Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 12
dakinta, in Goggo na nan ne take fara shiga gurin Goggo tayi sallama kusan sau uku ba'a amsaba idan da sabo ta riga ta saba da wannan aria ita rin ar ar li a e 73 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria halayayyar ta Suwaiba idan tazo dakin tayi sallama sai taga dama take amsawa ko kuma tace sam bata ji ba. Munceba na jin wasannin yaron can a dakin baccin Suwaiban, hakan yasa ta kutsa kai cikin dakin tare da kara yin wata sallamar jin Muneeban ta shigo yasa ta amsa sallama can a kasan makoshi. Muneeba na shigowa tasa hannu ta suri yaron ta daga shi sama tana masa wakar Dan bOy na Mama da Baba, inai timbidi boy dina" ya wangale baki yana bangala mata dariya ya ganeta, ta dawo dashi ta rungume a kirjinta tanawa Suwaibar magana. "Ina ta sallama shiru na dauka ma bacci kike yi, shi yana wasansa, ta wayance da kare kanta 'Sama sama naji sallamarki baccin nake son inyi ya hanani, shi bai san komai ba sai wasa? Ta ce yi baccinki bari mu tafi muyi wasanmu ko da yake yau zama zai fora koya" Suwaiban ta ce "Na yi ma babansa magauar Keke kullum sai ya ce ya manta ni kuma wallahi bazan koya asa zaman ba indai bui sayi keken ba" Munceba tayi murmushi ta ce, "Yi hakuri kinsan Yayara da mantuwa ni na fanshe shi, dana dawo makaranta yanzu.na biya na siyo masa shikenan ko? Suwaiban tadan bude baki cike da mamakin Muneeba, kullum bata kyautata mata, bibiyarta take da mugun kudiri amma ita ko a jikinta burinta a yanzu bai wuce na ganin tayiwa Baffa abu ba, kudi 14 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ko nawa ne zata kasha masa san bata kyashi, ita kuwa kishin banza ya hana ta saurara mata da irin abubuwan da take kulla mata a gurin miji da uwar miji da ma duk wani mai goyon bayanta bata fadar aikhairan Muneeba sai dai tayi mata mugun kulli kai jama'a inama wannan mugun kishin zai barta tasawa zuciyarta Salama ta rungumi kaddara ta aje duk wani mugun kulli su zauna lafiya kamar yadda Muneeban ke so sai dai kash! Ba zata iya ba tana tsananin jin kishin irin son da Mujeeb ke nuna mata, shi yasa take biyewa ra'ayin su Hajiyarta da Goggo na bin duk wata hanya ko wace iri ce don ganin an kushe wannan son da yake nuna mata. Muneeba ta fice rungume da Baffa tana masa waka ta bar Suwaiban zaune tana saka da warwarar abin da bazai kaita gaci ba. A falonta ta iske jume ya gama kwaso kayan ya aje mata makullin motarta bisa Tebur ya fita. Ta aje Baffa akan kujera sannan ta dauko Keken ta fiddota a ledarta, ta je ta duko batir ta sa a gurin da ya ke wakoki sai ta kunna wakoki suka fara yi tare da dan joji ta dauko yaron ta saka shi a keken ta daidaita masa zamansa ya soma wasansa yana kallon danjojin yana wangale baki sai ta barshi ta shige bayi tayo wanka saboda zafin da ake zabgawa ta dauro alwala tazo tayi sallar La'asar ta dawo falo tana shafa mai tana kallon yaron. 75 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Sai ga Suwaiban ta shigo ganin Keken Baffan ta ganshi a zaune yana 'yan wakokinsu na yara na sauran tarkacen kayan was an da Munceba ta siyo masa Ta dan dubi Munceban kadan t ace "Ni fa tun dazu da kika barni a daki ina ta mamaki da kika ce kin sayo masa keken zama ashe da gaske no" Ta ce "Meye abin mamaki? Baffa fa jinina ne wałlahi ko nawa nake dashi zan iya kashe masa ki daina shakku nayi domin Allah sannan a matsayinsa na dana ta 6angare biyu. Mujeeb ne ya shigo falon tare da sallama ya bisu da kallo, sannan ya tsaida kallonsa ga Baffa dake cikin Keke yace "Iye! Yaron mamansa Keke aka yo masa Lonchin Dalleliya haka? Lallai yaron nan ana ji da kai don Allah waye wannan taimakon Mama Babba ko Mama Kurama? Ya tsaida idonsa ga Suwaiban. Ta nuna masa Muneeba ta ce, "Mamansa ta sayo masa tunda kai ka kasa siyo masa harkar kasuwanci da Ofis sunsa har kana mantawa da sha'anin danka daya tilo ranar da sukayi yawa kuma sai Allah”. Gorin da tayi masa yayi masa ciwo tunda har ta nuna neman kudl ya fi ye masa da guda daya da A'lah ya bashi bai nuna mata ba sai yiata "Ko ni na' manta dashi ina da 'yar uwar da bazata manta dashi ba zata dinga fansata wajenyi masa duk abin da ni na manta ba tare dana bata ko sisi ba" ta kada kai, Ai nakan yayi kyau shi dai ya 10 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria suri yaron yana cilla shi sama yana masa wasa. Ya dubi Munecba yana mata godiyar dawainiya ta harareshi sai ya kyakyale da dariya. **** **** **** Lokacin da Baffa karami keda watanni bakwai a duniya har ya fara rarrafe yana ma kama abu ya mike, a wannan lokacin Suwaibar har ta sami wani dan karamin ciki wata biyu dama hudubar su Goggo kenan wai kadata ta yarda da tsarin 'yan asibiti da suka ce kada ta samu wani cikin sai ta sami akalla shekaru uku da haihuwa adalilin aikin da aka yi mata shine su Goggo na jin haka suka се sam wannan ba mai yiwuwa bane, ko ta sami ciki babu abinda zai same ta, shi yasa ta saki jiki har ta sami cikin. Mujeeb da ya fahimci cikin gareta ranshi ya faci yayi mata fada kamar zai ari baki tunda tana da matsalar operation da kansa ya amso mata wani magani na addini ne da akesha duk bayan gama al'ada to da izinin Allah mace babu abinda zai shiga mahaifarta har wani watan yayi ashe bata sha saboda su Hajiyarta sun zugata da cewar tayi ta hainhuwa ta cika gidan da 'ya'ya tunda ita Allah ya ba. Mujceb kuma yace babu ruwanshi idan ta sami matsala gurin haihuwa, sannan gashi .cikin 77 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria yazo mata da tsana in laulayi fiye ma dana Baffa hakan ne vasa konai na Baffan ya koma hannun Muneeba shan nono da kwanciyar bacci ne ke hadasli da uw rsa, sai kuma idan zata makaranta to zata barshi gurin Suwaiban wannan dalilin ne yasa ma aka vamo musu wata 'yar yarinya da zata din ga taya Suwaibar renon Baffan. Kiriniyar Baffan da barnarsa ne yasa ake kaffa-kaffa dashi tunda komai hannunsa ya kai kansa to zai 6arar dashi ko ya barnatart dashi idan abin na amfani ne sau biyu Suwaiba na barin reza a dakin ta yana yanka hannunsa. Ranar juma'a bayan saukowa masallaci Baffan yana dakin Munecban yana ta sana'ar tasa ya baro da wannan ya rarrafa ya damko soket idan ta kwace sai ya koma can ko kuma ya saka kuka ta dauko shi tana cewa 'Kai Babana wai kai wane iri ne, idan an harka mai ciki sai ka fadawa- mai goyo. Mujeeb ne ya fito daga bayi yana musu dariya y ace "Tun rannan nace don Allahki warware min wannan Karin maganar ni har yau bangane me alia nufi ba kinki” ta dora Ban bisa gadonta ya tura masa tarkacen kayan was sai da yayi daidai d su akan gadon sannan ta ce, Ai na gaya maka nima bansani ba tunda ni ba Bahaushiya ba ce kaje ka tambayi Hausawa ni fillo ce ya ce Fillo mai karambanin aron yaran wasu kenan, ni dai don ن WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Allah ki koya min Karin magana Hausawa na rasa a ina kika koyo" t ace Ai makarantar Boarding kasan akwai hausawa da yawa suma muna koya masu fillanci kowa yana karuwa da dan uwansa". Da gudu Muneeba ta isa bakin gado ta tare Baffa daya ziro kafafuwansa wais hi zai sauko. Mujecb ya ce Kai! Wannan Baba na mu đa karambanin tsiya yake saukeshi a kasan tunda yafison ya sauka ko ki ba Karime shi don hutawa nake son in yi ba zai barni ba". Ta sauke shi kasa tana cewa yaro fa shi da dakin Mamansa ba za'a kore shi ba Karime aiki takeyi tunda hutawa kake sonyi sai ka koma dakinka kaga can ba mai hanaka sakewa in munzo ma ka koromu". Ya dora kansa bisa filo yana murmushi ya ce, wane ni da zan koro ku kudai da kuke kora na idan na zo yaci ace nayi zuciya na tafi inyi muku yaji saikun nemeni kun kawo kanku tunda nasan........? karar fashewar wani abu da Baffa yayi shi ya dakatar da Mujeeb daga maganar. da yakeyi suka nufi gurinsa dukansu wani madubi ne babba da ke aje akan dirowar gefen gado (Side Bed Drower) ya dafa durowar ya mike shine ya dauko shi ya kwala da kasa akan tayes ya fashe kwatsakwatsa. Munceba ta daukeshi don kada yaji ciwo ta mikawa Mujeeb shi ta yi sauri ta fita ta dauko tsintsiya då abin kwashe shara ta shigo dakin ne ta 79 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria iske Mujceb ya kama 'yan hannuwan yaron yasa nasa yatsun guda biyu yana bugasu a yatsun yaron tare da masa fada wai ya daina barna in ba haka ba sai ya zane hannuwanshi da bulala. Muneeba ta kallesu tayi dariya ta ce wai Baba na kake yi wa wannan fadan? Bai ki ma yanzu ka sake shi ya sake wata sabuwar barnar ba yadda kasan ana masa allurar doki haka yake jin karfi don ko barnar zaiyi da karfinsa yake yinta Hajiya dai tace idan zamu zo Dukku bata gayyarsa in kuwa munzo da shi to Goggo tayi masa masauki a gidanta. Ya rungume Baffan yana shafa sumar kan yaron wadda ta kwanta Luf Luf a fatar kansa yace ita batasan dama haka Goggo keso ba idan yaje ya sauka gidanta don ta fara amshe cefanen da ya je da shi garin. Kinsan zuwansa na karshe gidansu daya fasa mata randa sanda ya radawa randar cike da ruwa ya fashe wai ta taho da gudu ita ma ya daga sandar ya rada mata da karfinsa. Muneeba tayi ta dariya hallayyar Baffa ta kara da cewa, "Ai ba kakanni kadai Baffa ke Musgaba har mu nan iyayeısa nima nan yasha kwalamin wata ran idan naji zafi inyi kamar in buge shi sai inga ban iyawa dole in kyaleshi" Ya ce ai ke kike shagwaba shi saura keya fasa maki wannan (Show Glass) din ta kayan turare inga yadda zaki yi masa ranar" tace Ni burina idan ya 80 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria fasa kada su yanke shi ai ba abinda zanyi masa illa abin kai zai shafa ka bani kudi in siyo wata insa ba shikc nan ba. a Washe gari asabarce kowa yana gida Mujeeb yana dakinsa yana aikawa da sakonni Laptop dinsa dama in dai Suwaiba ce ke da Girki to yawanci zaka fi samun Mujecb a falonsa nan ta kan biyo shi idan tana jin tsiya kuma taki zuwa to balle yanzu da take fama da laulayin ciki kuma suna takun saka da mai gidan. Muneeba kuma tana dakinta suna ta gogegoge ita da mai rainon Baffa Karime, yawanci ranar hutun karshen mako ne take samun lokacin zama tayi hidimar dakunanta sosai Sarkin kiriniya Baffa na nan yana ta 6arnarsa don har sai da ya zubar musu da ruwan goge gogen bokiti guda Allah yasa sun cire Kafet din tsakiyar dakin akan tayals ya 6arar Karime Kaman zata bugeshi don haushi Muneeba na lura da ita ta katse mata hanzari da cewa yi hakuri karime mu sake Gogewa kinsan dan nawa dan gwalne ba'a dukanshi idan yayi 6arna kiyi hakuri Karime ta ce "Anti Allah da kin barni na dan bubbugi hannunsa za ki ga ya natsu ya daina, ji fa hannunsa kamar kaikayi yake masa idan baiyi barna ba. Rannan fa na aje ruwa a baho a bayin mamansa zan yi masa wanka na je in debo ruwan da zan sirka sai ganinsa na yi zai shiga cikin 81 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ruwan bahon kuma tafasasshe ne Allah ya soni bai shiga ba na ganshi. Munecba ta rintse ido ta ce ke! Karima ki dinga kula sosai da yaron nan kada yaja maki fitina wata rana kinsan uwarsa ba zata dauki hakan a matsayin kaddara ba kiyi taka tsam-tsam kada ki rasa aikin ki kinga kina taimakon iyayenki. Jikin yarinyar yayi sanyi ta ce zan kiyaye Insha Allahu Munecba ta ce, yi sauri mu gama gogewa ki tafi Islamiyya bana son kina yin latti kinsan na gaya miki idan kina aiki ki dinga yi kina duba agogo da kinga lokaci yayi ki aje aikin kona waye ki tafi Islamiyya idan kin dawo sai ki cigaba da aikin dan zama ba karatun addini ba zai yiwu ba ga dan Musulmi kinji ko? Ta gyada kai. Muneeba ce ta sakata a makarantar ta 'ya'yan masu hannu da shunin unguwarne akwai ta matan aure da akeyi duk ranar Asabar da Lahadi da safe akwai ta rana karfe biyu zuwa hudu ita Muneeban ke zuwa tayiwa Suwaiba magana ko za ta shiga tayi kemadagas tace bazata shiga ba wanda tayi a gidansu ya isheta sai Muneeban ta nuna mata ai ilimi ba a gama shi ana nemansa ne (Minal Mahadi Ilal Lahadi) daga tsumrnan goyo har zuwa kabari, sai in ka mutu ne neman ilimi ya kare a kanka da Muneeba ta lura abin yana neman zama tashim hankali sai ta kyaleta tunda tace kowa tasa ta fissheshi inji Suwaiban. 82 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria Tana falo tana karasa goge-gogen ita kuma Karime hart a wuce Isla miyya sai taji kakarin Baffa da ke wasa a dakin baccinta ta yi sauri da gudunta ta isa dakin baccin saita same shi yana aman jini ta saka salati tayi kan yaron da gudu ta sungumo shi, tasa hannunta a bakinsa don a tunaninta wani abu ya hadiya ta kwakula bata ji komai ba illama aman jinin da ya ci gaba da bulbulowa ta fita dashi da gudu ta nufi dakin Suwaiban don a tunaninta Mujeeb na can ko sallama batayi ba ta fada dakin tana kiran sunan Mujeeb. Suwaiban ta taso a aguje ta fito ganin danta nata aman jini yasa ta kwarma ihu ta fita da gudu tayi dakin Mujeeb ita ma Muneeba ta biyo bayanta suka isa fallonsa a tare shima yana ganin yaron ya mike jikinsa na kyarma ya amshi yaron a hannun Muneeban yana tambayarta meya sani yaron tayi magana cikin kuka wallahi bansan me ya same shi ba ina falo shi yana wasa a bedroom dina shine naji kakarinsa ina shiga na iske yana aman jini "Suwaiba ta sake kwarma ihu tana cewa shikenan za'a kashemin yaro dama son da kike nuna masa bana Allah da Annabi bane don ki cutar dashi ne shi yasa ki ka jashi a jiki ya saba dake baya yarda da kowa sai ke tunda Allah ke bai baki ba bari ki dinga yiwa abinda na Haifa kisan mummuke ta yadda babu wanda zai yarda zaki cutar da shi in aka ga 83 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria irin so da kulawar da kika masa wallahi idan ya mutu bazan yarda ba kotu ce zata rabamu dakc". Ihu Suwaiba keyi tana buga bango tana kara fadar muggan kalamai Muneeba ta matsa ta riko hannunta tace "Ki yarda dani Suwaiba wallahi ban taba tunanin in cutar dake ba balle in cutar daBaffa bawan Allah baisan komai ba sai in cutar dashi wallahi nib a hali na bane kila wani abun yasa a baki ya yankashi wallahi bansaniba kiyi hakuri, tana maganar tana kuka Wiywiy. Mujeeb dai yana rungume da yaron yana ta kokarin kwakuloo ko meke bakinsa, amma abin ya faskara sai ma aman jinin da yake cigaba da yi gaba daya kayan jikinsa da na jikin MUjeeb din sun rine da jini, itama Muneeba kayan jikinta duk jinine. Suwaiba ta suri wayar Mujeeb ta kira Goggo tana dauka ta ce, Goggo ku taho Gombe yanzu ga Baffa nan sai aman jini yakeyi zau mutu Muneeba c eta bashi wani abu a dakinta bamu san ko meye ba so take ta kashe shi tunda ita bata haihu ba. Goggo ta rafka Salati tace A' kuwa idan ya mutu ita ma sai na kasheta, gamu nan zuwa yanzu ni da Hajiyarki gata nan muna tare. Mujeeb ya tsare Munceba da idanu yana mata kallon tuhuma yace "Ni fa banji komai a bakin yaron nan ba wai me yaci ne? Muneeba tazo gabanshi tace, wallahi babu abinda na bashi, nima 84 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria shiga kawai nayi na iske yana aman jini? Wata mika da yaron yaja tare da yin kara sai ga jini ta hanci da baki hard a guda guda, shikenan sai jikin yaron ya saki yaraf ba zakace akwai sauran rai a tare dashi ba. Wani kakkarfan Salati Mujeeb din ya saka, Muneeba ta kai hannu zata amshi yaron bata Ankara ba sai ji tayi ya zabga mata wani bahagon mari wanda yayi sanadiyyar daukewar numfashimta tare da ganintana wucin gadi ta fadi can gefe. Bayan ta farfado daga jinyar radadın marin ne ta nemeshi da Suwaiban a dakin ta rasa da gudu itama ta fito ta iskesu har sun shiga cikin mota ta suri hijabi a igiya cikin wadanda Jume ke wanke mata a harabar gidan ko bushewa baiyi ba ta fada motar suka nufi asibiti. Suna isa aka amshi yaron aka shiga dashi Emergency, su kuma suka tsaya a waje cirko cirko har a wannan lokacin Muneeba kuka take yi fuskarta a kumbure idanunta sun tara jini saboda marin da Mujeeb yayi mata. Ita marin bashi ke sata kuka ba kukanta na tausayawa halin da Baffa ya shiga ne shin zai rayu ko ba zai rayu ba, saboda jinin da ya amayar ba kankani bane zai iya sa jinin jikinsa ya kare. Hajaran majaran jume ya rako su Goggo asibitin suna zuwa basu bi ba'asin komai ba sai 85 a C 1 1 1 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ruwan ba'la'in fada da suką hau yi wai za a kashc musu jika. Muneeba ta tsananta kukanta ta durkusa a gaban Goggo tana mata bayanin yadda abin ya faru ta kara da cewa wallahi Goggo ko ban hada alaka da Baffa ba bazan iya cutar da dashi ba, balle Baffa fa dana ne duniya da lahira ko wani naga zai cutar dahsi sai inda karfina ya kare balle kuma ni in cutar dashi ribar me zanci idan na cuceshi me zancewa ubangijina ranar gobe kiyama. Allah shine shaida na, ina rokon ya fitar dani daga zargin da ake mini. Ta dan rage kukan sai ajiyar zuciyar da ke zuwa mata lokaci zuwa lokaci idanunta na kallon kofar shiga imajensin don ganin fitowar wani ko zasu ji wane hali yaro ke ciki. "Duk surutun dasu Goggo ke yayyafawa Mujeeb bai ce komai bat un bayan da ya gaishe su ya na daga bakin kofar imajensin yakai mari ya kai gwauro ya kasa zaune ya kasa tsaye. Wani likita ya fito daga dakin da saurinsa zai shiga wani dakin Mujeeb ya tare shi da tambaya, "Don Allah Dakta yaron yana raye ko ya mutu? Likitan bai waiwaiyo ba kawai ya gyada masai kace yace Yana raye" Kawai abin da ya fada masa kenan ya wuce. Mujeeb ya sauke ajiyar zuciya ya yi hamdala ga Allah, sannan yazo inda su Goggo suke, ya shaida masu abinda likitan ya gaya masa suma 86 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria godiya ga Allah sukayi Munceba ma dake rakube a gefensu Godiyar tayi ga Allah tare da fatan fito da yaron lafiya kuma a gano abinda ya sababba masa aman jinin. Kusan mintuna talatin da komawar likitan sai ga yaron ya fito dashi a hannun shi babu sutura a jikinsa ya mikawa Mujeeb shi da yake shi ne a bakin kofa dakin sannan yace gashin nan ya sami yin bacci idan ya farka a bashi nono ko baya sha? Mujeeb yace yana sha Likitan yaci gaba da cewa "Idan yasha nono gurin da yaji ciwo zai dasashe sai a bashi wadannan magunguna kada ku damu da kukan da zai dinga yi saboda makogoronshi ya yanke da yawa kun ganshi guntun madubi ne ya dauka ya hadiye sai ku dinga kulawa ku daina aje abubuwa na jin ciwo a kusa. Ya mika masu wani tiren silba dake dauke da ballin madubin da aka cirowa yaron duk sai kunya ta kama Mujeeb ya kasa hada ido da Muneeba sai su Goggo yakeyiwa bayani wallahi jiya garin kiriniyarsa shi ya fasa madubin a dakin Muneeban kuma tas aka share gurin kunsan kwalba da tsalle ina ga wani tsalle tayi ba'a share ba ba shine yau ya ganta ya dauka yasa a baki abin dai ya zo da tsausayi Allah ma ya tsare". Ya mikawa Goggo yaron ta saka shi a cikin gyalenta ta lullubeshi suka mike don tafiya ya kai kallonsa fuskar Mneeba har yanzun hawaye ne ke 87 a 3 C 1 1 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria zirarowa a kuncinta hakika yasaņ kukan da takeyi yanzun na nuna rashin yarda da amtinci nè da ya nuna mata idanunsa sun rufe yabi ra'ayin matarsa na cewa Munecban zata kashe masu da alhali ya fi kowa sanin halin Muneeban ko giyar wake tasha ba zata iya aikata abinda suka zargeta da shi ba. Kai! Subhanallahi Wallahi shi yasan baiyi mata adalci ba a irin tattali da kulawa da kaffa-kaffa da takeyi da yaron nan sam bai kamata in wani ya zargeta shima ya bi sahun, masu zarginta bay a kamata ne ya kyautata zato a kanta, to amma ba komai yasan tana da laushin zučiya suna komawa gida zaije ya lallasheta ya nuna mata lallai yayi kuskure tayi hakuri ta gafarta masa.» Basu dade da dawowa gida ba Baffan ya farka Goggo ta mikawa Suwaiba shi tace ta bashi Nono yana fara shan nono sai ya sak ya soma kuka duk yadda yake son yasha nonon yakasa sha Mujeeb ua shigo rike da ledar magungunansa yake tambayarsu "Au ya farka ne" Goggo tace Eh ya farka amma ya kasa shan nono sai dai Kuka. Ya mika hannu ya amsheshi yace 'Bari kawai in bashi magungunan akwai na kashe zugin ciwo da na bacci kila idan ya sake yin bacci ya farka zai iya shan Maman ya bude magungunan ya soma baashi, yana sha yana kallon fuskar baban nasa yana dariya dama in dai za'a bashi magani daga babansa sai Muneeba su kađai ke iya bashi ta 88 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria a dadin rai in kuwa Suwaiba ce bata iyawa sai an rirrike shi ba a jima ba bacci yayi awon gaba da yaron yaje ya kwantar dashi a dakin baccin Suwaiban. Su Goggo suka ce tafiya zasu yi tunda abin da sauki, Allah yakiyaye gaba yace "Haba Goggo b zaku bari sai gobe ba, sannan gashi ko abinci fa baku ciba Hajiya Harira tace 'Ba zamu kwana ba tunda jikin Adamun ai da sauki amma dan Allah ku dinga kiyayewa a daina barin abin jin ciwo a kusa ta yadda ba zai dauka yayi wasa dashi har yaji masa ciwo ba kunsan yaro ba hankali gare shi ba bai san abin da zai yi masa lahani ba shi komai ya dauka to shi agurinshi abin wasa ya dauka. Mujeeb ya gyada kai wallahi Hajiya muna kiyayewa tunda mun sanshi da kiriniya Muneeba ma har tafimu kiyayewa kasancewar ko da yaushe yana can gurinta ba ma yason zama nan dakin. Goggo ta wani tabe baki tace kai nan har wani dadi kake ji da baya son zama gurin uwarsa, tunda can an wanke rubutun mantuwa an dirka masa ya shanye harda manta dangi gaba daya an wanke an bashi irin yadda tayi maka, don ma a tsaye na ke da kila inda nake sai an mantar dakai sai tayi rashin sa'a nafi karfinsu ita da uwarta yaro baisan kowa ba sai ita har kai ance ba ya yarda da uwarsa mai bashi nono na balle kai wannan ai abin dubawa ne, amma ba komai zanyi maganinta 89 a, a 1a la ta 1 a a a WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria wannan karon sai nayi nasara akan kinibibinta da surkullen ita da uwarta, sai na nuna musu nawa surkullen yafi nasu taja kwata ta hau jijjikai nuna alamun lallai wannan karon matakin da zata dauka ba zaiyi kyau ba. Mujeeb ya risinar da kansa kasa muryarsa a tausashe yace "Don Allah Goggo kiyi hakuri kada kice zaki dau mumman mataki akanta wallahi zan iya rantse miki Muneeba bata yi wani asiri, ni na san ladabi da biyayyar da take min shine matakin nasararta na mallakar zuciyata ba wai asiri ba`ne, shi kanshi Baffan wallahi kaunar 'yan uwantaka ne take masa balle kuma ga ubansa a matsayin mijinta kinga ai in dai mace mai sanin ya kamata ce ko ba 'yan uwartaka tsakaninta da mijinta dole ta so 'ya'yansa tunda tana ikirarin son ubansu, yanzu da nunawa tayi bata sonsa bazan taba ganin farinta ba kuma ba zaku ga farinta tunda bata son jikan ku don Allah ku cire zargin asiri a al'amarina da Munecba. Goggo ta daka masa tsawa Kai ! tafi can, sakarai talasuru mijin tace kawai in banda ta wanke ta baka kasha har ka dubi ido na da tsabar idon sirikarka uwar matarka ga matarka duk a gabanmu kace wai ladabi da biyayyar ne yasa ta mallaki zuciyarka wato kama san ta gama mallakar zuciyarka kenan, to sai ka gayamin ita Suwaibar me take maka da har ta kasa mallakar zuciyarka? Bata maka ladabi ne? bata yin tsabta ne? ko bata iya 90 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria girki banc? Ko kuma bata biya maka bukata ne, koko bata iya bane tunda ku mazan yanzun fitsararrun ne wai har da wata mace da ta iya gamsar daku itace 'yar gaban goshinku, sai ka gaya min meye Suwaibar bata iya ba har Muneeban ta fita iyawa ta mallake zuciyarka. Ga koshi ga kwanan yunwa sannan ai idan ana dara fidda uwa ake yi, in bayan ga Hajiyar Suwaibar da daga shi sai Goggo da Suwaibar ne to zai gayawa Goggo cewa duk abinda ta zano Suwaibar bata masa na farko dai bata masa wani ladabi ga tsa-gatsa take gaya masa magana, sannan babu biyayya idan yace tayi abu sai taga dama takeyi sabanin Muneeba wadda bama sai yace tayi ba in dai ta san abin da yake so to kafin ya umurceta zata aiwatar. Suwaiba batasan ta tsaya ta gyara girkinta yayi dadı ba, ko yayane zata kwaba abinta ko su ci ko kada suci babu ruwanta, sannan gurin tsaftar jiki data muhalli duk bata damu dayi ba ko danta bata damu da tsaftarsa ba, Allah ya taimakeshi Kulawarsa ba'a hannunta take bad a wata rana sai ya kwana bata yi masa wanka ba tunda ita dinma takan kwana batayi ba, balle idan tana

Chapter 5 of 12