Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 12
san abin Karin safe na na can na jirana, ke da baki da lafiya me ye na wahalar da kanki", tace, "Meye na wahala don nayi abu zan ci na yi da kai? Allah yasa dai ba ni kadai na soma yin haka a gidan nan ba, da kanka ma zuwa kake ka ci ko girki na ne ko na taba hanaka?" ya amshi filet din ya debi cokali daya na naman ya kai bakinsa yana cewa, "To sarkin korafi, na ci shike nan? Zuba min kunun". 100 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Ta juya ana zuba masa kunun a kofi zuciyarta cike fal Da farin ciki, ita kam ko yanzu ya ce ya koshi bukatarta ta biya sai ta dauki sauran ta je ta yi fuioshin dinsa a toilket don kada danta ya shigo ya ci, sa boda bata son ta mallake shi yanzu ta dai fi son mallakar Ubansa, shi raba shi zata yi da uwar goyon tasa kwata-kwata ya dinga gudunta. Tana zaune tana kallonsa har ya kusan cinye farfesun, ya mika mata ragowar ya cigaba da shan kununsa. Ita kam tunda bukatarta ta biya sai ta ce masa tana zuwa ta baro dakin nasa, kai tsaye bayin dakinta ta shige ta juye ragowar farfesun a masai tayi filoshin dinsa ya bi ruwa sannan ta sauke ajjiyar zuciya tae da subucewar wani murmushin mugunta a labbanta, "Mujeeb ka riga ka zo hannuna, zan juya akalar royuwarka yadda nake so, ta yadda za ka ji maganata ka bi umurnina fiye da bin umurnin mahaifiyarka. Ke kurra Muneeba kin kade har ganyenki don sai na maida ke abin kwatance, zau raba ki da mujin da ki ke takama da shi, in mallake shi ya zama nawa ni kadai, karyarki ta kare." *** *** *** Kwana biyu kacal da faruwar hakan sai Awakwalwar Mujeeb ta birkice wani sabon al'amari ya bakunci zuciyarsa na tsanan al'amarin Munceba haka kurum sai ya ii baya son ya genta, amma in 126 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria bata kusa da shi sai ya ji yana son ya je inda take da zarar ya je kuma suna yin arba sai ya ji kunci a zuciyarsa, ya rasa dalilin wannan abu. Idan tunaninsa ya fara hararo masa zargin ko Suwaiba ta bi halin Hajiyarta sunje sunyi masa asiri sai kuma ya ji zuciyar tasa ta kasa gasgata hakan sam zuciyarsa ba ta son ganin wani laifi na Suwaiba ko aibu akan wani nakasu na halayyarta. Kwana biyun da ya yi a dakin Suwaiba sai yake jin tamkar ya zarce ya yi ta kwana mata ita kadai ba tare da ya raba mata kwanan da wata ba. Wata irin tsagwaron soyayyar Suwaiban ce take ratsa zuciyarsa, sai yake ganinma bai taba jin so irin haka a zuciyarsa ba sam ba ya son ya ga canji ko yaya ne a fuskar Suwaiba sai hakan ya tada hankalinsa. Ita kam Munceba tunda ta lura da wannan sauyin daga mijinta sai ta tsannanta tsayuwar daren da take yi fiye da na da tana kaiwa Allah kukanta don kuwa ta san an riga an tsunduma mijinta cikin wani hali na halaka, sabo da a kwana biyunta da ya dawo dakinta sam ya ki yarda su hada makwanci, wanda in ada ne it ace ma ke yakice iribn kulaficin da yake nunawa akan ta, amma sia gashi wai yanzu shine ke gudun hada makwanci da ita, hakan bai sa nayi fushi ba don ta san ba yin kansa ba ne, aikin asiri ne tunda ta ji da kunnenta lokacin da Suwaiban ke waya da Hajiyarta tana mata albishir da cewa 127 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria aiki fa ya yi dole aje a yi wa boka godiya da bayani don har ya juyawa Muneeban baya, ko hada makwanci ba ya yi da ita, kuma da ita Suwaiban yake shawarar komai yanzu. A halin yanzu abinda Muneeba tafi maida hankali a kansa shine karatunta da take a shekarar karshe, don bata fatan damuwar halin da take ciki ya shafi karatunta. Suna zaune a makaranta ita da wata kawarta, wadda tunda suka fara karatu tare suke, ita 'yar asalin garin Gombe ce kuma anan take aure da yaranta guda biyu. Ta dubi Munecba tace, "Wai Muneeba kwana biyu me ke damunki ne sam kin daina wata walwala sai in dinga ganin ki cikin zurfin tunani, ni kaina abin na damuna in na tambaycki ki ce min ba komai, alhalin ni idan ina cikin matsala kece abokiyar shawarata, kuma ba kya bani muguwar shawara har in yi aiki da shawarar taki inga na cimma nasara, amma ni sai ki dinga nuna kokwanton amintakar mu ne?" Munceba ta kada kai tana murmushi wanda ya fi kama da yake ta ce, "Wallahi sam ba haka bane Maman Dijah, don matsala na shiga cikin gagaruma. matsala to amma gani nake tunda na tsayu da addu'a matsalar zata gushe da yardan Allah shi ya sı ma ban gayawa kowa ba amma kiyi hakuri ba wai ina boye miki ba ne, kina daga cikin aminai na gari abin ayi shawara da su, ke din mutum ce da ba a cika samun masu 128 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria son mutuin tsakani da Allah irinki ba, wallahi ina alfahari da samunki a amatsayin aminiyata". Maman Dijah ta cc, "Bari fasamin kai, ke dinma ai baka kike da fatan zamu ci gaba da rikon AMANAR JUNA (Sunan littaf na gaba). Kuma ko baki gaya mini matsalarki ba zaki iya ce mini in tayaki da addu'a yanzu ma insha Allahu zan tsayu da miki addu'a Allah ya ya kawo karshen abinda ke damunki har muma sauran musulmi Allah ya yi mana maganin matsalolinmu, kar ma ki gaya min matsalar don nima tada min da hankali za ta yi. Amman ina fatan ba akan rashin haihuwarki ba nc?" Ta girgiza kai tace, "Ba wannan ba ne, maganar haihuwa ni kam tuni na fawwalawa Allah, kila rashin haihuwar shinc alheri a gareni, in kuma ina da rabo to ina rokon Allah ya bani masu albarka. Wani boka na ji Suwaiba na cewa Hajiyarta aje a gaya masa aikin da ya yi mata ya ci baban Baffa ya juya mini baya ko makwani baya hadawa da ni, kuma haka dinne yadda ta fada, wallahi yanzu maganar arziki bata hada ni da shi, ko dariya yake yi idan ya ganni sai ya canza fuska yadda kika san ya ga bakin maciji, yanzu kulum sai sun fita tamkar wasu sabbin amare, saukin abinma basu kwace Baffa a hannuna ba shi nake kalla in yi wasa da shi inji sanyi, in suka amshe shi anan ne damuwata zata dada 129 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Karuwa". Ta kare maganar fuskarta kunshe da tsantsar damuwa. Ita kanta Maman Dihjah nan danan ta shiga cikin damuwa a dalilin jin abinda ya samu aminiyarta, sai take jin tamkar ita hakan ya sama. Ta gyara zama suka fuskanci juna sosai ita da Munecba, ta soma bata shawara ta gari irin yadda ya kamata aminin kwarai ya ba amini ba cuta ba cutarva, "Abu na farko da ya kamata kiyi, yanzu shine addu'a don ita addu'a takobin yakin makiyi ne da duk wani mugun halitta mutum ne ko aljan, kada ki yarda zuciyarki ko wani ya baki shawarar bin irin hanyar da su ka bi, domin irin hanyar da suka bi ta fatattu ce kuma zuwa gurin boka yin shirka ga Allah ne babba kuwa. Sanann abu na gaba duk wata kulawa da kika san kina bashi kada ki gaza, kada ki ce don ya juya miki baya kema bari ki juya masa baya ki watsar da duk wani abu da kike masa na kyautatawa sam kada ki daina ki ci gaba, har itama kada, ki canza mu'amalarki da ita, ki ci gaba da kyautata mata, balle kuma dai ta da rikonsa ke hanunki, ki ci gaba da rikonsa tsakani da Allah yadda kike masa wallahi ba zaki tabe ba, kuma kada ki gaya ma sa kinji wayar da ta yi da Hajiyarta ki kyalesu kwana dari na baraw ne amma kwana daya tak ne na me kaya zai karna barawonsa (red handed) dunu-dumu, in dai kin dage da addu'a to 130 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ba za a kai ko ina ba kome ta yi masa zai zo iyaka, In shaa Allahu Allah zai warwarc kullin da suka yi zamu dage da addu'a tunda babu abun da ya gagari Allah, kuma shi ne da kansa ya ce, ku rokeni zan amsa muku, kada ki saka abin ya yi ta damun zuciyarki don zai iya haddasa miki wata cutar a zuciya ki dage da addu'a da azumi wallahi sai kinga karshen al'amarin". Zuciyar Muneeba ta sanyaya da jin nasihar aminiyarta, ta sauke nannauyar ajiyar zuciya ta cе, "Madallah da samunki a matsayin aminiyata wallahi ina alfahari da samunki a rayuwata,. Na godc na gode da shawarwarin ki, wallahi tunda abin nan ya sameni ban taba jin natsuwar zuciyata ba irin yau, kasancewar al'amarin na ta gwaguyar zuciyata, amma na gaza furta shi ga kowa, yau kadai da na bayyana abin da na boye a zuciyar tawa ga shi har na ji sanyi, lallai na yarda barin kashi a ciki baya maganin yunwa". Aminan biyu sun cigaba da tattaunawa har lokacin sake shigarsu aji ya yi sannan suka shiga. Koda suka tashi makaranta sai ta ji zuciyarta sam bata son komawa gidanta tana son ziyartar Mama Amina, don kawai ta je tayi hira da Maman da su Khairat ko ta ji sanyi a zuciyarta na abin da ke damunta. Ta lalibo sunan Mujceb a wayarta ta kira shi don ta nemi izinin sa ta kira sau biyar bai daga ba, 131 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ba ta yi tsammanin ba ya kusa ba, tabbas ta san yana kusa da wayar dauka ne ba zai yi ba, dama kuma a 'yan tsakanin na haka yake mata idan ta matsu da son tambayarsa anguwa to fadin wata maganar ko ta kira ba ya dauka sai dai ta tura masa sako a wayar, to nan ne yake bata amsa shima a rubucc. Yanzu ma sai ta tura masa sakon neman izini, ba a jima ba ya turo mata amsa, sai kin dawo, da manyan baki a takaice. Sun fito inda motoci suke da maman Dijah a inda direba ke jiran MAman Dijan sai Muneeba ke ce mata "Hanya daya zamu bi, zanje gidan Mama Amina ne", ta dubi Munceba fuskarta kumshe da tuhuma tacc, "Ba dai maganar nan zaki gaya mata ba, ki tada mata hankali?" ta girgiza kai, "Zanje ne kawai in gaishe su, inyi hira da su don inji sanyi a zuciyata, ba wai don in gaya musu matsalata ba, na san Mama da damuwa akan abin day a shafeni, yanzu ina gaya mata hankalinta zai tashi ta yi ta damuwa har ma ta fi ni damuwa, shi yasa ba komai ba ne na damuwata nake gaya mata na fi gaya mata abu na neman shawara". "Yauwa kada ki fada mata mu cigaba da addu'a babu abinda day a gagari Allah, Zai kawo mana agaji". In ji Maman Dijah. A gidan Inna Amina ta vi Sallar azahar ta ci abinci duk da walwalar da ta samu a gidan amma 132 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria saida Inna Amina ta gano tana tattare da damuwa har ta tambaycta, ta ce ita babu wani abu dake damunta. Tace, "To amma kinyi rama kamar mara lafiya". Tacе, "Karatun da na ke hana ido na bacci na yi inaga shi ya sa nayi rama, don bana samun isasshen bacci hakan ke sa in yi ta ciwon kai ni kuma in ba da daddare ba bana iya karatu don ko Baffa baya buri na in ba bacci yake ba". "Aiko dole ki daina karatun daren da rana sai ki dinga kaishi gurin Suwaiba ko mai rainon shi ba tana nan ba?" tace, "Eh tana nan amma ba ya zama a gurinsu in dai ya san ina gida, in kinga ya zauna a gurinsu to ya neme ni ya tabbatar ba na gidan shi ne yake hakura ya zauna a gurinsu" inna Amina ta ce, "To shi babansa bay a fada akan hana idonki baccin da kike yi shima ai kina shiga hakkinsa ni banga amfanin karatun dare ba ka dauki hakkin idon ka, ka dauki hakkin mijinka". Munceba duk sai ta diririrce saboda ta san bata shiga hakkin mijinta shine ma ke tauye nata hakkin, shine dalilin ranarta tun da har yau ta kasa gano kuskurenta a gurinsa da ya juya mata baya. Inna Amina dai duk hikimarta na son sanin abin da ya ramar da 'yar tata bata sami wani haske daga Muneeban ba, don har su Khairat tasa su bincikar mata Munecban tunda sune abokan 133 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria shawararta, to suma sun binciketa ba su sami wani haske ba haka suka kyaleta. Tana yin Sallar la'asar ta baro gidan Inna Amina, saboda zata je ta yi girki. Tana cinna hancin motarta harabar gidansa ta hangi Mujecb a jikin motarsa tare da Suwaiba za su shiga motar tasa ga dukkan alamu anguwa za su je. A bayan motar ne ta hango Baffa shi ma an yi masa kwalliya da shi za su je kenan tunda ta ganshi a motar. Tayi saurin zuwa tayi fakin din motar ta fito, ta nufo gurinsu, kafin ta karaso har sun shiga motar dai-dai da isowarta gurin a lokacin Mujecb ya ta da motar suka fice a harabar gidan suka barta tsaye rungume da jaka. Ta juya tana jan kafarta da kyar saboda nauyin da ta ji kafar ta yi mata, idanunta cike da hawaye a dalilin wannan wulakancin da Mujeeb ya yi mata, Allah dai yasa mai gadinsa bai fahimta ko ya ga wannan cin zarafin da aka yi mata ba, dan ganin hakan zai iya rage mata kimarta da suke gani. Zaune a tsakar gida a barandar kofar dakinta ta ga karime ta zuba uban tagumi. Ganin karimen ya sa ta yi saurin goge hawayen da ke idanunta, ta isa gurin Karime tana tambayarta, "Me ya faru kike zaunc anan kin yi tagumi?" Ta sauke tagumin da ta yi ta soma yi wa Muneeba sannu da dawowa sannan ta ce, "Babu komai, dama dawowarki na ke jira sai in tafi gida". 134 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Munceba ta mika mata makullin motarta tace, "Je ki bude gaba gefen da nake zama ki dauko min wani filas da na manta da shi". (kunun gyada ne Mama ta zuba mata tace ta taho da shi dan ta ga bata wani cin abincin kirki). Ta dauki makullin dakinta a inda take ajew ata bude dakin ta shiga Karime ta yi sallama ta shigo ta mika mata makulli da filas din tace, "Kunu ne idan zaki sha ki diba, in kin gama sai ki zo ki taya ni aikingirki sannan ki tafi". Dama yunwa ce ke kwakular Karime, don rabonta da abinci tun wanda Munceba ta bata da safe kafin ta tafi makaranta, da rana tana gani Suwaiban ta yi iya cikinta ita da danta suka ci ta hanata ko albarkacin dawainiyar datake da danta bai sa ta bata ba. Har baki ta cika kofin ta kafa kai tanakyankyana, Muneeba ta dubeta cike da mamaki tace, ", ba ki ci abinci bane? Tace "Eh ban ci ba, na duba kicin dinki ko zanga ragowa ban gani ba". Muneeba ta cika da mamakin halin mugunta irin na Suwaiba, ace yarinya ta wuni cir tana miki rainon danki amma don zalunci ki hanata abinci alhalin ke kinci, wannan wace irin rayuwa ce. "Shi Baffa me aka ba, shi?" ta ce "Mamanshi ta amshe shi ta bashi abinci". Munecba ta girgiza kai cike da al'ajabi ta ce, "Yayi kyau" sun shiga kicin ta shirya lafiyayyen abinci kala biyu. Tuwon semo da miyar kalkashi ta yi, miyar ta ji 135 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria nama sosai sabo da ta san Mujeeb na son tuwo miyar kalkashi, balle idan miyar taji manshanu, idan ta yi masa har santi yake yi, amma yau bata sani ba ko zai yaba mata, tunda ya daina yabon ko me zata yi masa na kyautatawa. Tayi lafiyayyen salat sannan ta yi farfesun hanta da koda nan da nan gidan ya dau kamshi. Kafin magriba sun kamala komai, har sai ta ji dadin tafiya da Baffa da akayi don da yana nan ba zai barta ta kamala komai akan lokaci ba, da kam har ta ji haushin tafiya mata da suka yi da shi. Duka abinda suka yi sai da ta zubawa Karime ta ce ta tafi da shi gida, son bata son gari yayi duhu bata tafi ba duk da ba wani tazara ba ne a tsakaninsu, kasancewarta mace akwai hatsari ga fitar mace a irin wannnan lokacin da ake Sallar magriba a dalilin 6ata gari sunfi amfani da wannan lokacin na daukewar sahun jama'a su bi duhun magriba su ja'ya'ya su lalata su, tun da su ba su da mu da zuwa yin jam'i ba. Tana fitowa daga wanka ne ta ji motsi a falonta, ta lekawa ta ga Baffa zaune da leda babba a gabansa ga robar ice cream da ya fiddo yana ta zubarwa a jikinsa, yana ganinta ya kyalkyale da dariya yana kiran sunanta "Mama, Mama". Ta iso gare shi tana mamakin da yaushe aka shigo da shi bata ji ba, sam bata ji dirin motar su ba, saukar ruwan wanka a bayi ta san shi yasa ata ji da 136 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria dawowarsu ba. Ta fauke shi ta goggoge masa jikinsa, ta bude ledar da ke gabansa ta ga kayan ciye-ciye ne sai pampers dinsa da mota da jirgi masu batir da ka siyo masa tunda duk ya lalata wadanda yake da su. Ta dauke shi suka shiga ciki ta kunna masa motar yana wasa da ita sannna ta tada ikamar Sallah. Tana idarwa ta yi kwalliya a gaggauce don kada Mujeeb ya shigo ba ta je ta kai masa abincinsa ba. Ta so ta je ta shirya abin cin a dakinsa sai ta iske bai aje makullin dakinba da abinsa ya tafi, wato ba ya son ta shigar masa daki abin ya sosa zuciyarta, amma sai ta lallashi zuciyar ta da kalmar hakuri. Har ta gama shirya abincin bai dawo daga masallaci ba, sai ta koma ta dauki Baffa tayi masa wanka ta samasa pampas ta canza masa kaya shi ma ta feshe shi da turare sannan ta dauke shi suka koma dakin babansa Sun tarar ya dawo har ya sauke da abincin da ta kawo kan kafet ya zuba yana cin abinsa. Ta aje Baffa a gefensa itama ta zauna a kusa da shi ta na masa sannu da dawowa, da kyar ta iya jiyo yauwan da ya furta can a kasan makoshinsa. Ta dauki kofi ta zuba masa ruwa ta aje a gabansa, ta sake daukan wani kofin ta zuba masa lemun abarba da kankana da ta hada ta aje masa, tana kallonsa a tsanake yadda baya son wata mu'amala ta hada su 137 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria amma yana son mu'amala da abincinta, to ko don matarsa bata iya banc yasa yake cin nata a dole? Oho! Babu wata hira da ta gilma tsakaninsu illa dansa da yake yi wa Magana idan ya rarumo wani abun zaiyi 6arna,ita kam ko kallonta ba ya son yi sai kace wata abar kyama ko an aje masa danyen kashi. Yana gama cin abincin ya mike tsam ya dauki Baffa suka koma kan doguwar kujera suka zauna ya daukki remote yana canza tashoshin talabijin.jikin Muncebaa sanyaye ta mike ta soma tattara kayan abinci taje ta kai kicin dinta sannan ta dawo dakin, suna nan zaune har dare ya yi sosai, ya mike ya je ya yi wanka ya saka kayan bacci ya zo ya yi Magana ba tare da ya dubeta ba “Ina son zan kwanta ki dauki Baffa ku tafi dakinki”ta dube shi cike da mamaki tace, "Mu tafi fa kace? Ko ka manta ni ke da girki yau?" yace, "Ban manta ba tunda har kinyi girki na ci". Tace, "Amma gąni na yi ka daina zuwa daki na duk da ko ka je ba kulani ka ke ba, shi ya sa yau ni na karya yanci na na biyoka, kuma ai yin hakan ba aibu ba ne”. Ya dan dubeta ganin sun hada ido sai ya yi saurin dauke idonunsa a kanta yace, "Ina bukatar kadaici ne yanzu in ina da bukatarki zan neme ki ko in kawo kaina yadda na saba, amma yanzu gaskiya ban son a dame ni!" zuciyar Muneeba ta sosu kwarai da Kalamansa amma babu yadda zata yi 138 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria kawai sai tasa hannu ta dauki Baffa da ya riga ya yi bacci ta dube shi ta ce, "Shi ke nan sai da safe". Bata jira amsawarshi bat a baro dakin. Tana bada baya ya rufe kofarsa har da makulli. Tana shiga dakinta ta aje Baffa a gadonsa, ta zauna a bakin nata gadon ta yi kuka mai isarta har sai da ta ji kanta ya sara mata da wani azababben ciwo, sannan ta saurarawa kanta, ta tashi ta rufe kofofinta, ta wuce bayi ta yi alwala ta zo ta yi nafilfili ta yi ta kaiwa Allah kukanta akan wannan al'amari da ya zo wa rayuwarta wanda ta dauke shi a matsayin jarabawar rayuwa, kuma In Shaa Allah zata cigaba da yi wa al'amarin juriya da hakuri har Allah ya kawo iyakarsa, don komai na duniyar nanamai faruwa ne kuma ya wuce in dai an yi hakuri, yanayi daya ba ya dauwama a rayuwar mutum za a iya samun sauyi daga fari zuwa baki ko daga baki zuwa fari iyakaci dai mutum ya yi ta yi wa Allah godiya idan rayuwar ta yi masa fari, idan ta bakanta a gare shi kuma sai ya yi godiya tare da jin istigfari ga Allah, sai da ta yi Sallar subahi sannan ta kwanta. 1 Rashin baccinta shi ya haddasa mata tashi a makare, hakan bai sa ta yi kasa a gwuiwa ba, ta shiga kicin ta shirya masa abin Karin kumallo lafiyayye. Sai da ta yi wanka sannan ta dauki kayan abincin ta nufi dakinsa tsayuwa ta yi tiris dauke da tire a hanntmta sabo da jin kofarsa a rufe har ya fita 139 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria kenan, ba tare da ya neme ta ba, hakan ya dada tabbatar mata da lallai baya bukatar ta na shiga rayuwarsa. Juyawar da za ta yi ta yi arba da Suwaiba da ke tsaye a bakin kofar falonta, Suwaiban na tintsirar dariyar mugunta sannan tace, "Kai shishshigi dai bai yi ba a rayuwa in banda rashin zuciya na wasu matan, yaushe ne zaka yi ta bibiyar miji yana wulakantaka ya na korarka amma don jaraba gobe ma ba zuciya ki dawo ko dan irin jan ajin nan na mata babu, jiya kin zo ya kore ki yau ma kin dawo, to tuni ya fita don ba ya son ganinki", Munecba sam bata iya fadi in fada ba shi ya sa sai ta rasa me za ta ce wa Suwaiba, kawa sai ta juya ta koma da tiren abincin dakinta ta hau sana'ar da a yanzu ta fi iyawa wato kuka, sabo da bakin cikinta daya ne yadda Suwaiba ta sani komai da ke wakana a tsakaninta da mijinta, wato har zuwan da ta yi dakinsa jiya da korar Karen da ya yi mata duk ya gaya wa Suwaiba, in ma bai gaya mata ba to tana bibiyc da al'amuran da ke faruwa a tsakaninsu. A irin wannan yanayin ne Goggo ta zo Gombe ta iske al'amuran gidan dan nata gabadaya sun sauya ragamar komai na gidan ta koma hannun Suwaiba, duk abin da tace shi ake yi a gidan, dama ab nda Goggo da aminiyarta Hajiya Harira ke so kenan to sun samu bukatarsu ta biya 140 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaría Abu biyu ya soma ciwa Goggo tuwo a Kwarya yanzu, na yadda Mujecb ya rage zuwa Dukku, sai dai in tana bukatar wani abu ta yi masa waya ya ce ta aiko Isah, kuma duk abinda zai bata ta hannun Suwaiba ake amsa don akwai zuwan da Isan ya yi da ya amshi sakon ya kaiwa Hajiyarta kayan sun ninka na Goggo biyu har da kudi cikin ambulan wanda Isan bai san ko nawa ba ne, sai da Goggon ta sa shi ya buda ambulan din ta ga kudi tsabar su dubu talatin 'yan dubu-dubu sababbi fil babu ko kari. Wadannan kudi sun ciji zuciyar Goggo don ta tabbata daga aljihun danta suka fito, amma ita gashi ko ficika bai aiko mata da shi ba, sai kayan abinci. Abu na biyu dake damunta irin hidimar da ya ke yi wa Hajiya Harira, har Umrah ya biya musu suka tafi su uku, shi da Suwaiba da Hajiyar da ta yi masa magana me ya sa bai biya da ita ba sai cewa ya yi su ai ya biya musu Aikin Hajji sun je shekarar da ta wuce da Muneeba da babanta da Baffaninsa, bai biyawa Hajiyar da 'yarta ba saboda ita ta taba zuwa, Suwaiba kuma na shayarwa shi ya sa yanzu ya biya musu umura tunda ita Suwaiba bata da ciki ita abinda ya fi ci mata tuwo a akushi, si ne rashin zuwa Dukku da ba yayi kamar da, a halm yanzu ya kan shafe fiye da wata bai zo ba, bata san wasa farin girke kenan ba kadan ta gani inji Suwaiba". WATA KUSAN 2 **** Rahmatu Hassan Zaria ****** ***** Shirye-shiryen haihuwar Suwaiba shine abinda Mujeeb ya fi maida hankalinsa akai kenan yanzun da watan haihuwarta ya tsaya ma sai ya koma da kwana dakinta kacokan ba tare da shawarar Munecba, ita ma sai ba tace masa komai ba ta kyaleshi tunda Hausawa na cewa kowa yayi nagari yayi ma kansa, kuma ko wa66ata ya sani ko wagygyara ya sani. Tana zaune da wani yammaci ta ji dawowarsa, sai da ya shiga gurin Suwaiba ya dubata sannan ya wuce dakinsa ba tare da ya waiwaye ta ba, idan da sabo ta riga ta saba da wannan juyin baya da yà yi mata. Ta tashi ta nufi dakin nasa don ta yi masa sannu da dawowa hakan ce take kasancewa a tsakaninsu in ya dawo bai nemi inda take ba to ita zata kaskantar da kanta ta bi shi tunda ita ke kasansa kuma zamansa takeyi hudubar da Inna Amina tayi mata kenan shi yasa take amfani da ita. Baffa ne ke rike a hannunta yana dan dagara Tafiyarsa da batayi kwari ba, har süka isa dakin Mujecbun yaron na gani Babansa ya saki hannu ya fara gudu yana faduwa tare da murna zaije gurin babansa. Ya taso ya tari yaron ya daukeshi, yana cowa "My boy" tafiya tayi

Chapter 8 of 12