Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 12
ya zamo ina wuta su Goggo su sakata cewa wai ta gama mallake Mujeeb tunda har bai iya aiwatar da komai sai itace mai aiwatar masa, baya shawara da kowa a al'amuransa sai da ita to ba ita bace zata haihu, sai ta bari tayi duk abin da taga dama a nata amma wannan ta ja baya taba mai haifuwa fili ta yi yadda take so lokacinta ne ita kuma sai ta jira nata lokacin yazo. Wadfannan maganganun sukansa Muneeba kuka, tunda ita tana yin komai domin Allah ne ba don a sota ko a yabeta ba, amma sai gashi bita da kulli ne ke biyo baya ana zargin ta kuma tasan wani 55 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria abun in bata sa baki ba Mujeeb baya saya cewa yake a bari ta haihu lafiya sai ya saya. Kullum Mujeeb cikin lallashin Muneeba yake yi akan ire-iren maganganun Goggonsa da matarsa, don ma yana takawa Suwaiban birki a daki yake wanketa da soso da sabulu batare da Goggo ta san anyi ba tunda itace ke daure mata kugun yin takama da duk iskancin dataga dama a cikin gidan shi kuma a daki har bara zanar rabuwa da ita ya keyi, a cewarsa don ya saketa ba wata tsiya bane, ita kuma da taji Kalmar sakin sai ta shiga taitayinta don a duniya babu abin da take so irin Mujeeb, balle yanzu da take dauke da cikinsa, ita ta sanma barazana yakeyi b zai taba iya sakinta ba, sai dai wannan barazanar da ya ke yi tasa zata shaidawa Hajiyarta a kansa tunda har yanzun basu mallaki zuciyarsa irin yaddda suke so ba, ta na jin idan ta haihu wani bokan zasu canza in har ba suga canji, ba tunda suna so yaso jaririn da Suwaibar za ta Haifa irin mahaukacin son nan da bai taba yiwa kowa irinsa ba a duniya, shi yasa. duk inda zasu sami asirin wannan soyayyar to za su je su bada kudi komai yawansu ba su da matsalar kudi Mujeeb na sakar masu bakin aljihu daidai gwargwado. 56 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria **** ***** ***** Cikin tsakiyar dare nakuda ta kama Suwaiba, Allah yasa Mujeeb a dakinta yake ihunta ya tashe shi ya farka a gigice ya ganta kwance a Rasa tana birgima tana ihu ya diro daga gadon yana tambayarta menene ta ce "Ciki na da marata da baya na ne suke ciwo zan mutu ka taimakeni kả kaini asibiti wallahi mutuwa zan yi ya zo ya riketa yana cewa "Ki dinga yin Salati ne ba ihu za ki dinga yi ba bari in taso Goggo ina jin haihuwa za ki yi sannu ki yi hakuri yanzun za mu je asibiti." ya mike zai tafi kiran Goggo, ta damko kafarsa ta rungume tana kuka tana cewa "Ni mu tafi asibitin ba za ka fita ka barni ba wayyoo Allah ka zo ka taimakeni" ya dawo ya tsuguna gabanta ya ce ki yi hakuri ki daina ihun nan sunan Allah kawai za ki kira shi ne zai taimakeki sakeni in taso Goggon mu tafi "Da kyar ya banbare kafarsa da ta danka ya fice da sauri ya je ya bugawa Goggo kofa, jikinta na rawa ta tashi ta bude tana tambayarsa abin da ya faru yace Suwaiba ce ba. lafiya ina ganin haihuwa zata yi shine na ce bari in gaya miki za a kaita asibiti. Tace to! Abin ya zo? To Allah ya raba su lafiya bari in je dakin sai ka yi maza ka fito da mota ta wuce dakin Suwaiban shi kuma ya nufi dakin Munceba tana zaune bisa Sallaya tana addu'o'i bayan ta gama nafilar dare ne ta ji ana bugun kofarta gabanta sai đa ya fadi a tsorace ta zo tana 57 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria tambayar "Wa ye? Ya ce nine Munceba bude tana jin muryar mijinta ta yi sauri ta bude kofar tana tambayarsa abin da ke faruwa ya gaya mata Suwaiba ce za ta haihu nan da nan ta soma jero addu'o'i ga 'yar uwar zamanta na Allah ya sauketa lafiya koma daki ta yi ta dauko wayarta dama da dogon hijabi a jikinta ta yi saurin rufo dakinta ta biyo shi zuwa dakin Suwaiban ta iske su da Goggo suna kokarin daukota don a fita da ita zuwa waje cikin mota. Munecba ta ce, Ka fito da motar ne? Ya cе, duk na rude wallahi na manta in fito da ita ga makullin can kan (Side bed) dauka ki fito da motar da dau makullin da sauri ta je ta fito da motar daga inda take ta juyata ta fuskaci hanyar fita sannan ta dawo suka kamata suka kaita bayan mota ta suka kwantar da ita tana ta aikin ihu da kiran Mutuwa Goggo na ta lallashinta da ta ji Mujeeb ya ce ta daina ihu ta dinga Salati sai ta haushi da fada, Don Allah ka kyale yarinyar nan in ma ta yi ihu ba laifi bane saboda haihuwa tamkar zarar rai haka radadin ya yake don dai baka san zafin bane, in ba za ka lallasheta ba to ka kyaleta. Muneeba na kokarin shiga gaban mota su tafi sai Goggo ta ce A'a ba da ke za a ba, wannan sabgar ta manya ce" Muneeba ta yi saurin ba Goggo hanya ta shige motar Mujeeb ya matso kunnenta yace "Yi hakuri bari mu tafi da Goggon 58 S WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ki tayamu addu'ah Allah ya sauketa lafiya, tunda kin tada hankalinki bana ma son ki je wata damuwar za ki karawa kanki" ya shafi kumatunta ya zagaya ya shiga mota suka tafi. Wasa farin girki, ashe ma nakudar somin tabi ne wai maye ya ci jariri domin kuwa da a ka je asibiti lokacin ne ma ta soma asalin nakudar wadda ta kaita har wayewar gari bata haihu ba sai bakar wahala da take sha tunda har ruwan nakudan an sa mata amma ba ta haihuwa ba. Muneeba tana gida hankalinta a tashe duk da cewar suna waye Mujeeb na gaya mata duk halin da ake ciki haihuwarta ta zo gadan-gadan har kan bebin ya fara kunnowa amma sam babu hanyar da zai fito Nosis din sun yi iya kokarinsu don ganin ta haihu da kanta amma abin ya faskara hakan ne ya sa suka yanke shawarar sai dai a yi mata operation (C.S) a cire bebin domin kuwa ya wahala sosai za a iya rasa ransa ko a rasa ran uwar tasa. Hajiya Harira da ta iso da Goggo suna jin maganar za a yi mata aiki sai suka hau kuka Mujeeb sai ya kasance shine mai basu hakuri lokacin da ya je ya sa hannu a yi mata aikin a ofishin likitan. Tuni har an kammala shirye-shirye sun shiga da ita Mujeeb ya lalubo waya sa ya kira Muneeba tana dauka cike da zumudi Tace, "Hala ta haihu?" ya sauke ajiyar zuciyar yace "Bata haihu ba yanzu haka ma (C.S) 59 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria suka ce zasu yi mata nasa hannu har an shiga da ita sai ki taya ta addu'a Munceba ta dafe kirji ta сс C.S ba za ta iya haihuwar bane za su yi mata C.S? Ya ce yaron ya kunno kai amma babu kofar da zai fito sun yi iya kokarinsu abin ya gagara, sunce za'a iya rasa bebin ko ita shi ya sa ya zama dole ayi aikin" Ta ce Innalillahi wa Inna Ilahiri Rajiun Haka Allah ya tsara al'amarinsa sai dai mu yi addu'ar Allah yasa ayi aikin cikin sa'a Allah ya basu lafiya ita da bebin gaskiya ba zan iya zama a gida ba gani nan yanzu zan zo asibitin. Ya ce "Yauwa gara ki taho, sai ki shiga dakin Suwaiban ki hado kayan bebi da duk wani abu da kika san za'a nema bayan an fiddo bebin sai ki hado ki taho da su, ta danyi jim sannan ta ce, 'Kana ganin ba matsala idan na shiga dakin? Don gaskiya ina gudun abinda zai je ya zo, ya ce ba wata matsala tunda zuciyarki Fes za ki yi abinda na umurce ki tace, shike nan, a ina makullin dakin ya ke? Ya dan yi shiru yana tunanin inda ya saka makullin lokacin da Goggo ta je ta rufo dakinta mika masa makullin, sai ya laluba aljihunsa saboda tunawa da ya yi kamar anan ya jeia shi ilai kuwa sai ya ji makullin ya ja tsaki ya ce k n ga ma makullin nan a aljihu na yanzun ya za'a y shi ya sani ba na son ana wani rufe-rufen kofa ko ne za'a dauka ko ayi mata a daki ban sani ba, g shi mun taho ba kayan bebi yanzun idan sun fiddo shi sai dai uwarta 60 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ni ta ban circ lullubin ta ta bayar a rufe mata jikan ta don san yadda zan yi ba" Abin dariya abin takaici duba Muneeba ta cc, yanzu ka yi sauri kawai kazo sai mu kayan idan muka dauka sai mu tafi tare" Ya ce shike nan gani nan zuwa". Ya je shaidawa su Goggo zai je gida ya dauka kayan jariri Hajiya Harira tayi Karaf ta се, "Bari in zo mu je sai in duddubo tunda kai ba sanin abubuwan da za'a dauko ka yi ba" ya ce a a ku zauna bari kawai in je ai Muneeba na nan sai ta taya ni mu duba". Goggo ta yi saurin cewa, Muneeban ce za ka sa ta shiga ta yi mata bincike a daki, wannan ai ba daidai bane in dai ba kai za ka dubo ba to ba zai yiwu ita ta shiga ta duba ba ehe! Ta kare maganar a zafafe kuma cikin bashi umurni. a Ba da son ransu ba ya tafi ba tare da wata a cikinsu ta bishi ba ya shiga gidan ya iske Muneeba tsakar gida tana ta aikin mai kawo cikin damuwa take sosai. Ta yi saurin ta zo ta rungume shi tace har yanzun basu fito da ita ba? Ya ce basu fito da ita ba amma muna sa ran za'a yi nasara ki kwantar da hankalinki mu je mu dibo kayan". Ya sa makullin ya bude dakin Suwaiban falon tsaf tsaf suka wuce d'akin baccinta nan fa suka iske fakin kaca-kaca tamkar me 'ya'ya goma sai karni dakin ke yi a zuciyar Muneeba tace kila shi yasa Mujeeb sam baya zuwa dakinta kwana sai dai kullum ita ke binsa nasa dakin ita kuwa kusan koda 61 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria yaushe a dakinta yake kwana a cewarsa yafi sakewa a dakinta a dalilin rashin dabi'ar da Suwaiban ke gwada musu sai ta bari Muneeba na dakin ranar girkinta kawai sai su ganta tsulum tayi sallama ta shigo babu ruwanta da bin dokar Musulunci na cewa sai an baka izini sai ta kutsa kai tace tazo daukan abu kaza ne idan yayi mata magana sai ta ce ita da dakin mijinta ba me kafa mata dokar idan zata shiga sai ta nemi izini. Tun daga ranar Muneeba ta kudiri niyyar sai ta shayar da ita mamaki in dai takamarta rashin kunya da nuna isa da Gadara aka kuwa yi sa'a wata rana ta kutso musu har dakin baccinsa tayi kyakkyawan gani don ba zancę mummuna ba dama

Chapter 4 of 12