yayi sai ya ji bakinciki ya taso ya tokare masa, a kahon zuciya, idan ta matso jikinsa kuma sai yaji tamkar ya hankadeta ko ya shaketa saboda tsanarta da yake ji, balle kuma aje ga batun kwanciya a tare har ya sadu da ita, sam baya jin sha'awarta dukkanin sha'awarsa nakan Suwaiba, ko da ta haihu yanzu baya jin sha'awar kusantan ta, duk da a matse yake gashi bai iya neman matan waje ballantana yaje ya rage zafi, shi kam ya rasa dalilin takamamen abun dake masa yawo a kwakwalwa, ko da yake ya taba gayawa wani amininsa a gurin aiki sai yake shawartar sa da ya dage da Sallar dare yana kuma addu'a da sadaka insha Allahu kullin da ke 157 tattare da zuciyarsa zai WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria warware, to amma matsalar da yake fuskanta sam baya iya tashi cikin dare yayi Riyamul laili balle addu'a, azumin Na fila da suke yi na litini da Alhamis ya daina yi dama muneeba ke tunatar dashi, sadakama idan zai bayar sai yaji zuciyarsa na hanashi, shi kam yana cikin tasku bai kuma san yadda zaiyi ba. Munceba ta katse masa tunani da cewa, "Don Allah kayi wani abu akan al'amari na, ka tausayamin kasan ni abin a tausaya min ce ya ce shi kenan tashi ki tafi zan san abinda zan yi zan nemeki. Ta mike jikinta a sanyaye ta tuna da dakinshi shine makwancinta, amma yanzu da aka shiga tsakaninsu har umurnin ta bar maşa dakin yake bata, babu ruwansu da ko wani hali zata shiga a dalilin kaurace mata da yayi na wata da watanni, ga ta lafiyayya ta ci mai kyau ta sha mai kyau ta kwanta a mai kyau aiko dole ta bukaci mijinta kusa da ita, amma ya zata yi dole ta cigaba da tausasar zuciyarta tana ba zuciyarya hakuri har Allah ya kawo daukinsa a garesu. Tana isa dakinta zuciyarta ta kasa hakurin rashin Baffa ga uwa uba rashin mai gayya mai aikin uban Baffa wanda idan daya baya tare da ita zata kasance da motsin daya akusa da ita koma su kasance su uku a tare sai gashi ita kadai tal a dakinta yanzun shikenan haka zata rayu ita daya babu mai debe mata kewa? Wani babin kuka ta 158 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria bude wanda saida dare yayi nisa sannan ta hakura a dalilin ınatsanancin ciwon kai da zazzabi da sukai maya rubdugu suka rufcta, duk da haka bata iya kwanciya ba sai ta gabatar da sallar Nafila. tayi addu'o'i sannan tasha magani ta kwanta lokacin Uku da Mintina biyar na dare. Ga dukkan alammu kwana Baffa ya yi yana masu kuka, don kuwa tunda ta tashi yin sallar subahi take jin kukansa har tayi sallah tana zaune tana lazimi bata daina jin kukansa ba zuciyarta ta soma yi mata zafi don bata son ko yayane ta ji kukan yaron, sai taji kukan nasa yana sukan ranta tana jin lokacin da Mujeeb ya dawo daga masallaci, ya shiga dakin Suwaiba ya gaida Goggo ya amso yaron suka fito zuwa dakinsa. Tabbas tasan kukan da yaron yake na rashin ganinta a kusa dashi ne, musamman irin gatar da takeyi wa yaron idan ya tashi daga barci wanka take fara yi masa ta wanke masa baki idan ta shafa masa mai ta sa masa kaya to zata hada masa lafiyayyan Ti yasha, yana gamawa zata goya shi ta soma ayyukan dake gabanta, duk abinda zatayi yana bayanta tunda har mamansa ta haihu bai cika shekaru biyu ba kenan bai wuce a goya shiba. Tasan kukan da yake yi bai wuce na yunwa dana goyo ba, tun da daga Goggon har Suwaiba babu mai goya shi, balle Suwaiba da aka yi mata aiki jinjirarta ma sai dai Goggo ke goya ta kasa 159 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria hakurin jin kukan nasa tayi, ta tashi sanye da hijjabin da tai sallah ta nufi dakin Mujeeb din A falonsa ta iske shi tsaye yana ta safa da marwa da Baffan a kafadarsa yana lallashinsa. Ta isa gare shi ta soma gaisar da Mujeeb, ai Baffa na jin muryanta ya yi saurin dago kansa daga kafadar uban ya dubi inda yaji muryarta, yana ganinta ya sake saka ihu ya soma zamewa daga jikin Mujeeb yana mika mata hannu don ta dauke shi, bata yi jinkiri ba tayi saurin amsan shi tana cewa, "My boy yi hakuri banje ko ina ba ina nan tare da kai har abada, babu mai iya rabamu sai Allah". Yaron ya kwantar da kansa a kafadarta yana sauke ajiyar zuciya. Ta dubi Mujceb ta na cewa "Gaskiya an dauki alhakinmu ni da yaron nan kamar yadda na kwana banyi bacci ba saboda kewarsa shima ina jin kukansa, don kwana ya yi yańa kuka kuma nasan rashin ganina tare da shi ya sa shi kwana kuka. Gaskiya kayi wani abu akan al'amarin nan, duk da dai anyi ne don a saka ni cikin kunci da bakin ciki a dalilin Allah bai bani haihuwa ba, alhalin ba laifi nayi masa ya hanani ba jarabawa ya ke yi mini, in ba'a tausaya mini ba ai ba za'a kuntata mini ba”. Ya dubeta fuskarsa a daure ya cе, "Mahaifiyar tawa kike

Chapter 9 of 12