Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 12
wayarsa ya ce idan sunje ya nemishi ko da zai taimaka masa ta wani fannin tunda yana da mata da 'ya'yansa. Suna isa dakin da aka basu wanka suka yo suka gabatar da salar da ke kansu, su ka yo odar abinci suka ci suka koshi, sannan suka yi shirin tafiya Ka'aba don su yi sallar Magriba da Issha'i a can su yi dawafi kafin su dawo gida tunda a washe gari ne Munecba za ta ga Likita da safe. Muneeba ku san bakauyiya ta zama saboda ganin kyawun kasar Saudiya wanda ke da tsarin gine-gine masu kyau ga hasken lantarki lungu da sako na ksar ko ina ka bi tamkar rana ba dare ba saboda haske ga zirga-zirgar mutane a ko ina balle idan kaje masallacin Madina ko na Ka'aba ba su dawo masaukinsu ba sai kusan sha daya na dare, а dalilin Muneeba ta makale tana ta dawafi tare da zubarda hawaye a dawafi tana gayawa Allah bukatarta don tun tana yi a zuciya har addu'ar ta fito fili da kyar ya lallasheta, ya ce ta bari gobe idan suka dawo sai ta cigaba. Washe gari bakwan Safe a asibitin tayi musu likita ya duba Munceba sosai ya basu wasu gwaje-gwaje da za'a yi mata saboda yana son tabbatar da lafiyar mahaifarta. A ranar.duk aka yi mata gwaje-gwajen suka it magunguna suka gaya mata ranar da zata davo WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria don amsar sakamako sannan ta sake ganin likita. Duk wasu abubuwa da ya kamata ayi an yi mata sakamakon ya nuna mahaifarta lafiya lau take ba ta da matsala wajen daukan cki a shirye take ta dauki cki ako wani lokaci idan Allah ya nufa wannan dalilin yasa shima Mujeeb said a suka yi masa gwaje-gwajen don ganin ko daga gareshi matsalar take tunda matarsa bata da matsala. Nashi samakon shima ya fito irin nata, komai nasa lafiya lau yake. Sun basu shawarar ci gaba da shan magunguna tare da sauraron lokacin da ALLAH zai kaddaresu da samun ciki hankalinsu kwance suka cigaba da gudanar da ibadarsu ba dare ba rana sannan Mujceb ya soma nemar musu bizar tafiya kasar Dubai don su shakata. Ana gobe zasu bar Saudiyya zuwa Dubai da daddare suna zzaune suna shan-shayi Munecba ta dubi Mujceb tace 'Wai ya aka yi ka shirya mana tafiya Dubai, Alhali daga gida bamu yi shirin zamu Dubai ba? Ya kurbi ruwan shayi ya lumshe idanu sannan ya, 'Yawon Shakatawa zamuje kinsan Dubai tana daya daga cikin manyan kasashen Larabawa da ta zamo cibiya ta yawon bude ido da Kasuwanci da Shakatawa ga Turawa, Larabawa harma da mu bakar fata, kuma Kasace da ke da kyau sosai, ga baruwan wani da wani zaman lafiya yayi dirshan a kasar zamuje a zaki gani sai kinji kamar mu yi ta zamanmu a can, ba tsangwama ba mai sa ki kuka ko a gaya miki 21 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria maganar da zata bata miki rai balle gaki da masoyinki, sai mun sha soyayya ta sati biyu a Kasar sannan zamu tafi, In sha Allahu ba zamu koma Kasarmu muba saida tsarabar Baby a mahaifarki". “Ta yi murmushi ta ce, Allah ya sa hakan ya tabbata don ni ina ji a zuciyata da jikina kuma ina da yakinin Allah ba zai wofintar da addu'arda rokon da muka yi ta yi masa ba ba dare ba rana tamkar ma nasami cikin haka nake jin jikina. Sauri Mujeeb yayi ya aje kofin shayin da yake sha ya janyo ta jikinsa ya zaunar da ita, ya soma shafar cikinta yana cewa 'Lokacin al'adarki yayi ne, Tace 'Bai yi ba ina ga sai nan da kwana goma" yace ko kinji alamun cikin ne? ta ce 'Banji komai ba kawai dai zuciya ta ce ke raya mini cewa addu'armu ta karbu" ya ce "To ko mu je asibiti ne tunda dare bai yi ba su duba ki don mu tabbatar wallahi har kin san a soma dokin zan zama baba" ta yi murmushi tana girgiza kai t ace "Ka bari har in banga al'adata ba sai muje asibitin a lokacin muna Dubai sai su duba ni. A Dubai sun yi masauki ne a daya daga cikin hotel mafi shahara a kasar Mujceb yayi haka ne don su hole su wataya tunda abin da ya kawo su kasar kenan, shi yasa ya saki bakin aljihunsa yana son ne ya farantawa Muneeba rai ta san cewa zai vin komai domin farin cikinta. 02 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria A kwana biyu da suka yi nan da nan fatar jikin Munccba ta sakeyin jajir tayi wani irin sheki wanda ta fara zargin kodai shigan ciki gareta sai dai ta kanyi saurin fatattakar wannan tunanin na zuciyarta don kada gasgata hakan ya yaudari zuciyarta ta sa ran samun abinda bata isa taba kanta ba sai in Allah ya kaddara zata samu. A wani yammaci suka yi shirin su tsaf! Zasuje sayayyar tsaraba tunda baifi kwanaki uku ya rage musu su koma kasa Nigeria ba. Leshi ne a jikin Muneeba riga da siket, sai ta kawo bakar abaya ta dora a bisa kwalliyarta, san nan ta kawo gyallen bayar ta nade fuskanta zuwa kafadarta tasa Pin ta matse gyallen saboda zamiyewa sai fuskar ta fara tas da tai luwai-luwai bako digon kurji fuskar kawai kake gani a waje ko ina ta rufe shi ruf, ta saka takalmi shim baki sawu ciki na (Toms) mara tudu ta fito tana rike da yar bakar jaka, tayi kyau tamkar wata Balarabiya er Kasar ta Dubai. Shima MUjcebun yayi kyau cikin wani yadi dan asalin Indiya da aka yiwa dinkin (GOOD LUCK) aka hade halar ash da baki, idan ka gansu zaka dauka amarene a satin aurensu da suka zo yawon shakatawa, don Mujeeb Makale matarsa yayi tsan a jikinsa a dalilin kallo da yag ana binsu dashi, shine yake nunawa duniya ba Budurwansa bace matarsa ce ta Sunnah Halak Malak. 23 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Wani Shago suka tsaya suka yi sayayya mai yawa, yana lura da ita duk abinda zata saya in indai nata ne to guda biyu take diba a kala ne kawai ta ke banbantawa, daya ta dauki mai haske daya mai duhu, har dai ya kare ya tambayeta 'Wai ke dawa kikewa sayayyar nan nc? Ta ce 'Ni da 'yar uwata mana' Y ace 'Wa ce 'yar uwar taki? Ta ce Suwaiba mana tunda na lura kai kanka kawai ka sani shi yasa nima nake zabar mana namu "Y ace, "Au abin haka ne Suwaiba ta fi ni shi yasa ko hankinci baki dauka nawa ba ko? Ta сe, Haba Yallabai ka manta kayayyakin dana zaba dominka a Saudiya kona Dubai ne suka fi tsole maka ido, "Ya yi murmushi y ace, "Ai zance yak are tunda naga kalar taki Soyayyar kin fara mantani. Ta rike haba ta ce, 'Ni na isa in mance abokin rayuwata? Ai wallahi kaine komai nawa, yi hakuri abokin rayuwa yanzun zaba me kake so, ya make kafada tamkar wani dan yaro yayi magana cike da shagwaba "Ni ke zaki zabar mini, ko ince bana so, Gaba daya suka tuntsire da dariya har mai shagon da bai san me suke cewa ba sai da ya tayasu dariyar, har ya kare yana tambayarsu 'da Turanci wai hala yawon amarci suka zo suka amsa masa cewa eh yawon amarci suka zo yace Kai kun dace da juna gashi kun iya soyayya don Allah kada ku raunana Soyayyarku idan kun haihu naga haka kuke vi mu kuwa Larabawa idan muka haihu da juna 24 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria lokacin ne muke kara son juna" suka cc Insha Allahu bazasu daina son juna ba". Sun gama sayayyarsu zasu tafi sai Muneeba ta hango wani shago na sayar da kayan karau na mata wato danginsu Zinarai, azurfa lu'u lu'u da yakutu, sai ta radawa Mujeeb yayana ga wani shago can ina son in duba 'yan kunne da sarka na Gold yan Dubai tunda gamu a kasar. Yace "Daga yau fa na tashi daga yaya na zama abokin rayuwa, bana son yayan nan ai kowama ya san ni yayanki ne ko baki fada ba". Ta yi murmushi tace "Au kaji dadin Dubai ka canzawa kanka suna ko? Ya ce ke kika canza mini nib a ruwana kuma ma idan nace banji dadin Dubai da Saudiyya ba a wannan tafiya ai nayi karya saboda nayi kyakkyawan amarcin da ban tabayin irinsa ba, don bazan boye maki ba wallahi kin jiyar dani dadi da kulawar da ban taba samun irin suba a rayuwata komai naki ya canza ko zamzam din da kike sha kulum ne yasa nake jin ki zam-zam kinga kuwa ai dole a canza min suna tunda na samu Sauyin Sabuwar Rayuwa" Dariya tayi tana nuna shida da yatsa tace "Kai ko ka saki baki kana ta zuba kamar fanfon da ya lalace a gaban mutane don kaga basa jin yarenmu ni dai mu tafi". Mujeeb ya dubi mai shagon ya nuna masa kayansu da ke cikin manyan ledoji irin na shagunan Dubai ya ce "Ga kayanmu zamu bari zamu shiga wancan shagon sai mun dawo zamu dauka. Mai WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria shagon yace "Aik » baku gaya min ba idan kuka tafi zasu davo iele kayanku babu abinda zai same su don babu wanda zai taba mu haka muke а Kasatmu idaa ka aje abu da izinin Allah inda ka aje nan zaka zo ka ganshi ko da an kwana ne. kuje kawai babu abinda da zai sami kayan ku", Su Muneeba suka tafi suna mamakin al'amarin wannan kasa da babu 'yan sane balle 'yan fizge ko 'yan yankan aljihu sabanin tamu Kasar da komai ya tabarbare ba tsaro ba tsari, kowa na yin abin da yaga dama tun daga na sama har zuwa na kasa. Allah dai ya shiryar mana da Shuwagabanninmu da mu na kasan ameen. Nan suka bar kayan suka tafi shagon kayan Karau. Rudewa da ruwan ido ne ya sami Muneeba a shagon saboda ganin idonta taga rowan gwalagwalai da lu'i lu' wato (Diamond) da bata taba ganin irin suu a idanunta wasi mata da suka tadda shagou sune suka tayata ta zabi dan kunne da Sarka da zobe sai awarwarokwana biyu tal amma masu *sananin kyau da ban sha'awa aka auna rnata kudinsu ya tashi a Dubu Dari Biyu da Hamsin, ta sake cewa a dauko wani setia wanda kucinsa zaiyi daidai dana farko amma disin dinsu ba i 'n tafi suna dubo mata ne Mujeeb ya kalleta ya ce, wanda kikace a dauko kuma na waye" Tana mumushi t ace, "Na Kanwata ne Suwaiba" ya dan daure fuska ya ce, kice s varshi don wallahi bazan 26 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria saya ba, ai na gaya miki Goggo ta matsa mini said a na saka mata hark ala biyu a kwati da irin wannan fan Duban da wani dan Saudiya amma aike ban saya miki ba shine ke yanzun zaki ce in kara siyan mata garamå in kara miki wani ya zama biyu kamar yadda na saya mata biyu amma wallahi b azan siyan mata ba. Ta shagwar-gwabe masa hard a dan kukanta irin na yaron da ke tsananin son abu yana son sai anyi masa tace 'Haba abokin rayuwa don Allah ka sayan mata na nan sun fi design ma kyau, kuma nima ai ina da wani ko" y ace, kinga yanzun idan na siya maki wannan kowa na da bibbiyu kenan" Duk inda ta 6ullo masa yaki ya sayi na Suwaiban dole ta Kyaleshi ya biya kudin natan kawai tunda ta san yafı ta gaskiya suka yi shatar taxi ta maidasu masaukinsu. Da daddare suna zaune suna cin abincin da sukayi Oda na dare, sai ga Kiran Isah kanin Mujecb ya shigo wayar Mujceb yana ganin kiran yasan Goggo ke son Magana dashi kuma bazai wuce akan Suwaiba ba don da ya kirata da safe take ce masa bata ji dadl to kila ciwon yayi tsanani ne don a muryanta ya gamo lallai bata da lafiya. Yana daga wa yaji Muryar Isah na masa sallama, ya amsa tare da tambayarsa komai lafiya ko tunda Goggo da Isah din suna gidansa na Gombe tun ranar da suka baro Nigeria a cewar WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Goggon bazai yiw a Suwaiba ita kadai ba sai wata yerinya da Hajiy: r tat a kawo ta tayata zama ba gara itama tazo su zauna tare sannan Isah ma yazo don gida ba namiji akwai matsaia. Yaawa Goggo wayar yana cewa "Ga Goggo zakuyi magana" tana amsa bata amsa gaiswar da yake mata ba sai cewa tayi 'Wai A ujcebu wannan wane irin ganin likita ne yau k ısan satin ku hudu a Saudiya kila sai kunyi aikin laji zaku dawo". (Bai gaya musu sun wuce dubai ba) sai ya ce, Nan da kwana uku zamu dawo Insha Allahu kinsan gari ba kusa ba garamu gama komai sannan mu dawo ai Insha Allahu muna sa ran an dace koga irin dawafin da mukayi a Ka'aba muna Lawai Allah kukanmu sanna ga kwararrun likitoci sun dubamu dukanmu sunce babu mai matsalar rashin haihuwa a cikinmu lokaci ne bai yiba shi yasa hankalirunu ya kwanta yanzu shirye-shiryen dawowa gida kawai mukeyi. Gogge tare kai kam bukata ta biya a gurinka addu'arka ta karbu ga suwaiban nan dauke da cikinka dan sati bakwai, dazu muka je asibiti in so samu ne gobe ka dawo don wannan abin farin ciki yaci, ace kana kusa avi arin cikin tare dakai ktayata jinya don bata da lafiya ar góut e mu koma idan aman da take bai tsaya ba z. kwantar da ita su sa mata ruwa". Yayi farin ciki to amma yana tsananin tausayawa Munceba shi WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria in son samunsa ne ace Munecban ke da ciki ba Suwaiba ba to babu yanda zaiyi da tsarin Allah, amma yana mata addu'ar itama Allah ya bata. Ya cewa Goggo “Allah ya sauwake zan kira da wayarta inyi mata sannu sannan duk abinda kuke bukata dangane da asibiti ga Isah nan zaije banki ya cire muku kudi sai kuyi amfani da su Allah ya bata lafiya sai da safe". Ya kashe wayar yana Duban Muneeba, ta rigashi cewa "Waye ba Lafiya? Ya ce 'Suwaiba ce wai har sun je asibiti ance tana dauke da ciki na sati bakwai". Ta riko hannuwansa tana mai cike da murna tace "Kai Alhamdulillah ai wannan zancen ya wuce wai abinda muke nema ne Allah ya amsa addu'armu tun bamu dawo ba ya bamu aini wannan cikin tamkar a jikina haka nake jin murnar samunshi tunda ni za'a haifowa bebin wallahi koni bansamu ba idan Suwaiba ta haifo maka tamkar ni ce na samu, tun da abinda zatra Haifa jininmu daya. Kira wayarta muji ya jikin nata". Jikin Mujeeb duk sai yayi sanyi ya kara jin tausayin Munecban a ransa sam babu kishi ko bakin ciki ita Allah bai bata haihuwa ba yaba 'yar uwanta sai ma murna da doki takeyi za'a haifo mata bebi tunda dama yayi alkawarin zai bata abin da Suwaiban ta haifan kyauta ta rike in dai Allah ya kaddara ta riga ta haihuwa. Kuma murnar da furucinta har zuci tayi 29 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hasşan Zaria sune tsakani da Allah hakan halinta ne ya riga уа sani. Jikinsa a sanyaye ya kira layin Suwaiban tana dauka yi masa Magana cikiu sanyin Murya Kiris ya roge ya ta saka masa kukan Kisisina saboda ta matsu ya dawo ya ce, "Ya jikin naki? Gorgo ta gayamin sunce cikine to Allah ya baki lafiya sai ki dinga daurewa kina cin abinci saboda abinda ke cikinki kuma cin abincin ko yaya ne zai rage miki wahalar ciwo ya baki kuzari sosai kina jina ta ce Eh ina jinka zanyi kokari, amma idan naci amai nakeyi ko ruwana sha sai nayi amai”. Ya ce haka nan zaki dinga daurewa ga Auntynki zata gaisheki da jiki ya mikawa Munecba wayar ita ta soma gaida Suwaiba ta kara da cewa, "Sai mukaji abin farin ciki to Allah ya albarkaci abin da za'a haifo, ke kurna Allah baki lafiya ki daure ki dinga cin abincin don a lhaifo mana Bebinmu kato, idan kika haifo лana dan Kuculi ba zamu yarda ba gara kawai ki daur ki dunga cin abinci da yawa." "Mhm" kawai tace saboda ba haka ta so Muneeba ta amshi al'amarin cikin ba, ita kam koda tazo gidan a baya ace MUneeba ada ciki ita bata dashi ana jin ranar sai ta kusa Ladiye zuciya saboda di ciki, ammına ita sai gashi murnama akeyı wata 2ta haitowa mijinta da, Allah yasa ba Kisisina Lae dama Goggo tace balinta ne baka taba ganin 30 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria bacin ranta akan abin alherin wani ta iya duniyanci tamkar tsohuwar Karuwa Babu wani almashi a kalaman da take mayarwa Munecba, shi yasa Munecban ta datse hitar tasu tunda ta lura tamkar ta matsawa Suiwaban ne bata son Surutu a yanda take amsa mata a dakilė tana cikin zafin ciwo ne, bata san haushine ya tabi zuciyar Suwaiban ba kuma haushinma ita muneeban ne tunda bata nuna kishi da haushin Suwaiban ta sami ciki ita bata samu ba. Mujeeb tashi yayi tsam daga inda yake zaune ya dawo kusa da Munecba, ya zauna yasa hannu ta bayanta ya riko kalauunta ya rungumeta a jikinsa ya soma yi mata Magana cikin kulawa da tausayawa a sanyaye". Muneeba kiyi hakuri kullum addu'ata da fata inga na fara haihuwa dake sai gashi Allah bai nufa kece zaki fara Haifa min 'ya'ya ba watanki ce zata fara haifamin to ki dauki hakan amatsayin wani iko ne na Aliah da mutum bai isa ya chanza shiba amma kamar yadda nayi miki alkawari idan Suwaiba ta haihu na baki abinda ta Haifa duniya da lahira, itama zan gaya mata ko da na mutu kafin ta haihu to abinda za ta Haifa naki ne". Hawaye ne ya soma zarya a kumatun Muneeba ta soma magana, wallahi ni bana kaico ko in nuna damuwata `akan Suwaiba ta haihu ni ban haihu ba, tunda nasanbawai Allah ya manta dani bane, yana sane dani to don me zan nuna masa garnjen hakuri 31 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria nada gazawar hakuri na alhalin bansan hikimarsa ta hanani haihuwar da yayi ba. Kuma ba tilaswa Suwaiba zakayi ba wajen yardanta ka bani abinda ta haifa, kabi abin cikin hikima don ba dole bane su Goggo su yarda gara inma zaka bani to muyi abin cikin hikima babu maganar tilastawa. Ranar Kwana sukayi yana lallashin zuciyarta cikin tausayawa da dadaddan kalamai duk daba wai ta damu bane amma shi sai abin yana bashi tausayi kuma hakan da ta yi ya kara masa kaunarta tare da wani matsayi mai girma a zuciyarsa. ****** ****** Sun dawo Kasarsu lafiya sun tarar jikin Suwaiban ya danyi sauki har tana dan iya cin abinci, amma ba da yawa ba sannan ba kowane abinci take ciba. Ta rame sosai tayi fari duk daba fara bace, daka ganta kaga mai shigar ciki sai zuba shawagaba takeyi tunda iyaye sun yayyabeta ga Goggo ga Hajiyarta itama tazo jinya, kasancewar abun nema ya samu matar falke ta haifi ja ki jira kawai suke Mujeeb ya dawo suga irin murnar da zai yi tunda neman haihuwa yake ido rufe bai samu ba, gashi nan ma har wata kasa suka tafi don maganin neman haihuwar, sai gashi wadda ta zo kwanan nan ita ce Allah ya ba wadda ta dade din ba. 32 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Murnar da ya nuna ba yabo ba fallasa, su kansu abin ya daure masu kai kuma ya basu mamaki to amma fa ya nuna damuwarsa akan ramar da ya tarar tayi don zama sukayi suka tasa ta gaba shida Muneeba har Muneeban ta kawo shawarar ya kamata a koma da ita asibiti ko akwai wani abu da zasuyi mata tunda har yanzu tana aman kuma bata cin abinci sosai. Kamar dama jiranta Goggo take yi, ta na gama kalamin kai Suwaiba Asibiti Goggon ta dirar mata, Babu wani asibiti da za'a kaita, ai munje babu abinda suka tsinana mata sai da muka dawo gida aka yi mata jike-jike sannan ne ta fara samun sauki babu inda za'a kaita, shi sauki an sai hankali ake samunsa cuta ce ke shiga farat daya. a Tunda Goggo tace haka Muneeba bata sake maganar kai Suwaiba asibiti ba da daddare Muneeba tana shirin bacci ne Mujeeb ya shigo yake mata sai da safe wai Goggo t ace tunda ya dawo sai ya amshe su jinyar da suke yi ya dinga kwana da Suwaiba. Muneeba ta ce 'Ai ya zama dole ka dinga kwana da ita, tunda bata da lafiya su Goggo ai sun nasu kokarin ba za'a bar mana tsofaffi da jinya ba sanda kuka yi abinku basa ma gurin”. Ta mayar da abin wasa saboda ta lura ya shiga damuwa akan wannan tsari dasu Goggo suka shirya su a nufinsu zaiyi ta kwana gurin suwaiba har sai ta warke, ita kuma Muneeba tayi alkawarin Insha Allahu ba zata 33 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria nuna damuwar komai akan haka ba in dai don su kwareta suka yi to ba zata nuna an kware tan ba zata bisu a duk yadda suke s. Tun daga ranar sai ya kasance Muneeba bata da rabon kwana a gidan Suwaiba ke da kwanan duka, amma girki Munceba keyi tsakaninta da mijinta sai dai da rana dare nayi zai kasance a dakin Suwaiba tunda bata tashi amai da numfarfashi sai in taga ya dawo daga Offis amma da zarar ya fita da safe zata yi wanka tayi kwalliya ta fito dakin Goggo su hadu da Hajiyarta da Goggon suyi ta hira, har kyakyale dariya, zakaji tana yi ita dai Muneeba ba ta kawo idanu ta zuba musu taga iya gudun ruwansu, tunda duk wani lanbo da Kissa su suke shirya mata-yadda zatayi gashi nan kuma sun sami sa'a a kansa tunda har ya biye musu yana danne hakkin Muneeba ba tare da damuwarsa ba ita kuma ta dukufa kaiwa Allah kukanta akan wannan danniya da Mulkin Mallaka da ake yi mata babu halin tayi Magana. A wata safiya jikin Suwaiba ya matsa mata, suka shirya da Hajiyar ta da Goggo su ne 'yan rakiyarta zuwa asibiti Mujeeb ne zai kaisu, sunje an duba ta aka rubuta magunguna sai ya dawo dasu gida yace idan ya fito zai sayo maganin ya bayar a kai masu. Suna shiga dakin Munceba ya isketa tayi wanka ta saka kaya tana tsaye gaban madubi tana gyara daurin kallabinta. 34 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Yana shigowa ta soma tambayarsa "Lah" kun dawo ne? sam ban ji tsayuwar mota ba ya mai jikin ya ce gata can taji sauki Lanbo ne kawai ki kyaleta, Likita ma ya gaya mata ta dinga motsa jikinta tace, Kai abokin rayuwa wane. irin Lambo don dai cikin ba a jikin ka yake ba da munga irin naka Lambon ya janyota suka fada kan gado yana cewa "Zo nan kiji tawa larurar wallahi nima bani da lafiya". Ta ture shi tana cewa 'Don Allah sake ni kada ka yamutsa min kwalliya ciwon me kake yi, Y ace Ciwon rashinki nakeyi wata daya ai ba wasa ba, na takura da wannan jinyar ana daukan hakkinmu yau kam ba zan iya ba na azabtu da rashinki. Abinka ga masu kewar juna ba musu ba gardama ta sakar masa jiki, suka soma wasassinsu na ma'aurata, sun kai kololuwar wata duniya ne suka ji ana buga kofar falon Muneeban bugu mai karfi bana wasa ba da kyar suka lalubo hankalinsu da ya gushe suka saisaita shi sannan Mujeebun ya tashi da kyar yana rangaji zai fita sai kuma ya dawo domin a yanayin da yake ko waye zai iya gano halin da yake ciki ya dawo ya dubi Muneeba ta tallabe kanta tana jingine da allon gado ya ce, "Je ki gani ko waye, in Goggo ce kice ban shigo ba" zata yi magana ya daga mata hannu alamar ta yi shiru ta bar maganar. Ta tashi ta suri dankwalinta ta daura sannan ta je bude kofar falon, ilai kuwa Goggon ta gani tsaye, ta dubi Muneeban ta ce 'Mujcebu yana 35 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ciki ne? muna nan muna jiranshi ya zo yaje ya siyo wa Suiwaba magunguna ya shanyamu". Muneeban ta ce "Bai shigo ba, ni ban ma san kun dawo ba, sannunku ya mai jikin" Ran Goggo ya baci ta amsa a dakile 'Da sauki" ta juya ta koma tana sababi. "To ina ya shiga ga motarsa a waje dakinsa kuma a kulle ita dai Muneeba ba tace komai ba ta biyo bayan Goggon zuwa dakinta don ta duba jikin Suwaiban tunda dama nan ne dakin jinyarta. Da Muneeba ta dawo ta zo ta zauna a gefen gado da yake kwance lakadan abinsa ta dube shi ta ce, Goggofa na nemanka ashe jiranka suke ka siyowa Suiwaba magani shine kazo nan ka kwanta, don Allah ka tashi ka tafi kada ka jawo mini laifi ni babu ruwana. Kansa na jingine da gado yana kallonta har ta gama maganar ta sannan ya ce je ki rufo kofar falonki da key kizo in gaya miki matsalar da nake fuskanta a 'yan kwanakin nan, ina fatan zaki magance mini su ba zakibi sawun masu sani cikin wata matsalar ba". A tunaninta wata gagarumar matsalace ta same shi duk sai jikinta yayi sanyi da saurinta taje ta sawa kofar makulli ta dawo ta zo ta zauna kusa dashi tana cewa 'Wace irin matsalace kai kuwa ka shiga da har ka kasa gaya mini tun tuni sai yanzun ne zaka gaya min", ya kai hann ıwansa duka biyu ya rungumota zuwa jikinsa yana cea, ki bani 36 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria lokacinki ko yaya ne in dan sami natsuwa, sai inyi miki bayani matsalar tawa". Zata yi magana yasa bakinsa a nata ya hadiye maganar da take son yi, cikin kwarcwa irin tasu ta nagartattun maza da sukan mantar da matansu duk wata damuwa ta rayuwa ya bi ya shagaltal da ita da wasanni irin na ma'aurata hakan yasa ta manta da komai ta rungumi mijinta itama dama tana bukatar abinta daga ita har shi jukkunansu rawa yake yi saboda kewar junansu, sai da ya sami natsuwa ya tabbatar ya samu gamsuwa irin yadda yake so sannan ya sassauta mata amma duk da haka yana rungume da ita tsamtsam a jikinsa ya sauke ajiyar zuciyar a hankali dalilin natsuwar da

Chapter 2 of 12