Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 12
ta matsa min sai na dawo wai ba haka muka yi da mijina ba, shi yasa na lalla6a haka nan na dawo, idanu a rufe na shigo gidan nan shi yasa ba ku ji dawo wata ba". "Munceba t ace, "Subhanallah! To Kin kira Baban Baffan kin gaya masa, kinga ai ya kamata ki ga likita tunda ba ke kadai ba ce, sannan ma dare ake tsoro". Suwaiban ta yunkura ta tashi zaune ta na cewa "Ai ina shigowa na sha magani, yanzu haka ciwon ya lafa min. Muneeban ta dora Baffa bisa gadon ta na cewa, "Baffana baka ga mama ta dawo ba ne, je ka yi mata sannu da dawowa". Tana aje shi, ya tsallara ihu ya makalkaleta yaki yarda ya zauna shi ala dole ba zai sauka ba, dole ta maida shi ta rike Suwaiba haushi ya kamata na irin kuiyar da Baffan ke mata ta ce, "Allah ya raka taki gona, ni dai ka ke wa kuiya ko? Zaka ga nayi wani sabon yaron kwanan 109 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria nan saura in ga 'yar kafarka a dakin nan sai na kore ka". Muneeba ta yi dariya ta ce, "Kar dai ki sa ya janye sabon yaron mu barki ke kadai". Ta cc, "In kuka yi haka ai bakuyi min adalci ba, gara dai a bar min sabon ke ki rike tsohon". Duk suka yi dariya Muneeba ta fice dauke da Baffa. Suna fita Suwaiban ta raka ta da wata muguwar harara tare da jan tsaki sannan ta yi kwafa ta ce, "Idan na so ne za ki zauna ki dinga yi min raino, idan kuma ban so ba, a yi waje road a bar min gida ni da 'ya'ya na mu sakata mu wala, har Goggon taku da take wani zakalkalewa kullum tana yawon gidan danta duk sai na yi maganinku bari dai miji ya zo hannuna, idan na mallake shi zaku banbance tsakanin aya da tsakuwa". Da dare ya yi tana jin dirar motar Mujeeb tayi saurin barin abin da take yi ta haye gado ta shige cikin bargo. Bai shigo dakinta ba saida ya gama abin da zaiyi a dakin Munceba, sannan ne ya nufi dakinta, duk da cewar yana shegowa Muneeban ta gaya masa suwaiban ba ta da lafiya baije dakin ba sai da ya canza kaya. Ya isketa sai kakkarwa take yi tana fadın wayyo Allah zan mutu. Ya dan tsaya a kanta yana kallon ta sannan ya sa hannu ya bude rufar da ta yi wa fuskarta ya ce, "Kin san baki da lafiya me yasa tun da kika dawo baki kira ni ba, da kuma ban dawo 110 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria da wuri ba fa?" ta yi Magana a sanyaye "Ka yi hakuri na dauka maman Baffa ta kira ka ta gaya maka". Ya ce "Ni ba a gaya min ba yanzu sai ki tashi mu je asibiti". Ta sake marairaice murya tace, "Ka ga dare ya yi kuma yanzu ciwon ya lafa min na sha. magunguna" Ta yi saurin fadın hakan ne don bata son zuwa asibitin tunda ta san ba ciwo ta ke ba, tarko ne ta ke son dana masa don ya kwana a dakinta, sannan ta bi duk wata hanya dà zata bi ta yaudare shi zata bi, don ganin ta karasa aikin da boka ya sata. Ya sake dubanta ya ce, "Kin ci abinci ko?" tace, "Eh, na ci" ya ce, "Allah ya kara sauki ni zan je ina da ayyukan ofis da zan yi na cike wasu takardu zan dawo kafin in kwanta" ya juya ya tafi, to damarta ta kufce kenan? Ta yi saurin yin Magana kafin ya fice."Don Allah dan dawo ina son yin Magana da kai", ya juyo yana dubanta ya ce, "Magana ? ina ga zai fi kyau ki bar maganar sai zuwa gobe kinga na ce miki akwai aikin ofis da zan yi, kuma gobe me zan yi (Submitting) takardun". Ta yi Magana cike da kisisina fuskarta dauke da yanayi na neman a tausaya mata tace "Yi hakuri maganar ba mai tsawo bace dama alfarma zan nema na yau kadai". Ya dawo cikin duban fuskarta tare da nazarin kalamanta wai na neman alfarma, sanan ya tambayeta, 111 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria in dai bata fi karfina "Wane irin alfarma ce fadl ba sai in yi miki", Shi anasa tunanin alfarma ce ta neman kudl tunda ya santa ya san halinta a kullum sai ta kawo kokon barar rokan kudi a gurinsa, shi sam bai saba ba saboda Muneeba bata rokarsa abu ko tana da bukatar, sai dai shi ya kangano lokutan da take da bukatar kudi, idan sha'anin 'yan uwa ya tashi to tun kafin ta nemi ya bata yake bata, in ma bai bata ba ta kan iya yin hakuri tayi amfani da dan wanda ke hannunta, sabanin Suwaiba da har abin nata ya ishe shi, don ko yau da za ta tafi sai da ta matsa masa ya bata dubu hamsin wai Hajiya ce ke da matsala za ta bata, kuma ba ayi sati biyu ba da ta amshi wasu dubu hamsin din sune aka hada aka ba boka dubu dari, ba su ci ba ba su sha ba ko da yake idan bukatarsu ta biya za su ninninka fiye da haka. 'Ta dan soma inda-inda don ta rasa ta inda zata bullo masa tunda ta san halinsa, ya ce "Ke nifa zan tafi tun da ba zaki fada ba". Ta daure tace, "So nake ka taimaka yau ka kwana anan don ni wallahi idan ina ciwo in baka kusa da ni sai inji ciwon na karuwa, amma idan kana tare da ni sai inji ciwon ya tafi". Ya yi dariya yana girgiza kai y ace, "Wannan abin da zuciyarki ta raya miki sam ba zan yuwu ba, tunda zuciyarki bata yi adalci ba da ta raya miki yadda za a tauye hakkin wani saboda ayi mata abin da take so, ko da can da kika ga a cikin 112 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Baffa na tare a dakinki ina kwana wallahi bisa tirsasawar Goggo ne, amma yanzu babu wanda zai tirsasani in tauycwa Munecba hakkinta, ai abin ya yi yawa don dai tana da kawaici da hakuri sai ayi ta mata cin kashe Allah fa sai ya tambaye mu". Ta marairaice murya, "ta na Magana da nuna alamun zafin ciwo, "Wallahi ni ba don in tauye hakkinta na roki wannan alfarmar ba, na rasa yadda zan yi ne, wallahi ni kadai ne san irin azabar ciwon da nake kwana cikinsa, ganinka kusa da ni yana rage min radadin ciwon amma shike nan ka tafi, dama tsiyar auren mijin wata kenan, ya zan yi dole in yi hakuri". Ta koma ta kwantar da kanta bisa filo, ta soma zuraro da hawayen kinibibi, ya dan dube a ya kauda kai sabo da tausayinta day a ja ya ji yana son yayi tasirin rinjayar zuciyarsa. Ba tare da ya ce mata komai ba ya sa kai ya wuce ya barta. Ya gama duk abinda zaiyi a dakinsa sannan ya nufi dakin Muneeba ya isketa kwance bisa 3 sita tana kallon wa'azin kasa da aka yi a Zaria a tashar Sunnah TV. Baffa kuma na kwance a ruwan cikinta tana dan bubbuga shi ya riga da ya yi bacci. Ya zauna a gefen fuskarta a kasan kafet yace, "Uwar gida ran gida yau kasaitar ake ji ba a biyo ni ba har na ci abinci na yi wanka kina nan kina riritar Baffa ni an watsar da kula da n”. Afuwan abokin rayuwa, yau rigimar Bafffa ta 113 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria 4 ! daban ce lallai shi sai a jikina zai yi bacci, naga baccin ya yi nisa idan na lallaba na maida shi gado sai ya farka, shine muka dawo falo yanzu nake tunanin in aje shi in bika sai ka shigo. Ya jikin Suwiaban ya hanani ma in koma in dubota sai daru yake yi". Ya shafi sumar yaron yace "Tun dazun na bar dakinta, jikin nata dai har yanzu shine ma nake tunanin ko zaki je can ku kwana tare ko kuma inje gidansu karime in fauko ta su kwana tare". Ta girgiza kai tace, "Haba dai kaje dauko Karime da daren nan, ni meye amfani na, sai dai kuma kai ya kamata ka kwana da ita saboda ni ko munje can kwana Baffa ba zai barta tayi bacci ba yadda yake jin rigimar nan yau, gara kai ka je can ka kwana”. Ya yi haka ne dama don ya sami yarda daga gareta ba wai koda yaushe su dinga tirsasata suna shiga hakkin ta ba, sai gashi ita da kanta ta bashi dammar ya je ya kwana da Suwaiban shi yasa a ko wace dakika a rayuwarsa yake jin son Munceban na kara yin tasiri mai girma a zuciyarsa. (da ya san gadar zare Suwaiba ta dana masa da bai je ba). Ya gyara zamansa yana fuskantarta yace, "Ba zai yiwu mu dinga' shiga hakkin ki ba, don bata da lafiya, ya zama ina kwana ko da yaushe a dakinta wancan karonma ganin idon Goggo sanan da bin umurninta ne yasa na tare da kwana a can amma yanzu ba zai yuwu ba Karime kawai za ta 114 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria dawo nan duk ranar da bana gurinta sai su kwana tare, tunda nima idan na kwana gurinta ai ba dauke mata ciwon zanyi ba". Muneeba ta ce,"Eh duk da haka ganinka kusa da ita zai dan rage mata radadin laulayin kasan sha'anin mata da miji, ko ni ce zan fi son kana kusa da ni, yanzu dai dan yau abar maganar Karime, na amince ka je ka kwana mene ne abin damuwa don ka kwana can ba matarka ba ce ni wallahi bana zafin kishi a kan wannan sannan kuma larura ai ta kori komai". Nan da nan ya Gata rai ya ce "Au yanzu ke ba kya kishin in barki in je in kwana da wata? Lallai ashe nine ke rawar jikin sonki tunda har ba kya kishin ina tare da wata. Dama nasan ba zaki taba damuwa da al'amurana ba balle har ki so ni, tunda tun farko ba ni ba ne zabinki, ni kuwa gashi na manta da son duk wata diya mace a duniyar nan ke kadai ce ke mulkin zuciyata" ya kare maganar tarc da sauke ajiyar zuciya. Munceba ta tashi a hankali don kada Baffa ya farka ta zauna idanunta kyar! Akan Mujeeb domin maganganun sa sun soki zuciyarta tunda har ya budi baki yace "Shine ke sonta ita bata sonsa alhalin inda bata son shi babu yadda za ayi ta iya zama da shi na tsawon shekarun da suka vi, ita kam in dai sai ta yi haukan kishi a kansa skane ba zata iya ba, zubda mutuncin kai ne da ragewa kai Kima. 115 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Ta tausasa muryarta ta ce masa "Nice kuwa ke kishinka, tunda ni kadai na san irin son da nake maka, sai dai ni ba zan yi shirmen kishi ba nc,irin na hauka yadda wasu matan ke nuņa wa,ku kuma maza kuna son ayi ta haukacewa akan kisinku kuna murna kuma jin dadi, idan kuka garo kan wannan ta nan sai ku garo na waccân ta can, daga karshe sai ku hado kawunan ku gwara a tare sai rikici ya balle ayi ta yi, ku kuma kuna gefe kuna jin dadi ana rigima akan sonku, wallahi maza kunji dadinku 'yan gatan mata ne", Mujeeb ya kyalkyale da dariya ya ce, "Au nan kuma kika bullo? To ni dai ba na gwara kawunanku, ni dai na sań nawa tsarin ta inda baki ya karkata nan miyau yake zuba kin gane ai?" Ta girgiza kai, "Ni ban gane wannan hausar ba, ka san ni dai ba bahaushiya ba ce". Ya ce, "Amma Hausa filani ce ko?" it ace, "Eh, Hausa fillo ce amma Karin maganganun suna da wuyar fahimta ni dai dorani a hanya yadda zan gane". Yace, "Wace unguwar zaki sai in gano hanyar da zan doraki". Ta watsa masa harara tace, "Yau dai na lura raha kake ji, yanzu dai mu aje rahar nan sai gobe ka tashi ka tafi ka taya kanwata kwana, ka san halın cıwənta sai ka na kusa shi ma harararta ya yi ya na dan murnushi yace, "Ni dai ki ke kora ko? Vallubi zan rama, ki bari ki shiga gona ta sai na. hoblala bayacki" Ta saki dariya tace, 116 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Lah, yaushe ka fara shuka? Ni me ma zai kaini gonarka balle ka ce in taya ka noma. Ni dai na sallame ka don Allah ka tafi dare fa ya yi?" Yace, "Au har korata ki ke yi kin kosa in bar miki dakin in tafi? To wallahi babu inda zan je sai an yi mini abin da nake so, don nima ina da hakkina a gurinki kuma ina da muradin in amshe his kafin in kwanta, yanzu sallame ni kawai sai in tafi". Ta girgiza kai tana dan murmushi ta ce, "Kai! Abokin rayuwa ka cika rigima, wai kai baka girma ne? "Ya kanne ido daya yana dubanta yace, "Girma? Da yake ma har yau bani da siriki ba a fara dukawa ana gaise ni ba ana ce min baba an kwana lafiya ki bari idan aka fara min irin wannan gaisuwar sai in san na girma in barwa yara, amma yanzu da saura na, tunda ma ni nan kokari nake in cikasa biyu kafin nan da badI, kinga ko ai sai gwarzó ne zai aje mata hudu". Ta zumbura baki tana harararshi ta ce, "In ka so ma gobe a daura zaka fi birgewa sai a san kai gwarzo ne kam da biyu ka karo biyu rana daya". Ya ci gaba da zolayarta "Au Allah kun yarda a daura gobe, ba zaku tayar min da yaki a gida ba?" tana son tayi dariya sai dai ta kirne ta share shi, ya leka fuskarta ya ce, "Au har kin soma fushi tun yanzu? Lalai yarinya kina da aiki ni dai 'lame ni ba ruwana fushinki".bata Ankara ba sai gani ta yi 'ya soma rage kayan jikinsa, yana gamawe ya wuce 7ין WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria dakin baccinta yana cewa "ina jiranki, gara ma ki zo ki kwantar da wannan rigimamman dan naki, karbi kin shagwaba shi yaro ba ya barin mutane su yi baccin kirki balle wata harkar arziki, Dukku ma zan maida shi gurin matansa ni ma ya barni da nawa matan. Ta mike safe da Baffan a kafadarta ta bi bayansa tana cewa, "In ka kaishi Dukku ai ka kai shi kusa ka kai shi Yola ko Jalingo ne, ko can Manbila tunda yana da wata matar a Manbila". Bai kulata ba ya haye gadonta ya latse fitila mai haske ya kunna mai duhuwar kala. Ta je ta kwantar da Baffa a gadonsa sannan ta isa gareshi tunda babu yadda ta iya dolenta ta amshi tayinsa. Saida ya yi wanka a nan dakinta sannna suka yi sallama ya tafi dakin Suwaiba, wadda har ta fidda ran bukarta ba zata biya ba ta rufe kofarta, amma sam ta kasa yin bacci tana dan kwance ne tana sakawa da warwara akan ya zata yi in dan ban kwana a dakinta yau ba, shike nan cikar burinta ya wargaje?. Ta yi zurfi a duniyar tunai ne ta ji alamun ana dan bubbuga kofarta, sai ta kasa kunne sosai sannan ta tabbatar lallai kofarta ake bugawa, ta yi saurin tashi ta je ta leka ta window ta ga Mujccb ne tsaye wata irin wawuyar ajiyar zuciya ta saukar duk da bata da tabbacin ko kwanan ya zo yi, amma ta sha alwashin ko ma me ya kawo shi to za ta yaudareshi har sai ya sadu da ita don dai ta samı ta 118 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaría kammala aikin boka a yau dinnan kamar yadda ya umurceta da aikatawa. Ta bude masa kofar ya shigo ta maida kofar ta rufe sannan ta bi bayansa. Ganin ya zarce kai tsaye dakin baccinta sai dadi ya lullubeta lallai yau hakanta zai cimma ruwa. Bayinta ya shiga ya dauro alwala ya fito, ya isketa zaune a gefen gado ta zuba uban tagumi, ya dan dubeta ya ce, "Meye kuma na tagumi tunda gani na zo taya ki kwana ko in tafine tunda na ga kin sami sauki?" ta girgiza kai sannan ta ce, "Та amince ka taya ni kwanan ne?" ya warware dardumar Sallah sannan ya amsa mata, "Da bata amince ba ai da baki ganni ba, don ba zan tauye hakkinta ba". Shiru tayi a ran nata tace "Tauye hakki ko? Yánzu kuwa za ka fara tauye hakkinta, ka bar wani ikirari ka dau bari ka shigo tarkona zaka san shayi daga ruwa aka samo shi. Amma a fili sai tayi 'yar ajiyar zuciya tace, "Nima ba zan so a tauye hakkinta ba. Bai sake ce mata komai ba, ya tada kabbara Sallar nafila. Kwanciya ta yi lamo tana kallonsa har ya idar da sallolnsa, yayi dogayen addu'o'l, ya shafa. Bacci na son daukar ta amma tana gaddamewa idanunta yiwuwar hakan, don in ta bari bacci ya sace ta to ta yi asarar nasarar ta ta wannan ranar, nan take dabara "ta zo mata sai ta fara mirgine daga farkon gado zuwa karshen gado, alamu ne da ta yi masa 119 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria nuni da ciwonta ya motsa, dama tallen zani ne kadai daure a jikinta, sai ta tattara shii ta yaye daga cinyarta tana fidda nishi a ħankali. Mujecb ya taso ya za bakin gadon ya zau yana tambayarta, "Mene ne kuma? Ciwan de? t gyada masa kai tare da miko masa hannunta, ya kai nasa hannun ya riko hata lhannun tare da yi mata sannu cikin tausayawa sannan yà ce, "In kina ganin ciwon nan ya matsa mikf sosai ki tashi kawai mu je asibiti, don ni ina tsoron tashin ciwo da daddare in ji Hausawa sukace ko bai yi kisa ba zai hana bacci". Ta kankame cin cinyoyinsa da ta mirgina ta yi filo da su tace, "Mu bari zuwa har da safe in sha Allahu zai lafa mini. Ka gyara kwaciyarka idan nå ji ni kwance a jikinka zan dan sami sa'idar ciwon". Ya murmusa yana kada kai cike da mamakinta ya ce, "Kai Suwaiba wannan laulayi naki yana bani mamaki, kina son ki yi wa kanki sabo da abinda ba na ki ba ne ke kadai, kin san dai ni na ku ne ku biyu, ba zai yiwu kama in mallaka miki kaina ke daya ba". Ya mike ya sauya kayan jikinsa zuwa na bacci, ya zo ya kwanta ta mirgina a hankali ta fora kanta bisa kirjinsa ta ja bargo ta rufe su, ya soma bacci sama-sama ya ji ta ta soma wasa da gashin. krjinsa, wanda yin hakan ta san yana haddasa masa mo:sawar sha'awarsa, ya yi saurin dakatar da ita da nasa henan domin ba shi da jimirin jure i 120 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria wadannan wasannin kasancewarsa lafiyayyen namiji. Hakan bai sa ta yale shi ba har sai da ya magantu, "Wai dama abinda ke ranki ke nan ki ka matsu in zo in taya ki kwana kawai don ki hana ni bacci?" magarsa ta soki zuciyarta wato ma jarababba ya dauke ta, shi ma ya san ba halinta ba ne zubar da aji ta nemi namiji ko shi ya zo da bukatarsa sai ta ga dama, yanzu ma don tana da kudirin da take son cimma ne da bata neme shi ba amma zata bi shi har ta sami biyan bukatarta. "Ni fa in dai kina son in hada jiki da ke ki tashi kije ki yi wanka, kin san ka'idata bana kwanciya da mace sai ta yi wanka, don na san baki yi ba". Wani tsami da wari ne ya ji yana tashi a jikintya wanda bai taba jin irinsa a tare da ita ba kuma ba komai ya kawo hakan ba sai janabar boka da gauraya da jikinta, wanda kila shi-kanshi bokan bai san iya adadin kwanankin da ya dauka bai yi wanka ba, ita kanta ta san ba karamar juriyar hada jiki ta yi da shi ba. sannan kuma ta karashe wunin ba tare da ta yi warka ba ai dole aji tsami da wari a jikinta, kazantar kam ta yi yawa duk dalilin cimma mummunar manufa. Ta mike ta shiga bayin nata tare da tararradin ya za ayi ta yi wanka tunda boka yace kada ta kuskura ta, wanke janabarsa har sai ta gauraya ta da ta mijinta in dai tana son biyan bukat. Hoda ta rurare ta dauka ta goggoga hodar a 121 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria hammatarta wadda ke cike cinkus da gashi kamar gonar shinkafe sam Cama ia bata aski, sannan ta bulbula turare duk don ta ragewa kanta warin da ita kanta ta san tana yi, to ya zata yi tunda boka yace bata wanka sai an kwana in cai tana son biyan bukatara. (sason Allah ne dai an riga an tafka sai dai Allab ya shiryi masu hali irin na Suwaiba da Hajiarta ta sirikarta). Tuk da wankan hoda da turaren da Suwaiba a yi b. lana ijeebu jin warin jikinta ba, ganin ta hana shi bac i da tsokane-tsokanen ta na tado masa sha'aw yasa babu yadda zai yi ya biya mata bukatar ta,. Shi kansi yau ya sha mamakin kansa na yadda ya ji sam ya kasa saurarawa Suwaiba don ya ji ta fiye da kullum sai ya rayawa ransa lallai wani maganin mata ta je ta sha don ta gigita shi kuma ya gigitan ita kanta yana jin tsumuwar maganin, a jikinta ne yasa ta kasa juriyan har sai gobe ta amshi girkinta yasa ta yi karyar ciwo. Lallai zai gargadeta kada ta kara shan wani magani domin sa baya so. Ya tashi ya je ya yi wanka ya dawo ya yi I wanciyarsa, sai a lokacin ne ta tashi ta dauki agan da boki ya bata ta je bayi tı yi fitsarin da ya mata m 2t2 0 ta vi tsar'i mma sa ta ji tsron in 'sarkin tunda ya ce mata babu taba ruwa har sai ashe garı. Haka nan ta dauki naman nan ta tura af1 gabanta sannan ta maida wandonta ta sa ta dawo ta kwanta. 2 1) WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Tun da ya fita sallar subahi bai dawo dakin Suwaiba ba fakinsa ya wuce a dalilin bashin bacci da ke idanunsa tunda ko baccin awa biyu cikakku bai samu ya yi a dakin Suwaiban ba. Ita kuma sai wajen takwas sauta na safe ta tashi, sai a lokacin ne ta yi wankan isarkin đa ke kanta tun jiya sanhan ta zo ta yi ramakon Salfolin da ta yi sakacinsu da gangan tun daga azahar din jiya har zuwa subahin yau ba kunya har tana iya daga hannu ta na rokon Allah wai Ya yafe mata rashin yin Sallah akan lokacinta da laifin da ta yi masa na fasikanci da boka (kunji fa jama'a shi kuma mijita da da sauran laifukan da ta riga ta nada gammo za ta yi dakonsa na mallakar miji a wulakanta 'yar uwar zama yaushe za ta roki gafararsu? Ko kuma sai an je kiyama? Dadin abin ma bayan duniya akwai kiyama wata shari'ar tafi karfin duniya sai an je gaban Allah. Allah ka tsare mu fi karfin zuciyarmu amecn). Ta shiga kicin ta shirya lafiyayyen farfesu da wannan naman, ita ce har da yi wa miji kunun gyada ta san yana so, alhalin sam bata damu da yi masa abin da ya ke so ba sai in ita ce ke so, idan ya ci shi ke nan in bai ci ba babu ruwanta ta san zai je gurin Munceba ya ci. Ta yi shirinta tsaf kamar ba ita bace ta yi wa kanta karyar ciwo. Ta debi kayan bisa tire ta tafi 1 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria dakinsa a falo ta ije tiren don ta ji alamun zubar ruwa a bayinsa ta san wanka yake yi. Yana fitowa ya ganta zaune a falonsa ya dut ta suka wa juna murmushi ya dan "hareta ya ce, "wa Suwaiba ke wace irin mai kunnen kashi ce?" 1 1 dan kashe ido ya ce, "Me kuma na yi baban Bafía, ni dai sarkin laifi ce a gurinka". Ya ci gaba da goge jikinsa da tawul yana Magana, "Wai sau nawa zan ce miki ki daina sa min tarkacen inagungunan ku na mata idan zan kwanta da ke amma ba kya ji abin naki ma na ga ya dada shahara ki na neman ki zautar da ni". Ta yi wata 'ya dariyar mugunta ta cc, "Yanzu don Allah mene ne laifina don jiyar da kai dadi, koko ka fi son ka jinni tamkar an dafa kaza da ruwa ba magi ba gishiri? Ai dai ba ni kadai nake sha ba ita ma tana sha wa ma ya san irin wanda take sha", ya daga mata hannu, "Ya isa! Bar ambaycki zancen wata ba, in ma tana sha ni ban ta ji ko gani ba, yadda na santa haka take ba ke ba ynu a ji dai-dai gobe kuma a ji akasin haka". kalamnsa ya tinzirata. A tinzira tacе, "Amma in tana sha ai ba bari za ta yi ka sani ba, nima yanzu ai baka ganni na sha komai ba korafi ne dai kawai, kuma mace mairon ciki ai ance kara 'imu take yi, sai ka zargi cikin jiki na". yace, "kunsai dai na taba ganin kulli kullin magurguna a dakinki ranar da zaki haifi Baffa kuma da kanki kika ce mini magungunen mata ne, ko ma dai na WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria meye kc kika faďda da bakinki ko ba a yi haka ba?" ta san anyi hakans shi yasa tayi shiru. Ya ci gaba da cewa, "Sabo da haka daga yau ki daina banso, sabo da irin wadannan magunguna sai su halakar da ke nima ki halakar da ni, tunda bana so ki hakura da su ki watsar da su in ace akwai ababen sha masu kara ni'ima irin su madara zuma, nono, ya'yan itace da sauransu kuma duk baki rasa su ba, in ma babu а gaya min zan siya". Ta mike tana cewa "Ai shike nan tunda baka so na daina,",", amma a zuciyarta sai ta cе "halaka kuma ai sai dai kada a kuma, yanzu kam ka riga ka zo hannu bari ma ka ci naman nan shine cikon aikin da zan kaddamar akan mallakarka" Ta zubo farfesun a filet ta mika masa ta се, "Ga farfcsu haka nan nayi sha'awarsa nayi, ga kuma mutuminka kunun gyada", bai amshi filet din ba sai ya ce, "Kin

Chapter 7 of 12