Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
12 / 12
gwanin wani mugun wani ne, sannan ni a 192 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria gurina kwace goruba a hannun kuturuba wuya bane, ina nan ina jiran dawowarsa nima da bakinsa zai gaya miki matsayina, na irin dawainiyarsa da nakc dauka wanda a yanzu ke ba za ki iya ba duk ikirarin sonsa da kike yi nidin nan nice zan iya, Da Mujceb ya dawo Goggo ta kara zayyana masa abinda ya faru ya kira wayar Suwaiba ya ce tazo ta sameshi a dakin Goggo. Ta shigo tana yatsina tana taunar Cingon ta tsaya kerere a gabansa shi da Goggo ta ce "Gani fadi maganarka don sauri nake yi ina hidimar abincinka ne kasan hidimomin ka a kaina na da yawa dana gama wannan zan yi wannan. Ya gyada kai ya ce eh! Ai na sani sannu da kokari meya hadaki da Goggo ne? ta kalli goggo tana tabe baki Babu abin daya hadani da ita illa abinda ta kitsa maka haka yake haka akayi, nace na gaji da girki biyu hidimarka nazo yi gidan aure ba ta wani ba in kuma dole ne inyi hidimarka in yi ta goggo sai in ji "ya raunana mura ga Suwaiban ya ce a'a sam ba zai zama dole kiy i hidimar Goggo ba ta wuce dole, saboda haka kiyi hakuri babu mai tilastaki yi mata dole "Ya juya ya dubi Goggo ya ce yanzu yadda za'ayi Goggo kawai ki dinga yin girkinki tunda ta ce ba zata iya ba indai ana neman zama lafiya don ni banason abinda zai tada min hankali. Tsoro da mamaki ne ya kama Goggo duk da yake ba yau bane Mujecb ya saba bin duk wani abu WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria da Suwabar ke so, amma na yau ya fi ba Goggo alajabi Lakika kowa ya debota da zafi bakinsa kadai zai Kona. fa juya ta dubi Mujeeb ta ce Mujecbu yanzu irin b tkraeun da zaka iya yiwa matarka kenan, kai keda il o akanta amma ba zaka iya sata tayi abinda zai faranta ran uwarka ba. To wallahi ka sani aljanarka na dugadugina sai na daga maka zaka samu ka wuce. In ka manta bari in tuna maka ni cc na haife ka bayan shan wahalar daukar ciki na wata tara nayi nakuda na haifeka na shayar dakai nayi rainonka har ka girma ka zama abinda ka zama, in har kana ganin akwai wanda zai wulakantani a doron kasar nan ka iya kyaleshi to kayi babban kuskure kuma wallahi idan nayi maka baki sai ya kamaka alhakin nono na da kasha don kuwa baka isa ka iya biyana ladan wahalar dana sha a kanka ba, kama daga haihuwa shayarwa zuwa rainonka saboda hak wallahi ka kiyaye don wannan shu'umar yarinya zata kaika ga halaka, ta Kare rnaganar tana nuna masa Suwaiba da yatsanta sabab. Mujeeb ya numfasa sannan ya ce Ni kam Goggo banga illar Suwaiba ba in ma har tana da ata illa ai da baki hada aurenmu ba tunda kullum alkhairinta ki ke fadi ita da mahaifiyarta, shi ya sa n kuma bana son Gata mata rai a dalilin bin umuninki kin ga kuwa ban yi laifi ba idan naso 104 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ९ Suwaiba fiye da kowa a duniya kuma ke cc ki ka nuna min muhimmancinta a rayuwata a matsayinta na uwar 'ya'yana saboda haka kii hakuri da ita tunda kc cc sanadin aurenmu.. Goggo ta muskuta ta ce, oho! Wato don nice sanadin aurenku ai ka kyalcta tayi mini cin kashi ba zaka iya daukar mataki a kanta ba? Ita din in 'yar halas ce ai ban cancanci wofintarwa a gurinta ba in har zata iya tuna tsayuwar dakan da na ke yi a kan zaman aurenku ya dawwama gata nan ai ta sani. Suwaiba ta tabebaki tana yatsina "Ni fa Goggo in wani taimako kike min a kan aurenmu ya kamata daga yau ki daina tunda ke bakya amfana da komai ni kadaice ke amfana, amma fa ko ba komai ni da danki duwaiwaine ya riga ya dame da kashi, babu yadda za'a yi sai hakuri. Mujeeb ya dubi suwaiba ya ce "Ya isa haka wuce kiyi aikinki magana ta kare kiyi girkinki itama za ta yi nata shi kenan Suwaiba ta juya ta yi ficewarta ta barsu tana fita Goggo ta rushe da kuka tana cewa, kaico na ni Rahina! Na dauko ruwan dafa kaina, na riga na yi babban sakaci a rayuwata wanda kafin in gyara wannan al'amarin zan sha wahala. Yanzu Mujeebu a gaban idona ka iya fifita matarka ka nuna ta fini matsayi ka lallasheta a gaba na amma ni tsakanina da kai ba Kalrnar lallashi balle ka bi umurnin ka yi abinda nake so sanin kanka ne hawan jinin nan ba zai barni in iya yin 195 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria girki ba sai ka nemo min mai aiki ta dinga mini girka da 'yan ayyuka tunda matarka ba zata iya ba. Mujeeb ya ce, shi kenan zansa a nemo maki zama kan yayi tsamari tsakanin sirikan guda biyu don kuwa kiri kiri Suwaiba ta hana a nemowa Goggo mai yi mata girki dole da kanta take miyarta in an yi abinci a kawo mata goyonsa taci da miyarta. Muneeba kam tana nan gombe hankalinta a kwance har ta fara bautar Kasarta a nan Gomben ta cire damuwar matsalar aurenta da Mujeeb a ranta tana nan tana addu'aba dare ba rana kan Allah ya daidaita al'amuransu, in kuma rabuwarsu ce alheri to Allah ya kawo sanadin rabuwar aurensu cikin saukI ba tare da tashin hankali ba don yadda su Baffa Adamu suka so sun so ne su je har Gombe su tsitsiya shi a gaban uwarsa ya bata takardárta da suka nemi shawararta sai ta ce su kyaleshi tana nan tana addu'a Allah zai kawo Karshen al'amarin saboda duk istiharar da ta ke yi a kan aurensu sai ta ji sam zuciyarta bata son rabuwar aurensu zuciyarta ta fi karkata akan son zama da mijin nata, kuma kullum kwanan duniya dada kara sonsa ta ke yi har bata son ta ji an fadi laifinsa ko ace ya yi ba daidai ba akan lamarin aurensu hakan ne ya ke bata tabbacin lallai akwai wani 6oyayyan alhairi da żai biyo bayan aurensu to amma. fa sai an yi namijin hakuri kafin a kai ga nasara kuma zata yi hakuri 196 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria tana addu'ar har sai an kai ga nasarar da take hararowa a wannan lokacin ne suka sha bikin khairi da Khausar, an kai ko wacce gidan mijinta duka anan Gomben sai fatan zama lafiya. **** ***** ***** Ranar litini Mujecb tun sassafe ya bar gida zuwa Ofis a dalilin neman gaggawa da aka yi masa a Ofis din wajen misalin sha biyun rana Suwaiba tayi bakuwa wata kawarta ce da suka hadu a asibiti gurin'awon cikin Baffa tun daga wancan lokacin ne suke zumunci da ita suna kuma ziyarar juna. Sun baje a falon Suwaiban suna ta hira da ciye-ciye har lokacin Sallah ya yi bakuwar ta nufi dakin baccin Suwaiban tayi sallah tana zaune a gaban madubi Suwaiban ne bayan ta idar da sallah suwaiban ta shigo dakin dauke da walida diyarta zata canza mata kaya. Tana zaune bisa gado suna hira da bakuwarta inda bakuwar ke tambayarta, wai ni maman Walida meye sirrinki ne yadda mijinki ke nan nan da ke, ga gida kin zama ke kadai ba kishiya kin kadata uwar miji ma naga lallaßaki take tamkar kwai, sai yadda kike so ake yi wallahi zanso haka a gidana nima, ko don ni mijina hutsu ne ba'a sanin gabansa balle bayansa. Suiwaba tayi dariya cike da nishadi tace, "Ai wannan siriin nawa na rike miji ba kowa zai iya 197 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria ba, kuma sirrine a gare ni, in har kinsan zaki iya in gaya maki in yaso sai in kaiki gurun da aka yi mani, wallahi zaki mallake mijinki tamkar dan da kika Haifa a cikinki zaki juyashi tamkar waina a tanda ke wallahi idan kika ce ya zauna anan kada ya tashi sai kinzo to ko motsi ba zai yi ba ina mai tabbatar maki ko fitsari yake ji bazai iya tashi ya je yayi ba sai dai yayi shi a wando saboda bin umurnin ki haka nake da baban walida ko uwarsa sai na bashi izini yake mata abu, in kuwa ina fushi dashi to tamkar mahaukaci yake komawa sáboda lallashi kuma kinsan wani abu wallahi da mamansa muka je akayi komai amma tana waje bata sani ba na amshi lakanina na zo na aiwatar ita a tunaninta idan na mallake shi zan raga mata, sai kace wata uwata in kina so in kaiki boka ne ai kinsa tamkar yankan wuka ki mallake miji ki kore kishiya kuma har abada bazai iya sake auren wata mace ba ke ko macen banza a titi ya nema ba zai ji dadinta ba kinga ko ai dole ya kyaleta tunda don lada ake yin sallah yanzu me kika gani zaki iya. Larai (Bakuwa) ta ce "Me zai hanani iyawa ni da nake neman yadda zanyi na rasa tun tuni ma ai da anyi an gama gaya min sirrin "Suwaiba ta gyara zama ta ce "To saurara kiji aiki ne na neman duniya kuma zaki samu amma akwai kauce hanya sai an danyi sa6o in yaso sai ki tuba daga baya (Kunji fa jama'a aikin sabo har da da, sannan idan 198 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria anyi a tuba tamkar amsar tuban a hannunsu takc, kilama kafin sutüban su mutu. Allah ka tsaremu amen). Ta soma zayyano mata irin fasadin da ake yi idan akaje gurin boka tun daga abin da za'a yi a bukka ta farko cite sutura kama daga dan kwali har wando sai a shiga gurin boka tsirara shima a same shi tsirararar har zuwa masha'ar da zai aikata da mutum umurnin hada najasar janabarsa data miji kafin a wanke gurin sai an kwana ake yin wanka da naman da za'a saka a farji ya kwana ayiwa miji miya yaci to idan fa yaci shikenan anyi an gama. Larai ta jinjina kai ta ce yanzu duk kinyi wannan aikin? Ta ce, kwarai kuwa duk nayi shine kuma jigon nasarar da kika ga na samu a gidan nan. Wani irin kakarin amai suka jiyo daga falo tare da amon salati mai karaji wanda ya cika falon Suwaiba da gudu suka fito falon don ganin waye a falon Mujeeb suka gani dafe da bango yana tafiya cike da tangadi zai fadi a dalilin tsaf ya ji kalaman Suiwaba tun shigarsu dakin ya shigo daidai lokacin da Suwaiba ke cewa sirrinta na rike miji ba kowa zai iya ba shi kuma ya labe don ya ji sirrin shine fa ya jiyo sirrin .daya gigita shi ya zautashi inda ya ji wai har ya taba cin naman da ya kwana a gaban mace bai sani ba. Kafin su iso gare shi ya zube Fasa warwas bayan ya yi wata kara mai firgitarwa Suwaiba ma 199 WATA KUSAN 2 Rahmatu Hassan Zaria yanka ihu tayi tana fadin 'Shi kenan ya ji sirrina da boka ya ce kada in bari ya ji in har ya ji to kada in yi kuka da kowa akan abinda zai biyo baya shi kc nan na shiga uku don bansan me zai biyo baya ba. KASH TO NIMA SAI KUYI HAKURI KU BIYONI DON JIN ABUBUWA DA DAMA DA ZASU BIYO BAYAN WANNAN BADAKALA. RAHAMAN ZARIA CE 08068895555, 08028434948. PRINTED:- BY ZAZZAU VENTURES PRINTING PRESS 08035336868, 08028401199 200 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 12 of 12