Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 12
ta saukar masa. Sai da ya natsu sosai sannan ya tashi ya shiga bayinta yayi wanka a lokacin ita hr tayo nata wankan tana zaune tana busar da gashinta da (Hand Dryer) yana fitowa ya dubeta yana murmushi yace, 'Meye naki na busar da gashi? Ce miki nayi na sallameki? To ni yanzu ma da na yi wanka sabon karfi ne ya zo mini..Ni fa yau ina dakin nan sai yamma zan fita. Ta marairaice murya, 'Don Allah ka yi hakuri kaje ka siyowa Suwaiba maganin, kasan dai bata da lafiya, "ya dan kanne ido ya ce, Nima ciwon ai ta jawo mini na rashinki kusa dani na wata daya, amma yau na warke garau tunda na samu magani, zanje in sami Goggo anjima bazai yiwu a 37 ..aanon 7aria WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria cigaba da danne miki hakkin kwananki ba ana kwararki sam bazai yiwu ba". Ta yi saurin cewa, "Ni fa in don nice don Allah ka bar wannan maganar na yafe har sai ranar da Suwaiba ta warke garau" ya hada gira ya ce, wannan kawaicin naki na cutar da kai ni ba zan yarda da shi ba, ni kina cutata kema kina cutar kanki yanzu dubi yadda jikinki ya dinga rawa da gani an san kina cikin bukatar kasancewa da mijinki amma saboda kawaici kin daure kina cutar kanki, to bazai yiwu ba daga yau zan kashe wannan tsarin nasu tunda ba Shari'a bace Muneeba ta ce “Au sharrin da zakaimin kenan wai ina bukatarka har jikina na rawa, wato don na tallabi bukatarka shine zaka yi min tsiya ko, in halinka ne gobe ma zaka dawo, na daina rawar jiki akan bukatarka zakaga irin amsan da zanyi maka ya janyota ya rungume yana lallashi yi hakuri kada kiyi min abinda zan gwammace bin kawo kaina da bukatata gareki ba, ni kuma gashi daga yau na daina hadiye kwalamata a kankihaka kurum ni da halas dina ansa ni ina hadiyaryawu ai an yi an gama. Miko min rigata ma ki gani inje in siyo maganin nan in dawo ayi wacce za'a yi?. Ya amshi rigar ya saka ya dan taje sumar kansa dake kwance Lamban, ya gyara tsaf sannan ya zura takalminsa yace zoki budemin kofar baya in fita kuma ki sani yau anan dakin zan kwana kadama Goggo ta tambayeki kice kin yafe 38 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria kwananki don wallahi nib a zan yafe maki ba, ai an gaya mini ina fita take yin wanka tayi kwalliya ta fito fakin Goggo suna hira suna dariya sai na dawo ne take langabewa ita ga mai laulayi, kyale ta kawai nake yi". - Muneeba ta rike haba cike da mamaki ya aka yi ya san abinda ke faruwa t ace "Kai ammamutane da a ido suke, yanzu waye ya gaya maka wannan maganar?" ya ce 'Ina ruwanki da wanda ya gaya mini tunda ke kinki gaya mini, ana yi mini ha'inci kun yi gum da bakin ki. Ta ce, "Ni babu ruwa na yanzu kada ka fiddo maganar nan don cewa zasu yi ni na fada al'alin ba nib ace, gara kawai kabar maganar?. Ya amshi makullin kofar ya bude ya fice ta baya, ya zagaya ya shiga kotarsa ya tada ta ya fice a gidan. A daidai lokacin Goggo ta daga labule tana kallon ficewarsa cik da mamaki, sannan ta juya tana duban Hajiya Harira t ace "Dubi yaron nan she yana cikin gidan nan amma da na tambayi matarsa tace bai shigo dakin taba lallai yarinyar nan munafuka ce sai nayi maganinta, ita ga jarababba ko? Hajiya Harira tayi wani murmushin takaici tace, "Ai yarinyar nan sai kin tashi mata tsaye don na lura ta kama miki da a hannu komai fa za'a yi a gidan nan sai da amincewarta". Goggo ta yi kwafa ta ce, sai na tashi tsaye ko sai mun tashi tsaye, ai abin da ya shafeni shine zai shafeki, tunda idan ta 39 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria mallake mujeebu tana juya shi yadda ranta ke so kinsan Suwaiba ba zata kai labari a gidan nan ba. Ni na rasa irin wannan jaraba wato tunda na hana shi kwana a dakinta shine zaiyo satar hanya da rana ya lallaba ya shige suyi abinda zasu yi sai tashin motarsa kawai mukaji. Kyale almuri zai dawo ya same ni, in banda taci darajar Suwaiban kada in kwareta dana sa tsidugu ya hana a bar aiki sai inga karyar jarabar ta". Hajiya Harira ta ce, "a'a kada ki yi haka ko don Suwaiba din amma ai za mu iya sa ya yi mana dan baka duk ranar girkin ja'ira mu dana ba zai iya aikin komai ba. Ko ya kika gani? Goggo ta yi dariya tace haka kuwa za'a yi aminiya ai mu kowacci tuwo da mu miyar ma bai sha ba balle ya ci tuwon. Sai dai ba yanzu za'a yi ba kin san bata da kwanan girki sai mu bari sai idan ta soma kwana da mijin sai mu yi mata lalata 'yar tselen uwa jarababba suka sheke da dariya suka tafa ita kam suwaiban tana kwance tana jin tuggun iyayen nata wanda hakan da suka shirya yayi mata dadi, dama kishí na ta nukursutarta tunda taji sunce gashi ya fito daga dakin Muneeban har suna fallasa abin da yaje yi dakin, sai take jin tamkar taje ta shake Muneeban don haushi, itafa in son samunta ne ace Mujeeb nata ne ita kadai babu wata mace da zata rabar mata shi, saboda shi kyakkyawa ne na shiga taro, gashi gwani ne gurin iya soyayya, ya iya tarairayar mace ya mantar da ita duk wani bakin 40 D WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ciki na rayuwa ya san hanyoyin faran ta wa mace rai da yadda zai jiyar da mace dadi ta ko wane fanni, sai dai Kash! Duk wannan jin dadin da tarairaya tare ake raba mata da wata ita kam duk hanyar da zata bi sai abubuwan nan sun zama ita kadai ake wa, ba tare da wata ba. Ta ja dogon tsaki tayi juyi saboda takaicin Mujeeb ya je dakin Munecba kuma ta san mai yaje yi tunda daren yau sai da ya neme ta taki yarda dashi a dalilin ta nemi wasu kudi masu yawa bai bata ba wato shine ya kai bukatarsa ga matarsa lallai sai sun sa musu ido ta yadda bazai sake fakar idanu ya je can ya yi wani abu ba (Kun ji fa karfin hali jama'a mutum da matarsa). Bai dade da barin gidan ba ya dawo dauke da ledar magunguna da ya siyo ya shiga dakin Goggo sai ya iske ita kadaice, Suwaiba da Hajiyarta suna can dakinSuwaiban. Ko amsar maganin bata yi bat a rufe shi da fada 'Wato ka mayar da mu shaka tafi kana jina na je dakin Muneeba neman ka ashe kana ciki kayi bülun bukui ta fito tace baka nan ita barama na ganka ba, in ita bata maida ni a bakin komai ba kaima sai kabiye tata to ka kyauta tunda kayi yanda ranka ke so ni ka bata nawa ran "ya zauna kusa da Goggo yana cewa "Wai nema na kika yi tayi a gidan to ai ni fita nayi gurin bako a waje ina shigowa na shiga mota na tafi siyo maganin ita Muneeba ma bata san na dawo ba, can 41 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria kika je nema na?. ta gyada kai, can naje mana ai na dauka kana can, ashe ba karya tayi min ba, sai ka dauki maganinka kai mata tana daki. Har ya mike sai ya dawo ya zauna ya ce "Yawwa Goggo dama ina son muyi wata magana". Ba tare da ta kalleshi ba ta ce, ina jinka ya rage murya, "Ga ni nayi tunda suwaiban ta sami sauki kuma ga Hajiyarta zan dinga yin kwana bibbiyun yanda nake yi a dakin kowaccensu". Goggo ta gyada kai ta ce 'Yaushe ne Suwaiban ta warke? Ina ce jiya ciwon tashin ya yi har muke je asibiti yau shine za ka kawo min wata tsirfa kokuwa ita Muneeban ce tace bata yarda ba? Ya ce "Ba ta ce haka ba nine dai naga dacewar hakan sabo da gaskiya an shiga hakkinta ina tsoron Kada Allah ya kamani da laifin na zalunceta". Ta ce to Meye abin zalunci anan inace da yardarta aka zartar da abin nan amma yanzun don munafunci zakace ana zaluntarta. To shikenan kaje kayi ta kwana a dakinta muna sa'ido muga abin da kwanan da take so zai tsinana mata, bakin ciki ne sai ya kasheta, ita ta hana kanta haihuwa wata tazo ta samu kuma bata isa ta hana ba, sai na rike danka nayi masa rawa a gidan nan yace "Goggo addu'a zamu yi itama Allah ya bata don rashin haihuwa wallahi ba daga gareta bane daga Allah ne kuma Insha Allahu zai bata Muneeba ai 'yar kice duniya da lahira bai kamata ki so wani fiye da ita ba". 42 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Tayi magana da zafin zuciya a kakkaushe, "ba zan so ta ba sai kazo kasa ni na sota, ita da uwarta ai ba sona suke ba, basu mai dani wata tsiya ba ki ya sa nima, na watsar da zumuncin na kama masu sona, Hajiya Harira ai ta gama min komai kaima ta gama maka komai har ta aura maka diyarta gashi yanzun kana zaune lami lafiya har ga karuwar zuri'ah nan ya baku, zuri'ah ma ba'a san iyakarsu ba tunda yanzun za'a soma, ai kuwa dole in sota ita da uwarta. Mujeeb ya raunana murya yace "Shike nan Goggo kiyi hakuri Allah ya huci zuciyarki". Tа се kaine abin aba hakuri tunda an ta6o gimbiyarka ka, mma ni ai banji haushi ba kuma babu abinda zai bani haushi akan Muneeba, so ne baka isa ina nan ka nuna kafi son ta da Suwaiba ba tunda bata fi Suwaiban da komai ba a gidan nan sai ma suwaiban da ta fita tunda itace tazo da albarkar haihuwa, Ganin idan yaci gaba da zama a dakin zancen Goggon zai fi haka nuni kuma Muneeban na iya shigowa ta riski maganganun Goggon kuma ko ta shigo Goggon ba fasawa zata yi ba, saima abin da zai karo shi yasa ya mike tsam ya ce "shi kenan Goggo ayi hakuri ni zan koma offis". Ta се " А dawo lafiya kada ka manta ka siyoa Suwaiba Kankan. da Abarba har da mangwaro dan juyo yana duban Goggo yace Ni yanzun ban san indan zan sami mangwaro ba tunda ba lokacinsa bane" 43 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Та се "Ка dai dudduba ko ka aika kila a samu, kasan mai ciki da kwadayi, ya za ka yi tunda Allah ya baka abin da kake nema shekara da shckaru. Ya juya ya fita yana cewa "Allah yasa a samu sai a siyo mata". A ransa yana kakabin yadda Goggo ta dauki son duniya ta dora akan Suwaiba balle 'yanda take da ciki ko yaya tai wani motsi sai tayi mata sannu tare da tambayar ta mene ko me take so in kuwa shagwabar ciwonya ya tashi to Goggo hart a kanfi Hajiya Harira nuna damuwa da ciwon koda yake ita Hajiyar ta san Lanbon 'yar ta duk da dais u ne suke kitsa mata komai har yadda zata marairaice cikin ciwo idan Mujeeb din yana gida, amma sam bata nuna kulawa ga 'yar dan uwanta yadda kason ba su hada alakar komai ba haka take nunawa Muneeba duk da yake ita Muneeban na yi mana tsananin kulawa a matayin ta na Goggonta kuma sirikarta amma Goggon wannan sam baya birgeta illama idan ta yi wani abun don kyautatawa ta rikideshi ya zama rashin kyautatawa, shine yasa Muneeban ta ja baya da yi mata wasu abubuwan kyautatawa tunda Suwaiba tazo gidan duk dadai ba dainawa tayi ba alhalin kuma ita Suwaiban bata yi, kamar yi mata wanki, da goge mata kaya, duk da akwai mai wanki, sannan ta share mata daki ta gyara shi tsab ta sa turaren wuta yayi ta kamshi, idan kuma tasan Goggo nason wani avu ko da bashi ta dafa a gidan ba zata sake shiga WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria cikin kicin ta girka mata, ko wajen tarban baki da jama'arsu na Dukku Munceba ce kan gaba wajen kyautata masu, amma Goggon duk bata gani, ita dai burinta shine ganin gazawar Muneeba tafi son a yabi Suwaiba. Wannan al'amari yana bashi mamaki yadda zumunci ya lalace yanzun kowa nasa ya sani ba'a son 'ya'yan ‘yan uwa sai mutum ya nuna yafi son bare kiri-kiri akan dan uwansa (Allah kasa mu gyara mu'alamarmu ta zumunci Allah ka bamu ikon son zumunci da son 'yan uwanmu na zumunci amen, kada ka bamu ikon cutar da wani ma balle mu cuci dan uwanmu na jini amin). Bai shiga dakin Muneeba ba Ofis kawai ya wuce don idan ya shiga zai karawa kansa da ita wani laifin ne. Da dare ya dawo a dakin Goggo ya iske su suna cin abinci amma babu Muneeba, Suwaiba na nan kishingide tana ta yatsina ga kayan abinci nan birjik a gabanta. Bayan ya gaida su Goggon sai ya juya yake tambayar Suwaiban 'ya jikin na ki" ta yi wani far da idanu ta juya su wai nan duk alamun tana jin jiki ne tace, "Jiki da sauki ya ce kinci abinci ko? Ta girgiza kai. Goggo tayi farat tace "Kasan bata cin tuwo bata son shinkafa to tuwo yau akayi tunda an san bata so". Mujeebu yace "To ai Goggo kinsan ka'ida indai 'kina gidan nan da dare tuwo ake yi tunda kinfi sce shi, itama Suwaiban ai naga tana cin tuwon". Ta ce "In wa tana ci to yau dai bata so sai a san abinyi".ya turawa 45 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Suwaiban ledojin da ya shigo dasu ya ce "Ga abarba da mangwaron nan an samo sai ki sha, ga gasassar kaza nan tunda bakya cin nama sai kici". Ta sa hannu ta ja ledar tana dubawa, shi kuma ya mike ya fita zuwa dakin Munceba. A kicin ya hangeta tayi kwalliyarta da wata doguwar rigar shadda Galila ya lallaba ya damke kugunta ya rungume ta, tayi kara saboda tsoro tace "Subhanallahi, haba abokin rayuwa wallahi ka ban tsoro' Ya cusa kansa cikin wuyanta yana jan numfashi ya ce, "In banda abinki wa zai cafke ki ya rungume in ba ni ba me kike yi ne a kicin zaki 6ata min kwalliya? Ta ce wallahi Suwaiba ceta ki cin tuwo ni ban son kuma yanzun bata son tuwo ba, shine nake mata faten (Arish) dankalin turawa da hanta ina ganin zata iya ci tunda ruwa-ruwa ne. Ya kara rungumeta cike da taiusayinta a zuciyarsa na irin wannan hidima da take da Suwaiba kuma tsakani da Allah takeyi amma su Gogo basa gani y ace "Allah ya baki ladan abinda kike yi dominsa, ya baki abin da kike so a duniya da lahira, amma ki daina wahalar da kanki don yanzunma wannan da kika yi ba Karamin aikinta bane ta ce shima bata ci". Tayi murmushi ta ce ko ta ce bata ci bazan damu da wahalar dana sha ba tunda masu ciki suna fama da irin wannan larurar ta rashin son cin abu kaza da kaza ni babbar matsalar La da ta kwana da yunwa kasan babbar matsala ce 46 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ga jariri idan uwarsa ta kwana da yunwa" ya ce Ba zata kwana da yunwa ba tunda ga su kankana can da mangwaro da ta ce a siyo mata na kawo mata ko su tasha ai zasu rikcta har gobe". Suna nan suna hira har ta gama ta juye a filet yadda zai huce sai tiririn kamshin dadi ke tashi, kai da ganin faten kasan zai yi dadi sosai tunda ya ji zallan hanta. Mujeeb ya dubeta ya се "Raina ya biya ni ba za'a sammini ba? Та се, Gaskiya banyi da kaiba, tuwonka na can bisa tebir wannan don mai ciki nayi shi ita kadai, sai ka bari idan ta rage sai a baka" Ya gyada kai ya ce, 'kwarai yanzu dai na lura kinfi kula da al'amuran Suwaiba akaina, shikenan nima zan rama" tayi gaba dauke da Filet a hannunta tana cewa, "Allah ba zaka iya ramawa ba, sai dai ka rame". A tare suka shiğa dakin Goggo ta wuce har gaban Suwaiba ta aje mata Filet din tana cewa "Ga fatan dankali da hanta nan nayi maki shi ruwa-ruwa yadda zaiyi maki dadinsha" Suwaiba ta dubi faten a yamutse ta ce "B azan iya sha ba nasha abarba da mangwaro sun isheni" Muneeba ta risına gaban Suwaiba tana lallashinta, tana jujjuya faten da cokali don ya huce tana cewa Ki daure I sha ko ba yawa, gara ki dinga cin abinci balle irin su hanta da dankali za su saki dinga jin karfin jiki. 47 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Goggo tayi karaf ta ce "Ke kuwa da naci kike tunda tace bata sha ki kyalcta mana sai kace dole, ina dalilin wannan naci ko so kike tasha ranta baya so ta kwana tana amai" Ba Munceba ba hatta Mujeeb sai da ranshi ya baci akan wafannan surutan na Goggo, amma sai basu nuna ba, Mujceb mai sai ya maida abin wasa don ya gusarwa da Munecba bacin ranta ya dauke filet din ya soma sha yana cewa," Ai ni gara da kika ki sha tunda kin ki sammani wai sai dai idan kinsha kin rage sannan kya bani, tunda ni an watsa ni a kwandon shara ke kadai ake tattali a gidan nan? Ya dibi faten da cokali ya kai bakinsa ya tauna ya hadiye ya lumshe ido ya ce "wonderful! Yarinya dadi ya barki wallahi, kin kuwa ji dadin faten nan gaskiya zaki cuci baby na in bai sha faten nan ba, oya bude bakinki in baki, da yake Hajiya Harira ta fita Goggo da Muneeba ne a dakin sai ta bude bakinta ita a dole miji na soyayya da ita gaban kishiya, don taba Muneeba haushi ne ya sa ta bude bakin bata san shi kuma yayi haka ne don Munceba taji dadin wadda tayi abu dominta tasha ba. A haka yayi ta bata suna sha tare, Muneeba na musu dariya, har suka shanye, ai dole ta shanye tunda yayi dadi girki ne na kwararru ba irin nata na 'yan kwiya ba nan dà nan ayi girki a gama sannan b bu wani dadi Goggo dai tana gefe tana wa Mujecou tsiyar bashi da kunya a gabanta yake ba X WATA KUSAN 2 3 Rahmatu Hassan Zaria matarsa abinci a baki mujceb yana barin dakin Goggo, dakinsa ya wuce yaje yayi wanka, ya gabatar da Sallar Isha'i da shafa'i da wutiri saboda bai samu jam'i ba, ya yi shirin sa tsaf! Ya nufi dakin Muneeba ya iske har yanzun bata koma dakinta tana dakin Goggo sai ya haye gadonta yayi kwanciyarsa yasa hannu ya latse fitíla mai haske ya bar mai duhu ta bacci. Bai dade da kwanciya ba Muneeban ta shigo, yana jinta ta mayar da kofarta ta rufe, ko da ta shiga dakin baccinta taga fitilar bacci bata dauka wani ne ya kunnaba sai tayi tunanin ita ta kunna kafin ta fita, kawai sai ta wuce bayi tayi abinda zatayi ta fito yana kallonta ta hau abin sallah ta kabbara sallah har ta gama duk yana kallonta. Ta cire kayan jikinta ta saka 'yar guntuwar rigar bacci sannan ta haye gado ta soma karanto addu'ar kwanciyar bacci, har ta yi ta gama bata fahimci da mutuma dakin ba sai da taji alamar saukar numfashi ne tatsorata, ta yi saurin kai hannu ta kunna fitila mai haske, kawai sai taga mutum kwance lakdan yana kallonta cike da murmushi a fuskarsa ta sauke ajiyar zuciya itama idanunta a kasan tace, Kai abokin rayuwa ka tsorata ni sosai yaushe ka shigo dakin nan? Sannan me ya kawoka har ka haye mini gado ka kwanta? Ni dai so kake kawai ayi ta dora mini laifi a gidan nan, ana ce min jarababba wai ni nake jawoka da ire-iren kwalliyar 49 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria da nakeyi" yayi dıriya yana girgiza kai yace "Ai ni ya kamata su kira jarababbe tunda nine nake biyoki, haka akeso mace tayi abin da zata janyo hankalin mijinta gareta, kinsan Allah nu jan bakin nan da kika sa yayi miki kyau nake ta kallo Allah ya so kima ban tsotse shi a dakin Goggo ba don wallahi ina kallon bakinki ne ina dada tsuma yau in ban tsotsa bakin nan ba ai sai na kwana ina mafarki da sumtatu shi yasa na nunawa Goggo gazawata tunda rana na gaya mata yau zaki amshi kwananki gaskiya ina shiga hakkinki kada Allah ya kamani in shiga uku, duk da dai amincewarki nake kwana dakin Suwaiban to amma wallahi na san kawaici kawai kikeyi kuma aka tialasta zuciyanki kika amince na dole amma ni nasan yadda ki ke ji da ni ba yadda za'ayi ki barwa wata ni, to yau na dawo na nuna musu nine jarababbe, kwalamata ta motsa a kanki bazai yvu du an lasamin zuma in hakura da ina ba". Ta t hi zaune tace, "Kayi hakuri ka tashi ka tafi in don nice har ga Allah na yafe, ka cigaba da kwana dakin Suwaibar har sai ta warke yadda yakamata" shima tashi yayi ya zauna yana mata "wani duba na baki isa ba yce "Wannan abin da akayi bafa tsari bane na Musulunci, an dai yi son raine saboda a farantawa Suwaiba ke kuma ko oho, in ba son rai ba me ye amfinin zuwan Hajiyarta da zaman da take yi anan tunda ba za ta kwana da JU WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria yarta ta yi jinyarta ba, sai ace dole ni zan dinga kwana da ita ina jinyarta wato tunda ni nayi mata cikin dole ne inyi jinyarta ko? To daga yau na daina daukar hakkinki duk randa nake dakinta nayi jinyarta in kuma banasan Hajiyar tayi itama ai tanason jikan. Duk yadda Muneeba ta lallashe shi akan yayi hakuri ya koma dakin Suwaiba ita ta yafe, sai ya nuna mata sam hakan ba zai yiwu ba, in ita bata bukatarsa kusa da ita to shi yana bukatarta balle ma yaga zahiri lalle tana bukatansa ko ga yadda tayi saurin amsar tayinsa na dazu da yadda ta dinga rawar jiki yasan tana cikin kewarsa, amma don gulma shine yanzu za ta koreshi shi kam ba inda zaije. ***** ***** ***** Cikin Suwaiba a halin yanzu ya sami watanni biyar kenan, don har ya fito, kuma ta sami lafiya garau su Hajiyarta 'yan jinya da Goggo tun yana wata kusan hudu duk suka koma Dukku, tun bayan komawarsu Mujeeb yace tunda ta sami sauki ta amshi yin girki don ba zai yiwu a barwa Muneeba hidimr girki wata da watanni ba, in ta yi mata lokacin tana ciwo to yanzun ta sami sauki sai ta amsa, in kuma ba zata amsa ba, to ba ta da kwana, in har ba zata amshi ..girki ba, don ba zai yiwu Munceba tayi mata girki WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ba idan darc yayiniya zuwa dakin miji ko da baije nata ba, ba kunya ba tsoro. Sanin halinsə yasa a ranar ta amshi girki ta soma sai Muneeban ta sami saukin hidindimun gidan, con ma wasu abubuwan yaron gidansu Jume yanayi kamar wankinsu da guga da sharar gida da wajen gidan. Suwaiba fitowar cikin jikinta yasa take yanga da cikin take takun kasaita a cikin gidan, don ta nuna wa Muneeba cewa yanzun it ace da gidan, tunda ita ce mai haihuwa, ita kuma bata haihuwa sai ta taya ta rainon abinda zata dinga haifowa. Ganin jikin Suwaiba yayi garau har taje Dukku biki ta kwana biyu ta dawo, ya sa itama Munecba ta roki Mujeeb tanason zuwa Dukku ta kwana ko daya ne, saboda zasuyi shirye-shiryen bikin Murjan Hedimasta da yayan Muneeban Mustafa. Tana sa Dukku Mustafane ya dauketa a mashin dinsa suka tafi gapin gidan da Mustafa ya gina a nan Dukkun a unguwarsu ta sego babu nisa sosąi tsakanı da gidan iyayensa gidan sasa guda biyu ya gina na gaban gidan shine nasa da amaryarsa, na ciki kuma shine na iyayensa, don yana son ya rabasu da zaman gidan gandu, ya raba imnaisu da matsi da Takura dasa ido irin na jama'ar gidansu, ko da yake yanzu wannan halayyar da suke nunawa innarsu duk sun rage a dalilin WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Lokacin biki ku-va ji tayi tamkar kafafunta zasu tsinke saboda zirga-zirga tsakanin gidansu da gidan Hedimasta. Ba ita ta huta ba hankalinta ya natsu har said a aka kawo Murja gidansu a daren ta shiga sasan nata tana mata tsiyar irin wahalar da ciwon jikin da bikin su ya haddasa mata "Murja ta hau bata hakuri da cewa, "Yi hakuri 'yar Kanwarmu, ai dole ki wahala Kanwar Ango kuma babbar kawar amarya bri in baki Panadol Extra kisha ki watsattsakc. Ta balla mata harara ta ce, ki rasa abin da zaki bani sai Panadol Extra Hmmm!! Allah Sarki duk rashin abokin rayuwata ne a kusa da banji wahala haka ba, idan dare yayi zai yi mini tausa nan kuwa ba maiyi mini sai ma kara mini zirga-zirga da kuke tayi". Murjs tace, "Kr wannan abokin rayuwa yaji dadi motsi kadan a yabeshi nima dai gobe-gobon nan z radawa nawa yayan sabon suna" ta i murmusai ta ce, Au abin gasa ne? to ko kin rau. musa ba zai yi dadin da yaya naba" ta mike tana cewa Linza ba zaki cikani da surutu ba ki kara min ciwon kai dama fansar wannan ciwon kai kaza. amarcinki ta daren yau in b naka ba bazan yarda ba sai na gayawa abokin raytwa kun wab nile da mijinki". Murja tana murmushi tace kwamtar da hankalinki kanwata kazar duka zan baki, harma da duk abin da zai kawo, kinga kura da shan bugu 54 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria gardi da amshe kudi kenan" suka kyalkyale da dariya suka tafa. Muneeba tayi mata sai da safe ta fita. Da kyar Munceba tayi kwana biyar a Dukku, saboda yawan waya da Mujeeb keyi mata lallai lallai zai turo a dauketa da yaga taki bashi hadin kai ta dawo sai ya biyo sawunta, ita kuma dama sati daya ya bata tayi shi yasa tace sai tayi satin zata dawo shi kuma yace gidan ba dadi a dalilin bata nan, dole yazo ya dauketa suka koma Gombe. Cikin Suwaiba a halin yanzun ya tsufa har ya kai watan haihuwa duk wani shirye-shiryen daya kamata ayi na tarar jariri anyi shi, Muneeba ce ya wakilta takeyin komai hakan sai

Chapter 3 of 12