Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
11 / 12
Gagarar da al'amarinta da ya ke yi ko meye aibunta a rayuwatsa? Oho!ert Ya matso ya amshi kofin shayin yace, bara in hutasshe ki mama.ta mika masa yassomalba muneeba tin. Haushin ya kama Goggo ganintyanda bai ji kunyarta ba, ta mike tana cewa zoka kami gida sai ka dawo Allah ya kara sauki ya karasarba munceba tin duk da bata sakar masa fuskaba tamkar yana bata madaci haka take hadiyar tin. sY Ya fita ya kai Goggo gida ko'šhiga bai yirba ya juyo kan motar ya koma asibitinA hanyarya tsaya za saya musu duk wanni.abu nnigokatandon sai da ya cika mazauain bayan motirsa dá' sayayya sannan ya koma asibitin. PAS IC SSIA Tun daga ranar Mujceb ke sintirin zuwa asibiti yana kashe kudadde wajen saye-saye har aka sallameta suka koma gida. Wani abin mamaki tun da suka koma gida sai al'amarin su gnaasibiti ya sauya ya koma 'yar gidan jiya sam ya daina shiga harkarta, sai dai abu daya dake damunsa idanıiya fito offis shine kewarta, duk iya kokarin san a hana faruwar hakan abin ya gagare shi. NUR EWOOL A tunaninsa rashin Suwaiba ne ya sa yakeе kawar Muneeban, tur da jego ta ke yi kuma aiki aka yi mata sannan ya rasa inda zai kaisbukatarsa, ga 177 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria lafiyayya yar mata yana da ita amma wani abu da bai san ko mene ne ba yayi musu shamaki da juna. Yau kam tunda ya shiga ofishinsa kewar matarsa ke damunsa, a dadafe ya iya kaiwa azahar suna dar da sallah ya shiga motarsa ya nufo gida, daga waje ya tsaya don har mai gadinsa ya bude masa get sai yace ba shiga zaiyi ba, ya dauki wayarsa ya kira lambar muneeba, tayi matukar mama kin ganin kiransa, ta katse tunaninta ta hanyar amsa wayar tasa. Ya ce, me kike yi yanzu? "Tace ina gida ne" ya ce, eh na san kina gida, so nake in san abin da kuke yi". Mamaki ya kamata na wadannan tambayoyi tace, na fito wanka ne ina shafa mai" Yace, " Good,to ki sa kaya ki fito waje ki same ni zamu je wani waje "Ta ce to, tare da kashe wayar. Wata lafiyayyiyar riga mai dan karenn kyau ta saka, tayi fakin din gashinta ta daura dan kwalin rigar ta sa hijabin rigar ta dauki wayarta ta fito. ، Goggo na ganinta tace, " ina kuma za ki je ke da baki da lafiya, ta ce nima yanzu baban Baffa yace in fito yana waje ban san inda zamu je ba, Goggo ta Gyada kai tace, yayi dai dai sai kun dawo", tana wucewa suwaiba ta fito take cewa Goggo" ba wani baban Baffa karya ne, tana dai son fita ne bari in gani in da gaskene". Isarta waje yayi daidai da juyawar kan motarsa suka tafi, ta tambayoyi mai gadi waye 178 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria a wancan. Yace Alhaji ne ya dauki Hajiya ". Tabbas shi dinne don motarsa ce. Tayi sauri ta fari wani mai mashin tace ya bi bayansu ya ga inda suka je ya dawo ya gaya mata zata biya shi. Mai mashin ya ji aiki mai tsoka, yayi saurin bin bayansu. Munecba tana shiga motar, kawai ta ga a juya kan motar ya hau titi ya soma tafiya. Ta dube shi kadan tace," lafiya baban Baffa? Me ke faruwane? ina zamu je? Ba tare da ya dube ba, hankalinsa na kan titin da yake yace, Duka wadannan tambayoyin na mene ne? kin san đai ba zan siyar da kanki bane. To sa ranki a inuwa kuma ki zuba min ido kawai kada ki kara tambayata komai, hakan ta yi taja bakinta ta tsuke ta zubawa sarautar Allah ido. Mujceb bai dire su ko ina ba sai a wani kebantaccen hotel. Abin ya bata mamaki an ma ba ta ce masu uffan ba. Ya barta a motar ya fita, ya dauki mintoci sannan ya dawo Ya bude mata murfin kofar ya ce ta fito ta biyoshi. Tamkar rakumi da akala haka tayi ta binsa har ya bude dakin tabbacin cewa kama dakin ya yi. A tsakiyar dakin kawai ta tsaya kikam tana karewa dakin kallo, tare da kallon Mujeeb da ke zaune bisa gadon dakin yana zuba ruwa a kofi. Shi ma ya sauke idanunsa akan nata yace, ki zauna mana, kin tsaya cikin tsoro kamar wacda na sato. Ba zata iya yi masa musu ba shi yasa ta zauna a 179 WATA KUSAN 2 Ramatu Hassan Zaria kujerar dakin yayi mata umuminh ta dawo kusa da shi akan gado. Ita dai bin umuninsa kawai take yi, amma zuciyarta cike take da wasiwasi musabban kawo ta hotel da Mujeeb yayi. Rabon da mujeeb ya taba ko da hannunta ne har ta manta, balle ya taba jikinta ko aje ga yin wani abu, sai gashi ya rungumeta tsan tsan a jikinsa yana sauke ajiyar zuciyarsa tare da lallashinta, ki yi hakuri akan abubuwa mara sa dadi waddanda sukai ta faruwa sam yanzu ba kya gaba na, ba kya birgeni irin da, bana ganin farinciki a cikin gidana, kullum bakin ki na ke gani, ki taya ni addu'a Allah ya ye mun wannan matsalan in dai na shiga hakkin ki. Idanun Muneeba suka kawo ruwa sabo da tausayin mijinta, ga dai bikin zuwa amma babu zani daurawa, magana ce a bakinta to amma babu halin furtawa don ba zai ji a bakinta ba wai kanwar sarki da kwarkwata ta langabar da kanta a kafadarsa ta ce, ni bana rikonka a zuciyata tsakani na da kai addu'a ce, kaima ka dage da addu'a ka hana idanunka barci In Shaa Allah komai zai daidaita. Bata yi musu kan bukątu varsa ba akanta, ta bashi hadin kai yadda ya kamata tunda ita ma kanta cike take da begen kasancewarta da mijinta nata, a dalilin lafiyayya ce ita, babu luwa abin da zai hanata mararin mijin nata, kuma a hakika ta sami gamsuwarsa da bata taba ji a ray uwarta aurensu sai 180 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria dai matsalar nan ta kunno kai a tsakanin su, shi yasa muneeba ta yi Masa tarba mai kyau. Yadda take jin nishadi ma sai ta ji tamkar su yi ta zamansu a hotel din kada su koma gidansu, su sake haduwa da matsalar da suka baro a gidan nasu. Mujeeb za ma ya yi shiru a gefen gado, bayan kammaluwar komai ya shiga zurfin tunanin akan wannan al'amari kwata kwata idan ya sadu da muneeba ba ya jin dadinta irin da wanda ya san a da tafi suwaiba nesa ba kusa ba, amma yanzu an wayi gari suwaiba tafi ta, in ma ya sami gamsuwa ita ma ba wata azo a gani ba. To yau ma hakan ce ta faru suwaiban ya dinga rayawa a ransa sannan ya sami biyan bukatarsa. Wannan abu yana daure masa kai, shi yasa ma yanzu bai damu da kusantar inda muneeban take ba ya fi na cewa Suwaiba sabo da canjin da ya samu. Ya mike ya shiga bayin dakin yayi wanka, yana fitowa yace tayi wanķa su tafi, jikinta ba kuzari ta tashi ta shigo bayin mamaki take yi na yadda farat daya ya sauya mata ya shiga cikin damuwa, zuciyarta na ta hararo mata abubuwa da dama dake damunsa amma a canke-cankenta ta fi cafko cewa yanzu baya jin dadinta baya gamsuwa da ita, saboda ta gano hakan ne a yanayinsa, idan ya gamsu da ita tana ganewa a fuskarsa da irin kalaman da zai yi ta mata na yabawa irin baiwar da 181 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Allah ye mata na mace mai ni'ima, sabanin yanzu da bata sami yabon komai ba, sai ma kunci da ta ga zuciyarsa ta shiga, sai dai abu daya kawai ta lura ya rage karfin sha'awar da ke damunsa a dalilin ba shi da madafa a yanzu kasancewar suwaiba tana jego, in bayan haka da ba zai neme ta ba, wato rashin uwa ne yayi uwar daki. Suwaiba kuwa bayan tafiyar mai mashin gida ta shiga ta shaidawa Goggo abin da ya faru da bin bayansu da tas mai mashin yayi yaga inda za su, suna kan tattaunawa ne maigadinsu ya leko yace musu mai mashin ya dawo. Ta fito ta sami mai mashin ya bayyana mata cewa hotel suka je, bai baro gurun ba ma sai da yaga sun shiga ciki kuma har tahowarsa baiga sun fito ba, a takkaice ma yana jin daki suka kama don ya ga shi Alhajin ya shiga ya fito da makullin daki a hannunsa, sannan ta fito ta bishi cikin hotel din. Taja dogon tsaki zuciyarta cike da tsananin kishi ta mikawa mai mashin din naira dubu daya, yayi godiya ya tafi ita kuma ta dawo cikin gida ta labartawa Goggo abin da me mashin ya je ya gano mata. Goggo ta jinjina kai tace, 'iye' lallai yaron nan to uban me ya dauketa zasu je su yi a hotel, sai kace wata karuwa, suwaiba tace, 'Ai wallahi zai dawo ya sameni sai dai ayi wadda za'a yi, zai gaya minme hakan ke nufi. Goggo ta tare ta, Akul kika 182 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria tada jijiyar wuya akan wanann abun, ina ganin al'amarinmu ya fara yin Sanyi, ina ga karyar zuwa asibit zakiyi masa gobe kije kiga boka bamu ga ta zama ba tun kafin al'amura su jagule mana. Suwaiba tace, sai dai mu je da ke don ni bazan iya kai kaina gurin ba, tace, ba zai yiwu ba mu je tare ba sabo da zan sa ido na sosai a al'amuran gidan nan, zan kira Hajiyarki inyi mata bayani sai ku hadu a can kuje tare. Da su ka dawo a waje ya aje muneeba inda ya dauketa ya juya ya koma offis, ta sha habaici gurin suwaiba har Goggo ma sai da tayi nata, abin da ya ba Munceba mamaki yadda akayi har su kasan hostel sukaje da abinda sukayi amma sai ta share lamari taji dadi a ranta tunda har abin ya basu haushi. Washe gari Suwaiba ta sami nasarar yaudarar Mujeeb cewa zata ganin likita asibiti ta tafi da karfin guiwarta suka yi mahada da Hajiyarta suka wuce kauyen da boka yake. Ya hada masu surkulle iri-iri tare da gargadin aiwatar da komai yadda ya tsara musu, sannan da gargadi mai karfi akan kada ta yarda kunnin mijinta yaji sirrin dake tsakaninta dashi,in kuwa ta bari yaji duk abinda ya biyo baya kada tayi kuka dashi tayi kuka da kanta. Ai kuwa tun daga wannan zuwa da sukayi, biyo bayan ayyukan da suka zartas sai komai ya 183 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria cabe tsakanin Muneeba da Mujeeb har bacin abin yafi nada muni ita kam a lokacin babu abinda da ta sa agabanta sai tsananin addu'ah. Cikin wannan halin ne Munceba taje Dukku halartar wani biki da suke dashi kwananta biyu ranar Lahadi tana shirin dawowa Gombe da misalin Karfe biyu na rana Mujeeb ya kira wayarta yake shaida mata wai ta zauna a Dukku kada ta dawo Gombe har sai yazo. Cikin mamaki ta tambayeshi wani abu ya faru ne, ko nayi maka wani abu ne ban sani ba? Ya ce babu abinda kikayi mini haka nan ne bana son ki dawo nafi son zamanki anan Dukkun yana fadin haka ya kashe wayar ta dade zauna tana jinjina wannan al'amarin har innarsu ta shigo ta sameta tayi zugum tana tunani. Ta tsaya a kanta tana mata kallon mamaki ta ce, ke lafiya kike zaune cikin tunani ke da zaki tafi shine kika zo kika zauna so kike dare yayi maki ke da ba kyason tukin dare. Damuwa ce karara a fuskarta ta bayyanawa innarsu abinda Mujeeb ya ce, itama abin mamaki ya bata, sai bata yi kasa a guiwa ba ta sa a ka kira babansu Muneeba ta shaida masa abin dake faruwa shima al'amarin ya girgiza shi har yake tunanin ko wani abu Muneeba tayi masa, tayi wa babanta rantsuwar batayi masa komai ba, itama ta tambayeshi laifin da tayi masa yace batayi masa komai ba. A 184 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria D tada jijiyar wuya akan wanann abun', ina ganin al'amarinmu ya fara yin Sanyi, ina ga karyar zuwa asibit zakiyi masa gobe kije kiga boka bamu ga ta zama ba tun kafin al'amura su jagule mana. Suwaiba tace, sai dai mu je da ke don ni bazan iya kai kaina gurin ba, tace, ba zai yiwu ba mu je tare ba sabo da zan sa ido na sosai a al'amuran gidan nan, zan kira Hajiyarki inyi mata bayani sai ku hadu a can kuje tare. Da su ka dawo a waje ya aje muneeba inda ya dauketa ya juya ya koma offis, ta sha habaici gurin suwaiba har Goggo ma sai da tayi nata, abin da ya ba Munceba mamaki yadda akayi har su kasan hostel sukaje da abinda sukayi amma sai ta share lamari taji dadi a ranta tunda har abin ya basu haushi. Washe gari Suwaiba ta sami nasarar yaudarar Mujeeb cewa zata ganin likita asibiti ta tafi da karfin guiwarta suka yi mahada da Hajiyarta suka wuce kauyen da boka yake. Ya hada masu surkulle iri-iri tare da gargadin aiwatar da komai yadda ya tsara musu, sannan da gargadi mai karfi akan kada ta yarda kunnin mijinta yaji sirrin dake tsakaninta dashi,in kuwa ta bari yaji duk abinda ya biyo baya kada tayi kuka dashi tayi kuka da kanta. Ai kuwa tun daga wannan zuwa da sukayi, biyo bayan ayyukan da suka zartas sai komai ya 183 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria cabe tsakanin Muneeba da Mujecb har bacin abin yafi nada muni ita kam a lokacin babu abinda da ta sa agabanta sai tsananin addu'ah. Cikin wannan halin ne Munceba tajc Dukku halartar wani biki da suke dashi kwananta biyu ranar Lahadi tana shirin dawowa Gombe da misalin Karfe biyu na rana Mujeeb ya kira wayarta yake shaida mata wai ta zauna a Dukku kada ta dawo. Gombe har sai yazo. Cikin mamaki ta tambayeshi wani abu ya faru ne, ko nayi maka wani abu ne ban sani ba? Ya ce babu abinda kikayi mini haka nan ne bana son ki dawo nafi son zamanki anan Dukkun yana fadin haka ya kashe wayar ta dade zauna tana jinjina wannan al'amarin har innarsu ta shigo ta sameta tayi zugum tana tunani. Ta tsaya a kanta tana mata kallon mamaki ta ce, ke lafiya kike zaune cikin tunani ke da zaki tafi shine kika zo kika zauna so kike dare yayi maki ke da ba kyason tukin dare. Damuwa ce karara a fuskarta ta bayyanawa innarsu abinda Mujeeb ya ce, itama abin mamaki ya bata, sai bata yi kasa a guiwa ba ta sa a ka kira babansu Muneeba ta shaida masa abin dake faruwa shima al'amarin ya girgiza shi har yake tunanin ko wani abu Muneeba tayi masa, tayi wa babanta rantsuwar. batayi masa komai ba, itama ta tambayeshi laifin da tayi masa yace batayi masa komai ba. C 184 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Ya je ya sami 'yan uwansa Baffa Adamu da Baffa Audu ya gaya masu abinda Muneeba ta shaida masa. Baffa Adamu ya lalubo wayarsa a aljihu ya kira wayar Mujeeb din, bayan sun gaisa ne yake tambayarsa meye gaskiyar abinda Muneeba ta gaya musu. Babu kunya ko fargaba wani abu sai ya ce "Eh haka ne nace ta zauna a nan Dukku Baffa ya ce "Ko meye dalilinka na cewa haka? Ya ce, Babu wani dalili ya cc "wani abu tayi maka" Mujeeb ya ce "Ba tayi mani komai ba" ni dai nafison ta zauna anan in yaso idan na warware matsalolin dake gabana zanzo in dawo da ita? Baffa ya sake tambayarsa "Ina kake nufin ta zauna kenan? Ya ce "Na bata zabi duk inda take son ta zauna ko nan gidansu ko gidan Goggo dakinta ai yana nan "Baffa ya harzuka ya ce, Abin da duk ka yi yayi maka daidai tunda da sanin mahafiyarka kake zartas da komai to mun gode zamu rike yarmu kamar yadda ka bukata zata zauna a gidan iyayenta, amma ka sani idan muka gaji da jiran zuwanka baka zo ba, to zamu kaika gaban alkali don ka bata takardar ta tunda mu dai bamu isa mu tilastaka zama da ita ba zamu tilastaka bata takardarta, tunda kai da uwarkа bakusan muhimmancin zumunci ba, duk al'amuran dake faruwa agidanka muna sane da irin cin kashin da akc mata, hakan bai sa kaga irin hakurin da take da ku ba har sai ka rabata da gidanka, to ka je duniya ce tafi bagaruwa jima, ka da wadda 185 zauna WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria kake so zabin mahafiyarka indai yar Hajiya Harira ce wallahi ba ba ki zan yi maka ba sai ta maida kai abin kwantance kamar yadda uwarta ta maida ubanta gashi nan har yabar duniya ana kwatancensa a matsayin mijin ta ce mijin da bai da iko da gidansa baida iko da 'ya'yansa balle matarsa data rabashi da kowa nasa, to kai ma yana zuwa kanka muna nan zamu ji labara har ita uwar taka in bata yi sa'a ba sai sun raba ku zata ga sharrinsu. Suna gama waya da Mujeeb ya kira wayar Goggo ya gaya mata abin da mujeeb ya yi. Kada bakin da zata yi sai cewa tayi tunda yace ta zauna anan sai ta zauna, mai daki ai shi ya san inda ke masa yoyo, nidai bazan matsa masa ya dawo da ita ba tunda ba sakinta yayi ba, kuma ai kila akwai dalilinsa da yasa ya ce ta zauna anan" cikin jin zafi Baffa y ace Abin da zaki iya cewa kenan ko? To shi kenan mun barku da Allah ke dashi idan kunyi hakan ne don musgunawa rayuwar yarinyar nan wallahi Allah nasa ne kuma sai ya saka mata inma, anan duniya ko sai anje Lahira, amma ki sani Hajiya Harira da 'yarta da kika rika hannu bibbiyu to zaki ga sharrinsu ki rike wannan a ranki. Ya kashe wayarsa ya dubi 'yan uwansa ya ce kun dai ji yadda mukayi dasu ko? To mu kyale su mu zuba musu ido Muneeba zata zauna a gida kamar ya ce kafin mu ga abin da allah zai yi amma ina sonmu taya yaron nan da addu'a don kuwa 186 S WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria al'amarinsa yana bukatar addu'ah an riga an farrakasu da yarinyar nan kuma sakacin duk na shashashar uwarsa ne, amma zata gane kuskurenta ranar da zasu raba ta da dan nata su sa ya koreta a gidansa tamkar yadda ya yi wa matarsa. Baffa Adamu da kansa ya tasa ta a motarta sukaje Gombe gidansu yace ta bude dakinta ta dauki duk wani da ta da ta san zata bukata tana gamawa yace ta rufe dakin ta taho da mukullinta. A gaban Suwaiba ya gaggayawa Goggo maganganu masu tsayawa a rai ko ruwan gidan bai sha ba suka juya suka koma Dukku kwananta bakwai a Dukku su ka yi mata umurninta ta koma gidan Mama Amina ta zauna don karashe karatunta wanda watanni biyu ne kacal ya rage mata ta gama. Zamanta gidan Mama Amina ya kwantar mata da hankali sosai saboda Maman da 'ya'yanta suna debe mata kewa basa barin ta cikin tunani ko damuwa, ga mahaifinsu ya zama tamkar shi ya kawo ta duniya saboda kulawar da yake nunawa akan al'amarinta sarnan yayi tsaye don ganin al'amura sun daidaita tsakaninta da Mujeeb ta koma dakinta amma abin ya faskara saboda irin kalaman da Mujeeb din yake gaya masa ne ya gano al'amarin nasu na bukatar addu'a shi yasa bai matsa masa ba ya Kyale sai dai yasa Malamai nayiwa al'amarin nasu add'ah shima da kansa yana tayasu addu'ar gidan ya koma daga Goggo sai Suwaiba da 187 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria 'ya'yanta. A halin yanzu ma goggo bata son zaman Dukku in dai ba wani sha'anin ake yi ba, kuma tana zuwa bata dadewa da an gama sha'anin zata tattaro ta dawo Gombe. Baffa kuwa tuniya manta da wata Muneeba a dalilin kulaficinta da yake yi ne Goggo ta amso rubutu akayi ta dirkawa yaron har sai day a manta da ita tun tana gidan ya daina yadda da ita sai mamansa sai Goggo da Babbansa. **** **** **** Ranar da Muneeba ta kamala jarabawar ta gama karatunta na Digiri a ranar sam bata cikin kuzari naimakon ta kasance cikin farin ciki duk sai tana jinta tamkar mara lafiya. Tana dawowa gida ta shige daki tayi kwanciyarta dama gashi tana fashin sallah, sai kwanciyar tata tayi tsayi Mama Amina ta shigo dakin ta sameta da waya a hannunta tana cewa'wai Muneeba yau lafiyarki kalau kuwa" Ta tashi zaune ta na cewa lafiyata kalau hakan nan dai nake jin kasala da faduwar gaba bansan dalili ba, ta.cc Allah ya kyauta amma fa ki kara dagewa da addu'a. me ya sami wayarki Innarki na ta kira tana ringim ba ki daga ba shine ta kirani taji ko lafiya. Muneeba ta luluba kasan filo ta dauko wayar tana cewa, "Na manta a (silent) take tunda z ru biga yin jarabawa ban cire (Silent) din ba shi 138 量 8 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria yasa banji ba bari in kira ta Mama ta ce "Kya iya kiranta amma rashi ne akayi miki ta kira ta gaya miki sai dai kiyi hakuri ki dauki dangana suma tace min gasu nan har sun iso gomben". Munceba ta dafe kirji cike da jin tsoron wanda za'a ce mata ta rasa Allah ya saba Mujeeb ta rasa ba ko Baffa ko kanwarsa ko kuma.Goggo ce, kai duk ba su bane. A tsorace ta tambayi Mama Amina "Mama waye nawa ya rasu? Ta ce kiyi hakuri Baffanki Karami ne Allah ya yi masa rauwa wai yasha maganin kwari za'asa a kicin din mamansa saboda kyankyasai ta manta ta ajiye shi kuma ya dauka ya sha ya dauka magani ne" Muneeba batasan lokacin da ta kwarma wata irin kara ba tare da sakin salati ta zabura ta mike ai ko taku biyu ba ta yi ba sai ta yanke jiki ta fadi Allah yayi taimako daga gado ta tashi data fadin sai ta fadi bisa gadon. Mama Amina da gudu tayi kanta tana girgiza ta tare da kiran sunanta amma shiru ba amsa hakan ne ya tabbatar mata da Muneeba suma tayi itama salati ta hau yi ta shiga bayin dakin ta debo ruwa su Khausar ma ashe sunji karar Muneeba sai gasu da gudu suka iske Muneeba warwa Mama Amina na shafa mata ruwa tare da tofa mata addu'a. su khausar suka tambayi Mama abinda ke faruwa ta gaya musu suma sun tausayawaMunecba rshin da tayi kasancewar irin tsananin son da takcyiva Baffa 180 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria wanda ko fan cikinta kila da kyar zata yi masa irin wannan so mai tsanani. Ganin ta dawo cikin hayyacinta yasa Mama Amina ta dinga yi mata nasiha da tayi hakuri dama iyakar lokacin yaron kenan a duniya ba zai taba Kara koda dakika ba akan wadda Allah ya kudira masa. Mama Amina ta kira mai gidanta a waya ta shaida masa rasuwa ya ce su tafi can gidan har da Muneeba shima yana nan zuwa don ayi jana'izar dashi. Gidan rasuwar ya cika da jama'ar Dukku maza da mata dakin suwaiban suka shiga tayi kuka har taba uku lada, sam bama ta cikin hayyacinta sai surutu marasa kan gado take yi na yadda aka yi ita da kanta tayi sakacin ajiye abinda ya zamo sanadin mutuwar danta. Sun shiga dakin Goggo sun yi mata gaisuwa sanna suka koma dakin Munceba wanda ana duk ilahirin danginsu da suka zo suke zaune Munecba ta je falon Mujecb inda Gawar Baffa take ta bude shi tana masa kallon karshe ganin yadda maganin ya fatattaka masa baki da lab6ansa ne yasa ta saka kuka har sai da aka riketa aka fita da ita. Kwanan Muneeba uku a dakinta a dalilin umurnin da iyayenta da Baffaninta suka bata na ta zauna ayi kwana uku, sannan ta koma gidan Mama Amina duk safiyar Allah Mueeb yana shigowa dakinta don gaisar da 'yan uwansa dake dakin WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria amma ita dashi har yau babu wanda yaccwa dan uwansa Uffan sai dai in ya shigo zata bi gaisuwar da jama'a ke masa amma batayi masa ita kadai ba tunda sam yaki yarda su hadu, yadda ta lura ma kamar kunyarta yake ji shi ya sa ya ke kaucewa haduwarsu su biyu. Tun bayan rasuwar Baffa sai al'amura suka soma sauyawa tsakanin Goggo da Suwiaba yanayin zamantakewar su ya fara canza salo, Goggo bata da iko akan al'amarin gidan danta yanzu Suwaiba sai ta nuna mata bafa zata takura mata ba ita da gidan Mijinta, sannan Goggon bata da ikon yin sirri da danta sai taji wannan sirri a bakin Suwaiba, Mujeeb din zai gaya mata in wani abu takeso yayi mata to sai ya nemi izini Suwaiba idan ta yarda sannan ayi mata in bata yarda ba to sai dai tayi hakuri ko kuma ta kaskantar da kanta ta roki Suwaiban sannan ayi mata. Abin duniya fa ya damu Goggo yadda ta dauko ruwan dafa kanta gashi kiri-Kiri ruwan na konata kuma babu yac da zatayi ba halin ta gayawa wani sai ayi mata dariya da Allah ya kara ai dama duk wanda yaja ruwa shi ruwa zai yiwa dukan tsiya. Saboda hawan jini da Goggo ke dashi yasa tun Munceba na gidan girkin Goggo daban aka koma ana yi mata, in miyace ma tata ta musamman ake mata, amma sai Suwaiba tą da ta yi, ds Goggon tayi magana sai Suwaiban ta ce, ni fa 191 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria a C gaskiya Goggo ki daina matsa mini da wanne zan ji da hidimar yara ko da ta ubansu koda taki gaskiya kawai ki dinga yin girkinki in dai ba zaki ci me gishiri ba wannan takura ne ace mutum duk lokacin da zaiyi girki sai ya dora tukunya biyu, nifa ba dole bane inyi miki abu in kuma kinga baki iya zama dani ki koma gidanki. Goggo tace, kwarai dole kiyi mini rashin kunya tunda nayi tsayuwar daka na hada aurenki da dana kin sami wuri kin baza shanyarki yadda kike so yanzu nice abin wulakantawa to zai dawo gidan nan da bakinsa zai gaya miki matsayi na idan kin manta ni uwarsa ce da na dau dawainiyar wahalar nakuda na haife shi nayi ta ba shi nono na ina rainonsa cikin kulawa har ya ya shekara biyu na yaye shi, sannan na ci gaba da kula dashi har ya yi girma ya shiga makaranta yayi ilimi daya sami aiki yayi kudın da kike takama dasu ya aureki, shine ni zaki wofintar da wulakanta masa saboda ke butulu ce, na fifitaki akan 'yar kanina na soki fiye da ita sai gashi kin watsa min kasa a ido tun ba'aje ko inaba to shi kenan ki sani akwai ranar Kin dillanci ranar da hajar mai gari zata bata". Suwaiba dariya tayi ta ce to ai Goggo kece baki sani ba ruwa cikin cokali ya isa mai hankaii yin wanka sannan ai ba kowa bane zai iya gane dingishin kwaďo sai mai tsananin hankali da basira kuma

Chapter 11 of 12